Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

sama ya fara ballewa yana zareta daga jikinsa saboda wani irin zafi da yakeji tun daga zuciyarsa har cikin fuskarsa. Iske me qarfi ya fesar daga bakinsa bayan ya zuqi wata

"Wanne abune meqarfi da girma a tsakaninsu bayan wannan?" Ya jefawa kansa da kansa tambayar yana motsa labbansa.

"Ita ta shiga jikin maamah ko maamah ce ta shiga jikinta?" Ya sake maimaita tambayar da ba wanda zai iya bashi amsarta. Yanzun har matsayinta da girmanta wajen maamah yakai ya samu sanyawar albarkar maamah din saboda dalilinta?,wanne aiki take mata haka me faranta rai bayan abinda yake suspecting?. Tunanin daya rakashi kenan har cikin office dinsa,ya kuma wuni yana tayashi zama,duk kuwa da uban tarin ayyukan daya samu suna jiransa. Duba documents da sanya hannu cikin wasu takardun,wasu takardun suna da buqatar hankalinsa da nutsuwarsa kafin yakai ga sanya hannu,da qyar ya hada hankalinsa bayan sallar la'asar ya soma duba wasun,bayan ya yiwa kansa matsayar matakin da zai dauka.

Komawa tayi ta sake kwanciya bayan sallar la'asar din,tana lissafin nan da awa daya koda rabi zata shiga kitchen saboda shi.....saboda mutumin da ba ganin girma qima ko martaba sam sam tsakaninsu. Idanunta ta runtse,a yau tana jin wani zafi zafi na yadda maamah ta bautar da ita. Batasan me yake tilastata lallai saita yi sai kuma ta cika muradin maamah din ba. Tsaki taja tana bude idanun nata,sai suka fada saman gift din da anni ta bata ranar da suka je.

Dan murmushi ta saki qasan zuciyarta,matar ta kwanta mata a rai,tana da wani irin calmness me taba zuciya nutsuwa da kuma wani irin kwarjini. Tashi tayi tsam ta daukosu ta dawo ta zauna saman abun sallarta data tashi ta soma budewa tana tuna fuskar matar da takejin kamar ta taba ganinta a wani wajen kafin yanzu.

Littafin farko ta dauka daya qunshi addu'o'i akan kowanne abu,harkokinmu na yau da kullum. Shafin farko ta bude,sai ta dinga tuna zamanin da ummensu ke raye,Lokacin da take tsaye a kansu kai da fata,ba batun fashin islamiyya ko wani abu da yayi kama da wannan. A duk dare itace malamarsu,zata zauna a tsakiyarsu saita tabbatar kowanne karatunsa ya zaunar masa akai,musamman karatun addini da a nan tafi qarfi,na bokon tafi jiran abbansu idan ya dawo,musamman idan ya zamana itace da girki,idan ba ita bace dole saita dauki uzuri an bata lokaci.

Hannu tasa ta shafi addu'ar farko da sam ta mantata cikin rayuwarta,ummensu itace ta fara koya mata ita tana kuma iya tuna lokacin har yanzu,sai ta tashi ta koma saman sofa ta zame kadan tana bin addu'o'in daya bayan daya tana dubawa suna kuma sake tuno mata da kansu.

Sosai takejin dadin karatun,don ya debe mata kewa me yawan gaske. Babu zato daga saman kanta din,daidai wata kyakkyawar qaramin luxury stand taji qaraurawa tana kadawa. Zubawa wajen ido tayi,wata mulmulalliyar na'ura ce da take zubi da telephone. Tunawa tayi amna ta taba dagawa tayi kira zuwa parlor sanda sukazo,sai a sannan ta tuna na'urar sadarwa ce da aka shiryata duka gidan da kuma tsakanin dakunan gidan har zuwa Kutchen,wannan ya bata qwarin gwiwar saka hannu ta daga ta sanya a kunnenta.

"Ranki ya dade......malamarki ce tazo,sabuwar malamar da yallabai ya daukar Miki saboda karatun yamma".

"Malama kuma?" Ta tambayi kanta da kanta cikin tsananin mamaki tana son tuna yaushe sukayi wannan maganar da shi?.
"Duk cikin salon da zai miki mugunta ya cusguna miki ne kaman yadda ya dauki alwashi". Ido ta lumshe tana budesu sannan a nutse tace mata

"Ki sallameta zuwaira......ko kuma ta jira wanda ya tattagota din" Daga nan ta kife wayar tana komawa ta zauna qirjinta a quntace.

