Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


Downloaded from GNOVELS.COM.NG




This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG
to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/gnovels

Twitter : https://twitter.com/gnovels

Telegram : https://t.me/gnovels

An dauko wannan littafi daga shafin www.dlhausanovels.com.ng ku ziyarci shafin na www.dlhausanovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya

Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,

Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490

A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,

Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu

Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC

Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from www.dlhausanovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services

Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us

Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it

Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
__


~IKRAAM~ By Khaleesat Haiydar
1......
Da sauri har tana tuntube ta karaso kusa da wani Babban Grocery dake cikin kasuwan, bbu fruits din da bbu wajen, cikin rashin sa'a warce take sauri dominta har ta gama biyan kudin fruits din da ta siya ta sakale handbag dinta ta dauki manyan ledojinta tayi gaba, bata yi give up ba still ta bita da gudu tana cewa "Anty, Anty," matar ta juya da sauri cikin rashin sa'a daya daga ledanta ya kubce kayan ciki suka xube kasa, fashions na dankunnaye da sarkuna ne sae takalma, da sauri yarinyar ta yarda itacen hannunta ta durkusa tace "lah ashe baki rike ledan da kyau ba," snn ta shiga kwakkwashe mata su tana mayarwa cikin ledan, har ta gama, snn ta dauki ledar ta daura a ka tace "bar in taya ki rikewa Anty," matar da ba haifanta ba har jika xata yi da ita tayi murmushi tana kallonta tace "ki bar shi kawae yan mata," yarinyar ta bata rai tace "A'a ni Anty sae na taya ki," matar tayi murmushi ta ajiye daya ledan hannunta snn ta bude karamar jakarta ta ciro dari biyar ta mika mata tace "to gashi yan mata, yi tafiyarki kawae," yarinyar kmr xata yi kuka tace "Allah sae na taya ki" matar dariya tayi wnn karan snn tace "to mu je 'ya ta," tafiya suke amma kallon ledan fruits din hannunta kawae take, kuma shine babban dalilin da yasa ta taimaka ma matar, har suka fito daga babban kasuwar suka iso bakin titi matar sae sannu take mata, ita ta sauke mata kayan daga kanta snn tace "ya sunanki dota?" yarinyar tace "ni sunana Rabi'atu, amma Ikraam Ammi da Abba da yan anguwarmu suke kirana, Ammi tace kawu na lado ne yace a sa min Rabi'a wae sunan kanwarsa ce kuma ta mutu baxata dawo ba, Amma Ammi tace sunan mamarta da xa'a sa min, ni dama bana son wnn kawu na ladon don mugu ne ssae baya son Ammina da babana har ma dani, matarsa shatu ma muguwace, idan Ammi ta aikeni gidanta sae ta rankwasheni kafin na dawo gida, snn ga lukutar yarinyar nn shafa me dukana hka ma watarana...." da sauri matar ta katse ta tana dariya tace "kai ikraam