Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ta nuna mishi kusa da ita bakin gado ya zauna, ta san sabo sai a hankali amma with effort komai zai zama tarihi.

"Maami zan tafi wurin baba"
Murmushi ta saki tace
"Toh a kula, a kuma maida hankali banda tuƙin ganganci Allah yayi albarka"
Wani irin farin ciki yaji marar misaltuwa
Yace
"in shaa Allah sai na dawo"
Ya miƙe ya fito, ɗakin Alayah yayi knocking shiru ba response, ya sake yi shiru sai ya tura a hankali ya shiga tana nan kwance rigingine cikin tunani, a take yaji wani iri a jikinshi menene matsalar? A hankali ya isa ganganta ya tsuguna bata san zuwanshi ba sai hannunshi ta ji...

*kar fa ku sha'afa tafiyar yanzu aka soma ta, akwai sauran rina a kaba, tsugune kuma bata ƙare ba, har ila yau dae muna nan book 1, book 2 zai muku a naira 500 kachal zaki iya biya ta wannan asusun
0545475847
Gt
Fatima Muhammad Gurin
Sai shaidar biya ta nan
09039206763



🖤Gureenjoh🖤

AL'AJABIN SO
(heart touching story)

Fatima Muhammad Gurin
(Gureenjo)

Adabi Writers Association

Book 1
*Page Twenty Two*

A hankali ta buɗe idanunta da suka sauya sossai ta zuba mishi su, zare hannunshi yayi daga goshinta chan ƙasa yace
"Are you alright? Da wata matsala ne?"
Da idanu ta amsa shi don bakinta yayi mata nauyin buɗewa.
Gefe ya ɗan kalla sbd yadda idanun suke wani irin tasiri a jikinshi, Miƙewa zaune tayi a hankali tace
"zaka fita ne?"
Sai a lokacin ya ɗan kalleta yace
"zan je wurin baba, me kike so in taho miki dashi in zan dawo?"
Murmushi ta ɗan saki shima yayi, Dukda babu wani shakuwa na musamman a tsakaninsu babu tsoronshi a ranta kaman kwanaki, hasali ma tausayinshi ya fi komai tasiri a gareta sai kuma tausayin ɗan cikinta.
"Nama"
Ta faɗa a tsakanin lips ɗinta
"wani iri?"
Idanunta ta ɗan juya da alamun tunani kan tace
"ko wani iri me daaɗi dai"
"an gama maman unborn, na tafi"
"Allah ya tsare"
Ya amsa kan ya fice daga ɗakin, ajiyar zuciya ta sauƙe kan ta ɗan yi murmushi.

Tuƙi yake a natse yana murza siterin motar tsakanin hannuwanshi, wani irin yanayi yake ji a jikinshi da ma zuciyarshi, jinshi yake sabon mutum a hankali ya miƙa hannu ya kunna karatun alqur'ani da ɗazu yayi downloading Dukda manyan surorin da be iya bane sai dae jinshi akwai saukar da natsuwa, gidan baba malam ya isa saida ya shiga ciki suka gaisa da kakkaninshi da wasu Aunties din nashi kan ya tafi parlorn baba, maraba ya mishi suka zauna aka kawo abinci fura kaɗai ya sha, da tambayoyi baba ya fara abubuwa dayawa be sani ba hakan yasa baba ɗauko komai daga farko, Allah ma ya sa shi ɗin akwai kwakwalwa da kam ba karamar wuya ze ci ba wurin koyon addini, kuma abin ka da wadda ya saka kai sossai ya natsu ya ɗauki karatuttukan ranan, sai goma na dare ya mishi sallama ya fito.

