Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

matsalar Maami, saƙe-saƙe kawai take har ta watsa ruwa ta sauko ta ci abinci bata samu Maami ba kila tayi wurin Alhj, wayanta ta ɗauko ta fara texting ummi sun jima suna magana kan ta miƙe ta shiga kitchen, ita tayi musu girkin daren ranar sbd gujewa tunanukan Muktar da ya addabe ta ta rasa me take ji a game dashi, tsoro ne, tausayin Maami da halin da yake jefa kanshi da fushinta ne ko zeal na son ganin ta kyautatawa matar da duk duniya itace mace ta farko da ta fara kyautata musu a rayuwa?

"woww daughter haka dama kika kware a girki?"
Maami tayi maganan tana gyaɗa kai, murmushi me sauti kawai Alaya ke yi, Alhj ma yayi ta yabon girkin shi dae Mukhtar ci kanku be ce musu ba.

Bayan gama cin abincin nasu ne Alhj ya mike yayi sama yana cewa
"Hajiya in ganki mana minti biyu"
Miƙewa tayi tabi bayanshi yayinda Alaya ke tattare kwanukan, tana kai na karshe zata juyo kenan taji tayi mugun karo da mutum, kafafunta suka Harɗe baya baya tayi zata faɗi yayi hanzarin riƙota, hannunshi yasa ya kama nata hannun ya matse kara ta saki tana me duƙawa kaɗan
"Zafi Don Allah"

"zafin dama nake so ki ji, wato ba zaki ji magana ta ba ko?"

Hawaye ta fara sbd yadda yake murde hannun da tsantsar mugunta
"Kayi hakuri"
"ba hakuri nake son ji ba, sbd bani dashi kwata-kwata, abunda na sani shine kiyi gaggawar bin umarnina ko ki cigaba da karawa kanki laifukan da na rantse sai kin biya su ɗaya bayan daya"

Idanunta a runtse hawaye wani na bin wani, ganin azabar yayi mata yawa ne yasa cikin kuka tace
"Na amince wlh zan mata mag..."
"MUKTAR"
Maami ta katse shi tana jin kaman ta rushe da kuka ko ta rufe shi da duka ko zata ji saukin abunda take ji akan shi.

"Ga nan irin abunda nake tsoron yasa na ki baka ita, amma zan kai maka ita cikin wani sati sai ka shirya ko ka riƙe ta saboda Allahn da ya halicce mu ko kuma ka zalunceta, Allah baya bacci kuma baya barin zalunci kuma ina faɗa maka kaji tsoron Adu'ar wadda aka zalunta don bashi da shamaki, fice ka bar min gida!"
Ta karashe da karfi tana nuna mishi kofa.

Tsayawa yayi yana kallonta sama da mintuna biyu kan ya wuce yana gunguni, da sauri ta ƙaraso wurin Alayar tana rike hannun tace
"Sannu daughter, ya ji miki ciwo ko?"
Girgiza kai tayi tana me Miƙewa tace bari ta shiga ɗaki.

Da tunanin tarewar ta cinye satin ko fahimtar abin da ake yi a class bata yi tsabar tsoro, amma ya zata yi abu sede in ba'a sa mishi rana ba sai ga ranar ya zo, sisters ɗin ta guda biyu ta kira akan su rakata gidan ta don already an gama haɗa mata komai da komai har akwatunan an riga da an kai chan, tana kuka tana komai aka kaita gidan muktar a chan suka barta bayan doguwar nasiha.

Ta jima zaune bisa gadon har ta gaji ta kwanta bacci ya fara fusgarta taji ana bugu kaman hauka, a tsorace ta tashi tsaye tana zare idanu ganin tsayuwar ba zai mata ba gashi sai karuwa bugun ke yi yasa da sauri ta fita, duba agogon parlorn tayi karfe ɗaya saura mintuna.

"Waye ne?"
Ta faɗa muryarta na rawa
"Wayewa! Ke dallah ki buɗewa mutane kofa in zaki buɗe.."
Muryar mace taji, a tsorace ta buɗe yarinyar na sarkafe da hannunta a kwankwason muktar ɗayan hannunshi na zagaye da kafaɗarta, ko be ɗago ba ka san ba karamin buguwa yayi ba, da sauri Alaya ta koma baya tana kama bakin ta da hannayenta, kukan sai ya ƙi zuwa sai idanu take bin su dashi har yarinyar ta shigo dashi tana karewa gidan kallo tana taɓe baki.

