Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

rayuwarsa yau karon farko ya jishi......wata mummunar faduwa gaba,sannan take yaji hannuwansa da qafafunsa sun fara rawa sakamakon tunanin daya bijiro masa. Sake xubawa wajen ido yayi,yayin da zuciya ta fara masa imagination na hannuwan mashkur a wajen,wani abu me qarfi ya daki zuciyarsa har sai da ya fusgo numfashinsa da kyau,dai dai sanda yaji itama ta ja numfashin da matsanancin qarfi har sai da qirjinta ya daga.



*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862

5 5 5
5 5 5 5 5
_Zafafabiyar_

6B6O6O6K 62

g,D D

5K5<5B5@ 59


59


Da wani irin yanayi numfashin nata ya soma fita,abinda ya sanyashi karon farko tunaninsa yazo masa cewa asthmatic ce. Miqewa yayi yana ranqwafawa saman kanta da nufin dagota ya canza mata makwanci duk da abinda yakeji,yana dagata din towel din jikinta yana zamewa ya kuma fadi saman qafafunsa.

"La haula wala quwwata illa billah" Ya furta a sarari da wani irin bugawa da zuciyarsa tayi yana jin sautin har cikin kunnuwansa. Wani jiri da dan qaramin duhu yaji yana mamayarsa har sai daya lumshe idanunsa yana jan numfashi da kyau,ya tattaro dukka ragowar qarfinsa ya hada waje daya sannan ya soma takawa da ita ya ajiyeta saman gadon.

Zamewa hijabinta ya qarayi,santala santalan fararen cinyoyinta suka fito,ya dauke idonsa da sauri yana jin yadda bugun zuciyarsa ya dake qaruwa,sai ya sanya hannu yana jan hijab din yana jin zuciyarsa na qara quntata waje daya kaman an daureta a tsakanin qirjinsa

"Why?" Ya fada da mabayyanin sauti yana jin idanunsa na masa wani yaji yaji. Ta yaya wani zai samu hanyan shigo masa gida?,garin yaya hakan zata faru?. Kai ya girgiza,hankalinsa bazai dauki wannan ba.......kanshi da tunaninsa ba zasu iya karba ba. Taimakon gaggawa ya soma bata kaman yadda sukewa anni idan irin haka ta taso. Sam ya kasa hada bakinsa da nata saboda warin wiwin da yake tashi daga ciki,wanda yana daya daga cikin abubuwan mayen da ya yiwa muguwar tsana.

Laluba aljihunsa yayi,sai a sannan ya tuna da wayarsa,ya cirota a nutse yana budewa gami da nemo number saddiq. Saddiq dinne kadai yasan bai fiya bacci da wuri ba,shima kaman shi yake,yanayin aikinsu ya sanya sukan iya raba dare a gida suna rage ayyuka. Bugu daya tak kuwa ya daga,muryarsa can qasa yace

"Barka da dare hamma..." Bai amsa gaisuwar tasa ba yace masa.

"Ka nemomin Dr rubayya......please ku kawota gida yanzu if possible"

"Subhanallah...waye baida lafiya hamma?". Rasa amsar ma da zai bawa saddiq din yayi,sai kawai yace masa

"Ba wani abu bane can.....just kayi sauri ku qaraso".

Sauke wayar saddiq yayi yana duban farouq dake zaune a gefansa,wanda tunda ya daga wayar yaji da waye suke waya ya maida hankalinsa wajen duk da idanunsa suna kan system dinsa yau din yana sashen su saddiq dinne,don shima aiki gareshi sosai,sun samu sabon iri da sukeson su fara gwadawa manoma da manyan manoma da 'yan kasuwa,yanaso yayi settling na komai kafin ya kwanta,charger dinsa na system dinsa tayi masa tutsu,dole ya shigo ya karbi ta saddiq din ya jona gudun kada tayi shutting down.

"Lafiya yace maka ba?" Farouq ya fada kansa tsaye yana duban saddiq. Daga masa kai saddiq din yayi,sai farouq din ya soma tattare ayyukan nasa waje daya ya killace yana cewa

"Ka kirata kace zamu biyo mu dauketa......fu'ad bazai taba gaya maka worsening na komai ba indai shine". Ya furta yana saving ayyukan da sauri cikin aikin nasa,wannan ya sanya saddiq shima ya soma qoqarin kiran nata.