Sai da ya tsaya ya sayi kaji gashin oven da aka yi su cikin wani hadaddiyar sauce na albasa da kuma Irish guda huɗu da su youghurt kan ya nufi gidan, a parlor ya sami Maami dake ta zuba ƙamshi tana kokarin tafiya part din Abba, da murmushi ta tare shi tare da wara hannunta ya matso yayi Hugging ɗinta tace
"ka dawo?"
"Eh Maami na dawo"
"ya karatun? Fatan an yi abin arziki"
Yana murmushi yace
"Eh Maami, na koyi dayawa har fa baba na mamaki"
Kai ta jinjina cikin jin daaɗin da ya kasa boyuwa mata tace
"Masha Allah, Allah ya sa a ɗore a haka"
Ya amsa da Ameen
Ledar hannunshi me kaji biyu ya miƙa mata
"Maami gashi a tafi wa Abba da shi"
Karɓa tayi ta mishi Adu'a kan ta juya kitchen zama yayi yana jiran ta fita don kunyar haurawa wurin Alayah yake a kan idanunta, a tray ta haɗa musu kan ta fito ta mishi sai da safe.

Sai da ta fice daga sashen ya miƙe ya shiga kitchen ɗin, yadda ya ga ta haɗa ya haɗa Dukda be iya ba duk ya ɓata jikin plate ɗin haka dae ya kokarta kan ya saɓi tray din ya haura sama dashi, a hankali ya ɗan yi knocking kan ya buɗe ya shiga tana tsaye ta gama saka night gown ɗinta kenan wadda dogon Cotton gown ne har ƙasa da tsagu gefe da gefe, cikinta ya ɗan tasa kaɗan akan rigar ya mata kyau sossai, murmushi yayi mata ta ɗan mayar mishi kan ta nufo shi ta karɓi tray din.

"Sannu da dawowa"
"yauwa fatee"
A ƙasa ta ajiye tray ɗin kan tattausan rug carpet dake shimfide a wurin, ya ƙarasa ya zauna ita ma ta zauna, shi yake cire mata ƙashi sai ya bata tsoka, Dukda ba wani hira suke ba moment ɗin ya mishi daaɗi ashe haka samun cikakken natsuwa yake? Godiya kawai yake yi wa Allah da ya bashi daman zama mutum a karo na biyu, sai da tace ta ƙoshi kan ya kyaleta ta miƙe ta shiga toilet ta barshi yana ci, brush tayi ta fito ta isa kan gado ta kwanta lamo gabanta na faɗuwa Allah Allah take ya gama ya tafi, tana kallonshi ya gama ya tattare wurin ya kai bakin kofa ya ajiye kan ya dawo ya shiga toilet ɗinta ya wanke hannu tare da kuskure baki ya fito.

Yana fitowa tayi hanzarin rufe idanunta tana damke blanket da take ciki dukda iyakarshi kan kwankwasonta ne, taku yake yana nufan gadon inda yake tafiya da bugun zuciyarta, murmushi ya saki ganin yadda take mirmisa idanun sai motsi gashin idanunta ke yi wai ita a dole tayi bacci, a ɗan space da ta bari ya ɗosana duwawunsa ya sanya hannu daga gefenta kan gadon ya tokare hakan ya bashi damar yi mata rumfa da faffadar kirjinshi, fuskanta ya zubawa ido yana ƙare mata kallo, tsawon dakika goma, kasa juran kallon tayi ta fara buɗe idanun a hankali har suka faɗa cikin nashi, murmushi ya ɗan saki yace

"Me baccin ƙarya"
Ta ɗan yi murmushi, idanunta ta kai kan hannunshi dake saitin kwankwasonta daga kan idon hannun har ya ɓace zuwa cikin half jumfar dake jikinshi wadda iyakacinshi damtsen shi daga sama duk tatoos ne a kwance, kallon hannun da take shima ya saka ya ɗan kalla, hannunta ta kai ta ɗan shafa tace tana maida idanunta cikin nashi

"Yana fita?"
Kai ya gyaɗa mata
"A da ne ba'a samo technologyn cire shi ba, amma yanzu ana iya gogewa"
Ta haɗiye miyau tace chan ƙasa kaman yadda shima yake mata magana
"Da me ake gogewa?"
"Da wuta kaman yadda aka yi shi da wuta"
Idanunta ta ɗan zare
"kuma ba zafi?"
Cikin kwaikwayan maganan ta ya ce
"akwai amma mijinki jarumi ne"
Murmushi tayi, shiru ya ɗan ratsa su idanunshi dake ta yawo bisa kanta duk ya bi ya tsarga ta, har gwara suna maganan ma da suna zaune shirun nan.