"Ke wato kin raina mutane ko? Waye ya baki iz....nin rrrrufe kofar nannn"
Cikin tsantsar maye yake maganar yana nuna ta da yatsa.

Bata ce musu komai ba..
"Kai muky wace irin dakikiya ka auro ne? Kina kallon mu ba zaki kama shi ki kai shi ɗaki ba?"

A tsorace taje ta fara kokarin riƙe shi yarinyar tayi tsaki tace
"Muky am sleepy, good night"
A maimakon Alaya taga ta fice sai gani tayi tayi wani ɓari na gidan wanda ba inda Alayar ta fito ba, tana tunanin tana layi sbd yadda yake sakar mata jiki shima kuma Layin ne yake yi, a haka suka nufi ɗakinta hawaye na wanke mata fuska warin giyar kamar zai kashe ta, galau galau suka yi kaman zasu faɗi kokarin tare shi take sai kawai taji amai a jikinta, wani irin tashin zuciya ne ya kamata, hawaye wani na bin wani haka ta jefa shi kan gadon bayan ya gama amaye mata jiki, bata iya ganin amai ba hakan seda yayi sanadiyar nata aman babu komai cikinta, tayi ta wahala a bayin kan ta fito tana kau da ido ta samu ta kwashe.

Kayanta ta cire tayi wanka tana fitowa ta ganshi zaune yana kallonta.

"Ke zo nan!"
Har lokacin mayen be sake shi ba
"na'amm"
Ta ƙasan jajayen idanunshi yake kare mata kallo kan yace
"kika bari na maimaita sai na lahira ya fiki jin daaɗi"
Cike da tsoro take takowa ko kan ta ƙaraso ya fusgota kaman wata ƴar tsana haka ta faɗa kirjin shi, toshe hancin ta take sbd gudun sake amai warin giyar gigitata yake ga tsananin tsoron abunda zai iya mata ko kan ta gama tunani taji hannunshi ya fara yawo a jikinta, idanunta ta zazzaro cikin sautin kuka tace
"Me...menene Ya muktar?"

"Hakkina da kuka hanani zan karɓa"
Girgiza kai take da karfi, tana kokarin Miƙewa ya matse ta yana cusa fuskanshi wuyanta, gigitaccen kuka ta saki ta fara cewa
"A'a don Allah, Don darajar Allah ba yau ba, ba cikin wannan hali ba! Karka zaɓi tarayya dani da kazantar abubuwa dayawa a jikinka... Ya....ya Mukhtar aure fa muka y..."

Bakinta ya rufe da nashi ta datse nata tana kakari sbd yadda abubuwan maye ke tashi a cikin bakin shi, kokarin kwatar kanta take Dukda ta san karfi ba ɗaya ba shima kuwa nuna mata ya fara yi cewa karfi ba ɗaya ba, dambe ne ya kaure a tsakaninsu, duk kokarin da tayi wurin ganin be samu abunda yake so ba ta kasa dakatar dashi, tayi kuka kaman zata cire ranta ta jefar, kirjinta yayi matukar nauyi, numfashi yayi mata wahalar shaƙa, ji tayi inama ta mutu a lokacin, be saurara mata ba seda ya samu natsuwa ya zube a kanta ya fara baccin hauka, nauyinshi ya kara mata nauyin kirjin da take ji, idanunta na kallon seiling yayin da hawaye ke ganganrawa gefen fuskanta wani na bin wani ta fara cewa cikin jiggata

