Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ɗaya da ga cikinsu ne yawo da hankalinmu kawai take son yi”. Ɗaya daga cikin jami'an ya faɗa a hasale.
               “Sam banajin hakan a raina, akwai dai wani ɓoyayyen abunda bamu sani ba. Karku manta shiɗin mutum ne mai matuƙar wayo da dabaru kala-kala. Tabbas ya fahimci ana bibiyarsa ne ya bada ƙafa. Kokuma yayi amfani da wanann location ɗin domin sakamu zargi.”
        “Nima zuciyata tafi rayamin hakan yallaɓai”. Wani ma ya sake faɗa cikin jin zafi.
        “Karku samu damuwa. ai rana 99 da tara na ɓarawo, ɗaya tak na mai kaya. Inhar kere na yawo, zabo na yawo watarana dole a gamu. Tunda yace shi hatsabibi ne ya samu dai-dai da shi kuwa. Zamu bar wasu a gidan nan har sai mun tabbatar da gaskiyar babu wani abun zargi a cikinsa”.
      Duk sun amsa da girmamawa. Shi dai mai-gadi kallonsu kawai yake yana kwasar dariya a zuciyarsa. Koda suka fito harabar gidan sun tsara wanɗanda za'a bari, wanda zasu koma kuma suka nufi hanyar barin gidan. Karaf idon ɗaya ya sauka akan bag dake rataye acan ƙarshen gate ɗin gidan ta waje. Saurin zuwa yay ya ɗakko yana nuna musu. Commander ɗin operation ɗin nasu ya amsa yana zazzage jakkar cikin kulawa gudun kar a saka musu bom a ciki.
    Agogon Hibbah ne ya fara faɗowa tare da takarda mai ɗauke da sunansa akoda yaushe da facemark. Sai ɗan gajeren rubutu a bayan takardar.
        *_“Bibiyata na nufin ƙare rayuwarku a wahala. Inhar bani naso kusan niɗin wanene ba, bazaku taɓa ganoni da kanku ba har abada insha ALLAHU rabbi. Dan haka ku daina azabtar da kanku wajen bibiyata komai yana da lokacinsa”_*
         _Master👌🏼_
    Wani wawan tsaki jami'in daya gama karanta takardar yaja. Ya cije leɓensa na ƙasa da ƙarfi, cikin alwashi yace, “Ni kuma na maka alƙawarin da wannan hannun nawa zan kamaka, sannan na maka horo mai tsananin gaske wanda sai ka gwammaci mutuwarka da rayuwarka shaiɗani”.
         Suma sauran zukatansu na matukar ƙuna suka ɗauki nasu alwashin.....

___________★★★__________

          Yaya Abubakar ya shiga tashin hankali matuƙa lokacin da yake isowa cikin makarantar su Hibbah yaji abinda ya faru a bakin Ammar da Zahidah. Tare da samun ƙarin bayani a bakunan wasu ɗaliban.
      Da taimakon wani malamin su Hibbah ya shiga Computers room nasu yay bincike a computer ɗin da ta gudanar da binciken. Sai dai kuma ta saka security, shiga yay gwada passwords kala-kala yayi wanda yasan tana amfani da su a gida ko zata iya amfani da su. Sai dai sam babu wanda ya buɗe. Cike da ɓacin rai ya mike yana bugar desk ɗin cikin ƙunar zuciya. Lalubo wayarsa da ke ring a aljihu yayi. Yaya Muhammad ne, ɗagawa yay sukai yar magana ya yanke. Wani abokinsa ya kira kasancewar shi jami'i ne a hukumar ƴan sandan ta farin kaya. Ya tabbatar shine kawai zai iya bincika masa idan Hibbah na hukumar tasu. Bayan ya ɗaga ko gaisuwar kirki ba suyi ba ya sanar masa bukatarsa. A take jami'in ya tabbatar masa lallai Hibbah na'a headquarters ɗin tasu dan yaji ƙishin-ƙishin ɗin zancen yanzu a bakin wani ogansu cewar akwai yarinya da ke da alƙa da case ɗin na jiya.
     Yanke wayar kawai yayi batare da sun ƙarasa maganar tasu ba, ya kira Yaya Muhammad yana sanar masa a inda zasu haɗu yanzun nan......