Sai daya ajiye wayar saman bedsheets dinnan sannan ya lura da hannunsa da har yanzu yake tsatsafar jini. Radadin dake cikin zuciyarsa ya danne wanda yake ji a hannunsa,shi yasa sam bayajin komai a hannun nasa. Idanunsa ya sake mayarwa kanta,sai kawai ya samu kansa da miqewa yana daukan wayarsa,ya daidaita iskar dakin saboda gumi daya gani saman goshinta ya qara hasken qwan dakin sannan ya fara takawa cikin takatsatsan gudun kada ya taka wani abu ya soma fita a dakin yana komawa parlor.

Tun bai qarasa ba ya hangesu sun cika hannunsu da wani baqin kakkauran matashi wanda ke sanye da baqaqen kaya full dress,tun daga hula riga zuwa wandon jikinsa. Iya riqon da sukayi masa kadai zai gaya maka yadda ya matsu a hannunsu.

Ci gaba yayi da takowa yana karantarsa,duk wani alamu dake nuna tashin hankali da rudani sun tabbata a fuska da jikinsa.

"Sakeshi" Fu'ad ya fadi yana jin hatta da security din gidan suma a yau bazasu tsira a hannunsa ba. Gaban mashkur ya qarasa ya zauna saman kujerar falon

"Ku zaunarmin dashi a nan" Ya fada yana musu nuni da gefan mashkur din. Wani mugun duka sukayi masa wanda ya sanyashi zubewa ba shiri yana fasa qara.

"Ku jirani a waje" Fu'ad din ya fadi yana qoqarin hana jinin dake diga a hannunsa bata sofa din da yake kai.

Kallon fu'ad kawai matashin yakeyi,yana jin yadda kashi da fitsari gaba daya suke neman kufce masa,saidai kuma yasan babban kuskure na gaba da zaiyi shine ya saki fitsari ko kashi a wannan kyakkyawan falon. Zai iya cewa a tarihin rayuwarsa kaf.....a tarihin manya manyan laifukan daya aikata a rayuwarsa bai taba cin karo da mutumin da yayi masa kwarjini irin muhammad jadda ba. Yana zube a gabansa yana jira yaji koda wata kalma daya daga bakinsa amma ko qwayar idanunsa bai daga ya kalleshi ba bare ya sanya ran wata tambaya zata biyo baya,ta goge jinin hannunsa kawai yake da lallausar tissue din daya ciro a tissue box din dake gefansa.

Bawai yayi hakan bane saboda ciwon yana da muhimmanci a rayuwarsa ba.....a'ah......yayi shuru ne saboda a yanzu babban muradinsa shine yayi mummunan lahani a garesu da babu me iya gane fuskokinsu,duk kuwa da cewa ko a yanzun fuskar mashkur ta haye tayi kumburin da dukka wata halittar fuskar ta sauya daga asalin yadda take,abinda yake sake sanya tsoro me yawa kenan ga zuciyar hanzari.

"Don Allah me gida.... Kayimin rai,ka tausayamin me gida......don girman Allah". Kalaman hanzari kenan wanda ya gaza jiran yaji abinda fu'ad din zai fada. Cillar da tissue din yayi,sannan ya daga idanunsa da har yau launinsu bai koma daidai ba ya aza akan hanzari

"Waye ya gayyato ka?,duka ku biyun kuma waye ya aiko ku?' Tambayoyi guda biyun da a wajen hanzari suke masa kamanceceniya da tambayar kabari ga kafiri a ranar daren farko

"Shine!.....shine wallahi" Hanzari ya fada yana nuna mashkur dake yashe a qasa har yanzu bakinsa na fidda jini.

A yadda mashkur din yake yayita qoqarin murgina kai ya kalli koda idanun hanzari ne amma ya kasa ballantana ya fadi wata kalma da zata zama kariyar kai a gareshi. Kiran sunan mashkur da hanzari yayi shine abu mafi sauqi.....mafita mafi sauqi a gareshi akan ya ayyana ko ya ambaci daga inda ainihin kwangilar aikin ta fito,wanda fadin daidai yake da fadawar mutanen da suka jibanceshi da yawa cikin masifa da bala'in da baisan ranar fitarsu ba......gwara ya danganta kanshi da mashkur.....kusan yasan waye.....kuma koda yafi haka hatsari yazan bazai zartashi a hatsari da hatsabibanci ba.......koda ya zartashi yasan bazaikai mutanen da suka qirqirar da aikin ba.