"Ya Allah kaine Allah, Allah kai kaɗai ka san dalilin hadani da Mukhtar a matsayin miji, Allah kana gani kuma na san kana ji na, ka bani haƙuri da juriya a kanshi ya Allah, idan kuma mutuwata ce hutu daga wannan radadin zuciyar ya Allah ka ɗauki raina a yanzu ya rabbi, idan kuma a rubuce yake a cikin kaddarata Ya Allah ka shiryar dashi ka kuma bani ikon yi mishi biyayya...."
Kuka me karfi ta fashe dashi ta saka ɗan karfin da ya rage mata ta fara kokarin ture shi, saide ta kasa duk yadda ta so tashi ta kasa, kaman yadda taga rana haka taga dare tayi kuka har ta rasa hawaye, jikinta ya dauki zafi, numfashinta ya fara nisa sbd tsananin ciwon da zuciyarta ya ɗauka, cikin tsananin rauni cike da ban tausayi take cewa chan ƙasa ƙasa
"Ummina ashe ba zan sake ganinki ba? Ashe ba zan taɓa jin muryarki a zahiri ba? Ashe ba zamu sake saduwa da ke ba! Ki yafemin in n...na taɓa saɓa miki, ummi ki yi min Adu'a zan tafi in samu Abbana....."
Ta karashe cikin jan wani wahalalliyar numfashi.

Mukhtar kuwa Ba shi ya farka ba seda gari yayi haske tarr, hantsilawa yayi gefen ta yana buɗe rinannun idanunshi ya zuba mata, ko motsi bata yi ba, fuskanta ya kurawa ido yayi wani haske yayi fayau, da sauri ya miƙe zaune ya ɗaga hannunta se yaga ya koma ya faɗi yaraf, kanshi ya ɗaura a kirjinta babu bugun zuciya..bai san sadda ya dirko daga gadon ba ya ɗauki boxers ɗin shi ya saka babu abunda yake tsoro se Maami, ya san idan har ya kashe yarinyar nan ko da me yake takama sai tayi shari'a dashi...

Da gudu ya kaita mota bayan ya sa mata riga wacce be tantance bata da tsawo ba seda suka shiga asibiti, a asibitin ma da gudu aka karɓeta zuwa emergency, likitan da ya iso cikin hanzari ya fara examining ɗin ta, girgiza kai yayi, yana saurin riƙo hannunta ya fara jin pulse ɗin ta....

"YA RABB I'M AFRAID WE LOST HER..."
Ya furta yana runtse idanunsa.


*Kar ku sha'afa Al'ajabin So book 2 is not free, a kan naira 500 kachal zaki same shi immediately after an kamallah book 1, zaki iya yin payment ta nan
3118518476
First bank
Fatima Muhammad Gurin
Sai ki tura shaidar biya ta wannan layi
09039206763*

#Vote
#comment



🖤Gureenjoh🖤

AL'AJABIN SO
(heart touching story)

بسم لله الرحمن الرحيم

FATIMA MUHAMMAD GURIN.            
         (Gureenjo)

ADABI WRITERS ASSOCIATION

Marubuciyar:
*Zuhraa*
*Hamrah*
*Igiyar Rayuwa*
*Noor Iman*
*Ruwan Sama..*
*Lelewal*
*GAMON JINI paid*
*Kowa Ya ga zabuwa..*
*Diddigar ƙaya... Paid*
And now..
*AL'AJABIN SO*

*BOOK 1*
*Page Ten*

"Dr Abdul what is the situation?"
Wani Babban likita ya ƙaraso yana yiwa wannan doctor da ya runtse idanu tambayar sanin cewa shi wannan intern ne kuma be gama gogewa a aikin ba.

Kallon Mukhtar dake tsaye ya zurawa gangar jikin Alayah idanu yayi yana cewa
"wannan fa? What is he doing here?"

Muktar da duk tunanin shi na ga Irin badakalar da zasu yi da Maami, sai kuma tunanin irin garɗin ni'imar da ya kwasa daga Alayah ace har ta mutu? Sau ɗaya kawai fa yayi?..
Idanunsa ya maida kan karamin likitar dake cewa babban
"her heart stopped beating doc, babu wani pulse dake harbawa a jikinta"

Maida kallonshi kan Mukhtar babban likitan yayi yace
"Me ya sameta? Me ke damunta?"

"blood?"
Ya faɗa ba tare da ya jira amsar Mukhtar da har lokacin yake tsaye ba, kallon kallo suka yi suka sake kallon muktar zuciyoyinsu na bijiro musu da abubuwa daban daban..