__________________________

           Master da yaransa kam bayan ƴar tafiyar da sukayi ta cikin hanyar kwata sai gasu sun ɓilla ta wani ƙaramin gida. Gidane ginanne mai ƙyau na dai-dai mai matsakaicin ƙarfi. Yanda yake bin ko ina cike da nazari haka suma suke kallon gidan. Bayan kamar mintuna biyu ya gyara tsaiwarsa sosai yana fuskantarsu. Binsu ya gamayi da kallo ɗaya bayan ɗaya batare da su suna kallon ko ƙwayar idonsa ba. Tabbas sun jima suna kwaɗayin ganin fuskarsa, amma sam yaƙi basu damar hakan koda da kuskure..
           _Gyaran muryar da yay ne ya katse tunaninsu. Ya sake gyara tsaiwarsa yana tura hannayensa duka cikin aljihun wandonsa. Muryarsa a kausashe da tabbatar musu da fushinsa ya fara magana cike da nutsuwa da ƙasaitar sa,
          “Yau mun tsallake rijiya da baya, amma wataran saboda sakacinku tabbas bazamu tsallake ba. A kullum ina faɗa muku duk sanda zakuyi aiki, ku ringa yinsa da *_ƘWAƘWALWA  DA ZUCIYA_* a haɗe. Dan duk lokacin da ɗan adam yay amfani da ƙwaƙwalwa kawai wajenin aikata muhimman abubuwa to ya tabbatar zai kasance mai yawan shiga ruɗani da tafiya yana dawowa baya saboda wani ya fika kaifin basirar. Idan ko da zuciya kaɗai ka dogara wajen ginin muhimman abubuwa, kasani nasararka ragaggiyace saboda zuciya abinda ke mata daɗi kawai take ayyanawa da buƙatar ya kasance mata. Bai kuma zama lallai ka kasance cikin jin daɗi da farin ciki ba a kowanne daƙiƙa na rayuwarka. Dan wani lokacin hanyar jin daɗi wahala ce, wata hanyar wahalar kuma jin daɗi ce. Wannan ya zama na farko kuma na ƙarshe, idan ba hakaba ni ɗin nan da kaina zan bada ƙafar da za'a kama duk wanda ya cigaba da sakaci a cikinku. Ba kuma zan taɓa kuɓutar da shi ba har sai ya jigata yasan muhimmancin bama kasan kariyar yin aiki cikin tsantseni. Duk wanda ya haremu ya sokemu akan dai-dai kuma na jinjinama ƙwaƙwalwarsa da kaifin tunani. Sai dai na baku awa goma kacal ku ganomin koshi ɗin ɗan gidan uban wanene. Dan sai ya amshi hukunci dai-dai da iyawarsa!”_.
        “Insha ALLAHU zamu kiyaye sir. Muna kuma neman afuwa daga gareka”. Suka faɗa a tare cike da girmamawa a garesa. Yayinda Habib da yasan komai ya farune ta sanadinsa yay ƙasa da kansa bayan ya sake matsowa gabansa. “Ka gafarceni Master, dan wannan tabbas sakaci na ne. Amma wlhy sam bansan ta yaya akai hakan ta kasance ba. Sannan koda muka dawo kuma ban fargaba.”
       Hannu kawai ya ɗaga masa batare da yayi magana ba. Sai kuma ya nufi ƙofar fita da ga gidan baki ɗaya. Da kallo duk suka bisa har ya isa ƙofar ya buɗe sannan ya juyo yana kallonsu shima.
      “Zan sake maimaita muku awa goma kacal, na samu cikakken labarin akan ko shiɗin wanene!......” Daga haka ya ida ficewa baki ɗaya.
         A tare suka sauke ajiyar zuciya. Sun tabbatar a salon da yay maganar babu wasa a cikinta, dama can kuma ba wasan ya ke musu ba ballema su ɗauketa wasa. Suma kuma har cikin ransu suna bukatar sanin wanene wanda yay musu wannan tarkon da suka tsallake rijiya da baya?..........✍


