Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Tana murza glass door din ta sanyo qafafunta ya daga idanunsa a hankali daga inda yake zaune ya zubesu fes saman fuskarta,idonta ya shiga nasa,sai ta janye nata idon a hankali,ta kuma ja da baya tana komawa da bayan a maimakon fitowa da tayi niyyar yi. Sam bata qaunar gamuwa dashi,a kwanakin data janye kanta daga komai da zai sanya su hadu ta kama karatunta sai take samun wata irin nutsuwa a zuciyarta. Ta dauki kwanaki rabon daya sanyata cikin idanunsa,daga shi har maamah sai takeji kamar Allah ne yayi mata maganin matsalarsu.

Janye nasa idanun yayi shima bayan ta koma da baya tana kuma komawa ciki. Yadan jijjiga kai kadan yana daukan mug din gabansa ya sanya a bakinsa. Tana gyara bedroom dinsa kamar yadda sukayi sharadi,saidai daga wannan ko gilmawarta bai sake gani ba tun daga ranar. Can qasan zuciyarsa tana cike da wasi wasi da kuma qiyasi akan abubuwa da dama. Sai yake zargin shurunta dana maamah dukka kamar akwai wani magana a qasa,don haka ya jawo wayarsa ya kira me sunan malam. Cikin qasa da second ashirin suka gama magana,ya shaida masa ya nema farouq ya turo amintacce kuma sirrintaccen me musu installing CCTV.

Mules din qafarsa ya maida,sannan ya ciri napkin guda daya yana goge dan abinda ya bata masa hannu kafin yace da ameh.

"At night.....ka dafa paw paw leaves ka ajiyemin da duminsa.....daga yau inaso ya zama first drink dina for morning". Kai ameh ya jinjina cikin girmamawa

"As you wish sir". Sai ya sauka a nutse amma hankalinsa yana dan kan qofar kadan,yanason sake tabbatarwa komawa tayi ta fasa shigowa saboda yana wajen?.

Murmushi ameh yayi yana binsa da kallo,sosai boss dinsa yake burgeshi,yayi aiki kafin wajensa gidajen manyan attajirai da dama,amma baiga mutum me kiyaye lafiyarsa da yasan sirrin abinci ba irin boss din nasa ba. Yasan duk wani abu da zai gyara lafiyarsa a matsayinsa na namiji,yasan duk wani abu da zai gyara masa lafiyar ido da fatarsa,hakanan yasan duk wani abu da yake natural anti aging remedies kala kala. Ire iren abubuwan da shi yake tanadarwa manyan da yayi aiki a qarqashinsu don inganta lafiyarsu da gina garkuwar jikinsu suke qin ci ko sha don ba dadi a baki ko basusan muhimmancinsa ba......sai gashi shi kullum ne sai an tanadar masa da wannan abun morning and evening. Akwai hadin salad daya dinga mamaki sanda yaga yana cinsa farkon xuwansa,musamman da yake yasan yadda yake inganta qarfi da lafiyar d'a namiji,da yawan wasu abubuwan ma shike qaruwa dashi a wajensa. Baya son maggi da yawa a abinci,kaman yadda sanyi zaqi da kuma maiqo da abokansa bane sam sam
(Mata da yawa suna complain din rashin lasting din mazansu a other room,sunsha magani sunsha maganin amma a banza,anata samun sabani da sauran masu matsaloli,to wallahi wallahi da yawansu maggi shine yake kashesu,inda kinsan yadda maggi yake kashe lafiyar mazajenmu da kinyi mugun gudunsa kuwa,kiga mace ta saka farin magi a abinci,tazo ta saka wadancan cubes din kala daban daban,ta hada drink ta laftawa miji sugar,ga uban sanyi,abinci mai yana kwanciya,ba ruwanki da manja ma sam sam,to billahillazi kunji na rantse muku haka zaita zame miki mace,kuma duk irin maganin da zaisha fa a banza,muddin ana kan cin magin nan,tashi daya ba zaki iya dainawa ba,amna gradually zaki dinga janyewa,idan goma kike sawa ki koma bakwai daga haka ki koma hudu,tabbas indai zaki dimanci haka zaki ga canji,ki ajiye farin maggi kwata kwata,zaqi da maiqo duka ki rage masa,hadin wancan salad din in sha Allah zan kawo muku shi a gaba,ya gwada cin na sati biyu bayan kin janye magin kiga ikon Allah,koda me gida yana da lafiya ma normal ne kina iya hada masa shi ya dinga ci,amma ina maimaita muku ku raba kanku da kayan d'an d'anon nan,Allah yasa mu dace).

