Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Boyayyen numfashi ta sauke,sannan ta tattara hankalinta a kanta tana hade ranta tsaf

"Wannan duka ba huruminki bane.....kiyi abinda ya cancanci kiyi kawai" Sai ta miqe daga saman kujerar tana niyyar tafiya. Da sauri zuwairan ba tare da ta ji ciwon tsaidata a wata iyaka da tayi ba tace

"To ranki ya dade abincin fa?,yauma saidai a zubda?"

"Idan kina da buqatar ci kya iya ci ai" Ta amsa mata da gatse tana sauka daga step din idanunta yana sauka kan laila dake shigowa parlor din.

Sanye take da robber gown wadda tabi kowanne shape na jikinta ta lafe mata. Fuskar nan fes da kwalliya zaka rantse ba safiya bane ba. Ba komai a kanta sai wani qaramin bandana da bai rufe komai a gashin kanta ba. Wani mahaukacin tashin qamshi jikinta keyi,wanda turaren turare ne na musamman da aka tanada saboda wani mutum na daban.

Duk da fuska ko kuma jikinta ba wata kwalliya.....amma haka kawai ta fusgi hankalinta. Sassanyan kyan nan nata da baya buqatar kwalliya ko wani abu makamancin haka yana nan shimgide saman fuskarta. Haka kawai taji ta muzanta duk da kwalliyar dake jikinta,amma duk da haka sai taji ta raina kanta. Tashin farko wasu kalmomi na hajja suka dawo mata fes cikin kwanya suka qara mata azama da qwarin gwiwa. Muhammad jadda kawai take da buqatar gani,don haka taci gaba da shigowa falon tana jin izza tare da fatan ko yaya ta gwadawa sabreen wani abu da zai sosa ranta.

Kallo daya ta yiwa lailan ta watsar da ganinta a wajen,taci gaba da wucewa ciki ba tare data damu da kallon qurillar da laila ke mata ba. Ita sam bata ma dauketa a sunan damuwarta ba,damuwarta ta tsaya ne kan yadda yake neman maidata boyi boyin qarfi da yaji. Ta share masa sassa ta hada da wankin bandakinsa dama underwears dinsa,tana jin koda sama da qasa zasu hade ba zatayi wannan aikin ba. Lumshe idanunta tayi tana qara jin takaici yana cikata. Bashi da masaniyar hatta da girkin da take masa dole ce ta sanya take masa ba?,har wani qyashi da baqinciki ke rufeta gami da kasalar bacin rai duk sanda ta tsinci kanta dumu dumu a kitchen tana hidimar dafa masa abinci.

Dakinta kawai ta wuce bayan ta saqale masa key dinsa jikin qofarsa,tana fatan ya dawo ya samu sassansa da muqullansa a inda ya barsu.

Dining din laila ta wuce kai tsaye tana wani taku kai kace itace matar gidan,ranta ya cika maqil da kishi da hassadar sabreen din. Ko daga nesa ka hangosu sabreen din ta fita quruciya.......amma miskilancin yarinyar da shegen girman kanta mamaki yake bata. Bata taba mata kallo biyu ba....kai zata ma iya rantsewa sau daya ta mata nutsasten kallon cikin idanu Randa taso blocking mata hanya. So take ko yaya taga wutar kishinta a idanunta,to amma kullum suka hadu tana yin kamar babu aka kawo gidan aka ajiye ba dan adam ba.

"Ma aka dafa?" Ta tambayi zuwaira Kai tsaye tana latsa wayarta sanda zuwaira ta kusa gama kwashe warmers din.

"Sai yanzu Allah yayimin tashi,don haka saiki jira na gama da aikin matar gidan tukunna" Zuwaira ta gaya mata gatse gatse gami da satar idanunta ta gasa mata harara. Kullum ta tuna warning da kuma jan kunnenta akan ta yiwa yarinyar biyayya da hajiya mariya da hajja uwar yarinyar suka mata akan tabi yarinyar sau da qafa bama matar gidan ba.....sai taji kamar ta zabge yarinyar da mari.