           *_Gadai jami'an tsaro basu sami nasarar aikin Hibbah ba, ga kuma Master ya bada awanni goma domin binciko wanda ya haresu, hibbah dai kuma itace ta kai harin da babu niyyar dalilin da su suke kallo. To yaya zata kasance kenan tsakanin Muhibbat Aliyu Hamza da Jami'an ƴan sanda da Master kenan?🤔. TAKUN SAAƘA wasa farin girki👎🏻_*



*TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥

*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*

*_NAJI DADI SHINE GARI......_*

*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*

_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_

*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*

     *NA SABUWAR SHEKARAR 2022*

*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*

*SABBIN LABARAI*

*SABUWAR SHEKARA*

*SABON NISHADI*

*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*

*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*

*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.

*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_

*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_

*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_

*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_

*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*

6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank

Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number

08184017082

*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*

09134848107

Littafi daya

1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).

*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽

#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥







*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
   





      


      *_Typing📲_*



*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*


*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK_*

https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

*_ZAFAFA BIYAR ISTAGRAM_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb

_________________________


*_MG's SKINCARE_*

*_Ina manyan Mata, da manyan yara masu buqatan gyaran jiki da fata akan tabbaci da ingancin kyawu da aikin me kyau?_*💃🏻

*_To maza kuzo ga mg's skincare inda sukeda nagartattun sabulai da creams masu kyau da aiki_*

*_mg's skincare nada black soap dasu molato soap hakama akwai gangariyar sabulu na musamman Mixed na Molato/black soap Wanda hadinsa da aikinsa karshene sbd mun gwada mun tabbatar 💯_*💃🏻💃🏻

*_Akwai Kuma herbal whitening black soap Wanda shima aikinsa na musamman ne a gareku💃🏻_*

*_Sai kuma beauty kit gbdy na gyaran jiki, su cream da komai ne acikin shi💃🏻_*

*_Then akwai bridal kit shima abu 6 be aciki Wanda sai angwada za'a San kayan MG skincare qarshe ne agurin aiki._*

_Duk zaku tabbatar da hakanne ta hanyar nemansu ku gwada kuma har sai kun bama wasu labari💃🏻😍🥰_.

Chat
08062991549
07046881166
07067210195
Call
08064532391
Instagram: glow_with_mgs
Facebook:mg's skincare
Location:kaduna buh we deliver Nationwide
Delivery is not free buh gamasu sari ko wnd yasiya Kaya dayawa kmn 20k above there will be free delivery+ gift


_*Sunada different varieties of frames gamai siyan daya Koh sari*_
_*Sannan muna karban order gamasu hidimar biki kmn dg abinci, snacks, juices nd so on*_
_*Kindly chat with us via 08062991549.*_


____________________


*_Chapter Nine_*


.............Tunda jami'an suka dawo da labarin rashin nasara zukatan manyansu yay matuƙar ƙunci. Awanni ƙalilan suka rage musu da ga umarnin gidan gwamnati. Cikarsu babu Master a hannunsu kuwa yana nufin sun gaza a idanun al'ummar jiharsu da ƙasa baki ɗaya. Hakama ga gwamna da muƙarrabansa.
        A gefe ga gidajen jaridu da duk wata kafar yaɗa labarai sun baza kunnuwa da idanun domin ganin yanda awanni ashirin da huɗu zasu cika tare da wannan ɓarawo a hannunsu ko saɓanin hakan.
       Waɗan nan tunane-tunanen nasu yasa su shirya zaman meeting na gaggawa.