"Gobe in Allah ya kaimu zan fara zuwa makaranta"
Kai ya gyaɗa yace
"Allah ya kaimu in zan tafi Hameed auto motors sai in yi dropping naki from their za ki duba motar da ya miki sai mu fara koyon driving"
Cikin jin daaɗi ta mishi godiya, idanunta ta ɗan lumshe ta sake cewa
"in na tashi ina so zan je asibiti ne na duba ummi"
Da sauri ya ɗan kalleta Sharp ya mance da zancen mahaifiyar tata, tunanin haduwarsu na farko kuma na ƙarshe yayi inda ya tureta a hanya har ta faɗi a sume, a take yanayin shi ya sauya, hankalinshi ya so tashi sai yaji hannunta kan kumatunshi ta ɗan shafa dole ta sa ya maida idanunshi cikin nata
"Karka damu, ummi tana da sauƙin kai da fahimta, bazata ƙi ka ba musamman in ta farka ta samu ka sauya kana kuma kular mata da ni yadda ya kamata"
Ajiyar zuciya ya ɗan sauƙe yace
"in shaa Allahu kan ta farka ɗin zan tabbatar da na baki kulawar da ba zata iya gane ki ba ma ta ganki"
A tare suka yi murmushi, hamma ta saki
Yace
"bacci ko?"
Kai ta gyaɗa mishi, ya duƙa yayi pecking goshinta a hankali ya ɗago idanunshi akan lips ɗinta baya so ya kai nan don bashi da control a fannin, kuma ba zai iya kusantarta ba har sai ya je asibiti ya tabbatar da lafiyanshi, bargonta ya ɗan ja ƙasa yayi pecking cikinta tafin hannunshi ya ɗaura a kai, yace a hankali
"Kuyi bacci cikin aminci, Allah ya bamu alkhairi"
Ta ɗan yi murmushi tare da furta Ameen kan ya ja mata blanket ɗin har kirjinta ya sake pecking cheek ɗinta kan ya juya ya nufi kofa tana ta kallonshinshi saida ya dau tray din kan ya kashe mata wuta ya fice, ajiyar zuciya me karfi ta sauke a hankali ta furta
"Alhamdulillah"
Sake dunkule wa tayi a cikin bargon a take natsatsen bacci ya dauƙeta, shima yana isa ɗakinshi ya watsa ruwa ya kwanta saida ya sake bitar karatun su na ɗazu kan bacci ya ɗauke shi.

Karfe huɗu da rabi alerm ɗin shi ya tashe shi, a natse ya miƙe ya shige toilet yayi alwala ya zo ya sanya Black jallabiya da ya mishi kyau sossai ya amshi skin dinshi dole yau zai je ya nemi kaya don da ya tsaya gaban kayakinshi na gidan duk babu na kirki, duka kyauta da su zai yi a yau, fita yayi ya tafi ɗakinta ya tashe ta kan ya fito, a haraba suka haɗu da Abba suka nufi masallaci dake kofan gidansu anan suka yi raka'atanil fajir wallahi be taɓa jin natsuwa irin na daga jiya zuwa yau ba a rayuwarshi, har suka yi sallahn asuba wani irin nishadi yake ji, ko da mutane suke fita shi qur'ani ya ɗauko ya cigaba da bitar ƙarin su na jiya, sai wuraren bakwai ya bar masallacin ya dawo ɗaki ya ɗan kwanta.

Karfe goma daidai ya fito a shirye cikin half jumpa ruwan ƙasa da ya kama shi ya mishi kyau sossai, tuni ya aske kanshi don haka hular shi ta zauna sossai ya fito a babban mutum me cike da natsuwa da haiba, a parlor ya same su, itama ta shirya cikin baƙin lace me adon peach ya mata kyau sossai, gaishe shi tayi ya amsa yana tambayar lafiyanta kan ya duƙa ya gaida Maami itama ta amsa cikin kulawa

"har kin shirya kina ta jirana ko?"
Tace
"A'a yanzu nima fitowana Yaya"
Dining ya wuce ta miƙe don serving nashi sai murmushi Maami ke zabgawa tana kallonsu gwanin sha'awa.

