Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*

*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*

*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.

*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_

*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_

*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_

*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_

*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*

6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank

Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number

08184017082

*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*

09134848107

Littafi daya

1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).

*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽

#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*




*_Typing📲_*




*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*


*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*

https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azbazb

_________________________


*_Chapter Twenty_*

.............A can wajen ɗaurin aure kuwa babu jimawa ƙanin Momy ya dawo. Ta gefen Sheikh Aliy yaɗan ranƙwafo yana magana a hankali cike da alamar ruɗani. “ALLAH ya gafarta malam akwai matsala fa. Na kira Alhaji Halilu yana faɗa min wai a jirasa kar a ɗaura yana zuwa akwai matsala”.
        Sheikh Aliy da ke saurarensa ya ɗan juyo ya dubesa cike da nazari, dan haka kawai sai yaga tamkar ba'a cikin hayyacinsa yake ba, saɓanin ɗazun da ya fita kiran Abba. Fahimtar hakan da Garba yay ne ya sashi sauri gyaɗa kansa cikin son kauda ma malam shakku. Ya sake buɗe murya da ƙyau yana satar kallon na kusa da shi daya ɗaura masa bindiga a kan gefen cikinsa ta cikin malun-malun . “Inaga fa akwai wani abune da bamu sani ba game da su yaran nan. Dan ƴar uwata ma ta kirani akan a dakata”.
        Cike da wasiwasi Sheikh Aliy yace, “To sai dai mu dakata da su na ɓangarensu ɗin, bara a ɗaura wannan. Idan ya iso kafin a kammala kaga sai muji ba'asi ko?”.
         Garba da ke ta faman sinne kai ƙasa wata irin mahaukaciyar zufa na cigaba da tsatstsafo masa ya gyaɗa kai da sauri. Gaba ɗaya jikinsa rawa yake zuciyarsa tamkar zata tsinke dan firgici. Tabbas da yasan abinda zaiyi gamo da shi kenan idan ya tashi kiran Abba da bai tashinba ya kirasa anan gaban su Sheikh Aliyn.
        Su Sheikh Aliy da basu fahimci halin da Garba ke a ciki ba babu ɓata lokaci suka fara gabatar da ɗaurin aure. An fara ɗaura na Yaya Muhammad da ɗiyar Sheikh Aliyu mai suna Maimunatu, sai Yaya Abubakar da Zahidah. Yaya Umar da tasa amaryar mai suna Farida. Sai yaya Usman da Hafsat. Yayinda Muhibbat Aliyu Hamza Gwarzo da angonta Muhammad Shuraim Aliyu suka kasance a ƙarshe.
        Kowa yasha matuƙar mamakin jin yanda al'amarin ya canja. Musamman abokan Abba da danginsu irinsu Kawu Bello. Cikin yanayin shiga ruɗani Kawu Hannafi yace, “ALLAH gafarta malam yaya akai hakan ta faru?. Abinda mukai tunani ba shine muka gani ba mu anan?”.
      Sheikh Aliy da ya dago ya dubesa cike da kamala da sanin darajar kai yace, “Eh lallai an samu tangarɗa ne a tsarin, amma tun farko a haka yake dama. Gaba ɗaya anguna za'a aura musu mataye bib-biyu ne kamar yanda na sani, idan ka cire Muhammad Shuraim mai auran Muhibbat kawai. To sai kuma na samu bayani da ga ɗan uwanku ga shinan.”
     Ya ƙare maganar da nuna musu Garba da shi kaɗai yasan a halin bala'in da yake ciki. Da ƙyar ya haɗiye bushashshen yawun da ya tokare maƙoshinsa tare da ɗan duban inda Shuraim ya ke zaune. Sai dai abinda zai baka mamaki shi Shuraim ɗin ma bashi yake kallo ba. Hankalinsa ma baki ɗaya yana kan gaisuwa da mutane. Ya ɗan muskuta da duban na kusa da shi a kaikaice kafin ya fara jawabi tamkar zai fashe da kuka a ƙasan zuciyarsa. “Eh na kira Alhaji Halilu ne saboda rashin isowarsa akan lokaci, to to shine yake min bayanin a dakata da ɗaura auren ƴaƴan wajen nasa yana zuwa akwai da... Da damuwa”.
        Damuwa?.
Suka haɗa baki kusan tare wajen tambaya. Kai kawai ya gyaɗa musu yana kai hannu ya shafe zufar da ke tsatstsafo masa a goshi.
        Tsofo mai furfura da ke amsa sunan ƙanin Hajiya mama ya mike a fusace. “Wanann ai zancen wofi ne. Anya kuwa Halilu na cikin hankalinsa. Kunga ku tashi muje gidan sai muji ba'asin wannan lalatar da ga ina ta fito haka ne?”.
        Garba ne farkon mikewa kafin kowa. Cikin rawar jiki ya shiga kutsawa tsakkiyar mutane domin samun damar gujema Idris. Shima ɗin bai bisa ba, sai wani shegen murmushin ƙeta da ya saki a kaikaice yay salute ɗin sauran ƴan uwansa da ke cikin taron a maban-banta waje.
         