Wannan abun da yayi me yake nufi kenan?,ita din jahila ce?,ko batasan komai ba saishi zai sanya a karanta mata?. Wannan tunanin ya tsaidata,sai data gama baqin ran da bacin ran sabon salon wulaqanta mutum daya bullo dashi......hakanan ba don taso ba ta miqe tana wucewa kitchen.

Tana shiga zuwaira na fadowa,sai ta waiwayo tana kallonta. Cikin jikinta wani abu ya bata,ta yaya duk wani motsinta zuwairan kamar tana biye dashi ne?

"Ranki ya dade dame za'a taimaka miki dashi?" A nutse ta juya kawai ta fara aikin gabanta,kamar ba zata amsa mata ba sai kuma ta tura mata lettuce da cabbage carrot da peas tace ta gyara ta yanka mata.

Zaman kurame kawai sukeyi cikin kitchen din,zuwaira nata satar kallonta tana son ta dan tabota da magana don ta gina alaqar sabo a tsakaninsu amma bataga wannan fuskar ba sam

"Tashin hankali" Zuwairan ta fada qasa qasa,daga ita har mijin haka fuskokinsu suke kamar na shanu? Ta tambayi kanta,ita dai har yanzu bata taba ganin fara'a ko dariyar dayansu ba.

Sai da suka kammala komai sannan ta fidda magungunan zata cakuda kaman yadda ta saba. Ta bude murfin ta karkata gorar,sai kuma ta tsaya cak. A hankali ta daga idanunta ta zubesu akan zuwaira data tsaida komai tana son tabbatar da zubawar. Karon farko da cikin jikinta taji kamar nauyin idanuwan wani yana kallonta zatayi abinda bashi ya dace ace tayi ba akan wani,duk kuwa da tasan jirgi daya shine ya debo zuwaira da ainihin me kwangilar,amma a yau saita ji wani nauyi.

"Zaki iya bani space?" Ta jefa mata tambayar taba dinke girarta sosai fiye da dazu.

"Au to....to ranki ya dade" Ta fada adan daburce sannan ta juya tana fita a kitchen din. Haushi ya sanyata kwarara da yawa,idan komai ya qare ai a huta,taga ta inda zata tuhumeta kuma,sai taja tsaki tana jefa roban a shara sannan ta juya ta fice tana baiwa zuwaira dake falo umarnin taje ta jerasu,sai ta wuce kai tsaye zuwa dakinta.

Itama din a gaggauce ta shiryasu tana kallon kayan,baki ta tabe,tana jin haushin yadda lafiyayyen abinci irin haka yake salwanta,ga nasu iyalan can cikin yunwa da buqatar abincin da baikai wannan bama,amma akan mutum daya anata asarar lafiyayyen abinci irin wannan. Hankalinta ta maido jikinta da sauri,saita juya tana barin falon cikin son kiyaye dokarsa da tsoron kada ya dawo ya sameta a wajen kamar yadda ya shardanta mata.

K'arfe Tara da wasu mintuna motocinsa suka tsaya a farfajiyar gidan bisa halastaccen parking da kowanne driver na kowacce mota ya qware akai. A nan harabar gidan ya barsu ya wuce ciki shi dame sunan malam,wanda iyakarsa qofar parlor din farko ya juya shima yana komawa cikin guard da security na gidan dake qoqarin tabbatar da tsaro da lafiyar kowacce mota kafin masu tafiya su wuce a sake tabbatar da tsaron gidan sannan a maidashi a rufe kaman yadda yake,shida da fita kuma sai da izinin masu gidan.

A hankali yake ratsa falon farko zuwa na biyu kafin ya isa stairs dinsa. A gajiye yake don duk sanda yayi dare irin haka a company to tabbas cinkoson aiki ya riqeshi ne.

Tun daga nesa yana taka stairs din ya hangi maqullin maqale jikin qofar,ya isa a hankali ya sanya hannu ya cire sannan ya tura qofar parlor din. A nan zarginsa ya tabbata,mug din da yayi amfani dashi a daren jiya yana zaune abinsa dirshan saman side table din,yayin da dish din da yayi amfani shima dashi yake zaune saman dining abinsa hankali kwance.