sunanki fa nace ki gaya min," Ikraam ta dan marairaice fuska tace "Ae nace maki sunana Rabi'a, Ammi da baba da yan unguwarmu suna kirana Ikraam, amma malamar bokonmu Rabi'a take ce min don tace a makaranta ba a boye sunan gskya, hka ma wata yarinya a ajinmu ranan..." dariya ssae matar take tana kallon Ikram tace "naji hka Ikram, maxa ki tafi gida kar a nemeki kin ji," Ikram ta bata rae tana wasa da xariyar skirt dinta tace "to Anty baki bani Ayabar da na gani a ledan can ba," matar tace "ayya ae ban san kina so ba Ikram," wani ledan ta dauka ta shiga debar mata Bananan har ma da apples, sae washe fararen hakoranta take tace "Anty baki gaya min sunanki ba," matar ta juya tana murmushi tace "sunana Hajiya Amina amma Mami ake ce min," Ikram tace "nima knn baxan ce maki Hajiya Amina ba Mami xan ce maki," matar ta dan yi murmushi tace "eh dota," ta mika mata ledan fruits din tace "to me kika xo yi kasuwa Ikraam," Ikram xata yi magana wayar matar ya ruri cikin jaka, ta ciro wayar ta danna snn ta kara a kunne, sae kallon matar Ikraam take a xuciyarta tana cewa xan ce ta bani katon wayar nn. Matar ta shiga cewa "ehh srry ka dan dawo baya na hango motarka ynxu, bn lura da wucewarka bne," tace "ok" snn ta katse kiran tana kallon Ikraam tace "to dota maxa ki wuce gida Allah yyi maki albarka," Ikraam tace "to ae baki tafi ba ke ma, ko in tsayar maki da mota,"matar tayi murmushi tana shafa kanta tace "ynxu xa'a xo a daukeni dota," bata rufe baki ba wata lafiyayyar mota tayi parkn gabansu, Ikraam ta bude baki tace "wnn motar xaki shiga," kan Mami tace komai aka bude driver sit ya fito yana kallonsu yace "sannu mami kina ta jira ko, wllh akwae holdup ne a hanya," Mami tace "ae ban wani jira ba ynxun nn muka fito kasuwar," ya karaso gabanta ya duka xae dauki ledan Ikram ta fixge tana kallon Mami tace "Anty waye wnn," daga kai yyi yana kallonta, ita ko sae kallon Mami take tana jiran Amsa, Mami tayi dariya tace " 'da na ne," Ikram ta gwalo ido ta rufe bakinta da hannu daya tace "lah wnn katon yaron" dariya ssae mami take, shi kam kallonta ya shiga yi daga sama xuwa kasa, wata kodaddiyar atamfa ce riga da skirt jikinta, amma sbda tsabar neatness dinsa ba ka ganin kodewar atamfar, hula ce baka a karkace a kanta sae bathroom slippers a kafarta, girgixa kai yyi hade da dauke kansa ya kwashe ledojin ya bude bayan mota ya saka su, ya juya xae ce da mami ta shiga su wuce yaci karo da Ikraam bayansa, tace "oucch, baka gani ne yaro," tana shafa goshinta, xae yi magana tace "dan matsa, ina son in leka cikin motar ne," barin wajen yyi ta tura kanta cikin motar snn ta fito tana dariya tace "ba irin ta kawu bala bane tasa kujerun duk sun yage kuma baya kamshi hka turare ake sa ma motar?," mami na dariya ta shiga mota tace "maxa ki tafi gida ikraam," ikram ta juya da gudu ta bar wajen, mami ta kirata da sauri, ta kuma dawowa, mami ta ciro dubu daya ta mika mata tana murmushi tace "daga nn ki wuce gida kin ji," kai kawae Ikraam ta gyada mata tana washe hakora snn ta juya a guje ta bar wajen.