"Kana da masaniyar cewa maqabarta ka kawo kanka?......nan da kake zaune Motuare ce?!" Ya furta da sautin da hatta da mashkur sai da yaji kaman an buga masa guduma still saman ka bayan masifar azabar da yake ciki.

Firfito da idanu hanzari yayi.......yayi gwagwarmayar rayuwa da yawa......ayyukan rashin imani bila'adadin......ya shiga komar Jami'an tsaro masu yawan gaske......da wannan kadai yana iya gane mutum da muhallin da ake magana ta gaske kai. Salati ya debo wanda ya manta rabon da ya ambaceshi a bakinsa,sallah kanta ba'a maganarta sam bars aje ga gurbin xama ayi wani xakiri ko tasbihi.

"Zip your mouth!" Fu'ad ya furta da fushi

"Ko burbushinku ba zaa samu ba.......daga yau ba zaku sake gigin tsallaka gonar wani ba"

"Innalillahi wa inna alaihi....." Ya jiyo muryar daga can gefe tana fada cikin maqyarqyata saboda tsananin tsoron data shiga. Duk tsawarsa guda daya sai taji kamar ana finco mata hantarta tare da qoqarin bintiko zuciyarta daga muhallin da take a dashe.

Waiwayawa yayi yana mamakin wanda ya rage a falon bayan ya bada umarnin kowa ya fice. Zuwaira ce tsaye yana rawar dari kamar wadda ruwan da yayi saura har yanzu yake sauka kadan kadan a kanta ya qare.

Sulalewa tayi a wajen tana jin wata razana tana saukar mata,idanunsa sun mata wani kaifi da bata da juriyar daukarsu. Yadda yake magana ga duk wanda yake falon zai tabbatar abinda yake fadin zai aikata ne. Ba wasa ko digo cikin kalamansa. Itakam a yanzun ina ta shirya mutuwa?,a irin wannan qadamin da take lissafin sake inganta rayuwarta da jin dadin da yake hange daga wasu?,itama ta samu ta dandala ta baza nata ikon da isar kafin zuwan randa zata bar numfashi?,shine tun a yanzu a gabanta wannan manya manyan alkaba'in yake faruwa?.

Idanu ya zuba mata da kyau yana qoqarin karantarta,saidai kuma kafin yayi nisa an murza pivot door din daga can wajen falon an shigo.

Farouq ne a gaba,Dr rubayya a tsakiya sai saddiq daga bayanta .

Shigowarsun kawai cikin falon....hada idanunsa da farouq sai yaji kaman an janye wani kaso na bala'i da masifar da yakeji tana kunnuwa cikin zuciyarsa. Wani irin tashin hankalin da baisan dame zai fasaltashi ba.

Dr rubayya na qoqarin gaidashi.....saidai shi hanyar hallway din kawai yake nuna mata da yatsa ba tare da yace komai ba,sai itama bata sake magana ba kasancewar halinsa ba baqonta bane,ta wuce da kayan aikinta kai tsaye zuwa hanyar.

"Ka leqa ka kiramin saddam......suzo.su biyu" Yace da saddiq da rinannun idanunsa da suka sanya saddiq shan jinin jikinsa bayan mutane biyun da ya gani zube a wajen. Shima baice komai ba ya juya yana fita daga falon.

A nutse farouq ya isa gabanshi,ba tare da yace komai ba duk da idanunsa na nuna kaduwa da abinda yake gani ya kama hannunsa yadan juya sannan ya saki

"Dude.......wai meke faruwa?" Ya qarasa maganar yana saka idanunsa cikin na fu'ad din.

Janye nasa idon faud din yayi daga na Farooq yana hadiye wani abu me tauri daga qasan zuciyarsa. To shi ta yaya ma zai fara bada wannan mummunan labarin?,yace meye?,yace masa wiwi ya kamasu suna sha har ya bugu asthma dinta ya tashi?,ko yace masa ta gayyato maza cikin gidan sun bugu sukaso gwada mata qarfi?,ko kuma yace sharri akayi mata?,barayi zai kirasu ko 'yan fashi?,zaice sun hauro masa gida ne?,gida ma irin nasa?,gidan da ba wani abu daya isa ya shiga ko ya fita cikinsa saida cikakken tsaro da kulawar security......waye hankalinsa zai dauka?,waye zai yadda da wannan labarin?.