      To su dai sauran mutane da basusan mike faruwa ba tuni sun mimmiƙe suna mai mikama angunan da suma suke a daskare da tunanin mike faruwa? hannu da tayasu murna. Cikin yaƙe kawai su Yaya Muhammad ke amsa musu. Dan tabbas sun shiga matsanancin ruɗani da wannan lamari. Tabbas basa tunanin Abba zai janye ɗaurin auren nan babu gaira babu dalili cikin sauƙi haka. A kuma shirin Ummi da Sheikh Aliy babu zancen ruguje auren. Dama sun shirya cewar za'a ɗaura auren, za kuma su zauna da matan bibbiyu. Da ga karshe su ginama Abba gadar zaren amfani da yaran wajen ganin dukiyarsu ta dawo hannayensu. Amma ta yaya Abba zai janye auren a wannan ƙurarren lokacin bayan sun san harda shi aka fito zuwa wajen ɗaurin auren ma.
          Duk yanda sukaso son tsayawa su gaisa da ƴan uwa da abokan arziki da suka taru dan tayasu murna hakan ya gagara. Dole suka kwashi tawagarsu suka nufi gida kamar yanda su Kawu Bellon sukayi.
          Wani mugun murmushi Musbahu ya saki lokacin da tawagar su Kawu Bello ke rige-rigen shiga motoci domin tafiya gida. Hannu ya kai bisa kunnensa ya gyara abinda ke maƙale, kafin ya fara magana cike da girmamawa. Yanda yake magana  hankali ne yasa babu mai jinsa, sai jinjina kansa da yayi tayi da kai  dubansa ga Zaidu da ke facing nashi. Da idanu yay masa alamar ya bi bayansu. Da alama yayi hakanne bisa umarnin wanda yake wayar da shi.
       Cikin masa jinjina Zaidu ya kaɗa kai tare da saurin buɗe motar gefensa ya shige ya rufama su Yaya Muhammad da suka wuce a ƙarshe baya.
        Shima janye jikinsa yay da ga cikin mutane yana yima sauran alama cikin inkiya. Motocin da duk sukazo a cikinsu suka shishshiga. Da sauri shima Rabi'u da ya tuƙo Musbahu da ke amsa sunan Shuraim a fuska ya buɗe masa motar da sukazo. Duk wanda ya ga a yanda suka bar massallacin zai ɗauka suma sunbi bayan su Yaya Muhammad ne. Sai dai sam ba haka bane. Dan suna hawa titi duk suka rarrabu.
       Rabi'u da ke ƙara gudun motar yace, “Musbahu kira Habib mu haɗu a roundabout”.
         Musbahu na ƙoƙarin zare malum-malum ɗin jikinsa ya amsa da faɗin, “Okay ka ƙara gudu mu samesu muma, dan Master yace karmu ɓata lokaci”. Yay maganar yana ƙoƙarin kiran Habib ɗin da ke can tare da Hibbah, wadda har zuwa yanzun a cikin sumar abinda suka shaƙa mata take.
        Musbahu ya ajiye wayar da kallon Rabi'u ta mirror. “Insha ALLAHU zamu isa a tare dan shima yana hanya”.
       Kai Rabi'u ya jinjina masa yana cigaba da tuƙinsa. Yayinda Musbahu ya kuma shiga ƙokarin kiran waya again. Ana ɗagawa daga can ya fara magana cikin tattaro nutsuwarsa. “Master komai ya kammala gamu nan a hanya. Kamar yanda kace kuma Zaidu ya bisu can”. Ya ɗanyi shiru yana sauraren mi ake faɗi da ga can, kafin ya sake faɗin, “Okay sir” cikin girmamawa tamkar yana  gabansa.
Yana ajiye wayar Rabi'u ya fara dariya. “Angon bogi sai ka cire facemask ɗin tunda mun baro wajen”. Dariya shima Musbahu ya sanya da kai hannu yana ƙoƙarin zame facemask ɗin. “Ai ka bari kawai ɗan uwa. A kullum al'amarin Master ƙara tsoratani yake. Shi wannan auren kuma ko miye manufarsa? Oho. Kaga dai komai ya tafi tamkar yanda ya tsara. Yarinyarnan ta saka kanta a ramin *Damisa*”.
“Tsundum ma kuwa. Sai dai ALLAH Musbahu har cikin raina ina addu'ar ALLAH yasa mun sami aunty ke nan har abada. Tunda kaga tunda muke bai taɓa saka mace a cikin lamarinsa ba, koda tai masa laifi ne sai dai ya hukuntata ya barta a inda ya ganta. Amma wannan harda su aure”.
“Ai ni kaina al'amarin na ɗauremin kai. Sai dai kasan shi mutum ne tamkar hawainiya, baka isa gane launin da yake sara ba. ALLAH dai ya ƙarama Master mu lafiya da nisan kwana”.
“Amin ya Rabbi” Rabi'u ya faɗa dai-dai suna isowa roundabout. Cikin ƙanƙanin lokaci duk suka gane junansu. Gefen titi suka gangara bayan sun shanye roundabout ɗin. Su Idris da ke a sauran motocin suka firfito suka shiga inda su Musbahu suke. Yayinda Habib yake tare da Hibba shi kaɗai. Nan suka bar motocin da su Salis ɗin suke ciki da suka tafi da mota biyu kacal.