        Dukkan wani babba mai alhakin faɗa aji ya hallara a ɗakin da meeting ɗin zai gudana. Sai wanda ya jagoranci jami'an da suka dawo yanzun nan da shirin kamo Master da yaransa..
         Kowa ka kalla a ɗakin meeting ɗin kasan yaci ya ƙoshi, dan babu wasu kamannin wahala tare da su. Da'ace ƙasace mai ƙyaƙyƙyawan tsari sun cancanci yin ritaya duk su koma gefe a kawo matasa masu jini a jika da basirarsu ke aiki da kaifin ƙwaƙwalwa a zuba a madadinsu. Su kuma su zama dattijai masu bada shawara wa ƙasa ta bayan fage matsayinsu na iyayen ƙasa. Sai dai sam a wannan ƙasar tamu ba haka bane ba. Anyi sakacin barin matasan da ke da basirar zuwa da salonsu na ƙuruciya wajen kawoma ƙasa cigaba zama ƴan ta'adda, dukkan tarin basirarnan tasu da ƙuruciya ta koma aiki ne ƙarƙashin aikata laifuka. Iyayenmu da gwagwarmayar rayuwa da raunin shekaru sukaima yawa sun zama sune masu riƙe da madafun iko wajen zartarwa da hukuntarwa. A duk lokacin da ƙasa tai sakacin rashin amfani da basirar matasa da ƙuruciyarsu wajen aikata alkairi, to lallai shaiɗanu zasuyi amfani da basira da ƙuruciyar waɗanan matasan wajen kafa tantin ta'addancin da zai ruguza ƙasa.
      A ƙasarmu ta gado iyayenmu sune ƴan siyasarmu, sune masu riƙe da madafun iko na mulkin gargajiya da na siyasa, sune riƙe da hukumomin ladabtar da masu laifi, sune riƙe da manyan kuɗaɗe na kasuwanci, sune riƙe da makarantun da ake bamu ilimi, sune.. Sune... Sune komai.
      Babu wata hanya ko ƙofa da suka barma matasan wajen nuna bajintarsu da ƙwazon da ALLAH ya haliccesu da shi. Kallonmu suke masu yawan wauta, masu shashanci, masu ƙuruciya, masu rashin kunya da rashin ganin girman na gaba da su. Masu... Masu... Ta ko ina. Amfaninmu kawai mu cigaba da zama a ƙasa har sai lokacinmu yayi. To yaushene lokacin namu zaiyi? Shin sai muma mun kai irin shekarunsu mu danne na ƙasa da mu kenan?. indai har a haka za'a cigaba da tafiya lallai da alamar ƙasar tamu bazata taɓa zama mai sauyawa ba ko samun ci gaba. Domin anyi sakacin ajiye lokaci an ɗauki rauni.
     Shi kuma lokaci a duk sanda aka gaza amfani da shi ta hanyar da ya dace wucewa yakeyi yabar mai shi da cizon yatsa da dana sani. A lokacin kuma daka buƙaci gyarawa sai ya kufce maka dan kayi sakaci wajen sarrafashi a sanda ya dace. To ya kamata manyan ƙasarmu su fahimci MATASANMU sune LOKACINMU. Cigaba da sakacin ƙinyin amfani da baiwarsu akan lokaci na nufin baragurbi amsarsu su su amfana da wannan damar wajen maidasu masu ruguza ƙasar da ku kuke ganin kunata ginawa. Sanda zakuyi ƙoƙarin son tarosu kuma sunyi nisan da bazasuji kiranku ba sam.
    Bawai munason fiddo da gazawarku bane ma duniya ko goyon bayan laifukan matasa. Muna buƙatar ku duba ku kuma fahimci sai da matasa ƙasa ke iya samun ci gaba. Basu dama kuma shike nufin daƙile dama a hannun masu ɗorasu bisa bigiren ta'addanci. Kun cancanci kuma muyi alfahari da ku, dan kun bamu gudunmawa ta musamman bayan kasancewarku iyaye a garemu.