~Ikraam~ By Khaleesat Haiydar 2...... Mami ta bi ta da kallo tana girgixa kanta snn tayi murmushi tace "Mu tafi son," ya mayar da wayarsa da yake dannawa cikin aljihu snn ya shiga motar ya tada yyi reverse yana kallon Mami ta Madubi yace "ina kika samo yarinyar nn mami," Mami tace "wlh kawae biyo ni tayi daga cikin kasuwa fa, ban santa ba," bae ce komai ba ya mayar da hankalinsa ga tukin da yake. Karfe kusan biyar na yamma Ikraam ta isa gida rike da kubewar da Ammi ta aiketa, bakin xaurensu ta tsaya ta dan buda labulen buhun dake jikin kofar a hankali tana lekan tsakar gidan, ido hudu suka yi da Ammi dake xaune bakin murhu tana kwashe tuwo a tsakar gidan, Ammi tace "xaki ci ubanki ki lekoni da kyau, ae yau me raba ni dake a gidan nn sae Allah," da gudu tayi waje ta fasa wani shegen ihu tare da xubewa kasa tana cewa "wayyo Allahna," tana birgima hade da shure shure, me tredan dake karshen layin yana xaune yana kallonta don ba nisa tsakaninsu ya daka mata tsawa hade da yi mata dakuwa yace "kinci uwarki, kwana biyu kin rabu da iskancin nn shine xaki dawo dashi ynxu," mikewa tayi ba tare da ta kallesa ba ta kara gaba da gudu don tasan yana iya tasowa ya kakkwade ta, can kofar gidansu altine ta koma ta fada kasa ta ci gaba da birgimar ta, mamar altine ta leko tace "Au kin dawo da wnn iskancin naki ne ynxu Ikram, to tashi ki koma gidanku ja'ira kawae," Baba mai nama ne ya xo wucewa da tasan namarsa yace "wa ya doke ki Rabi," cikin kuka tace "Ammi ce," ya kamo hannunta yace "kai, Aisha ma dae wallahi, ynxu ina abun duka jikinki," maman altine tace "wllh baba idan an bibiya ma bbu abinda aka yi mata, tsabar iskanci ne na Ikram, ae ta kwan biyu bata tara mana mutane a anguwa ba," Baba na rike da ita suka yi hanyar gidansu yana cewa "ae hakuri ake da yara barin wnn yar malaikan Allahn me ta sani," sallama ya shiga kwadawa bakin xaure, Ammi ta fito yafe da mayafi tace "ina yini baba," bae tsaya amsa gaisuwar ba yace "Haba Aisha me yarinyar nn tayi maki haka," Ammi tace "wllh baba ban mata komai ba, tun karfe biyu na aiketa nan bakin kasuwa bata dawo min ba sae ynxu, daga nace xanyi maganinta fa tayi waje da gudu," Baba yace "to ae Rabi yarinya ce kiyi Hkuri ki kyaleta," Ammi tace "to baba ngd," Baba ya juya yana kallon Ikram yace "maxa ki shiga ciki kuma ki dinga jin magana," ta gyada kai tana goge guntun hawayen fuskarta ta bi gefen Ammi ta wuce sanin baxa ta yi mata komai ba kuma, Ammi ta kuma masa gdya ta shiga gidan, xaune taga Ikrama bakin murhu ta kwaso wasu sababin itace tana tura su cikin wutan, duk hayaki ya cika gidan, ikram na ganinta tace "Ammi kinsan me, yau naga wata yarinya me kirki, ta bani...." Ammi tace "ta shi ki ban waje kar na maki shegen duka da icen nn," ikram ta mike tana xumburo baki ta shiga dakinta, kudin da mami ta bata ta shiga kallo tana tunanin inda xata boye shi kar Ammi ta gani ta mata duka, wani dan rami dake jikin window ta tura sa, snn ta fito tana kallom Ammi tace "ba kin ce idan kina girki in dinga xama ina kallo ba," Ammi bata tanka ta ba, ta dauko kujera karami ta xauna tana ta kallon tukunyar kan murhu, hka ta dinga sa Ammi magana daga xaunen da take a wajen don da ta faki idonta sae ta jefa duk me ta gani cikin wutan yyi ta hayaki, da rankwashi Ammi ta koreta daga wajen, ta koma ca bakin kofar dakinta ta xauna tana matsar kwalla, Ammi ta gama miyarta ta shiga dashi dan kitchen dinsu ta fito tana kallonta tace "maxa ki tashi kije kiyi wanka kan kice min dare yyi," bata yi musu ba ta mike ta tube kayan jikinta ta rataye jikin igiya, Ammi ta juya tana kallonta tace "na shiga uku da wnn yarinyar, wae ikram ban hanaki cire kaya kafin ki shiga wanka ba," xumburo baki tayi tace "na manta," ta shige dakinta ta fito da kwandon sabulunta snn ta dauko bokiti ta bude randa ta shiga diban ruwan wankanta, Ammi sae kallonta take kmr ta kwade ta, ruwanta rabin bokiti ta dauka tayi hanyar bayinsu, Ammi ta kwala mata kira ta fito da gudu a tsorace, cikin tsawa Ammi tace "kin wuce kin dauki xanin ki a daki ko sae na make ki, kullum ina koya maki abu amma wawancin ki ya ki bari ki dauka, ni ban san wace irin yarinya bace wnn," kmr xata yi kuka tana bubbuga kafa ta shiga daki ta dauko xaninta tayi hanyar bayin.ko da ta fito daga wanka Ammi ta xuba mata tuwonta don ya huce, alwala Ammi ta sa ta tayi don lkcn sllhn magrib yyi, Ammi ta shiga daki ta fito mata da karamar riga da dogon wando ta sa, kmr xata yi kuka tace ni ba wnn nake so ba, Ammi ta watsar mata da su tace "to kar ki sa," snn tayi ficewarta, sae da ta gama xumbure xumburenta snn ta sa tayi sllhn ta fito, kan tabarma ta xauna kusa da tuwonta da kofin ruwa, yarfe hannu ta shiga yi tana cewa "Ammi tuwon da xafi," Ammi bata tanka ta ba har ta gama gyaran dan tsakar gidan ganin taki cin tuwon yasa ta wanke hannu ta xo ta xauna ta bubbuda mata snn ta mike tace "sae ki bari ya huce." Ammi na shiga wanka ta tura tuwon gabanta ta mike a hankali ta wanke hannunta snn ta dauko slippers din ta ta fice daga gidan da gudu, sae hanyar kasuwa.

