Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

regular customer ne suka yi ciki, tana kuka ya cillar da ita a tsakiyar ɗakin
"Meyasa kake min haka? Yaya Mukhtar kaji tausayi na mana... Am not a slav..."

"Will you shut up! In ji wa yace u r not my slave? Ko baki san duk mace baiwa bace a gidan miji? Oya come and remove this clothes for me zan yi wanka"

Miƙewa tayi gudun kar ya kara taɓa lafiyarta taje jikinta na rawa ta cire mishi, hannunta ya ja suka yi toilet wankan ma ita ya saka tana kuka ta mishi, yace tayi nata ta same shi yanzu.

Haka tayi don miji irin Muktar ta fahimci in tace zata ke musu dashi watarana kakkarya ta ze umminta ce kuma da asara.

A daren ma be barta ba ta sha wahala kwarai a wurinshi, haka ya zube ya cigaba da bacci ta miƙe da kyar ta shiga bayi ta gasa kanta da ruwan zafi, ta fito da alwala, akan sallaya ta tsaya tana sallah tana kuka, anya suna da rabon farin ciki?
Sai kuma ta tuna maganan umminta

"Fatima tun da nayi sallama da ƙasata na shigo wannan na san nayi sallama da farin cikin rayuwa, na fuskanci kalubale iri iri da damuwa kala daban daban kan Allah ya haɗa ni da mahaifinki ya maida ni tamkar sarauniya ya bani duk wani farin ciki da na rasa a baya amma shima Allah be bar min shi ba, tafiyar shi ga rabbissamawati ya sarar dani, na ɗauka nima zan bishi a kowani lokaci amma tunda na tsallake baƙar wahalar da na sha daga rasuwarshi zuwa haihuwar ki na sa a raina cewa komai ze zo ya zama tarihi, iko na rabbi ne kawai dawwamamme, na sa a raina zan raineki kila sirrin farin cikina na gareki, sai kuma gashi yadda kema Allah yayi dake.

Dukda haka ban sare ba, kema ina me karfafamiki gwiwa da kwantar miki da hankali a kan cewa in shaa Allahu zaki wayi gari kiga duk wannan sun wuce, imani da yaƙini akan ubangiji yana riskar da bayi zuwa ga magantuwar matsalolinsu, wallahil azeem ubangijinmu na sane da lamuranmu kuma ina da tabbacin wata rana ze fidda mu daga cikin wannan jarabawa, ko ban riski lokacin ba in shaa Allahu wata rana zaki yi farin ciki, zaki yi murna zaki tuna kuma da cewa na faɗa miki hakan"

Hawayenta ta share ta zurawa muktar ido, kila watarana shine ze zama farin cikinta, kila kuma karshen zaman su na iya zuwa ko kusa ko nesa, amma ka fin nan tayi alkawarin yunkuri wurin chanza shi, zata kasance me yi mishi Adu'a a ko wani motsinta zata taya mahaifiyarshi yakin mai dashi mutumin kirki da yardar Allah ko da kuwa ita baza ta samu ribar komai ba.

Anan kan sallayan tayi bacci da asuba ma jin mutum kawai tayi ya ɗauke ta zuwa gado, bata mishi tirjiya ba ta hakura saide fuskanta be huta da ruwan hawaye ba don ba daaɗin abun take ji ba banda azabar ciwo, seda ta sake wanka na ruwan zafi sossai tayi na tsarki ta fito tayi sallah, yana kwance yana bacci, a hankali ta matsa kusa dashi ta sa hannu ta na ɗan bubbuga kafafunshi
"ya Mukhtar! Ya muktar ka tashi kayi sallah don Allah, lokacin sallah na wucewa"

Ko motsi be yi ba, da ta matsa mishi ya ja dogon tsaki tare da kaiwa hannunta harbi da kafa da sauri ta ja baya ya samu iska, tagumi ta zuba tana kallonshi har bata san sadda bacci ya kwashe ta a wurin ba.