"Dr is she alive or dead?"
Yayi tambayar yana kallonta still.

"Meke damunta? Did you raped her? Gsky ba zamu iya taɓa ta ba sai da Police, this case is serious"

Tsawa ya daka wa doctorn
"she's my fucking wife, do something if she's still alive tana da congenital heart defect..! Do something before Its too late"

Jin hakan yasa doc saurin bawa nurses dake tsaye cirko cirko umarni, a take suka turo automatic external difibrillator, aka zuba mishi cream din ya dirza kan ya ɗaura mata a kirji, fusga tayi daga ita har gadon suka sake komawa yaraf, cikin gogewa a aiki ya sake murzawa ya danna mata ta kara jan numfashi tayi sama ta dawo kasa, a na huɗu ne ta ja wani dogon numfashi wadda ya dawo mata da numfashinta gabaɗaya, taimakon gaggawa suka fara bata yana kallon nurses biyu yace

"We really need Dr Abdulrahman and Dr Eshrat here Its urgent!"
Da gudu suka fita, shi kuma ya cigaba da abin da yake.

Kaman mintuna goma sai ga wasu doctors guda biyu nurses din na biye dasu, rufuwa suka yi a kanta suka fara bata taimako barin ma Abdulrahman da ya kasance kwararren likitan zuciya, seda ta daidaita kan Eshrat dake gynae ta duba jikinta da sauri ta runtse idanu tana me Miƙewa tsaye, idanunta ta maida kan Muktar dake tsaye ya zura musu idanu bazaka tantance halin da yake ciki ba, a ranta ta raya dole hakan ta kasance daga kallo daya da ta mishi ta san yana apawa, ga ingarman jikinshi da ya watsawa tattoos na ban mamaki, cinyoyinshi dake waje sbd wandon jikinshi ƙarami ne a mummurɗe.

"She needs stitches” ta faɗa tana kallon likitocin, Abdulrahman da ya gama daidaita mata bugun zuciya da taimakon Allah yace
"She also need an urgent heart surgery, the heart is so weak and fragile"

"yanzu da wanne za'a fara?"
Likitan farko ya faɗa cikin tausayinta tana kwance banda oxygen dake taimakonta da numfashi da zaka iya cewa gawa ce kai tsaye in ka kalleta.

"Dr Eshrat yi aikinki, before then relatives ɗin ta su yi duk wani abu da ya kamata har da blood da komai we will prepare for the surgery"
Yana kai nan ya fice.

Juyawa Drn farkon yayi wadda suke kira da Dr Ahmad ya kalli Mukhtar yace su je waje, ficewa suka yi zuwa office nashi, jallabiyarshi ya ɗauka ya miƙawa muktar wadda sabo ne tsaraba ce ma aka kawo mai sai ya mance a office ɗin, da wani irin kallo muktar ke bin jallabiyar shi fa ba sa irin abubuwan yake ba.

"Babu daaɗi kana yawo a kan patients haka, you need to wear this ka zauna in maka bayani"
Karɓa yayi ya bare a ledar ya saka, coffee Brown ce me sulɓi, wani irin amsarshi yayi shi ko se taɓe baki yake yana tsaki ƙadan kaɗan.

Bayani likitan ya fara mishi sai ya nuna idan kudi suke bukata ko nawa ne ze iya bayarwa ayi komai, tsoronshi Allah tsoronshi Maami kuma baya so yarinyar ta mutu don yana da buruka a kanta, yana so ya nunawa abokanshi daban daban cewa ya kere sa'a, yana kuma kwadayin sake ɗanɗanata.

Wani paper Dr Adam ya mika mishi bayan dogon typing, Miƙewa yayi ya fice zuwa reception anan ya biya duk abunda ake bukata, ko jinin ma seda wata nurse tace ko za'a gwada nashi yace a'a a saya a blood bank, bayan ya tabbatar babu wani abu ya fice abin shi.