Kamar kowacce safiya muddin yana da isashen lokaci......ba baqi ba meeting na early morning da sauransu,zuwa duba lafiyar anni da gaida maamah din yana cikin schedule dinsa na kullum.

A farfajiyar gidan kamar ko yaushe ya samu guard dinsa,kowa na tsaye akan aikinsa. Bai qaraso bama amma tuni Jordan ya buda masa bugatti dinsa yana jiran qarasowarsa.

Cikin girmamawa da nuna kulawa suka gaidashi ya amsa yana bincikar lafiyar kowa kaman kowacce safiya,sai daya tabbatar da kowa lafiya sannan ya miqawa saddiq da kusan a makare yake isowa kayan hannunsa,wannan dalilin ya sanya baya samun shiga cikin gidan duk zuwan da yakeyi.

Sun dauki hanya sosai kiran musaddiq ya shigo masa,ya fidda wayar yana connecting nata da Bluetooth dinsa yana amsa wayar.

"Hamma na gama komai......sai yaushe zan dawo?" Musaddiq din ya amsa a karye da alama gida yakeson dawowar.

"Ka dawo kayi me?" Ya tambayeshi yana jin tantama a dawowar tasa.

"Hamma nayi missing anni......nayi missing saddiq". Iska kadan ya furzar daga bakinsa wadda ta fita da qamshin mint leaves saboda mouth fresh dinsa kenan na dindindin

" Anni kuna waya haka saddiq.....kuma ko ita nasan bata da damuwa me yawa a tafiyarka.... Dude ne kawai nakeji ban kyauta masa ba dana dauke masa personal assistant......shima nasan ya fahimceni.....oops......anyways......nan da sati biyu zamu hade a madeena in sha Allah,it was family trip time". Har a muryarsa yaji dadi

"Hamma na Manta da lissafinma.....okay..."

"Hope komai naka ba matsala ko?,daga can zaka iya shiga koda Jeddah ne sai ka qaraso madeena"

"Direct entry zanyi hamma.....i can't wait to see my family".

"Alright....ka kula da kanka" Ya furta cikin kulawa

"Na gode hamma" Ya ambata suna ajiye wayar. Wayar ya zubawa idanu yana tuna wasu abubuwa da suka shude..... Ita rayuwa dukanta tana komawa tarihi ne watarana......bai taba zaton a rintsin da suka fuskanta shi da musaddiq ba akwai ranar da zatazo kamar haka komai ya wuce ba......yadda kula da musaddiq da bashi rayuwa me kyau ya sanya hannuwansa sukayi kanta.....tunaninsa ya dimauta,kwanyarsa ta kusa jirkicewa da daina iya tuna kome me kyau.....ambaton sunan maamah ya zame musu kamar wata jarabawa.

Hannunsa yasa ya shafi fuskarsa yana son ajiye tunanin a gefe.....yanzu yanzu zai iya rasa kowacce nutsuwa tasa,ya kuma rasa duk wani courage na aiki daya fito dashi a yau din.

"Gidan maamah zai fara tsayawa" Yace da saddiq don ya shaidawa driver din shi kuma ya sanar da ayarin motocin. Yayi hakanne don yasan muddin ya shiga gidan maamah a yanayin da yake ciki na tuna munanan abubuwan data aikata baga rayuwarsu kadai ba......anni itace zata zamewa zuciyarsa yayyafin ruwan sanyin da zai wanke duk wani baci da ransa yayi.

Kamar kullum da qafa ya taka daga inda suka ajiye motocin zuwa cikin gidan. Malam sa'adu ya matso da sauri yana bude masa qaramar qofar kasancewarsa shugaban masu gadi na gidan a yanzu. Tunda aka mallakawa maamah din wannan gidan yafi qarfin gadin malam sa'adu shi kadai,dole sai daya hada mata da security,amma kuma kowa yana qarqashin malam sa'adun ne wanda shike da permanent chair. Har kullum burgeshi hali da dabi'ar muhammadun takeyi,ya taka dukkan wani matsayi da bawa zaizo ubangiji ya kaishi a rayuwa,amma bai dauki hakan a bakin komai ba.

Gaisawa sukayi kamar kullum,sannan ya taka yana shigewa cikin gidan da ma'aikatan dake bakin aiki kowa yake zubewa yana gaidashi.