Sai misalin karfe goma ta tashi, yunwa ne ke dawainiya da ita kuma har lokacin bacci muktar ke yi, idanu ta zuba mishi tana aikin kallo, da zai shiryu muktar ba karamin kyau yake dashi ba, tana nan tana kallonshi tana sake-sake, ya buɗe idanu.

"Wani maitar ne kike yi da zaki tasani a gaba kina kallo haka?"

"Ba komai, ina jin yunwa ne"

"Ni zaki cinye kenan sai ki koshi?"
Da sauri ta girgiza kai, tsaki ya ja kan ya sauka seda ya tsaya wurin landline yayi call kan ya shige bayin, tana nan zaune har ya fito yayi wanka sede ya maida kayanshi ne don shima babu komai nashi anan ɗin, tsayawa yayi da niyyar sallah kaman kar tace komai sbd tsoron shi sai kuma tace

"Ya Mukhtar namiji fa daga cibiyar shi zuwa guiwowinshine al'auranshi, Kaga zaka yi sallah kuma wandon be kai guiwa ba be kamata ba"
Ta faɗa a tsorace

"karki karɓa in nayi" ya faɗa yana jan tsaki tare da tada Sallar shi ita dae ta san sallahn nan kam se a hankali karfe sha ɗaya sallahn asuba sannan da gajeren wando.

Knocking aka yi ta miƙe ta buɗe, tray ne me ɗauke da abinci kala uku da ruwa da wani energy drink, karɓa tayi ta zo ta ajiye ta zauna jiranshi har ya idar ya juyo.

"Ɗauki abin da zaki iya ci"
Ya faɗa ba tare da ya kalleta ba.

Shinkafa jollof ta ɗauka da ruwa, ya ja sauran, tana ci tana satan kallonshi ga mamakin ta ya cinye duka abincin trayn nan bata ma yi rabin nata ba, energy drink dinshi yake sha sai wayanshi ya fara ringing don yanzu ya kunnata, dubawa yayi ganin Maami yasa ya ƙi dagawa kiran duniya ta mishi ya ƙi ɗauka, chan kiran Alhajinsu ya shigo mishi kaman kar ya ɗauka ba sai ya ɗaga.

"Muktar ina ka kai ƴar mutane Maaminka ta kasa natsuwa? Kana so sai ka tayar mata da hawan jini ko?"

"Dad naga dae matata ce, me nata?"

"Ka amsa mini kuna ina? Taje gidan ku bakwa nan"

"Hotel"
Ya faɗa yana haɗe rai.

Ita dae tausayin Maami ne ya rufe ta ta san duk don ita ne hankalin Maamin yake a tashe, a hankali tace
"ya Mukhtar ka bani Maamin zan yi magana da ita don Allah"

Harara ya zabga mata kan yacewa mahaifinshi da ya gama ce mishi su dawo yanzu
"gaskiya ba zan dawo ta rabani da matata ba, ni ban rabata da mijinta ba haka kawai"

"Don Allah yaya Mukhtar"

Wayan ya jefa mata har yana dukan kirjinta ta dauka tana gaida Alhajin cikin girmamawa ya amsa yana tambayar lafiyanta tace da sauƙi Maamin na kusa?

muryar Maamin ta ji tana cewa
"Fatima? Kina lafiya kam?"

"Lafiya ta ƙalau Maami, eyaa Maami ki mana alfarma ki kwantar da hankalinki kinji don Allah, in sha Allah babu abunda zai faru"
Ta faɗa a karye cikin son karfafawa Maamin gwiwa, Maamin da taji hawaye na son zuba mata ne tace

"Fatima ki yafe mana mun kuntata miki rayuwa"

Girgiza kai tayi tana share hawayen da ya zuba mata
"ko ɗaya Maami idan da ba don auren ba ai da ban sanki ba, amma yanzu na sameki bayan Ummina babu abin da ya kai hakan farin ciki a gare ni"

"Ki bashi wayan"
Maami ta faɗa, miƙa mishi ta yi.

Karɓa yayi yana kau da kai daga kallonta yana taɓe baki
"Ina kwana?"