*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862


5ØÜ 5ØÜ 5Ø
Ü 5ØÜ 5ØÜ 5ØÜ 5ØÜ 5ØÜ
_Zafafabiyar_

6B6O6O6K 62

g,D² D¥ ³

5ØKÞ5Ø<Þ5ØBÞ5Ø@Þ 36


_An karbo daga abu hurairah Allah ya qara yarda dashi yace,manzon Allah S A W yace,idan miji ya kira matarsa zuwa shimfida taqi zuwa,mala'iku zasuyita la'antarta har gari ya waye_

*_qarqashin wannan hadisin akwai qarin haske,idan a wannan qin da tayi kuma ta samu ciki koda ta rasu wajen haihuwa wasu malamai suna ganin bata samu wannan shahadar da mace me naquda ke samu ba idan ta rasu_*



36


"Ki gaggauta da Allah.... Am starving,ko ki bani wannan da kike debewa in fara dashi"

"Sannu akuya......" Zuwaira ta fada a ranta,amma a fili saita ajiye mata warmer din tana cewa

"Zaki iya ci mana.....amma kafin kicin ki fara sanarwa tsohuwarki gudun maida laifi a kaina" Ta fada dadan zafin rai. Haka kawai sai laila tasha jinin jikinta,don haka ta miqe tana sauka daga wajen

"Fresh nakeso.....kada ki wuce minti talatin" Bata ma iya amsa mata ba ta dauke ragowar warmer din tana wucewa kitchen din gami da jan tsaki qasa qasa.

Tafiyar minti arba'in da shida ta sadashi da mansion House din alhaji hamza kibiya. A qofar tafkeken gate din dake qara nuna alfarmar dake cikin gidan motocin suka tsaya bisa umarninsa,don yanaso ne ya gaida anni ya fito......ya kuma haida maamah din sannan ya wuce office din. Akwai cushewar ayyuka sosai yau din bisa schedule din da saddiq dinsa na yau da saddiq ya tura masa tun jiya da dare,wannan ya sanyashi fita da wuri. Wani irin qarin investors suketa samu a dukka kamfanoninsu,duk da yana yin komai bisa kula don ya tabbatar akwai mutanen dake bibiye dashi,kuma nasararsa a wancan lokacin yayi imanin ta tarwatsa musu dukka shirinsu..... Faduwarsu kuwa da shurunsu yayi amannar bawai suna nufin komai ya wuce bane.

Gidane dake cike da tsari,da kuma kusan duk wanda yake gidan bisa tsari da sanin ya kamata yake zaune. Kowa yasan aikinsa,tun daga kan security guards da sauran masu aiki na cikin gida dama farfajiyar gidan,hakanan bayin Allah da suke daukan nauyi dake wani sashe daban na cikin gidan me kama da qaramin estate kowa bisa tsari da sanin ya kamata yake.

Duk girman gidan ko.ina fes yake da wani irin tsafta da qamshi. Ya zuqi qamshin har cikin hunhunsa sanda yake zama saman sofas na qaramin falon anni da mutanen da suke mafi kusanci da ita ne kadai ke iya haurowa har nan. Ba abinda ke saukar masa da nutsuwa kasala gami da tayar masa da wnai Tsunammen feelings irin qamshi. Duk sonshi da qamshin wannan ya sanyashi haqura dashi kan bedsheets da duvet nashi da pillow,wanda muddin ya kwanta akai da qamshi irin wannan to zai wahala bai kwana cikin wahala ba,ko kuma ya tashi da mafarkin da zai wajabta masa wanka kafin yakai ga sallar asuba.

Normally yanaso kowanne kusurwa na inda zaiyi mu'amala dashi ya zama kaman haka,sai ya lumshe idonsa kafin ya budesu sanda yaji sallamar anni.