★★★★★

        A ɓangaren abokan Abba suma abin dai ya basu mamaki, dan da yawansu sun san wanann aurene na manufa mai muhimmanci ga rayuwar Abban. Musamman ma abokan shiɗancinsu su Alhaji Alu. Gashi tun kiran da Alhaji Alu ɗin yay masa bai daga ba kowama bai sake samun lambar tashi ba. Sai lamba busy ake nuna musu.
      Ran Alhaji Alu ya ɓaci matuƙa, yayinda wani gefe na zuciyarsa ke tunanin kodai ba lafiya ba?. Dan shi kam yasan Abba tamkar yunwar cikinsa. Hasalima shine wanda ya sakashi a harkar Homo tun farkon zuwansa garin. Dan haka yasan sirrinkan abubuwa masu yawan gaske na Abban.
       “Yauwa ga ɗayan layinsa ya shiga”.
     Cewar Alhaji Balele abokin shaidancin su Abban shima.
       Gaba ɗaya su Alhaji Alu suka zuba masa ido dai-dai shi kuma yana saka wayar a kunne kasancewar an ɗaga. Cikin nishin sheɗancin da Abba suke tsaka da aikatawa shi da A.G ya ɗaga wayar da ƙyar yana kaiwa kunnensa.
       Cikin suɓutar baki da takaicin kishi Alhaji Balele ya ce, “Iyee. Wato kai kana can akan wani ana nan ana dama fura akanka. Halan daɗin abinda kakeyi ne ya sakaka janye ɗaurin auren ƴaƴanka bayan ka taramu anan tamkar wasu marasa aikinyi Alhaji Halilu!!”.
       A wani irin firgici da dukan zuciyar Abba da maganar Alhaji Balele tayi ya sakashi hankaɗa A.G gaba yana janye jikinsa a nashi da faɗin, “What?!, Alhaji Balele mi kake faɗa haka ne?”.
      Tsaki Alhaji Balele yaja tare da yanke wayar. Hakan ya saka Abba sake rikicewa ya ingije A.G da ke ƙoƙarin sake ruƙosa. Wandonsa ya fisga a firgice yana ƙoƙarin sakawa.
       “Alhaji Halilu wai miye haka?”.
       “Bazaka gane ba A.G.”
Abba ya faɗa yana fincikar tissue ya goge jikinsa tare da ƙarasa saka wandonsa. Sandunan da ke taimaka masa a tafiya ya ɗauka cikin rawar jiki da tsallen da zuciyarsa keyi a ƙirji ya fice.
      Wani irin wawan tsaki A.G ya ja cike da tsantsar takaici yana raka bayan Abba da ke tafiya da ɗangyashi da harara. Ina Abba baima san yanai ba. Dan gaba ɗaya a birkice yake da jin bayanan Alhaji Alu. babu wanda yake zuwa masa cikin ido sai Hibbah da labarin da A.G ya basa akan Hibbah dama tayi agreement da su akan su kamashi da duk mai hannu a ɗaurin auren. Inhar abinda yaji da ga bakin Alhaji Balele gaskiyane kenan matsiyaciyar yarinyarnan bada Jami'an tsaro kawai ta shirya hakanba? Ko kuwa ta fahimci A.G wasa zaiyi da hankalinta shiyyasa ta canja salo. Su suna mata kallon ƙaramar yarinya shakatafi ashe ba haka bane sam, sune takema kallon shakatafin.
         Tun fitowar Abban maigadi ya fahimci babu lafiya, musamman da ba jimawa yay da gama reren gudun bin matar ɗazun ba. ya mike zaram tare da nufar gate danya buɗe ganin mota ya nufa shima. A wani irin mahaukacin gudu Abba ya fice a gidan..............✍


     
TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥

*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*

*_NAJI DADI SHINE GARI......_*

*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*

_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_

*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*

     *NA SABUWAR SHEKARAR 2022*

*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*

*SABBIN LABARAI*

*SABUWAR SHEKARA*

*SABON NISHADI*

*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*

*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*

*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.

*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_

*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_

*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_

*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_

*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*

6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank

Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number

08184017082

*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*

09134848107

Littafi daya

1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).