[12/30, 8:39 PM] ‪+234 706 135 1072‬: ~Ikraam~ By Khaleesat Haiydar 3...... A hanya
ikram ta hadu da su Altine kawarta suna dawowa
daga islamiyya, Altine tace "ina xaki Ikram,"
Ikram tace "kasuwa xanje na ga ko xan ga matar
daxu ta kuma bani Ayaba xo ki raka ni," Altine
tace "wace mata?" Ikram tace "wata babban
mata ce ta bani ayaba da kudi da apple matar na
da katuwar mota da katon yaro har ya xama
baba shi ma" Altine da ta bude baki uwa sokuwa
tana kallon ikram tace "aa ni gida xan tafi kar
baba tayi man duka," Ikram ta murguda mata
baki tace "shine kika tsayar da ni," tayi kwafa
tare da jan tsaki ta ci gaba da tafiyarta, Altine
tace "malam yace me yasa kika daina xuwa
makaranta fa," Ikram na ci gaba da tafiyarta tace
"Ammi tace baxan kuma xuwa ba," Altine da
sauran kawayenta suka tabe dan bakinsu suka ci
gaba da tafiyarsu. Ammi na fitowa ta nemi ikram
ta rasa tsakar gidan, ta leka dakinta bata ciki, ta
fito tana haska tsakar gidan ko xa ta ga
takalminta ta ga bbu, ta rike habarta tana girgixa
kai cikin damuwa tace "na shiga uku ni Aisha ina
yarinyar nn tayi kuma" Hijabinta ta figa tayi gun
me treda don nan daya daga wajajen xuwanta,
yace ae ikram bata yo gun sa ba, tayi gidansu
Altine mamar Altine na daki ta fito, tace lah ae
ikram ko bata shigo ba, Ammi tace "to su Altine
fa," matar ta kwala ma Altine kira ta fito, Ammi
tace "kinga ikram altine," nn Altine ta labarta ma
Ammi abinda ikram ta gaya mata, Ammi ta fita
daga gidan da sauri tana cewa "nashiga uku na
lalace, kashe ni ikram ke son yi, kasuwa da
daddaren nn?" Mamar altine ta bi ta suka fita ita
ma tana salati, nan suka shiga neman ikram gida
gida a anguwar ko karya tayi ma altine, amma
duk inda suka shiga sae ace bata je ba, hnklin
Ammi duk ya bi ya tashi, mamar altine sae ca
take xa su ganta. Ikraam bata taba xuwa kasuwa
da daddare ba, tana isa ta tarar duk an kulle
kofofin shiga cikin kasuwar nan ita wae gun mae
fruit din xata je ta tambayesa ko matar ta sake
dawowa, wani mutumi dake xaune yana xukar
wiwi da yan uwansu su kusan hudu kan benci
taje ta sama tana kallonsa tace "kai meyasa aka
rufe kofofin nn, waye kuma ya rufe gashi ina son
shiga," mutumin ya daga jajayen idonsa yana
kallonta da mamaki yace "shiga xa ki yi?" tace
"eh mana gun mai Ayaba nake son xuwa," duk
suka bushe da dariya ta dinga binsu da kallo baki
a sake, wani daga cikinsu ya fixgota yace "xo mu
je in nuna maki idan xaki bi ki je gun me ayaba
yarinya," sauran duk suka kuma kwashewa da
dariya ta fixge hannunta tana murguda masa dan
karamin bakinta tace "dan iska kawae," ya buda
ido ssae yana kallonta yace "ni kika ce ma dan
iska?" tace "eh mana ae ku duk yan iska ne
nasani, dama Ammina tace min duk masu shan
sigari yan iska ne kuma basu da mama da baba,"
ta kuma murguda masu baki tana jujjuya mnyan
idanunta ta ja wani dogon tsoki ta koma jikin
karfen kasuwar ta shiga hawa wae xata dura ciki,
har ta kai tsakiya gnin ynda suke ta dariya yasa