Da dogon hijabin nan nata har qasa ta shigo wanda ke alamta masa sallar walaha take ya tasota. A wajenta ya koyi sallar walaha,tun yana yi yana fashi batabi jininsa ba har takai ya saba,ko a ina yake,kome kuma yake yi sai ya katseshi yayi,saidai idan abubuwan sunsha kansa ko sunfi qarfinsa ba yadda zaiyi.

Fuskarta shimfide da kararramammen murmushin nan nata ta qarasa shigowa,tayi bismillaha tana zama saman kujerar abinda ya sanyashi zamowa daga samanta yana gaidata.

"Tashi ka koma ka zauna" Tace dashi don ba kasafai yake iya zama saman kujerar ba idan suna kai ko ita ko abbansu,harma da maamah din kanta.

Kai ya girgiza yana tanqwashe qafafunsa saman carpet kamar qaramin yaro

"Nan ma ya isa anni.....akwai kunun tsamiya?" Kai tadan daga tana dubansa. Batayi tsammanin zai qara tambayar abinci ba sam sam daga wajenta,don kuwa a yanzun magidanci sunansa,saidai kuma ta masa uzuri,don tunda akayi auren bai taba neman komai ba,don haka tace dashi

"Akwai.....kasan dole ne kullum sai an yiwa abbanku.....har yanzu gargajiya taqi barinku,bari nasa a kawo maka" Ta fada da murmushi. Shima tsadajjen murmushin nan da kusan annin tafi kowa ganinsa a duniya ya sake


"Anni akwai abubuwa masu muhimmanci me tarin yawa a gero,inda mutane sunsan meye gero anni da kusan duka mun koma cinsa". Murmushi ta kuma yi tana miqewa gaba daya

"Gaskiya mana naga kun qulla kyakkyawar alaqa da fura.....nikam wannan traditional doctor din naka ya sake canzaka gaba daya" Murmushi kawai ya saki,shi kansa ya sani kalar cimarsa ba iri daya bace data kowa,sau tari a wani taro ko a sanda ya buqaci cin abinci da baqinsa na Africa ko nan Nigerian,sukan cika da mamaki idan sunga kalar abincin da yake ci.

Da kanta annin ta shiryo komai saman tray,harda qarin lafiyayyen qosai da kuma farfesun kan rago da yasha kayan qamshi tafarnuwa da wadatacciyar albasa. Akwai abinda takeson ta karanta a tattare dashi a fakaice a matsayinta na uwa bawai kai tsaye ba. Tun daga ranar da amna ta gaya mata zaunuwar zuwaira a gidan ko sau daya bata taba hutawa da tunani ba. Ta kasa aminta hakanan ta kasa gamsuwa. Fu'ad dan maamah ne halak malak,duniya ma ta shaida hakan,saidai tana jin bai kyautu tabar mata rayuwarsa ba,rayuwar da aka fafata aka sha fama kafin fara daidaituwar komai a cikinta. Allah shine ya raya muhammad fu'ad din,amma kuma itace sila,tasha fama qwarai da gaske,faman da har batason tunawa,faman da shine ya zama silar shaquwa tsakaninsu me yawan gaske. Har batason tuna wahalar da tasha dashi kafin cire shi daga depression daya samu kansa a ciki.

Tana shigowa ya miqe,bai barta ta qaraso ba ya isketa a hanya ya karba tray din ya qaraso dashi. Sanda yake shan kunun a nutse yana kuma cin qosan tana zaune a gabansa tana karantarsa,tana jin zuciyarta na matsewa,ta kuma damu tayi masa maganar dake qasan ranta,duk da haka tayi jarumtar sanda ya kammala sannan a tsanake tace dashi.

"Muhammadu...."

"Na'am anni" Ya amsa mata a nutse yana jin wata nutsuwa da qoshi na musamman yana ratsa cikinsa.

"Nace anya yarinyar nan basai an taimaka mata da qarin masu aiki ba?,gidan nan sai nakega ko masu aiki nawa aka zuba masa yana buqatarsu ko don sauqaqawa matar gidan,duk da yake kai baka fiya son mu'amalar masu aiki ba cikin sha'aninka". Murmushi kadan ya saki,baisan wanda a duniya ya sanshi sosai ya kuma karanceshi tas sama da anni ba.