*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862

39

_Daga abu hurairah Allah ya qara yarda dashi yace:mazan Allah S A W ya ambaci ranar juma'a,yana cewa "A CIKINTA KAWAI WANI LOKACI,BA WANI BAWA MUSULMI DA ZAI RUSKETA YANA ME TSAIWA YANA SALLAH YANA ROQON ALLAH WANI ABU FACE SAI ALLAH YA BASHI ABINDA YA ROQA DIN". sai manzon Allah yayi nuni da hannunsa na qanqantar lokacin (ma'ana baida tsaho,Allah yasa muna cikin wadanda zamu yita ruskarshi)_



Wani bacin rai ne karon farko ya sauko masa,ba abinda ya dawo masa akai sai abinda ya faru a dazu. Yadda maamah ta fitittike tana jaddada masa yadda takeso ya mu'amalanceta ko ya kula da ita,amma ko kusa ko alama shi baiga alamun tasan darajar kalmar aure ba koda kuwa auren 'yar tsana aka daura,ballantana shi data deba kudaden da ranta keso,karamci kuma ya sanya suka qara mata da wasu abubuwan da shi kansa baisan me su anni suka kashe ba.

Duka sai yaji abun bai masa ba bai kuma zauna masa akai ba,ya kamata ya qara bata lesson. Yana takawa zuwa bedroom din nasa yana watsar da kayan hannunsa,kama daga socks takalminsa suit briefcase dinsa da sauran tarkacen daya shigo dasu. Wani budewa hancinsa yakeyi yana tsukewa saboda bacin rai,ya tsani raini ya kuma fahimci halinta ne,ya tsani rashin kunya ya kuma karanci dabi'arta ne. Bai dakata ba sai da yayi wanka,ya hadawa kansa fruit salad a gurguje yasha,sannan ya zauna yana jawo wayar sadarwar yana kiran number dakin nata.

Ta gama komai tuntuni,ta kuma jima da kwanciyar saidai baccin da baizo ba. Tayi mamakin jin kiran,saita sanya hannu ta dauka tana tunanin zuwaira ce,ko meye kuma ya faru a daren nan oho?.

Muryarsa taji sabanin muryar zuwaira da tayi tunanin itace. Har tsakiyar kanta sautin muryar ta sauka mata da wani irin zuzzurfan amo

"Hello" Ya fada yana qoqarin hadiye bacin ran dake taso masa. Matsar da kan wayar tayi daga kunnenta da zummar sauke wayar,kaman yasan abinda take shirin yi ta tsinci muryarsa cikin zafi yana magana

"Kika kuskura kika sauken waya....zakisha mamaki na". Tsauri umarnin nasa yayi mata,saita samu kanta da gaza ajiye wayar. Sau tari tana mamakin yadda yake cin galaba a kanta haka da sauri,umarninsa yake saurin ratsata,wani abu guda daya da ta raina akan kowanne d'a namiji. Bat 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~a taba zato ko tunanin akwai wani lokaci da zaizo da wani namiji zai iya juyata ko ya canzata daga abinda yayi mata daidai cikin rayuwarta ba,sai ga abun yana tafiya cikin rashin zato bare tsammani.....kamar a cikin duniyar mafarkinta.

Ci gaba tayi da riqon wayar ba tare data ce komai ba,haka daga nasa bangaren bataji ya sake furta komai ba. Kusan minti daya wayar na a riqe a hannunta,sakannin kuma suna ci gaba da motsawa. Kaman daga cikin wayar taji an murda qofa an kuma budeta. Sauyin yanayin qamshin daya soma mata sallama ne ya shaida mata tabbas an bude mata qofa,ba kuma cikin wayar bane a zahiri ne.

Tana kwance ne rub da ciki,don haka ta waiwaya kadan don tabbatarwa da idanunta. Muhammad jadda ne,tsaye daga baki qofar dakin yana riqe da handle din,daure da lallausan farin towel wanda ke dauke da tambarin VERSACE baro baro a jiki. Gaba daya towel din ya daurashi ne daga iya qugunsa,ya kuma sauka sosai zuwa mararsa,abinda ya bata damar ganin full ginannen jikin nan dake cike da lallausar gargasa data kwanta tayi luf luf.

Fadin kafadunsa ya sanya bata ko iya hangen qofa,sai yau ta sake fahimtar GIANT ne na gaske,da murjajjen jiki da kuma ginannun tsokokin damtse dana qirjin wato(muscles).