       Bayan ƙarin bayani da suka samu a bakin jami'in da suka fita bibiyar Master zukatansu sun ƙara ɗaci. Ɗakin yayi shiru kowa na nazari da tunani a cikin zuciyarsa. Ɗaya da ga cikinsu da zuciyarsa ke raya masa wani abu ya nema izinin yin magana.
          “Bismillah, an baka dama. Ya kamata kowa ya faɗi abinda ke bakinsa ko hakan zai bamu wani haske da ga kullewar da kawunanmu sukayi.” Ogan nasu ya faɗa cike da taraddadi.
         Kansa ya jinjina da faɗin, “Thanks you sir. Dama wani tunanine yakemin yawo a zuciya game da ita wannan yarinyar datai mana aikin. Shin baƙwa tunanin shine ya tsara duk hakan kasancewarsa shu'umin mutum kuwa?. Al'amarin da matuƙar mamaki ta yanda ta bibiyesa cikin sauƙi. Idan har dama ba shirinsa bane ta yaya akai ta jefa masa abunda ta samu damar bibiyarsa?”.
       Da sauri wanda ke a kusa da shi ya ashe da faɗin, “Ashe bani kaɗai nake wannan tunanin ba. Tabbas da alamar akwai lauje cikin naɗi game da wannan al'amarin. Nasan za'a iya samun mai ƙwazo da kaifin basirarta, amma yanda al'amarin ya faru da ƙanƙantar shekarunta sai nake ganin kawai shiri ne na musamman akai. Dan bana hangen tana da wani ƙyaƙyƙyawan tunanin da har zuciyarta zata bata damar aikata hakan. Banda shirme da shiririta mi yaran yanzun suka iya? musamman ma ita da ta kasance MACE”. Ya ƙare maganar cikin jin zafi sosai.
          Wanda ya gana da Hibbah dake ta faman buga pen a kan laɓɓansa yana kallonsu da nazarin maganganunsu yay murmushi. “Wannan tunanin namu na ganin yaranmu bazasu iya komai ba wajen taka rawar gani ke maida ƙasarmu da mu baya a koda yaushe. Da hakan kuma suke samun damar yin amfani da basirar tasu a gurɓatacciyar hanya. Tabbas ita ɗin MACE ce kuma ƙaramar yarinya, amma kallonta da rauni na *ɗiya mace* shine babban kuskuren mu. Banace inada tabbacin bata da alaƙa da shi ba, dan shi shu'umin mutum ne hatsabibi da zai iya aikata duk ma abinda bamuyi tunaninsa ba ko munyi. Sai dai banason mu kasa fahimtar cewar itama duk da kasancewar tata MACE zata iya taka wata rawar gani a harkar tsaro da duk wani sha'ani na rayuwa duk da raunin da ALLAH yay mata. Shawarata anan itace mizai hana mu jefa tsuntsu biyu da dutse ɗaya”.
        Sake maida hankalinsu sukai garesa domin sonjin ƙarshen zancen.
      Ya gyara abin maganar gabansa yana binsu da kallo ɗaya bayan ɗaya. “Ma'anar mu jefa tsuntsu biyu da dutse ɗaya shine muyi amfani da wannan yarinyar ta hanyar riƙeta a jikinmu ta zame mana ma'aikaciyar sirri. Ta wannan hanyar zamu amfanu da alkairinta da kaifin basirarta. Mu kuma saka mata ido wajen gano shin akwai alaƙar da zuciyarmu take zargin tsakaninta da shi ko babu?”.
          “Yes! Wannan shawarar taka tayi matuƙa *A.G*”. Ogansu ya faɗa yana tafa masa. Hakanne yasa suma sauran tafa masa duk da wasunsu batai musu ba sam. Dansu babu abinda zukatansu ke ayyana musu sai ganin babu abinda Hibbah zata iya matsayinta na ɗiya MACE mai kuma ƙarancin shekaru.
          Sun cigaba da tattaunawa har zuwa wani lokaci, kafin ogan nasu ya bada damar shigo da Hibbah.