"Kiyi duk yadda ya dace anni......" Ya bata amsa cikin girmamawar data sake sanyata ta jishi a ranta sosai.


*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862

5ØÜ 5ØÜ 5Ø
Ü 5ØÜ 5ØÜ 5ØÜ 5ØÜ 5ØÜ
_Zafafabiyar_
6B6O6O6K 62

g,D² D¥ ³

5ØKÞ5Ø<Þ5ØBÞ5Ø@Þ 37


_Daga ibn juhaim bin haris RA(wannan sunan sahabin annabi ne=ØÞ),yace:Manzan Allah S A W yace "da me wucewa ta gaban me sallah yasan abinda yake kansa na sabo,tabbas da ya tsaya(ya jira me sallahn ya gama)tsahon gwargwadon shekara arba'in shine yafi masa alkhairi akan ya wuce ta gabansa_

_Bukhari da muslim ne suka rawaito_




37


"Da ina tunanin na tura mata ma'u da maigidanta malam ibrahim.......zataji dadin zama da ma'u sosai.....ina kyautata zaton haka,malam ibrahim kuwa koda kana da ma'aikata da sauransu zakaji dadin zama dashi in sha Allah".

"Anni ki zartar da komai da kike ganin ya kamata......ba buqatar sai kin gayamin anni" Ya sake fada har a zuciyarsa yana jin annin ta isa ta zartar da komai din.

Kai ta jinjina tana dan murmushi,har qasan ranta tana jin dadin yadda ya bata girma da kuma dama,duk da cewa tasan cewa abune me wahala ya musanta akan duk abinda tace din. Har bakin parlor na biyu tayi masa tattaki,bakin ta fal cike da addu'ar data zame mata dole,kowacce rana dukkaninsu su hudun basa kaucewa samun kyakkyawar addu'arta da bata gajiya da binsu da ita.

Qafarta daya saman daya take zaue cikin qawataccen parlor din nata da idan ka kirashi kai taaye da aljannar duniya bakayi kuskure ba,duk da ita a nata ganin sam har yanzu bai kai matsayin da take buri tsari da kuma mafarkin yakai ba.

Dukkan hankalinta ta baiwa zuwaira dake zayyane mata jawaban da muhimmancinsu a wajenta ya wuce kimar komai data mallaka a duniya. Jawabin dake da wani irin kima tamkar ta zinare a idanunta. Duk da bayanan ba abinda suke haifar mata sai wani irin tashin hankali. ba irin bayanan da take buqatar taji kenan ba.....amma duk da haka suna da muhimmanci a wajenta,don sune zasu zame mata tamkar tsani kuma fitilar da zata haska mata matakalar da zata taka zuwa matakin gaba.

"Amma fa tana qoqarin ganin ta aiwatar da aikinta......saidai ban hangi wata shaquwa soyayya ko kusanci da junansu ba ko kadan"

"Wannan kuma aikinta ne......ita kuma ya kamata ace ta fara samar da wannan dangantakar a tsakaninsu......a nan gazawar tata ta fito.....ta kowacce hanya ya kamata ta yaudari zuciyarsa har ya aminta da ita ya miqa mata wuya.......aikinki yana kyau zuwaira,ina buqatar magana da ita yanzun nan kafin na yiwa tufkar hanci tun daga tushiya"

"Yanzun zan sadaki da ita uwar dakina" Zuwaira ta fada cikin karsashi gami da jin dadin lambar yabon data samu.

Batasan adadin sau nawa ta duba agogo ba tana zaman jira da dakon kiran zuwaira. Qaguwar da tayi ya hanata jira zuwairan ta kirata ta maida kiran zuwa wayarta.

Ya shiga a daidai kuwa,sanda take rusune daga bakin bedroom din sabreen tana qoqarin fahimtar da ita amfanin kiran.