*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽

#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*za





*_Typing📲_*




*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*


*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*

https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS


*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*

https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw


_________________________


*_Chapter Twenty one_*

............A matuƙar hargitse Abba ya samu gidan, da ƙyar ya iya kutsa kai ya isa ga su Hajiya mama da Garba kema bayanin yanda akayi. Saboda labarin yanda ɗaurin auren ya kasance na faruwa Hajiya mama ta nufi sashen Ummi a hargitse zata fara zubar da tujara Garban ya dakatar da su.
        “Sam ba laifin Asiya bane. Dan a wannan gaɓar tafi kowa cancantar aima jaje, a kuma tausaya mata.”
        A fusace Hajiya mama ta juyi garesa kasancewar ɗa ne a gareta. dan kuwa ɗan ƙanwarta ne. “Garba har yaushe kasan makircin Asiya? da shaiɗancinta da zakayi ƙoƙarin kareta akan abinda yake zahiri. Ni dama nasan shurun da tai da yarda da wannan auren bana arziƙi baneba. To wlhy yau ɗin nan......”
      “Inna ku saurareni”. Garba ya katse hajiya mama. A dai-dai lokacin kuma Abba ya iso da ƙyar garesu, dan illahirin ƙafarsa rawa ma take tamkar karayar tasa na neman dawowa sabuwa ne.
        Garba ya cigaba da faɗin, “Sam ba laifin Asiya bane. Dan ba kowa ne ya canja ɗaurin auren nan ba sai shi yaron da ya auri ita Muhhibatu.
        Cikin matuƙar mamaki hajiya mama ta ce,“Shi Shuraim ɗinne ya canja ɗaurin auren? To a dalilin mi zaiyi hakan?”.
        “Wlhy Inna nima ban saniba. Sai dai gaskiya kunyi ganganci haɗa auren yarinyar nan da yaron. Dan hatsabibin mutumne fiye da hasashen mai hankali. Na tabbatar da hakan da idanun. Shine ya hanani kiran Yaya Halilu. Ya tsaramin abinda naje na sanarma Sheikh Aliy. Ya tsoratani da inhar banyi yanda yake so ba zai kasheni. Ya nunamin mutanensa da ke a kowace kusurwa na cikin massallacin, wanda alama kawai zai musu numfashin duk wanda ke cikin massallacin ya dakata da aiki. Na tsorata matuƙa, dan nasan zai iya aikata abinda yafi haka. Mutumin daya iya zuwa muku da fuskar mutanen kirki ya yaudareku sai kasheni zai gagaresa. Hakanne ya sani bin umarninsa naje na faɗama malam yanda yace. Wlhy ban sake kiɗima ba sai da na tsugunna gaban malam ina faɗa masa wani yaro dake gefen malam ɗin ya ɗoramin bindika akan ciki batare da kowa a cikinku ya lura ba. Tayaya kuke tunanin zan iya ƙin bin umarninsa.”