           Hibbah da damuwar ahalinta kecin ranta ta shigo fuskarta a cinkushe babu ko ɗigon walwala. Babu abinda zuciyarta tafi bukata a yanzu kamar tozali da Ummi da yayunta dan tabbatar da babu abinda ya faru da su. Zama tai a kujerar da aka nuna mata bayan ta gaishesu ranta fal jin haushinsu, musamman mutumin ɗazun da tun shigowarta da shi ta fara haɗa ido yana mata murmushi.
          Bayan sun gama nazartarta da ƙare mata kallo ogan nasu yay gyaran muryar da ta saka Hibbah ɗago manyan idanun ta kallesa. Ganin yanda ya kafeta da nasane ya sata sake maida kanta ta duƙar tana wasa da yatsun hannunta.
       “Muhibbat Aliyu Hamza!”.
Ya kirayi sunanta murya babu alamar wasa. Hakanne ya saka gabanta faɗuwa, ta sake ɗagowa tana amsa masa da rawar murya. “Na'am yallaɓai”.
        “Miye alaƙarki da Master!?”.
  “Master kuma yallaɓai? Ni ban sanshi ba”.
       “Kin tabbatar?”.
Kanta ta jinjina masa.
     “Taya za'ai mu yarda baki da alaƙa da shi?. Bayan tsahon shekaru biyu kenan kowace hukuma ta jami'an tsaro farautarsa suke, amma sun gaza koda ganin farcen yatsansa. Sai gashi ke a cikin kwana ɗaya rak kin haresa akan dai-dai?”.
        “Ni wlhy yallaɓai bansanshi ba, bakuma ni da wata alaƙa da shi ko sanin wanene shi. Na aikata duk abinda kukaga nayi ne saboda wasa da rayukan mutane da sukeyi ta hanyar power rider amma badan wani dalili ba”.
       “Okay, mu ɗauka hakanne kamar yanda kika faɗa ɗin. Yanzu wane tunani kikeyi game da makomar ahalinki?”.
        Saurin ɗagowa tai tana kallonsa idanunta cike da ƙwalla. Muryarta na rawa tace, “Amma yallaɓai naga na muku aikin da kuka buƙata dan na tabbata kun kamasa. Kuma kun tabbatar min hakan shine fansar ahalina ai”.
        “Eh tabbas haka muka faɗa, sai dai kuma ba'a samu nasara ba kamar yanda mukai tunanin za'a samu. Rashin samun nasarar kuma na nufin shigar ahalinki a haɗari ta fuska biyu. Na farko mu jami'an tsaro ba zamu barsu ba har sai wancan hatsabibin yazo hannunmu. Hakan shine zai wankeki a garemu mu tabbatar baki da alaƙa da shi, ahalinki kuma su kuɓuta. Na biyu dole ne mu baki kariya yanzun dan tabbas zaki zama abin farautarsa kema dan bazai barki ba tunda kin karya masa tarihi. Dolene kowane motsinki dana ahalinki su kasance a tare damu. Idan kin amince ki cike wannan. Kokuma kiyi tafiyarki amma babu ruwanmu da abinda zai samu ahalinki. Zakuma mu fitar da bayanan sune ke aikata laifukan da muka nuna miki ɗazun da mabanbanta fuskoki. Kinga za'a kamasu a kaisu kotu, da ga ƙarshe a yanke musu hukuncin kisa bayan duniya ta sansu matsayin ƴan ta'adda”
           Sosai tashin hankali ya bayyana a fuskar Hibbah. Idanunta suka ciko da hawaye ta shiga girgiza musu kai laɓɓanta na rawa. “Dan ALLAH yallaɓai karkuyimin haka. Wlhy bani da alaƙa da mutumin nan sam, iya gaskiyata na sanar muku.”
           “Ta hanyar shigowa kiyi aikin sirri da mu ne kawai zai tabbatar mana da hakan, ahalinki kuma su kuɓuta da ga garesa da mu kammu. Gashi ki cike waɗan nan takardun idan har kin amince”.
         Da ƙarfi Hibbah ta rumtse idanunta. Wani irin zafi da ɗaci na sauka mata cikin zuciya. Karan farko na rayuwarta da taji tsiwa batai mata rana ba. Tanajin tsana mai yawan gaske akan mutumin da batasan wanene shi ba. Yayinda gefe na zuciyar tata ke jin haushin waɗan nan jami'ai da ke son yin amfani da damar da ALLAH ya basu ta hanyar amfani da ita. Wani gefen kuma na haske mata ahalinta cikin bala'i mai muni da idan har ta zama sanadin shigarsu cikinsa har gaban abada bazata taɓa yafema kanta ba. A take wani irin kangarewa da bushewar zuciya suka saukar mata. Batare da yin wani dogon nazari ba wautar ƙuruciya ta fisgeta da zuciya wajen ɗaukar pen ta hau cike takardun da ɓarin jiki, batare data duba mi suka ƙunsa ba..
       Fusatar tata ta basu matuƙar mamaki da al'ajabi. Sai dai zukatansu na ayyana musu tanayin komai ne domin ahalinta. Dan fahimtar sune rauninta ya sakasu yin amfani da su wajen tursasata. Aiko sunci nasara, dan ta cike takardun kamar yanda suka buƙata. Ta kuma saka hannu bisa takardar contract ɗin zatai musu aikin sirri har sai sun kama Master. Su kuma bazasu saki wancan bayanan ƙaryar da suka shirya ba domin mata ɗaurin talala saboda ƙarancin shekarunta.
         Sun mata bayanai sosai da zata iya fahimta. Tare da bata date ɗin da zata fara amsar horo na musamman a ɓoye. Da ga ƙarshe sukai mata dogon gargaɗi akan riƙe dukkan abinda suka tattauna matsayin sirri. Dan inhar ta fitar tamkar ta bayyana ƴan uwanta ma duniya ne matsayin ƴan ta'adda. Daga haka suka sallameta.