"Ina jinki kamar d'iyata ko jikata....ki daure ki saurareta,taqi kadan zai rage ku rabu in sha Allah". Duk bata gamsu da matar ba,duk da batajin nutsuwa da matar ko kalamanta,amma a ciki akwai abinda takejin gaskiya ne,a ciki akwai abinda takejin da gaske ya kusa tabbata din TAQI KADAN YA RAGE SU RABU.

Hannu ta saka ta karbi wayar,sai ta tura qofar bedroom din ta rufe ta koma ciki. Tana takawa cikin idanunta suna kan fuskar wayar,yau din a matuqar tunzure take,so batason wani magana da zata sake hasala hali da kuma yanayin da take ciki.

Gaban madubinta taja stool ta zauna,sannan ta kunna wayar ta sakata a hands free ta dorata saman madubin,sannan kuma a hankali ta maida idanunta saman fuskarta kamar me kallon maamah din zaune a gabanta.

"Ina jinki" Ta furta a nutse yana goye hannuwanta a qirjinta.

"Ina fata kina cikin lafiya da kuma aminci qarqashin kulawar d'ana?" Tayi maganar a nutse tana son kamo bakin zaren ainihin maganarsu. Kamar ba zata amsa mata ba,sai ta daga idanunta daga kallon dogayen yatsunta da gaba daya lallen da akayi mata na aure ya fice tas,tamkar ma ba'a taba digawa yatsunta lalle ba,ta maida oily eyes din nata cikin madubin daya bayyanar da fuskarta dinnan me shimfidadden kyau dake dauke yau din da wani irin kwantaccen fushi. Zubawa fuskar tata idanu tayi kamar yau ta fara ganin kanta da kanta,iya kallon kawai yana motsa zuciyarta gami da tuna mata a karan kanta wacece sabreen,wani sashe na zuciyarta ya motsa yayi aikin daya jima baiyi ba,taji wani abu ya darsu a zuciyarta wanda ta jima tana yunqurin daddago dashi amma yana komawa

"Ki ajiye wannan a gefe.....yaya jikin huda?" Tayi mata tambayar da take kwana da ita tana tashi ba tare da tasan waye zata yiwa ita ya kuma basu cikikkiyar amsar da take buqata ba.

"Jikin huda?.....alhamdulillah......saidai ban da tabbacin yadda ya kamata ya kasance". A hankali ta lumshe idonta tana son yiwa amsar tambayar tata fashin baqi. Bugun zuciyarta yana son ninka gudunsa saboda samun mabanbantan amsoshi daga mabanbantan lunguna da saquna na zuciyartata wadanda basuyi daidai da fatanta dama abinda takeso taji ba.

"Mu ajiye wannan......zan dan yaba miki game da yadd kike qoqarin ciyar dashi abinda muka baki,saidai har yanzu kin gaza cimma manufar abinda kikeyi din......caring kulawa.....ba wata halitta da batasan kulawa.....dole ki fara samun zuciyarsa kafin ki samu cikinsa da jikinsa....."

".......ba wannan cikin jarjejeniyarmu.......wai shin..kina zaton ina da buqatar zuciyarsa?,ko ina da buqatar hanyar da zata sadar dani ga shiga zuciyarsa?". Tayi maganar kanta tsaye da wani irin tsauri,saboda zafi da a yau zuciyarta keyi mata,tana jin kamar wani abu me kama da gajiya da kuma fara jin takura yana mintsinin zuciyarta.

Murmushi me sauti maamah din ta saki tana gyara zamanta

"Bana fatan ki samu zama ko shiga zuciyarsa na dindindin,a taqaicema dai....banda yanayi irin na lalura banjin kinkai quality din da zan baki license na shiga zuciyar mutum me tsada,namiji irin muhammadu ba.....amma karki manta,dole ne ki sadaukar masa da komai don isa ga burinmu.....idan nace komai ina nufin komai da komai fa,na zabeki ne saboda ina da tsammanin zaki iya bada komai don cikar muradina.....koda kuwa jikinki ne...."