             Yaya Abubakar da zukatansu ke neman faso ƙirazansu su fito a rikice yace, “Uncle Garba kace shine Shuraim?”.
         “Abubakar wlhy shine Shuraim, na tabbatar da shi kuka ɗaurama ita wannan yarinyar Muhibbatu aure”.
           Ai gaba ɗaya wajen ya sake ruɗewa. Ummi tai baya zata faɗi sai da Hajiya Mardiyya ta tarota. Abba kam wata mummunar hajijiyar ruɗani ce ke neman zubar da shi shima. Yayinda wani tsoro-tsoro firgici-firgici ya sashi fara waige-waige tamkar Shuraim ɗin na tare da su a wajen.. Abinda bai ganeba anan, miyasa Shuraim zai dakatar da ɗaurin auren ƴaƴansa da su Usman? Tunda gashi ya cika umarnin aikin auren ita Muhhibat?. Wayarsa ya shiga lalube yana ƙoƙarin fita a wajen.
      A.G ya kira, wanda sai da tana gab da tsinkewa ya ɗaga cikin ɓacin rai. “Malam miye kuma na kiran....?”
     Katseshi Abba yay da faɗin, “Ko kasan Master ne ya rusa ɗaurin auren ƴaƴana bayan shi an ɗaura nasa da yarinyar nan”.
     Cikin taɓe baki A.G yace, “To kai mi kake tunani? Kasan dai shi baya abu da ka, zata iya yuwuwa akwai dalilinsa nayin hakan, dan kawai ya bada ƙafa kamar yanda ya saba”.
      “Ina ba haka banee!!”.
Abbah da ke a birkice ya faɗa cikin matsananciyar tsawa.
     “Ya kake min ihu haka ne? Alhaji Halilu?”.
       “Ya bazan maka Ihu ba bayan kai ne ka tsara komai.....”
      “Muka dai tsara, tunda komai da yardarka akayi, a kuma gabanka bawai a boye ba.”
        Abba ya buɗe baki zaiyi magana A.G ya katsesa da faɗin,
    “Kaga ina zuwa gashi ana kirana da ga office. Zan kiraka”. Bai jira cewar Abba ba ya yanke kiran dan ogansa ne ke kiran nasa, da alama tsiyar da Master ya tafka harta fito kenan. Wani irin ƙarajin baƙin ciki Abba ya saki shi kaɗai a ɗakinsa, ji yake tamkar ya rotsa wayar tasa da ƙasa kawai ya huta. Jikinsa kansa ta ko'ina rawa yake da tsatstsafo da zufa, kansa ya kulle ya kasa fahimtar komai game da abinda Master ya aikata.