"Ka kwashesu ka sakaminsu a cage din dogs dincan....." Ya fada yana miqewa sanda hanzari ke qoqarin riqo rigarsa a gigice

"Kayi mana rai oga.....ka hukuntamu duk yadda kaso,amma kada ka hadamu da karnukan can.....wallahi ko kafin safiya sun gama cinye namanmu oga...." Yayi magana fitsarin da yaketa son riqeshi yana kubce masa. Tun shigowarsu gidan yanayin karnukan ya tabbatar masa sunsha banban da dukka karnuka daya sani. Basu bi ta gefensu ba.....amma wani abun mamaki yadda suketa haushi ya ninku,yana ganin sanda me kula dasu ya dubasu,ya kuma yiwa security na gidan magana suna sake bincike sassannin gidan amma basu ga komai ba saboda sun shigo ne ta hanya mafi sirri da samun tabbaci,kuma sun samu mafakar da binciken me bincike bazai taba kaiwa nan ba.

"What are you waiting for?!!!" Fu'ad da dama dukkaninsu suma a cike yake dasu ya fada a tsawace,ba shiri suka durfafesu,hanzari yayi wuf ya kama qafarsa yana sake roqonsa.

Wani wawan duka yakai masa da qafar daya sanya hanzari zubewa warwas,basu saurara masa ba suka sungumeshi suka hada da mashkur da tsabar razana ya kasa magana,sai yakejin kamar qiyama ce zata tashi. Yasan illar karnukan,don sanda yake sharafinsa ya ajesu a gidansa sun kusa guda biyar,hakanan baisan adadin mutanen da ya sanya suka yagalgala ba.

"Karku sakasu a cikin cage din.....ku ajiyesu dakin kusa dashi" Ya basu umarni sanda suke kicin kicin fita dashi.

"Okay sir" Suka amsa masa sanin wayeye farouq wajen boss din nasu. Shi daya ne duk duniya yake tada hukuncin da fu'ad yayi kuma ta zauna ba tare da haufi ko kankare ba,shi yasa suka karba umarnin nasa kaman yadda ya basu.

Yadda yaga komai yasan ba lafiya ba.......yadda kuma yaga yanayin hannunsa da gidan ya tabbatar akwai gagarumin wani abu daya faru.....uwa uba wani kwantaccen fushi d yake gani a fuskar Fu'ad ya sanar masa akwai matsala ko a yadda ya fita a fusace.




*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862

5 5 5
5 5 5 5 5
_Zafafabiyar_

6B6O6O6K 62

g,D D

5K5<5B5@ 60



60


Tun bai qarasa inda yake hangen security na gidan daya tara ba yakejin muryarsa dauke da fushi me nauyi. Fada yake da duka zuciyarsa da jikinsa ma,sam kaman ya manta dare ne a yanzun......daren ma kuma irin daren da akayi ruwan sama ya dauke wanda ke ninka kowanne dare a shuru da daukewar sawu.

"Your services are no longer required......you were fired!"

"Ya salam" Farouq ya fadi,abinda yaketa sauri ya dakatar dashi kenan. Fushinsa na yau yanata bashi mamaki,sau tari shike daukan abu da sauqi......yawancin lokuta shike jan qafa da jan lokaci akan abubuwa irin wadannan......yana bin komai da lura a kuma tsare,har sai ya tabbatar dashi a inda ya dace.

Kasa cewa komai yayi,don su kansu ma'aikatan da security din dake on duty a daren kowa cikin matuqar tashin hankali yake. Yadda suke roqonsa da mabanbantan harsunansu dukka sai suka bawa farouq din tausayi. Kowanne a cikinsu idan ka dubi fuskarsa ya kadu da hukuncin ba zata na me gidan nasu.

"Calm down.....ya isa" Farouq ya isa gabansu yana fadi bayan komawar fu'ad din ciki. Hankulansu kuwa suka bashi cikin mutuwar jiki hankali a tashe.

"Ku kwantar da hankalinku.....kowa ya koma bakin aikinsa kafin wayewar gari......but,ku sake tsaurara kula kafin muga abinda hali zaiyi.

Duk da bawai tabbaci ya basu na cewa ya dawo dasu bakin aiki ba amma hakan ya faranta musu. Sun sani babu wani guri da zasu samu walwalar rayuwa da 'yanci da albashi me tsananin azabar tsoka kaman gidan jadda.....salary yake musu na kece raini......irin salary din da sunyi imani ko a villa suke aiki babu me biyansu irinsa. Uwa uba ga ihsani da alkhairi da suke samu kowanne lokaci,wanda ya kusan kamo abinda ake biyansu albashin aikinsu. Da yawansu suna jin idan ba gidan Muhammad jadda ba babu a inda zasu iya aiki,shi yasa suke riqe da aikinsu fiye da yadda ma yake tsammanin zasuyi.