Gida ya dawo yayi wanka ya sa kananun kayanshi as usual wando baya kaiwa ƙasa in ko ya kai to irin wasu mahaukatan crazy jeans ne da suke nan kaman palazo, da karamar riga marar hannu, daga nan ya leka Rita buduruwarshi bata nan ya tabbatar tana club don haka chan ya wuce, hayaniyar ganinshi ta hautsina club ɗin a take ya fara rabar da kyaututtukan giya sai rawa en mata suke yana shafasu cikin kwarewa da barikanci.

A asibiti kuwa aiki aka mata dukda anasthesia da take kai da kuma rashin hayyaci daga ka kalli fuskanta zaka san tana jin zafin stitches ɗin har aka gama, aka fara shirya batun surgery babu kowa nata aka shiga da ita theater, seda suka shafe sama da awanni bakwai kan suka fito, Alhamdulillah aiki yayi Kyau atleast zata ji saukin ciwonta ba kaman baya ba Dukda ba warkewa gabaɗaya tayi ba, abun mamaki har lokacin mijin be dawo ba kuma babu wadda yazo a family.

Aminity da ya bada umarni after the surgery nan suke so aka turata babu abunda take sai baccin wahala da gajiya, wasa wasa har dare sede nurses su zo su duba ta su tafi haka ta kwana be dawo ba, Washegari da misalin karfe goma na safe ta fara buɗe idanunta cike da kokonton kasancewar ta a duniya har a lokacin, ɗakin take karewa kallo a hankali hankali se ta fahimci asibiti ne nan ɗin, ga wasu na'urori jikinta, lumshe idanunta da suka faɗa sossai tayi ta sake buɗewa daidai lokacin wata nurse ta shigo ganinta ido biyu yasa ta koma ta kira Dr.

Checkup suka yi mata sossai kan suka rage na'urorin jikinta, Dr. Eshrat tace
"Fatima..."
Kaman yadda ta gani a rubuce a jikin file nata, da idanu Alaya ta bita.

"Waye ne ya kawo ki asibiti? Ina nufin me matsayinsa a wurinki?"
Tayi tambayar ne sbd su tabbatar da zancen Mukhtar kar karya ce ya musu gashi har yanzu yaki dawowa wani miji ne ze bar macen dake sharafan mutuwa ta yini ta kwana ta kuma hantse, har a mata surgry me hatsari irin na zuciya be dawo ba kuma ba aike?

Ta san mutum na karshe da ta kasance tare dashi Mukhtar ne, runtse idanunta tayi da karfi tana jin kuka na son zuwar mata tuna irin azabar da tasha a daren, a hankali cikin rawar murya tace
"mi..jinaa"

Ajiyar zuciya suka sauke me karfi, Dr Abdulrahman yace
"kina da iyaye a raye ko wasu Ƴan uwa?"

Cikin rawar murya ta sake cewa a raunace
"Ina da mahaifiya amma ba zan iya gayamata wannan hali da nake ciki ba, ku kira min mahaifiyar mijina"

Da mamaki suke kallonta, taya mahaifiyar mijinta zata iya taimakonta alhali ɗan ta ne ke da kaso mafi girma cikin abunda ya faru da ita?
Dr Ahmad ne ya karɓi Layin Allah ya sa ma ta riƙe sbd numbern special number ce, kira yayi cikin hikima ya sanar da ita komai nan take cikin tashin hankali tace gata nan zuwa.

Ba'a yi mintuna Talatin ba sai ga Maami, hawaye tayi ta zubarwa na tausayin Alayah wadda seda ta saka Alayar kuka, ƙanwarta ta kira tasa ta dafa mata abinci irin na marar lafiya ta kawo mata yanzu, Alhj hammad ta kira ta sanar dashi halin da ake ciki, sam ta ƙi ambaton sunan muktar sbd gudun mummunar kalma akan shi, iyayenmu mata kenan(ki kasance me gudun mummunar kalami akan yaron ki musamman idan ya kuntata miki sbd duk maganar da zaki yi a lokacin walau sharri walau alkhairi Allah na iya amsawa a take).

Har misalin sha ɗaya da wani abu sistern ta ta zo da abincin, da taimakon Maami tayi brush ta taimaka mata ta fara bata kakkauran shayin kan taci dankalin turawa da aka sarrafa shi cikin kayan ciki(offals) kaɗan, magunguna nurses suka zo suka bata, da wasu Iv injections aka sake ɗaura mata drip, wayan Maami ne yayi kira a hankali ta duba sunan se ta lumshe idanu kana ta sake buɗewa ta miƙe ta fice.