A chan ma cikin natsuwa yake shigar da kanshi gareta, har ya gama ci suka fito magana yake mata a hankali tana bashi amsa, anan ta yafa babban mayafinta ta ɗauki jakanta tace
"Maami mun tafi"
Maami tace
"Allah ya tsare ya bada sa'a, sai kun dawo"
Suka fice a tare gwanin sha'awa, shi ya buɗe mata hadaddiyar motar tashi sport car ce BMW ta shiga shima ya zagaya ya shiga ya ja suka fice, kaman yadda ya faɗa campanin motocin shi suka tsaya suka shiga, ana ta miƙa gaisuwa cike da tsoro saboda sanin shi masifaffen marar haƙuri, kuskure kaɗan kashin ka ya bushe, ga mamakin su yau sai gashi sai murmushi yake saki ba wannan hayaniya da hargagin, har kyautar kuɗi ya musu suna ta mishi godiya cikin jin daaɗin sauyin da suka gani a tare dashi.

Wata coffee hyundai ta zaɓa ya mata kyau sossai, a take ya bada umarnin ayi wa motar duk wani checking kan yamma a kai mishi gida, daga nan school suka nufa duk yadda ta so ya barta daga haraba ya tafi zata yi duk abinda bata gane ba ya ƙi, a tare dashi suka yi ta yin komai, duk inda da bin layi zai nema mata seat ta zauna shi ya bi Layin sai an iso ya kirata ta zo su yi abinda zasu yi su kara gaba, kowa kallonsu yake gwanin sha'awa lallai haƙuri na da riba, duk masu yi mata kallon ta dace ta tsinci dami a akala basu san irin tsanin wutan da ta taka zuwa wannan wuri bane.

Karfe ɗaya suka gama komai, sai da suka tsaya masallacin makarantar ta shiga ɓangaren mata shi ya shiga cikin masallaci suka yi sallah kan suka fito, restuarant me kyau ya kaita suka ci abinci kan suka nufi asibiti, har yau ba'a bari an shiga wurin ummi ba, hanganta suka yi ta fara hawaye tuni ya jinginata da jikinshi yana lallashinta, sun ɗan jima kan suka fito a reception yace ta ɗan jira shi anan yana zuwa, wayanshi dake ta ringing tuntuni yana rejecting yanzu ma shi ya sake ɗaukar ringing wayan ta bi da kallo har ya ɗan yi nisa kan ta ga yayi picking ya ɓace mata.

"Rita i Said leave me alone! Ki kyale rayuwata na fita daga cikin sabgar rayuwarku daga ke har su Zee wacce ta sake kirana wallahi sai na mata rashin mutuncin da baku taɓa tunani ba, rubish"
Yana kai nan ya yanke wayan ba tare da ya jira amsar ta ba sim zai chanza bazasu dagula mai lissafi ba, yana kokarin zare sim ɗin saƙo ya shigo, kalma ɗaya da ya gani shi ya ja hankalinshi wurin dubawa, wani irin jiri ne ya kwashe shi da sauri ya dafe gini don ƙoƙarin zubewa ƙasa yake, a take zufa ta karyo mishi a kan lips ɗin shi ya furta
"Innalillahi wainna ilaihi rajiun.."

*Kar ku sha'afa Al'ajabin So littafin kuɗi ne part 2 din zai zo muku akan naira 500 kachal har yanzu muna da gagarumin tafiya a gabanmu.
Zaki iya biya ta wannan asusun
0545475847 Gt bank Fatima Muhammad Gurin
Sai ki tura shaidar biya ta wannan layi
09039206763
Sai na ji ku*



🖤Gureenjoh🖤

AL'AJABIN SO
(heart touching story)

Fatima Muhammad Gurin
(Gureenjo)

Adabi Writers Association

Book 1
*Page Twenty Three*

Zaune a gaban Dr Ahmad dake ta murmushin ganinshi da yanayi na daban yace
"Na zo ne ina bukatar a yi min tests ba zan iya haƙurin cire folder da sauransu ba please do the needful"
Sarai ya gane shi their rude patients husband Dukda yanzu Meddy specialist sun karɓe musu ita sbd finsu kwarewa a harkar zuciya sai dae ya san Maami ya kuma san Umar tunda ta hannunshi suka karɓi ummi.