        Hargitsewar gidan yasa babu wanda ya farga da rashin Hibbah. Dan ita kanta Ummi ƴaƴanta nacan zagaye da ita kowa nason ganin hankalinta ya dawo jikinta. Yayinda acan tsakar gida Hajiya mama ke doka rantsuwa tana direwa akan sam bata yarda ba wanann shirin Ummi ne da ƴaƴanta. Tabbas sune suka saka Shuraim ɗin yayi haka. Da yawan mutane maganar Hajiya maman tayi tasiri a garesu, musamman da ya kasance alaƙar Hibbah da Shuraim ɗin kawai kowa ke kallo a zahiri da kuma ɗaura auren su Yaya Muhammad da wasu matan daban alhalin su su Hajiya mama basu san da zancen ba sai yanzu da aka ɗaura.
      Gidan ya ruɗe sai cece kuce ke tashi ta ko ina. Kowa na faɗin albarkacin bakinsa da hasashen zuciyarsa.

        Cikin ƙarfin hali Ummi da tun fara tujarar Hajiya Mama yaranta suka kamata suka shige ciki da ita ganin yanda duk suka tattara kansu gareta ta haɗiye tashin hankalinta da ruɗani tana mai duban su Yaya Usman ɗin da su kansu bawai suna cikin cikakken hankalinsu bane akan al'amarin. Kan Yaya Abubakar da ke kusa da ita ta dafa tana murmushi. “Har yanzu zuciyata ta kasa daina yimasa ƙyaƙyƙyawan zato. Dukkanin cikamakin kamala da mutunci a bayyane suke garesa, shiyyasa nai saurin aminta da aura masa Tanee. Amma ta yaya fari zai koma baƙi a wanan ranar?, bayan har yanzu idanuna da zuciyata sun ƙi kallon komai da baƙin”.
        Cikin taraddadi da jan gwauron numfashi Yaya Abubakar yace, “Dama nasan hatsabibin nan bazai ƙyale Hibbah ba. Dan ta masa tabo irin wanda bazai gogu a cikin tarihinsa ba. Hakan yasani yarda da amincewar aima ta aure ko zata kuɓuta daga garesa. Ashe mun riga mun daɗe da kasancewa cikin lissafinsa, ko tantama banayi akan lallai shu'umin nan Master ne yazo mana da fuskar Shuraim. Sai dai ina mamaki matuƙa ta yanda ya kuɓutar da mu daga auren waɗan nan yaran. Mi hakan ke nufi ne?”.
          Ammar ya ɗago kansa da ga ɗorawar da yay bisa cinyar Ummi a firgice yana faɗin, “Yayamu Master fa kace? Gawurtaccen ɓarawon da kuke nema ruwa a jallo ko wa? Danni ban gane ba”.
         Numfashi yaya Abubakar ya fusga da ƙarfi yana jinjinama Ammar kai alamar tabbatarwa. Tare da bin fuskokin sauran ƴan uwansa da suma ruɗanin ne ƙarara ya bayyana akan fuskokinsu har suka gaza motsawa.
      Cikin ɗan rawar jiki Ummi tace, “Abubakar mi kake faɗane haka? Kana nufin yaron kwanaki da ƴan sanda suka sakata tai aiki akansa?”.
      Yaya Abubakar da shi kaɗai yasan lissafin da zuciyarsa keyi ya ɗan firzar da numfashi yana ciza lip ɗinsa na ƙasa da duban Ummin tasu cike da kulawa. “Ummi ki kwantar da hankalinki. Babu abinda zai samu Muhibbat da izinin ALLAH.....”
      Da sauri Ammar ya amshe zancen da faɗin, “Ummi mugodema ALLAH ma da kafin a kaita gidansa ne komai ya fito. Yanzu kunga ko a kotu ne a raba auren kawai sai a bama Yaya Isma'il dama sunfi dacewa”.
        Sosai maganar Ammar ɗin tai tasiri a garesu har Yaya Muhammad ya shafa kansa yana ɗan murmushi.
        Yaya Abubakar kam ɗago kai yayi ya kallesa tamkar wanda zancen yayma allura. cikin nazarin furucin na ammar, ya ɗan kaɗa kai yana jujjuyawa, dan baya son faɗar abinda a yanzu zuciyarsa ke hasko masa kai tsaye saboda Ummi. Miƙewa yay yana faɗin, “Komai ma da baƙwa tunani zai iya yi. Sai dai inaji a jikina Muhibbat ce tarkonsa a wannan karon”.
        “Yaya Abubakar kana nufin zai cigaba da bibiyar auta?”. Cewar Usman a tsorace yayinda duk suka bisa da kallo har Ummi.      
     Numfashi Yaya Abubakar ya fesar yana gyaɗa kai dai-dai yana ƙoƙarin kaiwa ƙofar fita. “Bazaka gane lissafinba Umar. Ku dai da ga yanzu dukkanin idanunku su kasance akan Muhibbat ne. Dan duk yanda kuke tunanin wanann shu'umin mutumin yafi ga haka. tabbas bazai taɓa bayyana kansaba bayan bai gama tsara yanda komai zai tafi masa ba.”
      Da kallo kawai suka bisa harya fice yana ƙoƙarin kai waya bisa kunnensa. Da alama kira yayi. Kafin Ammar ya miƙe yana faɗin “bara na nemota itama.”
      Kai kawai suka iya jinjina masa, dan jikin kowa ya gama sanyi a cikinsu.