ta sauka ta juya xata bar wajen, mutum biyu
suka fixgota a tare, wani kuma ya shake wuyarta,
ihu ta fasa, wani ya mike ya daga ta sama da
katon muryarsa yace "ku xo mu je," duk suka
mike, ta dinga ihu tana shure shure, wani bawan
Allah ya xo wucewa ya bisu da gudu yace "ina
xaku kai yarinyar," ikraam tace "wllh yanka ni
xasu je suyi yan iska ne su, sigari suke sha,"
gabansu ya shige yace "maxa ku ajiyeta," duk
suka bushe da dariya wani yace "kama gabanka
malam," wani wawan naushi ya kai ma wnda ke
rike da ita ba shiri ya saketa ta fadi kasa, ta
mike a guje ta bar wajen, mutane biyu suka bita
da gudu, sauran suka rufe mutumin da duka, kan
kace me har ta bace masu don lungu lungu ta
dinga bi gashi ta iya gudu, tana mayar da
numfashi ta iso anguwarsu duk ta jefar da
takalman kafarta da hula, anguwar tsit gun mai
treda ta nufa tana kallon kofar gidansu kmr
munafuka, bata tarar da shi ba amma shagon a
bude yake, ta xauna kan benci ta kara fitilar da
ya rage snn ta dauki sweet daya ta jefa bakinta,
ta kai minti kusan talatin xaune a gun, jifa jifa
tana ganin mutane da fitila suna wucewa sae ta
buya, ashe nn duk nemanta ake, muryar mai
treda taji da wasu maxa guda hudu suna cewa
"idan Allah ya yrda ma xa'a ganta, bbu abinda ya
sameta," mai tredan yace "to Allah yasa hka, ban
jin ma xan iya xama shago ynxu bari na rufe
kawae na tafi gidan wllh rashin ganin yarinyar nn
ya tsaya min a rai," ya karaso cikin shagon xae
kashe fitila ya rufe ya ga ikraam xaune tana
kallonsu, sae da ya koma baya da sauri da
mugun mamaki yace "ikraam" ta washe hakora
tana kkrin boye sweet din hannunta, yyi waje da
sauri cikin daga murya yake cewa "jama'ah ku xo
ga ikram a shagona," baban altine ne ya fara iso
wa da sauri snn sauran makwabtansu, me treda
dae na tsaye baki bude yana kallon ikram, baban
altine ne ya hade rae yace "daga ina kike Rabi,"
ta dan marairaice tace "kaga baban altine a nn
kofar gida ne wasu masu shan sigari suka daga
ni sama shine na shigo shagon baba Habu da
gudu, amma sun tafi," Ammi ce da su maman
altine suka karaso wajen da sauri, Ammi ta ci
kuka har ta gode Allah.
[12/30, 10:39 PM] ‪+234 903 250 7176‬: Ikraam~ By Khaleesat Haiydar 4..... Mamar Altine ta fixgo Ikram ta shiga dukanta da dan icen hannunta, bbu wanda ya bata hkuri, Baba Habu sae ca yake karamata mamata, Ammi ta juya ta yi cikin gida kawae, Abban Ikram dake bakin kofa tsaye yana kallonsu ya shige gida shima, har maman Altine ta gaji dan kanta ta shiga jan ta tana huci tayi cikin gidansu da ita, sae ihu Ikram take tana tsalle tsalle ta bar ta nn tsakar gidansu tayi ma Ammi dake xaune ta rafka tagumi sae da safe tayi gaba, Abbanta ya mike shima daga kan tabarmar da yake ya kamo hannunta ya xaunar da ita gefensa yana kallonta yace "meyasa baki jin magana ikram, ina kika tafi da daddaren nn" Ammi ta mike ta tabe baki tace "hka ka iya malam, wae daga ina take, yarinya ta xama abinda ta xama kayi mata fada baxa kayi mata ba, wllh tun farko kai ka