"Wani iri kenan?"
Numfashi ya ja kan yace
"Komai da komai, precisely HIV/AIDS"
Da sauri Dr Ahmad ya kalleshi, jingina yayi ya lumshe idanu yace
"don't be suprise, it might be the product of my sins"
Ajiyar zuciya Dr Ahmad ya sauƙe kan ya danna kiran wata ma'aikaciyar jinya ya bata umarnin zuwa da kayan diban jini, tubes biyar ya buƙata.
Ko da ta kawo da kanshi ya tashi yayi sticking finger ɗin shi for the rapid antibody test na HIV kan ya saka syringe ya zuƙi jini sossai a tubes din nan, a na karshen ne ya ɗaga kwalban sama yana kallon jinin for seconds kan ya ajiye kan tray ɗin, rubutu yayi a kan plain sheet me ɗan tsawo da Mukhtar ba zai iya tantancewa ba sbd rubutun likitoci ba irin na normal mutane bane ya bata yace ta kai lab please.

"Sai zuwa yaushe duk results din zasu fita?"
Dr Ahmad yace
"zai iya kaiwa five hours kan a kamallah komai sbd suna dayawa"
Miƙewa Mukhtar yayi ya miƙa mishi hannu suka yi musabaha kan yace
"Zan dawo ko zuwa anjima, nd I will make the payments yanzu in na fita thank you very much"
Murmushi kwance a fuskan Dr. Ahmad shima ya bashi hannu kan ya juya ya fice, da kallo Dr. Ahmad ya bishi a fili ya furta
"Masha Allah, he's indeed a changed person"
Ko daga maganan shi ma ya fuskanci hakan.

Yana isa wurinta ya sakar mata murmushi tare da miƙa mata hannu ta kama ta miƙe yace
"Sorry madam na ajiye ki ko?"
Girgiza kai tayi tana murmushi, bata tambayeshi abin da yaje yi ba sai dae ta fahimci kaman akwai abinda yake damunshi, yanayinshi ya sake sanyi har suka isa gida babu wadda yayi magana, a tare suka shiga parlor Maami na musu maraba da dawowa, duk amsa mata suka yi suka mata sannu da gida kan kowa ya nufi ɗakin shi don freshening, sai bayan la'asar ta fito ta zauna da Maami a parlor suna hira.

Chan shima ya shigo yayi joining ɗin su Dukda ba wani magana yake ba, a kusa da Maami ya zauna ya ɗaura kanshi akan shoulder ɗinta, tsoro ne fal ranshi, hankalinshi rabi baya jikinshi rabuwa da Alayah shine fargabarshi a yanzu ba ciwo ba, Maami ta tambayeshi ko akwai wani damuwa ne yace babu, yana ji suna maganan Ummi akan yadda babu wani improvement saboda sun ce damuwa yayi mata over ta yadda jinin da ya tashi hitting yayi sama ba na wasa ba kuma laluranta ma na rashin ji da magana kaman musababbin BP ɗinta ne.

Adu'ar samun lafiya duk suka mata, dab Magrib ya miƙe yace
"Maami zan ɗan fita zan tsaya wani wuri ina ga daga chan zan wuce wurin baba kawai"
Suka mishi Adu'ar dawowa lafiya ya fita.
"Maami baki lura kaman yana cikin damuwa ba?"
Alayah ta faɗa tana kallon Maami
"Kwarai kuwa na kula, sai dae kila tunanin rayuwa ne with time zai sake in sha Allah"

Zaune a gaban Dr. Ahmad bayan sun gaisa yace
"ya ake ciki? Sun fito results din?
"Yeah sun fito, for now babu HIV but ka san test na HIV yana ɗaukar 90 days ne kan ya zama successful, zaka dawo after 30days a sake yi haka after another 30 days again, sannan duk wasu STIs(Sexual transmitted infections) cututtuka da ake iya samunsu ta hanyar saduwa kaman su
Syphilis da gonorrhoea da sauransu duk babu"
Ajiyar zuciya ya sauƙe kan ya miƙa hannu ya ɗauki wani paper daban ya miƙa mai...