Daidai sanda yake sallama a falon daidai sanda take fitowa daga kitchen din gidan,Hannunta dauke da qatuwat warmer kamar ma rinjayarta takeyi.

Huda ce,ta bishi da kallo tana amsa sallamar tasa cikin kallon baqunta. Yadan sake dubanta kadan,sai yake jin kamar yasan fuskar,amma kuma sai ya kauda wannan tunanin yana neman wajen zama,daidai sanda take gaidashi cikin ladabi daya zame musu jiki tun tale tale

"Ina kwana?" Ko daya maida dubansa kanta sai yaga har ranqwafawa tayi irin na ban girman nan

"Lafiya la....." Amsa gaisuwar ta katse saboda yadd warmer din taso subuce mata daga hannunta. Cikin zafin nama ya isa ya karba yana fadin

"Kibi a hankali......" Sai ya taka yana kaita saman dining din ya ajiye.

"Maamah ko?" Ta tambayeshi qasa qasa kaman me tsoron tambayar,don itadai yana mata kama da mijin adda sabreen din su. Kai ya jinjina kadan a ransa yana mamakin ina kuma maamah ta samota?.

"Bari na kira maka ita" Ta fada da dan saurinta,can qasan ranta yana cike da murna,yau kam taga wani daya danganci addansu.....ko gaisuwa ta aike mata tunda yawan lokuta maamah tana cewa ta kira basa kusa. Wayar hannunta da maamah ta bata kuwa da komai akai,hasalima suna waya kusan kullum da momma bahijja,amma batasan me yasa number adda sabreen din kota kira sam sam bata shiga ba.




*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862

43

_Daga anas dan malik R.A yace:an rawaito daga manzon Allah S A W,ya 'yanta matarsa SAFIYYA,kuma ya sanya 'yantata din a matsayin shine sadakinta_

_bukhari da muslmin suka rawaito_



A step na biyu taga maamah din tana saukowa daga saman,hannunta cikin na haneefa daketa bata labari.

"Yammatana ya akayi?" Ta tambayi huda tana dan sake mata murmushin nan nata da kusan sun sana dashi.

"Baqo ne kikayi" Ta fada tana dan waiwayawa inda fu'ad ke zaune,hannunsa dauke da remote yana sauya tasha,bawai kuma don yanason kallon bane aah....sai don kawai bayason kallon fuskar maamah din sakamakon abubuwan daya tuna da suka motsa ranshi.

"Muje to" Ta amsata har qasan ranta tana jin dadin yadda huda din ta kasa gane wanene. Tanason sanyata ta koma daki don kada suyi wata magana da zata fahimci wayeshi a wajensu?,amma kuma ta rasa wanne uzurin zata bata tunda dai abinci zataci akan dining. Uwa uba kowanne motsi nata da maganganunta tana yinsu ne a ankare,bata bari tayi wani abu da zai sanya shakka a ransu ko ta gaza juyasu yadda takeso.

Tunda suka sauko din haneefa ta zubawa fu'ad ido. Tabbas shine mijin adda sabreen,ta ganshi har sau biyu bata kuma mance ba,sannan bata sake ganinsa ba sai yau.

Saman kujerar maamah ta zauna,haneefa ta zauna a gefanta still idanunta suna kanshi ta kasa daukewa. Sanda ya gama gaida maamah din sai nasa idanun suka sauka akan yarinyar. Kamanninta suka fusgi idanunshi sosai,ya sake ganin wata kamar ta daban bayan wadda ya baro dazu tana me komawa falo bayan sun hada idanu. Murmushi haneefa ta sakar masa sanda taga shima ya dan kafeta da ido. Ya murmusa kadan tana shirin janye idanunsa sai yaga ta zame tana fadin

"Ina kwana mijin adda sabreen?". Kallon mamaki yake bibta dashi,mamakin da bai gama sakinsa ba tace

"Sunana haneefa nice autan adda sabreen,'yar mitsisiyar dakinmu". Baisan ya akayi murmushi ya ratsa miskilar fuskar nan tasa ya bayyana ba,ashe masu son sarautar autancin suna da yawa. Yanayinta sak sai ya tuna masa da yanayin amna.

" Ya isa haka haneefa....kije kuyi break ko ki koma daki wajen nadra ku kalli cartoon" Maamah tayi hanzarin dakatar da tattaunawar tasu. A nutse ya cira kansa yana duban fuskar maamah din,haka kawai sai yaji yana da buqatar ci gaba da magana da yarinyar.