"Baka damu da kwana na ba ai muktar da ka damu da ba haka ba, ka ɗauki yarinyar nan ka maida ta gidanta ka bar Hotel da ita, sannan ka tabbatar ta cigaba da zuwa makarantar ta ranar Litinin"

Tana kai nan ta kashe wayan, hawayenta ta share Alhj dake tsaye yace

"menene kuma ne Maamin su? Ina dae yarinyar nan tace miki babu komai ki rabu da ita da mijinta mana"

Cikin takaici ta kalle shi tace
"Zurfin tunani da tarin tarbiyar da yarinyar nan take dashi she's too good for muktar wallahi"
Tana kai nan ta miƙe ta bar mishi ɗakin.

Su kuwa bayan ya ajiye wayan ya taɓe baki yace
"Maami matsala"

"Subhallah"
Ta ambata chan ƙasa, ba don tana tsoron yin magana ya zama laifi ba da tace yayi saurin tuba da wannan kalma da ya je fi mahaifiyarshi dashi in har yana son rabauta duniya da lahira iyaye ba abin wasa bane amma inaa.

"Ke! Tashi mu tafi"

Da sauri ta miƙe tabi bayanshi, a cikin harabar gidansu yayi parking, ajiyar zuciya me karfi ta sauke ko ba komai zata je ta samu tayi magana da Mahaifiyarta, bata jirashi ba tayi ciki zuwa ɗakinta ta ɗauko wayanta ta fara turawa ummi text message.

"Alaya ina kika shiga kwana biyu nayi sako shiru babu amsa? Kina lafiya dae ko? Ko ciwonki ne ya tashi? Ina ma ina da bakin kiranki in ji muryarki don tabbatar da lafiyanki... Don Allah kar ki min karya baki da lafiya ko?"
Kuka ta fashe dashi a fili tace

"Ummi bani da lafiya, ummi bana son wannan aure bana son shi, mugu ne, ummi marar tsoron Allah ne, bashi da ibada be san menene addininshi ba, ummi abubuwan da nake son faɗa miki kenan amma ba zan iya ba..."

Typing tayi
"na ɗan yi rashin lafiya amma da sauki Maami ta kula da komai yadda ya kamata"

"Subhallah ya jikin? Allah ya sakawa Maami da alkhairi"

"Alhamdulillah ummi babu komai yanzu, Ameen thumma Ameen kefa ummi? Babu wani damuwa? Su Hajiya Zeenat basa takuraki? Aiki be miki yawa ba ummi?"

"Babu wani matsala Alayah, Allah ya baki lafiya"
Tattaunawa kaɗan suka kara taji an turo kofan, da sauri ta ɗaga kai ta kalleshi..

"Ina da baƙi da dare ki shiga kitchen ki shirya musu abinci"

A hankali tace
"Toh"
Har ya juya ya ce
"Ki tabbatar mutane akallah ashirin zasu ci su koshi"
Yana kai nan ya fice, bata kawo komai ba bayan tayi la'asar ta shiga kitchen dinta Allah ya sa tana jin karfin jikin nata sossai Alhamdulillah, sossai ta zage tayi girkin har kala biyu jollof nd fried Rice pepper chicken sai ta ɗan yi snacks ta haɗa fruit drinks masu daaɗi, dab Magrib ta fito daga kitchen din wanka ta sake da alwala ta zo tayi sallah, ta jima tana karatun alqur'ani da rokar wa kanta mafita a wurin rabbisamawati har aka yi isha ta tashi ta gabatar kaman wasa tana zaune nan ta soma jin hayaniya a ranta take ayyana baƙin sun zo kenan.

Bata gama nazari ba ya shigo
"Tashi ki shirya jarrey baƙi na na jira a yi serving ɗin su"

A hankali tace
"Amma Ya muktar abincin ai yana dining naga be kamata sai na fita na sassa......"
"Kina so in wanka miki mari?"
Shiru tayi ta miƙe shine ya shiga drawer ɗinta ya duba ya zaɓo wani pencil gown ya wulla mata, seda ta gama kallon kayan kan ta saka a hankali babu shape na jikinta da be nuna ba.