Sama da kusan mintuna Talatin ta dawo, bayanta Alhaji hammad ne, shi karan kanshi be ji daaɗin abunda Muktar yayi ba, barin ma watsar da ita a asibitin da yayi yanzu da bata rike Layin Maami ba fa? Sede fa Dukda haka ba wai ze mishi faɗa bane ko ya nuna mishi rashin kyautawarshi tana bacci don haka be zauna ba ya fice, a harabar asibitin ya tsaya ya kira Layin muktar, dagawa yayi cikin alamun baya ma cikin natsuwar shi.

"Kai kuma haka ake yi? Toh wlh ka tanadi abunda zaka kare kanka dashi a wurin maaminku ni kam ba ruwana"

A ɓangaren Mukhtar wara Red eyes ɗin shi yayi yace
"What? Maami tana asibitin? Ayyaa Abba duk bala'i karka bari ta rabani da yarinyar ba zan iya kyaleta ba"

"karka damu ai tunda kaine ke da igiyar aure a hannunka zancen maaminku ta raba ku be taso ba, amma fa ranta ya ɓaci kuma ta zub da hawaye sossai"
Cikin rashin nuna damuwa da hawayen mahaifiyar tashi yace.

"Maami kuma hawaye na mata karanci ne Abba? Bari dae ina wani abu zan shiga asibitin zuwa anjima, duk bala'i babu zancen rabani da Fatima daga Asibiti kuma se gidana"

Alhj hammad na gyara zamanshi yana kallon gefen titi sbd driver dake ja a natse yayi murmushi ya katse wayar, Abban Meelah ya kira ya sanar dashi an yiwa Alayah aikin zuciya sede be wani yi Adu'a ko nuna damuwa akan ciwon ba, kuma yace ba ze iya gayawa mamarta ba sbd baya so hankalinta ya tashi, sallama suka yi Alhj hammad na tayiwa Alhj Alhassan kirari.

Mukhtar be tashi shiga asibitin ba sai dare, Maami ta tafi sai Aunty rukayya da me aikinta da zata kwana asibitin, an ɗan ɗaga gadon Alayah na kwance a kishingiɗe idanunta a lumshe amma ba bacci take ba, tana masifar kewar umminta gashi ko sanin halin da take ciki ummin bata yi ba, wayanta na chan gida bare tayi mata message ko bata faɗa mata ba ta ji lafiyarta, kai tsaye ya shigo ɗakin ba tare da ya damu da sallama ba tunda yayi knock.

"Barka da dare Aunt"
Ya faɗa idanunshi na kan Alayah da takara runtse idanu gabanta na tsananta faɗuwa har jikinta na ɗaukan rawa.

Aunty rukayya dake ta kallonshi ta kasa cewa komai, kafada ya ɗaga yaje ya tsaya gaban gadon yana kallonta, sarai ya fahimci ba bacci take ba baki ya sake taɓewa, abunda ya hana shi zuwa asibitin kenan don be san uban da zs tsinana mata ba tana wannan abu kaman taga dodo, tsaki yaja ya juya ya fice abunshi a cewar shi yana da abin yi.

Haka ta shafe kwanaki goma curr a asibitin duka duka zuwanshi biyu shima se chan dare lokacin me aikin dake kwana da ita ce kawai, Maami tayi kokari sossai wurin ɗawainiya da ita hakan yasa dole ta koyawa kanta shanye damuwarta saboda damuwar matar, fargabarta ɗaya yadda zata koma gidan muktar, zata iya kuwa? To in bata koma ba ina zata je ga Abunda Abban Jameelah ya faɗa mata, sannan kuma bata Yiwa Maami kara ba Dukda har lokacin Maamin bata ce mata komai akan abunda ya farun ba.