Tsawon mintuna talatin ya ɗauka cikin office ɗin kan ya fito, a cikin asibitin yayi isha kan ya isa wurin Baba suka yi karatu, Dukda baba ya lura kwazonshi ba kaman na jiya ba sai dae ya maida hankali sossai da sossai, daga nan ya tsaya ya saya masu gasashen kifi yayi gida.

****

Wasa wasa haka rayuwa ta zo ta sabar mishi da wani yanayi na daban, duk yadda yake karfafa zuciyarshi damuwarshi ba wani boyayye bane, yana iyakacin kokarin shi wurin bautar ubangijinshi kaman yadda yake matukar kula da Alayah da kuma Maami, bashi da wani buri illah ya shigo ya tarar dasu su biyu suna hira da raha hakan na kautar mishi da duk wani matsaltsalu na duniya, har ya sabar musu duk dare baya dawowa daga gidan baba hannu banza, ita kanta Alayah ta riga da ta saba bata cin komai sai ya dawo ya kawo ko balangu, tsire, kifi ko kaza gashi daban daban, yana riritata yana bata duk wani kulawa tsabar yadda hankalinta ke kwance Dukda yadda karatu yayi nisa wani irin kyau take narkawa tayi fresh abin ta.

Ta fannin mu'amalar aure bai taɓa nemanta ba wata huɗu ake nema kenan bata damu ba kasancewar ita wahalar abin kawai ta sani, ya kan rage zafi idan ta ciyoshi da gaske Dukda yana yawan shan tea me lemon tsami da gishiri, bata da wani matsala banda ciwon ummi da har yanzu babu wani cigaba, jiya e yau, duk ta tashi makaranta shi yake zuwa ya ɗaukota daga nan wucewa suke yi koyon tuƙi tun bata iyawa har ta soma kwarewa wani lokacin ma ita ke dawo dasu gida, in tace a watannin nan basu yi wani irin shakuwa na ban mamaki ba tayi ƙarya, yana bata duk wani kulawa da mace take fata ko buri, cikinta ya shiga wata na bakwai kenan duk zuwanta awo a tare suke zuwa, har yau babu wadda ya mishi maganan su koma gidansu ko ya ɗauke ta su tafi saboda daga Maami har Abba basa so su takura shi, kila ya fi so su zauna nan ɗin don duk wani shakuwa da be samu ba da Maami a yanzu ya same shi Dukda ya san ba kaman na umar da ita ba, amma kwarai zuwa yanzu sun shaku matuka.

Wani abu da yake yi yake ƙara burgesu shine yawan sadaka da taimako, har an san shi sai dae idan be ji taimako ba zai yi, abinci duk Litinin da juma'a yana ciyar da akallah mutane ɗari biyu zuwa uku, kuma lafiyayyen girki ba laga laga ba don a babban restuarant yake da contract, wani lokaci ma har ya ɗauketa su kai ziyara su orphanage, asibiti da sauransu a yanzu in ya ga rayuwarshi sai ya tsinci kanshi cikin zub da hawaye, lallai Allahnshi yana son shi.

***

Tsaye take gaban dressing mirror tana shafe tattausan skin ɗin ta da mai fitowanta wanka kenan, wani irin zafi take ji sannan kirjinta ya tokare sossai wadda rabon da ta ji ciwon zuciyarta ya motsa ta mance sai dae rashin ƙiba da nauyinta na nan, ta dae murje ta ƙara kyau sossai, cikinta ya fito sossai sossai bayan ta gama ta feffeshe jikinta da turarukan ta mabanbanta a take ɗakin ya bule da sassanyar kamshin, night gown da be da wani nauyi da tsawo ta saka tana kokarin tufke gashin kanta ya turo kofan ya shigo, ta madubi suka sakarwa juna murmushi.