Hijab ta fara dubawa yayinda shi kuma yake sake da baki yana kallonta don ba karamin gigita shi tayi ba sai gani yayi ta saka hijab

"ke ina zaki je da wannan abin?"
"Wurin baƙin naka ba?"
Tsaki me karfi ya ja yarinyar nan an yi bagidajiya
"ke kin san me sunana kuwa? PIYA-PIYA nake maganin kwari shine matata zata fita cikin abokaina da wannan abun a samu abun nuna ni? Kin cire ko kuwa?"
Ya daka mata tsawa daga karshe

"Ya Mukhtar ba zan iya fita da wannan rigan cikin maza ba hakan ya sabawa Addi...."
Wani wawan mari ya sauke mata har seda ta faɗi
"ke wai yaushe na zama sa'anki da zan faɗa ki faɗa?"
Tana dafe da kunci cikin gunjin kuka ta miƙe
"Babu biyayya a bijirewa ubangiji ya Mukhtar ba zan iya..."
Sake kifa mata mari yayi ya ja hijab ɗin ya fisge ya yar kan ya janyo hannunta suka yi cikin parlorn tana tirjewa.

Chak ta tsaya tana karewa parlorn kallo, mata da maza ne daban daban cikin shiga irin ta rashin sanin darajar kai wasu na rurrungume da juna yayinda kwalaben shiha suka yi bakwai a parlor hayaƙi har ya fara cika parlorn yana maida wutan wani fari fari baki baki, ganinsu tare yasa aka hau ihu sai kallon maita mazan suke mata da sauri ta koma bayanshi ta ɓoye.

Rita wacce tsab Alaya ta gane ta ita ce ta kawo shi daren farkonsu a Buge tace
"Ga dae kyau sede babu wayewa duhun kai yayi yawa"
Shewa suka ɗauka don a yadda tayi maganan har da kishi.

"Omoo kuna ganin kaya!"
Wani ya faɗa yana zuƙar shisha ɗin shi yana wani karkata kai yana kare mata kallo.
Fusge hannunta tayi da karfin tuwo ta juya da gudu tana ji suna mata ihu akan bayanta ta faɗa ɗaki ta rufe kofar da key ta zube a wurin tare da fashewa da matsanancin kuka tana squezing zuciyarta dake zafi da hannu biyu gwanin tausayi...


*Kar ku sha'afa Al'ajabin So book 2 is not free, a kan naira 500 kachal zaki same shi immediately after an kamallah book 1, zaki iya yin payment ta nan
3118518476
First bank
Fatima Muhammad Gurin
Sai ki tura shaidar biya ta wannan layi
09039206763*

#Vote
#comment


🖤Gureenjoh🖤

AL'AJABIN SO
     (heart touching story)

بسم لله الرحمن الرحيم

FATIMA MUHAMMAD GURIN.
(Gureenjo)

ADABI WRITERS ASSOCIATION

Marubuciyar:
*Zuhraa*
*Hamrah*
*Igiyar Rayuwa*
*Noor Iman*
*Ruwan Sama..*
*Lelewal*
*GAMON JINI paid*
*Kowa Ya ga zabuwa..*
*Diddigar ƙaya... Paid*
*Rubutu a kan ruwa... Paid*
And now..
*AL'AJABIN SO*

*BOOK 1*
*Page Twelve*

*Sometimes idan muna karanta labari mu kan ji kaman almara har mu kan yiwa kawunan mu tambayar cewa anya hakan na faruwa? Wannan Page is a dedication to waenda suke cikin ibtila'in auren mashayi, masu haƙuri da juriya da kaddararsu. Sadaukarwa ce ga uwar da Allah ya jarraba da haihuwar ɗa wanda jarrabawarshi ta zama shaye-shaye, Allah kana ji kana gani ya Allah ka shirya mana zuri'a, ya Allah ka kara musu haƙuri da juriya, ya Allah Alfarmar annabi da alqur'ani ka musanya musu kaddarorinsu daga baƙi zuwa fari*
(Ni kaɗai na san what i went to wurin rubuta wannan Page, a painful True life story)