Wani mahaukacin faduwa gabanta yayi,a yau taga abinda bata gani ba a wancan ranar data sameshi a parlor dinsa.....ko don yau din a tsaye yake da dukka tsahonsa da kuma wadataccen haske a dakin nata?.

Duk yadda take da kafiya da taurin rai sai data gaza ci gaba da kallonsa,wani irin tsoro ya kamata wanda ya tilasta mata maida kanta ta kwantar saman pillow tana baiwa qofar dakin baya,wato qeyarta ke kallon qofar kenan.

Gabanta ya sake yankewa ya fadi sanda taji ya maida qofar ya rufe gami da murxa key,ta fidda idanunta dukka biyun waje tanason yin hasahen abinda zai iya faruwa da ita,saidai bata gama wannan ba taji an sanya hannu an birkitota gaba daya,sai gata ta koma rigingine a maimakon rub da ciki da take a dazu.

Gaba daya ya zame mata rumfa saman kanta,tamkar me barazanar hanata ganin komai na dakin sai wannan mudadden jikin nasa.

Da hanzari ta sanya tafukan hannayenta guda biyu da zummar tureshi saboda yadda yake neman hade space din dake tsakaninsu,amma ko gezau kamar ma ba wani hannu daya sauka a jikinsa. Bai bata second chance ba ya kama hannuwan nata ya matse cikin hannunsa guda daya.

Qoqarin qwatar kanta sosai ta farayi tana tureshi,amma baiko motsa ba,yana riqe da hannuwanta gaba daya yana kuma ci gaba da zube mata idanunsan nan

"Ka sakeni......ka cikamin hannu" Ta fada sanda ta fahimci ko kusa ko alama bata da qarfin da zata iya amsar kanta a hannunsa. Ta cikin idanunta ya fahimci laushi tayi,hakanan qarfinta ne ya fara qarewa. Bayajin zai qyaleta haka sai ya bata mummunar barazanar da ba zata qara kai qararshi wani guri ba. Duk dabaya tunanin wani tsoro me yawa a tattare da itan duba da ita din WACECE?. Ba wani sabon abu bane a wajenta cudanya da maza,duk da maza suna suka tara kamar yadda mata suma suka tara suna.

"Inajin a matse kike a sauke miki jarabar da take damunki ko?,wannan ya sanya ba kunya cikin idanunki kika je kina kai qara a inda kike tunanin za'a sanyani sexual affairs dake ko?". Duf wuta ta dauke mata,daga iya kalmar sex data shigo maganar ta tabbatar lallai babbar magana aka baro. Yaushe takai qararsa?,kuma gurin waye?,me tace tana da buqata?,duka wadannan tambayoyin sune suka soma mata yawo saman kai,kuma inda tana da hali tana da buqatar amsarsu,saidai a yadda komai yake a hautsine bata jin tana da tattararriyar nutsuwar nemansa da wadannan amsoshin.

Tana aje wannan tunanin yana sakin hannun nata,ya miqa hannu da wani irin zafin nama zuwa Coller din rigarta,wadda tsaurin riqon da yayi mata ya bawa bottom daya damar tsinkewa fit. Fitarsa sai ya zamana kamar ya hada da fitar nutsuwa daga gangar jikinta,wani tashin hankali ya rufto mata har kala biyu. Na farko yadda yayi kusa da ita da towel din da kadan ya rage marabarsa da tsirara,don babu abunda ya lullube illa mararsa zuwa gwiwarsa,na biyu kuma fitar maballin rigarta sai ya tuna mata waccan ranar a kitchen. Ranar da har yau idan ta dauki rigar data sanya a ranar sai taji qamshin wannan mayataccen turaren nasa,abinda ya sanyata kenan tayi adabo da rigar duk kuwa yadda take sonta. Saboda duk sanda ta sakata haka yadda abin ya faru zai yita dawowa kanta,hakanan kuma zatayita tuna yadda ya azabtar mata da lips haushinsa yayita kai komo kenan a ranta har sai ta raba kanta da ita.