★★★★

       A ɓangaren su Musbahu kam koda suka iso L.E street. Habib ne ya shiga sanarma ogan nasu isowar tasu, duk da kuwa sarai yasan yaji.
         Zaune ya sameshi ƙafa ɗaya kan ɗaya a katafaren falon nasu da yaji kayan more rayuwa yana sarrafa system da ke saman cinyarsa. Duk da yaji shigowar Habib ɗin bai ɗago da ga abinda yake ba, sai dai ya amsa masa sallamar akan laɓɓa.
        Habib da ya ɗan kallesa ya risinar da kansa ƙasa da girmamawa yace, “Barka da hutawa Master”.
      Uffan baice ba, bai kuma ɗago ya kalli Habib ɗin ba har tsahon wasu sakanni, sai dai ya jinjina kansa alamar amsawa.
       Habib da ya fahimci ƴan mulkinne a kusa yau sai kawai ya cigaba da magana. “Aiki ya kammala, itama gata tare da mu”.
       Dakatawa yay da ga sarrafa lap-top ɗin, a hankali ya ɗago idanunsa cike da ƙasaitarsa ya saukesu kan Habib ɗin da ya nutsu waje guda saboda tsabar girmamawar da suke bashi.
       Kallo daya yay masa ya janye idanunsa ya maida akan system ɗin da faɗin, “Su Salis?”. Yay maganar a taƙaice cikin sigar tambaya”.
       “Dukanmu tare muka shigo”. Habib ya bashi amsa.
         Lap-top ɗin ya ajiye ya miƙe, batare da ya sake cema Habib ɗin komai ba ya nufi hanyar fita cikin takun da ke nuna cikakkiyar lafiyarsa da nutsuwar da ALLAH ya azurtashi da ita.
       Shima Habib bayansa

Please Login or Register in order to submit comment