A wurin wani wahalallen bacci ya kwasheta ba ita ta farka ba sai da aka kira assalatu, Miƙewa tayi ta shige toilet ruwa ta fara watsawa kan ta ɗaura alwala tana jin yanda zuciyarta yayi mugun nauyi haka dae tayi sallah ta nemi magunguna ta sha kan ta kwanta, bacci ta sake yi ba ita ta fito ba sai karfe tara sanye da hijabin da tayi sallahn asuba dama da shi ta kwanta, a parlorn ta tsaya tana kallon yanda suka maida shi, kyamar parlorn gabaɗaya ya shige ta, haka dae ta daure iya dauriya ta soma tattare parlorn har ta gama ta share ta fesa air freshner kan ta nufi kitchen don neman abinda zata ci.
     Bata gama dafa indomie din ba taji motsi, da sauri ta juya tana kallon kofan kitchen ɗin a tsorace sai suka haɗa idanu, babu kaya a jikinshi daga shi sai karamin wandon jeans, daga dukkan alamu har lokacin ba wai ya dawo daidai bane daga abubuwan da ya ɗurawa kanshi.

"ke wato ma ina wasa dake ko? Ni zaki dizga? U are very stupid...don ubanki sau nawa na buga miki kofa kika barni shanye ana min dariya?"

A tsorace take matsawa ganin yana kokarin cire belt din jikinshi muryarta na rawa tace
"Kayi haƙuri, don Allah ka saurareni ya Mukhtar..."
Tun kan ta sauƙe sunan ya fara zuba mata belt ɗin, be ji tausayinta ko na minti ɗaya ba sai da yayi mata duka har da kafa kan ya juya ya fice yana cewa gobe ta kara...
"Innalillahi wainna ilaihi rajiun! Innalillahi wainna ilaihi rajiun" abinda take ta nanatawa kenan tana kuka, da kyar ta iya lallashin kanta ta miƙe ta nufi daki bayan ta kashe gas ɗin indomien da bata ci ba kenan, tana hawaye tayi wanka idonta ɗaya yayi jajazir jini ya kwanta gefen fuskanta ga shatin belt nan har kusan uku jikinta yayi wani irin Red abin ka da farar fata.

Cikin uniform ta shirya don ta yankewa zuciyarta duk wuya zata yi karatu ko don nan gaba ta iya tsayuwa da kafafunta idan Mukhtar be yi sanadin ta ba, ji take kaman zata mutu kwana kusa a yanda take jin kirjinta da ciwonshi da ya dawo sabo fiye ma da na baya, tafin hannunta ta ware ta ɗan zubawa idanu kan ta gimtse tana sake ajiyar zuciya me nauyi na tsantsar damuwa a haka ta tafi makarantar, dayake bata kula kowa babu wanda ya damu ya tambayi me ya sameta ko ya akayi ta ji rauni har aka tashi bata iya ta ci komai ba.

Bayan ta dawo ta haɗa custard ta sha ta sake shan magunguna kan ta janyo wayanta don jin lafiyar mahaifiyarta.

Wani irin sabon baabin wahalar rayuwa ne ya buɗe mata, Mukhtar bashi da tausayi ko imani ko na miskala zarratin, ga zafin zuciya matukar ya sakata yin abinda ya saɓawa addininta in ta ƙi haka yake mata dukan mutuwa, marin shi a gareta ya zama kaman man shafawa da da matukar wuya a wayi gari a yini be kai hannunshi jikinta ba, ga bautar yi masa girki da abokansa wanda ba kadan ba idan suka tashi zuwa, a kullum se sun nemi ganinta ita kuma bata fasa ƙin fita ba ta kulle kofan ta gam shi kuma da safe ya mata dukan mutuwa, ko yaushe in yana bukatarta haka ze je mata walau yana hayyacinshi walau yana cikin maye, duk wani alwashi da ta ci a farko akan Mukhtar bata iya ta soma tabuka komai ba don gani take har Abada Mukhtar baze chanza ba, bata da lafiya sossai don zuciyarta ya sake rauni kan rauni sede babu wanda ta faɗawa haka take lallaɓawa kuma take karatu.
     Yau suke gama waec ta yi jamb tun sati biyu da suka wuce, Alhamdulillah sun gama lafiya da Fatan jiran sakamako me kyau, a koyaushe tana jinjinawa Maami da irin jajircewarta a kanta Dukda wani sa'in idan muktar ya mata wani abin sai wata zuciyar ta raya mata dole ne ai Maami ta so ta don ta san zama da ɗan ta sai wanda iyayenshi suka sallama, da sauri kuma sai ta yi a'uziyya ta kawar da tunanin don ta san Maami da zuciya ɗaya take mata hidima kuma take tausayinta, babu wanda ze ganta ya shedata sbd wani irin rama da tayi a watannin da ta durfafi yi gidan muktar, tayi wani irin haske har kana ganin kalar green green a jikinta in kana kallonta, idanunta sun kara girma da haske haka hancinta ya sake fita zirrr, bata wani ado bare kwallaya in tayi wanka ta shafa mai ta sa kaya shikenan.