Matse hannunta yayi yana saukar dashi daga gaban rigar don so yake ya tsinke maballi na biyu,kafin ta iya komai har ya samu nasarar yin hakan,ya kuma wuce zuwa maballi na gaba,abinda ya sakata saka hannuwanta dukka biyun ta cukuikuye gaban rigar,cikin fushi kuma taci gaba da magana

"Don't touch me.......ka daina tabani mana.... Wai mene haka?!". Ta qarasa fadi sanda ya tattara hannuwanta da zummar turesu,cikin rashin sa'a hannuwan nasa suka samu nasarar sauka daidai saman tudun qirjinta wanda ke tsaye car babu bra. Sabonta ne idan zata kwanta dukka saita ciresu,don tana jin kamar suna hanata cikakken bacci.

Daga shi har ita ba wanda baiji kaman an yarfa masa wuta a jikinsa ba,yayin dashi ya hada wani azababben shock daya ratsa jininsa da wani irin mahaukacin gudu ya aike saqo qwaqwalwarsa ya kuma dawo da saqon yana rabawa zuwa sassan jikinsa gaba daya.

Taji komai har cikin jinin jikinta,sai taji kamar an zare mata dukka wata laka tata da wani irin firgici da tsoro bakinta ya furta

"Please......don Allah ka bari" Kalaman nata na qarshe ya fito da zirarowar hawaye zuwa saman kuncinta.

Duk yadda yaso ya zarce da tsoratata gami da gigitata cikin mugunta sai yaji ya kasa,haka ya sake mata rigar yana dauke idanunsa daga kanta ba tare daya bari sun sauka a inda take boyewar ba tamkar sulalewar ruwan kalkashi a tafukan hannun mutum. Zuciyarsa ta cika da wani irin mahaukacin mamaki......daga ina wannan weakness din ya taho?,ya tambayi kansa da kansa can qasar zuciyarsa. Bai taba niyyatar zai dauki mataki akan wani abu ba tare daya qarasa aiwatar da qudurinsa ba,bai taba jin rauni akan duk wani abu daya sanya a gaba ba sai akan wannan dan qaramin aikin.

Tattare jikinta tayi waje daya tana neman hanyar sauka daga saman gadon,amma sai ya sanya gwiwarsa ya take gefan rigar,ya waiwayo a nutse ya zube mata idanunsan nan masu dauke da wani kakkaifan maganadisu,wanda duk yadda sukakai ga haske sun surka launi a yau din.

"Kina zaton zan hada jiki dake ko?,over my dead body......duk randa zan hada jiki dake ki sanya a ranki ranar mutuwarki ne kawai yazo,don zan niqaki da kyau kaman yadda engine ke niqa tsaba ya koma gari....." Yatsunsa ya murza saman fuskarta sannan yace

"Sharadi guda biyu ne zan baki idan kin kiyaye shikenan.....na farko....kada ki kuskura ki sake kaiwa maamah qarata koda akan meye kuwa....ban hanaki kaiwa anni ba idan kinga zaki iya fine.....sharadi.na biyu duk randa na sake miki umarnin yin wani abu kika watsar kina daukan kanki wata tsiya.....zakiga abinda zai biyo baya,sai na sanya an sako Michael yayi dambu da namanki,ki tashi kizo ki gyaran sassa.....ki kuma samu note pad ki rubuta day one don lissafinmu yafi tafiya daidai" Yana kaiwa nan yaja jikinsa yana sauka daga gadon,ya kuma fara takawa hankali kwance yana fita daga dakin.

Da sassarfa yake haurawa saman cikin tuhumar kansa da kansa. Baisan kanshi da kasawa ko gazawa ba,ya akayi ya kasa bata mummunan punishment yadda ya kamata?. Koda ya tsaya gaban mirror na toilet din,sai ya dinga jin haushin kansa da kansa. Baisan wani weakness nasa ko kadan ba......amma sai ya samu kansa yana tsoron kada fa wannan ya zama shine weakness dinsa?.


*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862

5 5 5
5 5 5 5 5
_Zafafabiyar_

6B6O6O6K 62

g,D D

5K5<5B5@ 40


_Daga sumrah dan jundub RA,yace manzon Allah S A W ya kasance yana nemawa mumunai maza da mata gafara a kowacce juma'a_

_harda ni dake da kikazo a wannan zamanin kin shiga ciki,LALLAI HASARA DA TABEWA TA TABBATA GA DUK RUHIN DA BAISON ANNABI,ALLAH KA DAUKI RUYUKANMU RUHINMU YANA CIKE DA MATSANANCIN SONSA S A W_
________________________________



Moroccon cotton jallab ya saka ta maza maroon color me gajeran hannu,wadda aka yiwa ado da gold din zarurruka masu kauri. Har hantar cikinta sai data kada sanda taji fitowarsa zuwa falon,amma ta dake bata nuna ba,tana duqe tana goge stand tv lokaci lokaci tana goge 'yan hawayen daketa qoqarin lallai sai sun sake karya mata zuciya.