"Ya isa!" Ta furta a tsawace saboda jin maganar tata ta fara shallake guri,uwa uba tana neman fin qarfin kanta.

"Kibi a hankali......a yanzun duk da ban mallakeshi ba,amma zakisha mamakin abinda zai biyo baya idan har na shaida masa matarsa tana min shouting tana kuma dagamin murya....." Zafin radadin maganarta ta farko bata saketa ba,don haka bata maida hankali sosai akan maganarta ta biyu ba. Burinta shine ta furzar mata da abinda yake ranta,tana jin kamar takai maqurar da zasu dinga wasan tamaula da ita tsakanin ita da d'anta.

"Zanci gaba da ci dashi kaman yadda iya abinda yake zayyane kenan a bisa yarjejeniyarmu......daga hakan banajin zan qara akan komai.....faduwarki ko nasararki ya ta'allaqa ne da yadda na samu tabbacin lafiyar qannena" Daga haka ta katse wayar kawai tana ajeta a gefe.

Taso tayi tariyar maganganun da sukayi da maamah din,amma a yau sai taji gaba daya bata da buqatar tuna komai.....kawai tana jin ba zata iya ci gaba da zamowa kamar tamaula tsakanin su ba. Wani irin confidence takeji,saita miqe tana komawa bakin qofar da zummar ajewa zuwaira wayarta,ta dauka duk sanda ta dawo,don ko haduwa da ita bata sonyi. Ga mamakinta a tsaye ta sameta a bakin qofar kamar wadda aka bawa gadinta. Wani kallo ta jefeta dashi tana jin sam matar bata mata ba

"Ba wani abu da ake buqata?" Ta fada da sauri bayan ta karbi wayar ganin sabreen din na zummar shigewa ciki

"Babu" Ta bata amsa a taqaice tana maida qofarta ta kulle.

Yadda yau yarinyar ke amsa mata magana a tsaitsaye sai takejin kamar akwai abinda ta taka,akwai abinda ya bata confidence a kanta. Ci gaba tayi da juya wayar a hannunta tunaninta yana yin nisa gami da rarrabuwa kashi kashi. Wani tunani ya kutso mata cikin kwanyarta

"Me yasa ba zaki murza kambunki ba?,ki gwada qarfin iko da mulkinki ba har akan fu'ad din?" Wani sashen na zuciyarta ya bata shawara. Shuru tayi tana sauraren daya bangaren tare da juyar maganar cikin kwanyarta. Kai ta gyada tana bawa kanta tabbacin tabbas wannan din zaiyi aiki.....koda baiyi diki dari bisa dari ba to akwai yiwuwar samuwar galaba.

Tana qoqarin kiransa ta shaida masa tana buqatar ganinsa sallamarsa ta mamayeta. Tana amsa sallamar farinciki na cika zuciyarta yadda Allah ya dubeta ya jefo mata shi,saidai a saman fuskarta ba haka bane. Ranta yana hade,hakanan ta boye duk farincikinta don tanason ko meye zata gaya masa ya daukeshi da muhimmanci.

Sai daya iso gabanta ya zame yana gaidata ta hanyar tsugunawa saman qafafunta. Bayan ya gama gaidata din shuru ya biyo baya,a nutse yace

"Ba komai da ake buqata?,ba wani matsala?" Yayi tambayar data zame masa wajib duk sanda yazo gaidatan don qoqarin sauke haqqin Allah da yakejin ya zama wajibi ya sauke din.

Kai ta girgiza fuskarta a daure.

"Ba abind nake buqata.....amma matsala dai akwaita". Daidaita tsugunnonsa yayi kafin ya zame ya zauna sosai a gabanta. Duk sanda tayi wannan yanayin kota furta magana makamanciyar wannan zai wahala idan ba wani aikin bane zaya zameshi. Idanunsa yadan lumshe gami da budesu duka lokaci guda cikin qoqarin hadiye fargabarsa,yana tunkarar qalubale komai girmansa.....gaagwarmaya komai wahala da kuma taurinta,amma har yanzu zuciyarsa baya iya jure wadannan halayen da maamah din,dabi'unta suna kassarashi,ya kasa sabawa,baisan me yasa ba,ko don ita dinn wata jigo ce da abubuwanta ke tafiya ba yadda ya kamata ace sun tafi ba?.