Yanzu da ta gama Waec zaman gidan ya zame mata kaman wacce take rufe a prison na karkashin ƙasa, Rita a gidan take rayuwa daga parlor zuwa kitchen duk nata ne yayinda Alaya ke ɗaki a koyaushe abinda ke fitar da ita yunwa sai kuma idan shine ya zo ya sakata girki amma bata yi ta ajiye kam don ba lallai ma wasu ranakun yana kwana a gidan ba, kaman yau, gabaɗaya yinin tayi shi ne ba daaɗi sbd hayaniyarsu da suka yini yi bidiri kala kala a gidan, kaman wani kwarya kwaryar lifaya ne suke yi a gidan, daga inda take a ɗakinta babu irin warin ababen Mayen da bata ji, tana dukunkune kan gado, tana bukatar shan sassanyar iska marar surki irin wannan, ji take kaman zata mutu ne sbd wari da tashin zuciya.

Kofan ta da ta kulle ne yinin ranar gabaɗaya don ko abinci bata iya fita ta nema ba taji ana bugawa da karfi, chan ta jiyo dakakkiyar muryarshi yana kiran ta da sunan da shine ya raɗa mata wato
"ke! Ke!!"
Gabanta ya faɗi, zuciyarta ya hau tseren bugu me zata mishi a wannan yanayi da yake ciki? Kallon jikinta tayi idan tana son lafiyan jikinta kuma abu me sauƙi shine ta bude kofan taji me yake tafe dashi sede tsoro kaman ta narke ta ɓacewa gani da sauraranshi ya lullubeta, jin kaman ze ɓalla kofan ne yasa ta sanya kafafunta ƙasa kaman wacce kwai ya fashewa a ciki ta nufi kofan hannunta ɗaya na kan zuciyarta da bugawarshi har ya shafi numfashinta, hannunta na kakkarwa ta miƙa ta buɗe, banko kofan yayi sai gata gabanshi ya fisgo ta riƙo na mugunta yayi mata
"yarinya in ba zaki bi abinda nake so ba kina cikin wahala, buɗe bakinki ki karɓa"

Girgiza kai tayi tana kauda kanta daga wani abu da yake shirin bata.
"Ya..m...mukhtar menene?"
Kashe idanu yayi yace
"ko kin san menene ko baki sani ba dole zaki sha"
Ya karashe yana janyota zuwa fili abokan shi suka ɗauki shewa.
"Game muke kin san Truth or dare?"
Be jira amsanta ba yace
"an yi daring ɗina na bugar dake don haka buɗe baki malama"
Idanunta gabaɗaya ta fitar, a lokaci ɗaya jikinta ya ɗauki mazari, me yaya muktar ke nufi? Shayar da ita abun maye ze yi? Hawaye ne suka soma zuba babu birki cikin girgiza kai tace
"Don Allah yaya Mukhtar kar ka yi, kar ka cutar dani, ya muktar hannuna zafi...kirjina ciwo don Allah kar ka sa ni saɓawa mahallicina a dole, karka zalunceni dayawa mana have a pity on...."
Bakin ya murɗe se sowa suke suna ambaton sunanshi ya soma bata, duk yanda tayi ganin ta kubce ko bata sha ba hakan be yiwu ba, gimtse hancinta yayi seda ta sha kaɗan kan ya sake ta ganin yana shirin kisa, a wurin ta zube ta tura yatsa cikin bakinta ta soma amai, tun tana yi har ta gigice ta fice hayyacinta gabaɗaya, wata ce a cikinsu da jikinta yayi sanyi da tausayin Alayar tace
"Gaskiya baku kyauta ba, tunda bata sha me na shigo da ita cikin wannan game naku? Kullum baku da buri da ya wuce ku wulaƙanta ta, mu faɗawa kan mu gaskiya mana kai Mukhy kaine babban wawa, wanda be san abinda yake yi ba, taya zaka shigo da matar aurenka na sunna cikin wannan irin rayuwa, wani irin jahil....."