A parlor ya sameshi a tsaye kaman wanda zama ya gagareshi. Baice masa komai ba ya taka inda yake tsayen ya riqe hannunsa sannan ya wuce dashi,suka ratsa hallway din suka saura samansa.

Saman monotti sofa ya zaunar dashi,ya taka da kansa zuwa shiyyar da aka tanada don ajjiye first aid box,don kusan yasan komai na gidan tunda shine ma tsara yadda zai kasance din.

A gabansa ya zauna,ya bude box din ya ciro cotton wool da spirit ya tsiyaya ya fara goge masa ciwon. Sai a yanzu yake danjin radadin da hannun ke masa amma kadan kadan,saidai har yanzu abinda yakeji a zuciyarsa ya dara wanda ke a hannunsa.

"Ko meye da sauqi ake daukarsa......da irin wannan temper din da kake ji a ranka komai fa bazai warware ba" Farouq ya fada yana qarasa goge masan,har yanzu kuma yana mamakin abinda ya birkita nutsatsen mutum irin fu'ad din. Duk da ya sani,ba abu bane me sauqi a keta alfarmar gidanka a shigo maka ba......to amma kuma yadda yasan fu'ad zai iya cewa tun wani zamani can daya shude rabon da yaga wannan attitude din a tattare dashi.

Wayar tafi da gidanka din dake falon,wadda ke ajiye kusa da console mirror din parlor din ce ta dauki tsuwwa. Saddiq dake zaune daga gefe dukka jikinsa a mace ne ya dauka

"Daga hallway bedroom ne"

"Ka daga ko Dr rubayya ce" Farouq ya fadi sanda yake tattare ragowa ragowan audugan da yayi amfani dashi. Maganan second goma sukayi kwata kwata,ya sauke wayar yana duban farouq

"Dr ce ke magana.....tace ta kammala......amma wai tanason ganin hamma".

"Ka gaya mata tayi abinda ya dace kawai basai nazo ba" Ya fada yana jin ciwon kan daya tashi da jin dadin ya sauka yana son dawowa. Kai farouq ya girgiza yana dubansa,muryarsa a qasa qasa yadda saddiq bazaijishi ba yace

"Dole kaje tunda tace kaje din.....dole saika gwadawa duniya halinka?" Idanunsa da har yanzu basu koma fararensu ba ya watsawa farouq,kaman zai magana sai kuma ya fasa ya tsuke bakinsa. Kamar bazai tashi ba kafin ya miqe yana kiran sunan Allah,wanda motsawar bakinsa ne kadai zaisa gane hakan.

A hankali yake sauka zuwa qasan,saidai duk sanda ya kusanci dakin sai abun daya faru mintunan baya yayita dawo masa. Bama irin idan ya tuna ba komai a jikinta......daga ita sai towel sai hijab,sai yaji tamkar iskar da yake shaqa tayi masa kadan. Su biyu a daki tana daga ita sai shi.....su biyu a dakin da babu cikakkiyar sutura a jikinta......gaban hijabinta yasha cukuikuiya?.....duk sanda ya kawo nan sai ya lumshe idonsa saboda ji yake kaman an dauka adda an kafta masa sara a tsakiyar kansa.

Handle din ya murza ya tura ya shiga da sallama saman labbansa. Ma'u dake gyara dakin ta dago daga kwashe sharar data gama,ta rusuna tana gaidashi duk da dare ne,sannan ta kwashe dustpan da vacuum cleaner din tayi waje dasu.

Haka kawai ya samu kansa da bayason kallon fuskarta,don ba abinda yake tuna masa sai a yanayin data fado jikinsa.

"Numfashinta ya koma normal,kuma yanzun haka bacci take me kyau.....ko da wanne lokaci ma zata farka abinta........amma please sir......koda asthma dinta baiyi tsanani ba at least ya kamata ace an ajjiye mata in healer.....and ya kamata ta dinga kula da gujewa ta'ammali da abubuwa masu hayaqi da yawa". Kai kawai ya jinjina ma Dr rubayya

"Allah ya qara afuwa yasa kaffara.......idan kuma ana buqatar wani abun.....am ready in sha Allah,koda yaushe kuka kirani am available for your needs".