"Qyaleta muyi hira maamah....she's very smart" Ya fada da wani irin tone a muryarsa,wasu abubuwa da wani irin gudu suka fara bijiro masa,yayin da gumi ya fara tsargawa maamah ta cikin rigarta.

Ta sani,tafi kowa ma samin haneefa she's very smart,fiye ma da zatonta,wannan ya sanya tafi janta a jiki da kuma kaffa kaffa da ita.

"Indai surutun haneefa ne saika gaji dashi......ni kuma magana nakeso nayi dakai,next time idan kazo sai kuyi hirar" Ta fada tana dan hade rai gami da gyara zama.

Sake dubanta yayi a karo na biyu,abubuwa biyu suka hade masa waje guda. Har yanzu dabi'ar nan tata tarashin son yara tana nan?,banbanci qarara me kuma fadin gaske na farko tsakaninta da anni. Indai haka ne yara uku ne cikin gidanma kenan?,akwai daya a cikin daki?. Me ya kaita dauko yara har uku?,ita da basu dameta ba?. Meye abun damuwa don yana hira da yarinya qarama?.

Agogonsa ya kalla,sai ya maida dubansa ga fuskarta.

"Ba damuwa ai,yau muna da enough time sama da kullum". Kafin ya sake cewa wani abu haneefa tace

" Zaka kaini naga adda sabreen?......don Allah hamma kada kace aah" Ta fada tana narke murya. Maganar taja hankalin huda dake saman dining,itama saita ajiye spoon din abincin da takeci ta maido hankalinta kansu.

Gumin dake tsatsatsafowa maamah din ya sake yawaita,da sauri kamar ana tankadata tace

"Aah fa haneefa......ni da kaina mukayi zan kaiku haka ne?".

"Eh amma har yanzu baki kaimu ba maamah,shi kuma hamma ma daga can yake ko?" Ta maida tambayar kansa. Kansa ya gyada a nutse yana karantarta.

"Maamah ki barshi ya kaimu ko anjima ne,in yaso saimu dawo da kanmu" Huda itama ta saka baki,don da gaske sunyi tsananin kewar sabreen din.

Sanda ta waiwaya da nufin yiwa huda din magana sai maganar fu'ad ta dakatar da komai.

"Jeki dauki hularki kuzo muje nasa a ajiyeku" Yayi maganar kansa tsaye,maganar data daki tsakiyar kan maamah da wani irin ba zata.

Har ga Allah kanshi tsaye ya fada kuma hankalinsa kwance,kawai dai a cikin zuciyarsa ya dade da rashin aminta da kowanne motsi na maamah din. Bashi da gamsuwa akan abubuwa da yawa sa suka shafeta,shi yasa a kusan komai idanu da zuciyarsa suna akai.

Cikin qasa da minti uku sai gasu kowacce da mayafinta. Dab da zasu fita daga falon ta kirayi sunan huda da yanayin da tunda hudan tazo gidan bata taba gani cikin muryarta ko sautinta ba. Fuskarta a dinke ba fara'ar nan da suke kwana suke tashi da ganinta akan fuskarsu

"Kada ku wuce ko ina,daga can ko dawo gida,zanwa driver magana zai biyo bayanku,karku wuce awa daya......." Idanu huda tadan zuba mata,sai kuma kawai ta gyada kai mamakin sauyawar maman tana kamata. Tasha musu alqawarin fa zata kaisu.......sai kuma daga baya tace ai wani uzuri ne ya taso sai bayan wani lokaci,duk da ta lura akwai permanent driver a gidan da yake zaune baya aikin komai.

Yana zaune daga cikin motar saidai qafafunsa suna a waje ba'akai ga rufe masa murfin ba suka fito. Yadan daga kai ya kallesu,dukkaninsu suna kama da ita saidai qaramar ta fisu daukan kamanni sosai da ita. Mamaki kadan yana dan kamashi na ganin banbanci muraran tsakaninsu. Dukkansu da alama suna da sauqin hali da kuma tarbiyya sosai,don ba wanda ya gaidashi a tsaye a cikinsu saida suka rusuna

"Ta fita zakka kenan" Ya gayawa kansa da kansa yana sauko qafafunsa qasa ya fito waje.

"Abdulgaffar" Ya kirayi shugaban tawagar tsaron nasa,ya matso da gaggawa yana rusunawa

"A cire mota daya a sakasu a kaisu gida" Ya bada umarni hankalinsa yana kan kiran fareeda dake shigo masa. Kaman yadda baya gajiya da qin dagawa hakanan itama bata gajiya da kiran nasa,yaja wani dogon tsaki yana komawa motar,ranshi yana tsananin baci da kalar wannan kiran nata da dukkanin numbers dinsa,kamar wadda batasan abinda ya dace ba,baisan ma ya akayi take da dukka numbers din nasa ba.