Gigitaccen marin da Muktar ya sake mata ne ya saka ta kwala ƙara ta yanke maganan, kan tayi motsi saurayinta ya tashi ya rama mata, kwalba mukhy ya janyo ya rotsa mai, a take jini ya fara tsiyaya kaman wasa sai gashi wurin na shirin zama karamin Abbatoir don faɗa ne sossai ya kaure tsakanin saurayin chan da shima ɗan wani ne da kuma Mukhtar kowanne kuma yana da abokan zagi, ita dae Alaya ta samu ta rarrafa ta faɗa ɗakinta ta datse kofa a wurin ta kwanta, kanta se juyawa yake da alama de kayan Mayen ya taba ta, tayi kuka har ta rasa hawaye, tana ta rokon Allah ya yafe mata yana gani ba laifinta bane, an fi awa biyu kan taji gidan yayi tsit, a wurin tayi bacci Washegari ma seda ta kai wuraren sha biyu kan ta farka sbd buga mata kofa da ake tayi kaman za'a ɓalla.

Dafe kanta dake sarawa tayi ko Sallar asuba bata yi ba, hawaye ya gangaro mata ta sanya hannu ta share kan ta motsa a hankali ta miƙe dafe da gini ta miƙa hannu ta buɗe kofan jin bugun ba na ƙare bane, woman Police ce tsaye tana kallonta
"Madam ko zaki iya ara mana mintuna biyu a cikin lokacin ki?"
Kaman bazata yi magana ba tace cikin dasashiyar muryarta
"Lafiya?".
"Shin kina cikin gidan nan gabaɗaya yinin jiya zuwa dare?"
Kai ta gyaɗa ba tare da ta amsa ba
"ko kin shedi hatsaniyar da ya faru a jiyan?"
Nan ma ta girgiza kai tana kallon matar da take ta karantarta..

"Ba zaki samu ko wani sheda daga gareni ba, ko ma menene kike so pls ki samu waenda suka asassa abun, ina da uzuri se anjima"
Ta ƙarasa a sanyaye kan ta tura kofan ta rufe ta juya zuwa bayi, seda tayi wanka ta zo tayi sallah tana rokon yafiyar Allah kan ta fita ta nemi abinda zata ci ta sake dawowa ta rufe ɗakin ruff ko bi ta kan wargajejjen parlorn bata yi ba, idan tace yanzu bata soma developing wani irin tsana na Mukhtar ba to wlh tayi ƙarya, a ƙasan ranta tayi ta ja mishi Allah ya isa kuma tana fata ya saka mata, ashe a chan kam case sossai aka yi sbd karfe da karfi ne suka haɗu sai da shudin Goshi case din ya mutu, nan Alhjnsu yayi ta mishi faɗa akan hakan ze iya ɓata mishi siyasa kar ya sake, ya dae ji ne ko da ya dawo ya tarar parlorn haka buga mata kofa yayi ta buɗe ba tare da ta kalleshi ba sai shima ya ji shakkan kallonta don fuskanta ba digon walwala ko farin ciki.

"Ki je ki gyara parlorn nan"
Yana kai nan ya juya ya fice, ta jima sossai kaman bazata yi ba se ta

Please Login or Register in order to submit comment