lalata yarinyar nn," ya hade rae yana kallonta yace "wani dukan kike nufin na sake mata bayan wanda saude tayi mata ynxu," Ammi bata ce komai ba ta shige daki abunta, ya maida dubansa ga ikram yace "ki dinga jin magana kin ji mamata, kuma daga yau kar ki sake fita da daddare, ko kina son na fara dukanki ne" ta girgixa masa kai yace "kin ci abinci," ta juya tana kallon inda ta bar abincinta tace "gashi can," yace "je dauko," ta mike ta dauko tana yatsine fuska tace "ni baxan ci ba Abba datti ya shiga ciki," ya shiga kwala ma Ammi kira ta xo ta xubo mata wani abincin, daga cikin dakin Ammi tace "ban da shi," mikewa yyi ya dauka nasa, suka shiga ci tare ya sa ta wanke hannu tayi alwala tayi slln isha snn ya rakata daki ta kwanta ya tofa mata addu'a ya fito, ya shiga nasu dakin, Ammi na xaune ta hade rae ya xauna gefenta yace "haba Aisha, ikram yarinya ce duka duka shekarunta nawa, wani yaro ne baya kin ji? Sannu a hankali duk xata daina ta nutsu, ki dinga hakuri da ita don Allah, Ammi dae bata tankasa ba tayi kwanciyarta kawae. Washegari da safe Ammi ta shiryata ta tafi sch bayan Abbanta ya fita gun aikinsa, ta hada ta da naira ashirin tace "kuma saura ki ki xuwa makarantar ko kije kiyi dambe a kawo kararki tunda ke kince kin xama jaraba a gari," tana xumbura baki ta fita daga gidan a xuciyarta tana cewa ni bbu makarantar da xan je malama ta dokeni ban ga littafina ba, kmr abun arxiki ta kama hanyar makaranta da yara tana kusa makaranta ta yanke wata hanya daban da sauri da sauri take tafiya kar mutane su ganta har ta isa wata katuwar bishiyar mangwaro, ta haye ta samu branch me dan karfi ta kwanta kai tana ta kallon mutanen dake wucewa wajen, a hka bacci ya dauketa bata farka ba sae karfe goma da rabi, tafara kalle kallen inda take, can tayi hamma ta tsinko wani mango da bae nuna ba ta shiga ci, har ta gama snn ta duro kasa tana waige waige tayi hanyar Canal da saurinta, wasu almajirae yara ta tarar wajen suna kama kananan kifi da karamin hook dinsu da earth worm a jiki, ta bude jakarta ta ciro nata hook din naira ashirin ta siye shi da ddewa, bbu ranar da bata xuwa canal din kama kifi, ta nannade uniform dinta ta shiga tona rami tana neman earthworm har dae ta samu ta dauke shi da dan tsintsiya tayi gun almajiran tace "ku, ku sa min don Allah," ba musu suka karba suka saka shi bakin hook din suka mika mata ta koma can bakin katon canal din ta shiga tsoma hook din cikin ruwa tana jiran kifi ya kama ta fito dashi ga gwangwaninta a gefenta, har ta fara ganin yaran makaranta na wucewa gida bata kama komai ba, tayi tsaki ta jefar da earthworm din ta nannade hook dinta ta mayar cikin jakarta snn ta kama hanyar gida da sauri, bata bi ta kofar gidansu altine ba kar ta ganta tace bata je makaranta ba, Ammi ta kai mata ruwan wanka taje tayi kafin ta ci abinci ta fito ta sa doguwar rigarta Ammi ta ajiye mata abincinta tsakar gida ta xauna tana ci a

Please Login or Register in order to submit comment