"Soulmate" Sunan da tayi kiransa dashi kenan da wani irin salo na kashe murya da jan ra'ayi.

"Why?.....ke bakya gajiya da kira ne?,it's so annoying.....please don't do it again.....stop it" Ya fada da sautin bacin rai a muryarsa.

"Haba ka fahimceni mana" Ta sake fada da hanzari cikin tsoron kada ya katse mata wayar..... Kada ya ajiye wayar bayan ta samu dama ya daga wayar bayan dukka wahalar da tasha

"Na fahimci me?....ke bakya ganewa cewa macace ke?,ke ya kamata abi bawai kibi ba?.....kina mantawa mace da kamun kai aka Santa?.....". Da sauri take girgiza kai

"Indai a kanka ne bani da wadannan qualities din....."

"Okay....then karki sake kirana....." Yaja qaramin tsaki yana yanke kiran hadi da jan dogon tsaki yana wurga wayar gefe.

Gaba daya soyayya tana sake tona masa kanta a matsayin wani abu da yafi komai zama matsala da takura a rayuwa,shi yasa bazai bari ta kunno rayuwarshi yanzu ba har sai sanda ya shirya ya kuma kebe mata lokaci nayin nata.

Idanunshi akan motar BMW din da aka sanyasu a ciki,sai da yaga fitarsu a gidan sannan yayi musu umarni suka tashi motocin suna fita suma daga layin.

Sauke labulen window din da yake bata daman ganin farfajiyar gidan tayi cikin wata irin matsananciyar fargaba da kuma tashin hankali. Gaba daya kowacce idea tata ta kunce,ta rasa wanne zaren tunani zata kamo?.

Wacce irin baqar rana ce yau?,wanne tsautsayi ne qaddara ya sanyata lokacin shigowarsa ya kubce mata har ta saki yaran haka?. Idanunta ta mayar saman agogo......sai a sannan ta lura,yau ya sabawa lokacin shigowar tasa ne,ya shigo da wuri ba kaman yadda ya saba ba,sai tasa hannu tana sharbe gumin fuskarta da tafin hannunta.

Da dan hanzari ta taka da kanta tana fita farfajiyar gidan tana qwalawa mansir kira,kiran daya sanyashi sakin duk abinda yakeyi ya qaraso babu shiri.

"Ka fito da mota,kabi bayan motar jadda diamond zuwa gidan muhammadu......akwai yara da sukaje gaida matar gidan,suna shiga minti goma kacal ka aika su taso ka dawomin dasu......mansir?,idan ka kuskura aka samu akasi baka maidominsu akan kari ba to ka kuka da kanka......ban yarda ku biya ko ina ba......ban kuma yarda ka ajesu ako ina ba" Ta fada tana zare idanu tanaji a jikinta tamkar wani abu zai faru.

"In sha Allahu ba zaa samu ko daya daga ciki ba" Daga haka saita juya tana komawa ciki.

Kasa zama tayi ko a cikinma,a jikinta takejin kamar akwai wani abu da ba daidai ba

"Ki kira zuwaira kisa ta kula miki da motsinsu" Wani sashe na zuciyarta ya bata shawara.

Bibbiyu ta dinga hada stairs din tana haurawa samanta,cikin lokaci qanqani ta isa dakinta,ta zauna gefan gado tana daukan wayarta dake saman drawer ta fara kiran zuwairan.

Saidai kash!,kiran farko aka shaida mata kwata kwata wayar a kashe take,ta sake gwadawa cikin rashin gamsuwa da bayanin farko na na'urar......still sukace mata yana a kashe,ta sake dai gwadawa a karo na uku,nan dinma amsar dukka daya ce,saita ajiye wayar a gefanta tana jan wani matsiyacin tsaki

44

_Daga hassan dan sumra R A yace,daga manzan Allah S A W yace:Duk macen da waliyyai biyu suka aurar da ita ga maza mabanbanta a lokaci guda,to ita din mallakin na farkon ce(wanda aka fara daura mata aure dashi)_



"Tur da halinki zuwaira,Allah wadai da halinki" Ta fada tana cika tana batsewa,har cikin ranta tana jin kamar tayi tsuntsuwa ta tafi gidan da kanta. To amma kuma idan tayi duba ga wasu abubuwa,hakan bame yiwuwa bane,dole taci gaba da zama tana gwada kiran akai akai,yayi da idanunta ya ta'allaqa akan agogo tana qidanye da mintunan fitarsu daga gidan.