"Wacce matsala ce?,me yake faruwa?" Ya tambayeta a nutse.



*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862
5ØÜ 5ØÜ 5Ø
Ü 5ØÜ 5ØÜ 5ØÜ 5ØÜ 5ØÜ
_Zafafabiyar_

6B6O6O6K 62

g,D² D¥ ³

5ØKÞ5Ø<Þ5ØBÞ5Ø@Þ 38


_Daga abi sa'eed RA yace:manzan Allah S A W yace; "idan dayanku yazo masallaci,ya duba takalminsa,idan akwai qazanta ya shareta ya kawar da ita daga jiki,yayi sallah da takalminsa_

*_halal ne sallah da takalmi a qafa,na haramci a ciki muddin ba najasa a jiki_*


38


"Muhammadu" Ta kirashi da ainihin sunansa,ba tare kuma data bari ya amsa ba ta dora

"Nikam bansan a rayuwa akwai wani abu da yafi haihuwarku da nayi muhimmanci ba" Idanu ya zuba mata yana jin tamkar ya tashi ya fita da gudu ya tserewa maganganunta,don yasan zai wahala ba kamar kullum bane,dora masa nauyi da mas'uliyyar da zai gaza dauka kota masa tauri. Kai ya girgiza,ya buda baki zai magana ta sake danneshi da kalamanta

"Bansan wanne irin rashin muhimmanci nake dashi a rayuwarku ba da har zan zartar da hukunci cikin rayuwarka,nace kum ga alfarma ko abinda nakeso kayimin ka gaza yi din,ace har yanzu maganganun ameenatu da umarninta yana zama gaba da nawa?" Ta qarashe maganar tana jin dacin haka sosai har cikin zuciyarta. Batasan wanne tozarci ma ya kamata ameenatu ta fuskanta ba aduk sanda haqanta ya cimma ruwa,har yanzu idan tayi hasashen abinda zata saka ta fuskanta sai taga wannan hukuncin yayi kadan.

Sam baya qaunar ta dinga sanyo maganar anni cikin maganganu da ayyukansu,don bazai iya tuna sanda anni ita tayi magana a kanta ba indai ba alkhairi ba.

"Muhammadu.......yanzu ni da hannuna na baka amanar yarinyar mutane......na roqeka ka mu'amalanceta kamar kowanne miji da mata.......ka kyautata mata ma faranta mata,ka jata a jiki amma haka ga gagara?,ka kasa cikamin wannan alfarmar da zata bayya a irin kima da martabata a idon yarinyar?". Qasa yayi da kansa,shi maganar ma nauyi tayi masa sosai akai. Ta wani gefen kuma ranshi da zuciyarsa suma motsa. Yanzu har taurin kan yarinyar da tsaurin idonta yakai ace ta kawo ma maamah qararsa?,har da maganganu irin wadannan marasa dadin ji?. Sai data gama dukkan wani fada baice komai ba,har sai da tayi shuru sannan yace

"Kiyi haquri,in sha Allah za'a sake yin qoqarin gyarawa da canzawa". Ya furta a taqaice. Har cikin ranta yadda ya amsa mata haka a sauqaqe ya faranta mata sosai

"To Allah yayi albarka" Ta fadi kalmar da bazaice when last da yaji ta fada ba. Muryarsa a sanyaye ya amsa mata,sannan ya miqe yana mata sallama yana fita daga falon.

Tun kafin ya qaraso Jordan ya wangale masa qofa,da wani irin zafi ya isa ya shige motar Jordan ya maida murfin motar ya rufe. Suit dinsa na

Please Login or Register in order to submit comment