Kai tsaye ya wuce saman minotti sofa dinsa yana lumshe idanunsa,wata azababbiyar kasala nason saukar masa. Dole yana buqatar wani abu da zaiyi awakening dinsa for some hours don yana da aiki.

"Ke..." Ya kirata idanunsa suna lumshewa kadan. Kiran ya mata ciwo,amma kuma dole ta nuna tasan da ita yake maganar.

"Bring me some coffee" Ya furta yana dauke idonshi a kanta ya lumshesu don kaucewa kallonta.

Ajiye duster din hannunta tayi qirjinta na mata wata suya,ta fara takawa don isa qofar da zata saukar da ita daga saman

"Hey.....ina zaki?" Ya furta da rashin qwarin murya. Sai kuma ya mata nuni da nasa kitchen din da idanunsa,kai tsaye ta gane me yake nufi,ta kuma canza akalar tafiyar tata zuwa can din.

Tayita dube dube da tsoron kada ta tabo wani abun duba da yanayin machine da utensils din dake kitchen din daya sake shan bamban dana qasa nesa ba kusa ba. Da qyar ta samu ta kammala,duk da bata da guarantee din yayi ko baiyi ba,don itadai ba damunta yayi ba,koda ya dameta ma ba irin wannan bane.....nasun irin nasun ne wato daidai matsayinsu yaku bayi.

Saman tea tray ta hado da cups. Ta qasan idanu cikin lumsassun idanunsa yake kallonta sanda take nufoshi da wani irin kallon da zaka rantse da Allah bacci yakeyi. Yana qoqarin binciken kansa me yasa yaketa tunawa da abinda ya faru?,amma ya rasa dalili,haushin kansa sosai yakeji a yanzun,yana ganin kamar wannan hanyar ta sanya tsoro a zuciyarta bazatayi aiki ba.....zata iya dasa masa matsalar da zata gagari gangar jikinsa watan watarana.

Yadda jikinta yayi laushi sosai yake karanta,yana mamakin macen data saba mu'amalantar maza kala daban daban me ya sanyata jikinta yayi laushi don ya mata wani qaramin riqo da bai taka kara ya karya ba?.

"Kana murzata ne ta hanyar da ba haka su suke mata ba,da ta irin tasu hanyar ce qila ba abinda zai sanya jikinta laushi" Wani sashe na zuciyarsa ya bashi amsa.

A gabansa ta ajiye tana jin inama zata samu wata dama ta zuba masa wannan abun cikin tea dinsa?,qila cikin kwanaki uku ta samu nasarar da zata cika aikinta,ta tattara tabar wannan DUNIYAR tasu ta koma tata ainihin duniyar.

"Serve me" Ya fada da murya can qasa. Sake baci ranta yayi,gaba daya a hankali yana son canzata ta koma 'yar aikinsa kenan kome?. Tsugunnawa tayi a nutse ta soma zuba masan tana qoqarin danne zuciyarta amma ta kasa jin relief. A sanda parlor din ya dauki shuru,wayarsa da tafi kusa da ita ta soma kuka alamun shigowar kira. Kallo daya ta yiwa wayar ta dauke kanta,yarinyar kullum ce dai wato fareeda khaleed mustapha. Qaramar tsuka taja,ita ta sani zaa rina,mutum kamar muhammad jadda ace yana zaune lafiya bisa kyawawan dabi'u?,ai ta qalubalanci wannan. Banda akwai wata gurbatacciyar alaqa me zai dinga shigo da kiranta cikin wayarsa a kowanne dare?,a daidai lokaci irin wannan da mafi yawan lokuta yake kebancewa shi kadai?.

Tana miqa masa coffee din yana daukan wayar yana kallon screen din ransa yana baci,ya dauke dubansa daga kan fuskar wayar da yakeji kamar ya bugata da bango saboda yadda tsananin nacin fareeda ya soma shallake hankalinsa,ya aje dubansa akan fuskarta dake a dinke sosai.

"Fara sha kafin ki bani" Yace da ita a taqaice. Duban rashin

Please Login or Register in order to submit comment