Yau da take cika kwanaki goma sha biyu muktar ya zo da misalin karfe 12 na dare kai tsaye office na Dr in charge ya wuce
"Ina so ka bani takardar sallamar matata"

"wani irin sallama by this hour? Kuma ai tana da sauran medication da checkups"

"Yau bazata ƙarasa kwana a asibitin nan ba, duk kuma abunda ya saura ko ma menene zata zo daga baya"
Ganin fa baya ma cikakken hankalinshi kuma ze iya hautsina musu natsuwa anymoment sbd yanayin shi yasa babu yadda likitan ya iya duk yadda ya nuna mishi ya barta sai ko safiya ce ya ƙi haka ya bashi sallamar.

Tana kwance bacci ya fara ɗaukar ta bayan doguwar hira da idanunta suke yanzu kawai taji Shigowar mutum, da farko ma ta zata nurses ne sai taji muryarshi yana ce mata
"ke tashi mu tafi"

Mummunan faɗuwa gabanta yayi, taji gabaɗaya numfashi na shirin barin jikinta, ko kwakwaran motsi bata iya yi ba bare ta buɗe idanunta har ta fahimci shin shi ɗin ne ko ba shi bane, kuma da ita yake yi ko da wata....

"Kika sake Kika bari na maimaita kaina wallahi sai na lahira ya fiki jin daaɗi.."

*Kar ku sha'afa Al'ajabin So book 2 is not free, a kan naira 500 kachal zaki same shi immediately after an kamallah book 1, zaki iya yin payment ta nan
3118518476
First bank
Fatima Muhammad Gurin
Sai ki tura shaidar biya ta wannan layi
09039206763*

#Vote
#comment

🖤Gureenjoh🖤

AL'AJABIN SO
(heart touching story)

بسم لله الرحمن الرحيم

FATIMA MUHAMMAD GURIN.            
         (Gureenjo)

ADABI WRITERS ASSOCIATION

Marubuciyar:
*Zuhraa*
*Hamrah*
*Igiyar Rayuwa*
*Noor Iman*
*Ruwan Sama..*
*Lelewal*
*GAMON JINI paid*
*Kowa Ya ga zabuwa..*
*Diddigar ƙaya... Paid*
*Rubutu a kan ruwa... Paid*
And now..
*AL'AJABIN SO*

*BOOK 1*
*Page Eleven*

A hankali ta buɗe idanunta hawaye na gangarowa tace
"Ya..Muktar ba zamu bari da sa...fe in Maami ta z..."

Hannunta da ya fisgo ne ya yanke maganan, ta sauko ta sa takalami cikin tsananin tsoronshi, jan hannunta kawai ya dinga yi har motanshi ya buɗe ya jefata ya zagaye ya shiga, ya ja suka bar wurin da mugun gudu, har wani jiri da amai take ji sbd gudun da yake yi bata taɓa fuskantar irin shi da ita a cikin mota ba, a harabar wani Hotel ya tsaya chan wajen garin ya kife kanshi a jikin steering sbd baccin dake son kwashe shi...

"Ya muktar..! Ya muktar..!!"
Take kiran sunan a tsorace tana ɗan kalle kalle sai kuma ta kai hannu ta tattaɓa shi ko motsi be yi ba, hawayen da dama basu daena zuba bane suka ƙaru
"na shiga uku na ni Fatima"
Ta faɗa cikin karaya da tsantsar damuwa.

Wani tunani ne ya faɗo mata, tayi saurin sa hannu ta murda handle ɗin sede motar a rufe, da sauri ta sa hannu cikin sanɗa ta duba wayanshi ta taɓa screen ɗin ba password, hannu ta kai jikin kofanshi ta buɗe motar daga madannin wurin, jikinta na rawa kaman wacce aka sato ta buɗe ɓangaren ta ta sa kafafunta waje hannunta dake rawa na dialing Layin Maami, kaman an tsikareshi ya farka wani irin fusgo hannunta yayi ta dawo da karfi har tana buguwa dashi ya tsinka mata mari yana kashe wayan da har ya soma ringing..

Kuncinta ta dafe tana kuka
"Zan ɓaɓɓalla ki in baki rufe min baki ba... Wuce mu je"
Ya fito ya zagaya ya fusgo hannunta suka yi ciki.

Key ya karɓa alamar dae

Please Login or Register in order to submit comment