"Thank you" Ya fada can qasa da kalar miskilancin nan nasa da ba wani baqon abu bane a wajenta.

Already kafin ta fita ya kira saddiq ya gaya masa gata nan su maidata gida,yana kuma sauke wayar kiran farouq ya shigo masa

"Mu duka mun wuce gida,but.....na kira wasu daga cikin guards dinka an qara akan na cikin gidan......in sha Allah kome zaiyi daidai......but please please.....karka dauki doka a hannunka akan mutanen nan". Farouq ya fada cikin narke murya. Ya dade da sanin halinsa,muddin ranshi yakai qololuwar baci irin wannan bai iya hukunci ba.

"Kaji?" Farouq ya sake maimaitawa jin yayi shuru baice komai ba.

"Alright" Ya fadi a hankali kamar wanda maqoronsa ke masa ciwo yana gintse kiran.

Iska ya sake furz 
arwa daga bakinsa,daga jikinsa har zuciyarsa babu wani abu dake masa dadi,sai ciwo kawai.....wani irin ciwo me radadi a gangar jiki da zuciyar.

Karon farko ya maida dubansa saman fuskarta,wanda daidai nan idanunsa suka hangar masa wayar dake gefan pillow dinta. Wani abu ya tsarga masa har yatsun qafarsa,sai ya miqa hannu ya dauko wayar.

Tabbas itace wayar daya gani a hannunta shekaran jiya.....wayar da baisan yadda akayi taxo gidan ba ta kuma zama mallakinta har take amfani da ita.

Jujjuya wayar yayi sosai yana qare mata kallo,sai ya latsa malatsin gefe haske ya kawo,ya sanya dan yatsa ya shafi fuskarta take ta bude.

Bangaren kira ya shiga ya soma dubawa,kirane da numbers barkatai wanda kusan dukansu babu suna. Ci gaba yayi da dubawa har zuwa kan date din shekaran jiya wanda wata number data qare da 01 itace number qarshe da aka amsa kira da ita.

Kai ya jinjina a hankali yana komawa bangaren saqonnin karta kwana wato sms. Dunqule hannunsa yayi da kyau yana ci gaba da duba saqonnin da suka shigo da mabanbantan numbers suma,wanda dukkaninsu suna dauke ne da nau'ikan kalaman soyayya iri iri,saidai kowanne saqo ba wata amsa guda daya da ta maida masa.

Kasa ci gaba yayi da dubawa saboda yadda dukka jikinsa ya dauki tsuma,sai ya kashe wayar ya jefata aljihunsa sannan ya miqe yana dubanta da wani zafin zuciya. Takawa ya soma yi a hankali,har cikin jiki da zuciyarsa yana jin bazai iya zama da ita na daren gaba daya ba a daki daya,sai daya hau saman sannan ya kira sashen ma'u yace taje ta kula da ita,baima aje wayar daidai ba ya dora kansa a hankali saman sofa din yana fidda numfashi kansa kaman zai fado.

Tunani ne iri daban daban suke barazanar tarwatsa masa kai,ya rasa da wanne zaiji?,da wanne zai fara?,meye daidai cikin hasashensa meye ba daidai ba?,ganin yana neman rasa nutsuwarsa cikin qasa da minti talatin,sai ya miqe a gaggauce ya jawo earpiece ya toshe kunnuwansa da karatun qur'ani,abinda ya sanya duk abinda yakeji ya soma sauka a hankali,nutsuwarsa ta soma daidaita,nauyin da yakeji a qirjinsa da zuciyarsa suka soma raguwa,sannu a hankali ya maida idanunsa ya lumshe wani bacci yana yin awon gaba dashi a cikin falon.

*_TO ASUBA TA GARI......SAIDAI KUMA KO DAME SAFIYAR RANAR ZATA WAYE MUSU DASHI?_*




*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862

5 5 5
5 5 5 5 5
_Zafafabiyar_

6B6O6O6K 62

g,D D

5K5<5B5@ 61



61


Tun daga sanda ta farka bata samu wata nutsuwa ko kwanciyar hankali ba sai bayan data tabbatar ba wani abu a jikinta da mshkur din ya samu kaiwa gareshi

"Allah na gode maka.....Allah na gode maka" Ta dinga maimaitawa cikin bandaki hawaye na layi bisa kuncinta.

Wanka ta sakeyi dab da asuba da ruwa me dumi sosai,koda

Please Login or Register in order to submit comment