        Fitowar Hibbah da aka haɗa da jami'ai biyu zasu mata rakkiya zuwa gida yayi dai-dai da isowar Yaya Abubakar da Yaya Muhammad station ɗin. Tana ƙyalla ido a kansu ta kwasa da gudu garesu. Jikin Yaya Abubakar dake gaba ta faɗa tare da fashewa da kuka.
        Shima rungumeta yay yana mai rintse idanunsa da suka kaɗa sukai jajur. Yaya Muhammad ya ƙaraso garesu da sassarfa shima. Dafa kanta da yayine ya sata barin jikin Yaya Abubakar ta rungumeshi shima. Cikin son danne nasa ɓacin ran ya saki murmushi yana ɗagota da shafa kanta. Hannu yasa ya shiga share mata hawaye. “Kukan ya isa haka nan, ba gamu tare da ke ba”. Ya ƙare maganar da sake sakar mata murmushi mai kwantar da hankali.
       Yaya Abubakar da shima ke ƙoƙarin ganin ya shanye tasa da muwar ya ce, “Bara naje zanyi magana da su”.
     Da sauri Hibbah ta riƙo hannunsa tana girgiza kanta. Cikin sanyin da basu santa da shi ba ta ce, “Yaya karka je. Ka barsu kawai babu abinda sukai min”.
            “Karki damu, ba wani abu bane yanzu zan fito”. Yay maganar da zare hannunsa cikin nata yana shafa kanta. Kama hannunta Yaya Muhammad yay shima ya buɗe mota ya sakata, tare da ɗaukar goran ruwa ya miƙa mata. “Sha ruwa ki wanke fuskarki ina zuwa”.
    Hibbah na ƙoƙarin dakatar da shi bai jira cewarta ba ya nufi cikin station ɗin shima. Jitai kamar ta fasa ihu, dan gani take kamar shigar tasu na nufi jami'an zasu riƙesu su sanarma duniyar ƴan ta'adda ɗinne su.
         Ganin an shafe kusan mintuna a shirin tai yunƙurin bin bayansu, sai dai tana buɗe motar suna fitowa kowannensu ransa a ɓace. Ta sauke ajiyar zuciya da yin sagade tai tana kallonsu har suka ƙaraso. Yaya Muhammad ya sake kama hannunta ya sata a motar sannan ya zagaya ya shiga shima. Yayinda Yaya Abubakar ya zauna mazaunin driver.
         
      Suna fara tafiya kiran Ammar ya shigo wayar Yaya Muhammad. Kamar bazai ɗaga ba sai kuma ya ɗaga ɗin. Da ga can Ammar ya fara magana cikin ɗacin murya. “Yaya kazo gida dan ALLAH akwai matsala. Hajiya mama da Abba na nan sun taru akan Ummi harda Junaid. Nayi magana kuma ta dakatar dani. Wlhy zanma Haƙilu (Abba) dukan mutuwa sai dai Ummi ta tsinemin. Har wannan shegiyar tsohuwar ba raga mata zanba dan mahaifina ta haifa ba ni ba.”
        “Ammar!!”
Yaya Muhammad ya kirayi sunansa a tsawace jin zai yanke kiran shima

Please Login or Register in order to submit comment