A hankali ya ƙaraso ya ajiye tray din hannunshi kan ya nufeta slowly yayi Hugging ɗinta ta baya very tide yana zagaye hannunshi bisa kan cikinta a lokaci ɗaya ɗan cikin yayi motsi suka saki dariya a tare
"ka ji min yaro da gulma"
Yace
"kyaleshi ya marabci babanshi watarana sai labari"
Kallonshi tayi sai ta ga ya ɗan faɗa mata, sajen da ya tara ya mishi kyau ainun, tafin hannunta ta sanya ta ɗan shafa sajen tace

"Ya Mukhy menene yake damunka? Jikinka da ɗan zafi kuma ramarka tun bata fita har tana nunawa, can you please share ur problem with me? Karka manta turawa fa sun ce a problem shared is a problem solved"

Sakinta yayi ya karɓi ribbon ɗin hannunta yana tufke mata gashin yace
"bani da damuwar komai Fatee, in da ina dashi ba zan ƙi faɗa miki ko Maami ba saboda har duniya ta nade bani da tamkarku"

Bayan ya gama ya ja hannunta suka zauna bakin gado sbd zaman ƙasa na mata wahala yanzu, ya buɗe soyayyayiyar Irish da aka yi ta da liver sauce ya fara bata tana ci, sai da ta ƙoshi ta karɓi spoon ɗin ta dibo zata kai mai baki ya riƙe yana saukewa a hankali yace
"bani da apetite ba zan iya ci ba"
Tace
"kuma dai? Ya Mukhtar kullum fa haka kake cewa da matukar wahala ka sha wani abu ma bare ka ci abinci me nauyi"
Murmushi ya sakar mata.

Miƙewa yayi zai fita da kwanukan ta riƙe hannunshi
"zaka kwana anan? Ko in zo?"
Ya kalleta yace
"bari naje na dawo maman unborn tunda yau so ake a danne min kirji"
Tana dariya ya fice, toilet ta shiga tayi brush ta ƙarasa kimtsawa tana zama yana shigowa sanye da jallabiya coffee Brown me taushi, jallabiyar ya cire ya saura daga shi sai dogon wandon bacci ya haye gadon ta kuwa samu masauki a kirjinshi suka yi Light off bata jima ba bacci ya sure ta.

Sai da ya bari tayi nisa a baccin ya maidata kan pillow ya kwanta, baya so ya tashe ta cikin dare sbd ya san kanshi, juye juye kawai yake sbd baccin da baya samu a kwanakin gabaɗaya, chan kuma zufa yake ta karyo mai Dukda Ac dake ta aiki a ɗakin kusan kure wa tayi, ya yaye bargon yana cigaba da ɗan juye juye, wuraren sha biyu ta farka fitsari idanunta suka sauƙa kanshi.

Taɓa shi tayi sai taji hannunta ya sauƙa kan zufan dake ta gangara a jikinshi, wuta ta kunna sai suka haɗa idanu
"Ya Mukhtar zafi kake ji haka? Ko mu kunna standing fan?"
Yace
"No karki damu zan watsa ruwa yanzu ina jira ne ɗaya yayi gabaɗaya in miƙe nafilfili na"
Sauƙa tayi ta shiga toilet tayi fitsari kirjinta ke damunta da ciwo tana tunanin dole gobe taje meddy, ta fito ta zo ta kwanta ya kashe wutan don ya san bata iya bacci da wuta a kunne.

Bata iya ta yi baccin ba, tana ta kallonshi ga dukkan alama duk daren be yi bacci ba, ya kwana biyu da tayi noticing rashin baccin shi, in yayi ma baya wuce awa guda duk tsanani, tana ta kallonshi har ya sauka ya shiga toilet ya jima wadda ya tabbatar mata da wankan yayi kan ya fito ya sanya jallabiyanshi ya tafi

Please Login or Register in order to submit comment