Daga qarshe ta sare kan samun xuwaira,to amma dole tana da buqatar kiran wani da zame zame mata garkuwa a can gidan

"Laila" Zuciyarta ta tunasar da ita.

"Yauwa" Ta fada da madaukakin zumudi,ta soma lalubar number wayar lailan.

Duk da safiya ce amma ta kusan awa guda da rabi a gidan nasu. Cikin asalin dakin da yake shine mallakinta,saman gadon sun qule ita da mahaifiyarta hajja harira wadda ta tsareta da idanu bayan ta gama zayyane mata karonsu da fu'ad na qarshe.

Sai da tayi kaman ba zata daina kallon nata ba kafin taja wani tsaki tana dauke dubanta daga kanta.

"To wai meye ma amfanin zamanki a gidan laila?,kada ki zama albasa mana wadda batayi halin ruwa ba?,na kaiki gidan badon kin rasa wajen zama ci sha ko sutura ko kuma gata cikin naku gidan ba.....na kaiki ne saboda ki karanci komai.....ki haddace komai ki kuma bi kowanne taku da motsi na kowa a gidan kafin mu fara gabatar da namu shirin koda kuwa.mariya batayi nasara ba......nasarar mariya ko faduwarta ba damuwata bane.....hasalima inda zata fadi hakan shine daidai a tare dani......kinsan me?" Kai laila ta girgiza tana jin faduwar gaba da kiran sunan maamah da akayi.

"Nasarata itace ya kamata ta fara samuwa......nasarata ita ya kamata ta fara wanzuwa kafin ta mariya........ni ya kamata na fara samun fu'ad na mallaka miki shi......muddin mariya ta rigamu samun fu'ad to ba shakka dukkan wata nasara da muka sanya rai a kanta zata iya zuwa mana da tsauraran hanyoyi da matakai......shan kai nake da buqata mu yiwa mariya laila.....donme kikaje kika kwanta kina bacci?,waye ya gaya miki nasara na zuwa ta sameka har inda kaka?,bakisan fita ake a nemota ba?!" Tayi maganar da alamun qunan rai a cikin muryarta,hatta kuma da lailan ta karanci haka,saidai batasan me yasa a kwanakin nan takejin sam bata da damuwa akan wannan lissafin na hajja ba......tamkar wannan lissafin an zare mata shi kwata kwata daga zuciyarta.

"Ban sauka ba hajja......kawai dai saina dinga jin kamar idan mukayi hakan bamu kyautawa maamah ba,kamar idan mukabi komai a sannu zaifi....." . Baki kawai hajja harira ta sake tana kallon laila da wani mamaki daya taru a fuskarta,kuma koda ta zubawa lailan idanu saita karanci da gaske take maganar. Tana shirin yin magana aka turo qofar aka shigo.

Madeena ce dauke da serving tray data jero dukka kayan dadin da aka dafawa hajjan a matsayin abincin safe. Tun asuba take tsaye don kawai ta faranta mata,kuma bata da tabbacin zata yaba ko kuma tayi accepting abincin gaba daya.

"Gasu hajja an gama....." Ta fada tana rusunawa ba tare data iya hada ido da ita ba. Wani abu me nauyi da girma ya riga ya sauka a zuciyarta game da zancan laila,don haka bacin ran daya taso mata maimakon ta huceshi akan laila sai ta fara ragewa akan madeena

"Wannan wanne irin iskancin banza ne?,ina ciki muna sirri da yarinya saiki wani bankowa mutane daki?". Murya a karye cike da ladabi tace

"Kiyi haquri,kin manta ke kikace idan na gama na kawo miki a daki zakici"

"Naji da Allah.....koma dashi ki aje saman table......tsnnnnn" Ta qarasa da tsaki.

"Awnnn..... Me dame kika dafa mata ne?" Laila tayi tambayar tana maida dubanta ga madeena wadda je tiri tirin fita da tray din. Ido kawai hajja ta zubawa laila tana mamakin yadda take nuna halin ko in kula da magana me muhimmanci irin wannan. Dawowa madeena tayi ta durqusa ta bude mata dukka bowls da warmers din,sai lailan ta karyar da wuya.

"Wallahi meat pie nake mugun kwadayin ci da safen

Please Login or Register in order to submit comment