Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

cewa komai. Dan zuciyarta a matuƙar raunane take da tausayinsa. Yayinda a gefe takejin matuƙar nutsuwa da kasancewar sa miji ga ɗiyarta ɗaya mace tilo marainiya duk da yaƙi faɗar dalilin nasa na shiga wannan harkar, sai dai tana masa ƙyaƙyƙyawan zato. Sai ɗunbin al'ajab na son zuciya da shahara a zalunci na Halilu wanda suma su Yaya Muhammad ɗin duk yake cin zukatansu......
     Master ya katse tunanin Ummi da faɗin, “Ƴan uwana kuyi haƙuri wannan sirri ne mai matuƙar daraja a gareni, badan ban yarda daku ba kuma na ɓoyesa. Insha ALLAH zaku san dalilina wataran. Na yarda ku san niɗin wanene saboda kuma kun sanar dani sirrinku a lokacin da baku gama sanin niɗin wanene ba. Kun kuma yarda dani duk banzo muku a yanda kukai tsammanina ba. Dan ALLAH ina roƙonku ku bizne wannan sirrin a wannan falon har sai ranar da ya kamata gaskiya ta bayyana kanta ga kowa”.
         “Tabbas ita amana abuce mai nauyi Isma'il. Kuma ka cancanci muriƙe maka ita dan kaima ka riƙe tamu, yayinda kaketa hidima da gwagwarmaya a kanmu batare da mun sani ba. ALLAH ya saka maka da alkairi, ya cigaba da baka kariya akan ayyukanka. Ya kuma baka ikon sanar mana dalilin naka wataran. Bani da haufi game da sauran ƴan uwana akan riƙe maka wannan sirrin, dan nasan mahaifiyarmu ta mana horo akan hakan tunba yanzuba. Ballema wannan sirin riƙesa a garemu tamkar rike namu sirrine. Fita da shi kuwa tamkar tozarta kammune.”
       Yaya Abubakar ya amshe da faɗin, “Wannan gaskiyane Yaya Muhammad. Insha ALLAHU bazakai baƙin ciki akanmu ba Isma'il. A matsayina na jimi'in tsaro kuma zan cigaba da baka gudunmawa insha ALLAH a duk sanda kake buƙata, sai dai ina roƙonka ka tabbatar duk abinda kake aikatawar nan kanada hujja ta gaskiya aranar kare kai, dan idan naci karo da saɓanin hakan komai zai iya faruwa”.
        Murmushi yayi na ƙasaita yana jinjina kansa, “Nagode matuka yan uwana da Ummin mu. Abubakar karka damu kaima insha ALLAH, dan na jima da saninka da kuma gaskiyarka da ƙwazon aiki.
         “Shiyyasa kazo kaketa min ƙafar angulu akan auta ko?”. Yaya Abubakar ya faɗa cikin barkwanci.
    Dariya suka sanya baki ɗaya. Banda Master da murmushi ne kawai nasa dan dama can yawan fara'a ba ɗabi'arsa bace. Sunema yake sakewa da su matuƙa fiye da zato da hasashe. Duk da dai lokacin baya yana zuwa musu ne da fuskar mutane masu sanyin hali saboda salon acting daya ƙware akai like wani ɗan film. Miƙewa yay yana duban agogo ganin dare yaja. “Kai kai bara na barku kuje ga amare fa Yaya Muhammad kar mu take shari'a. Ummi samin albarka na gudu nima”.
         Kansa Ummi ta dafa tana murmushi dan ita kallon ɗa take masa bawai suruki ba. Tai masa addu'a da sanya albarka saboda har yanzu zuciyarta bata gama dai-daita da sheɗancin da Halilu ke shiri akansu ba. Dan ma bataji yana aikata ƙazantar luwaɗi ba kenan. Sallama yay musu ya fita akan zai dawo zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu dan zai zama busy a satin nan.
     Har ƙofar gida su Yaya Umar suka rakoshi zukatansu sakayau bakamar yini da kwanan jiya ba da suka kasance a damuwar rasa Hibbah. Yana tafiya suka rufe gidan suka dawo ciki, zukatansu kuma fal tunanin miyasa yake aikata yahoo? Dan suna buƙatar sanin hakan kodan ƙanwarsu da ke a hannunsa matsayin mata. Bazasu so ta kasance a gararin rayuwa ba, ba kuma zasu so ta kasance da mijin da zai ciyar da ita ta hanyar haram ba.
Sun so zama su tattauna maganar Ummi ta korasu suje ga matansu da safe zatai magana da su.


★★★★

     Tunda yabar gidan su Ummi ajiyar zuciya yaketa faman saukewa da dafe kai saboda ciwon da yake masa na rashin sabon dogon surutun daya zuba a yau. Sai dai kuma yanajin zuciyarsa sakayau tamkar ya sauke wasu kaya masu azabar nauyi dake a kansa ne. Sai da ya biya ta gidan A.G ya amshi takardun aikin Abba sannan ya wuce gida.

       Koda ya isa gidan a falo ya samu su Habib sun baje kowa da hidimar da yakeyi, ga kayan ciye-ciye sun baje tamkar wata sabuwar bola. Shigowar tasa ce ta saka falon ɗaukar shiru kowa ya nutsu. Cike da girmamawa a garesa tamkar yanda suka saba suka shiga masa barka da zuwa. Hannu ya ɗan ɗaga musu yana bin falon da kallo fuska a tamke da binsu da harara. Sun san laifinsu dan haka suka shiga sosa ƙeya kowa na kai hannu a sace yana ɗauke ledar gabansa da su gwangwanaye.
    Komai baice musu ba ya nufi upstairs ɗin yana hawa steps ɗin a kasalance da izzar data zamewa gaɓansa jiki. A dai-dai nan Hibbah da yunwa da damuwa ke neman halakawa ta fito daga cikin ɗaki itama cikin ɗan layin barcin data fara tun bayan idar da salar isha'i. Abincin data hanga a shirye a dining ɗin falon saman ya sata nufar can duk da ta fahimci mai faɗa ajin gidan aka shirya mawa. Kujera taja ta zauna a fili take faɗin, “Daga gani shegen ci ne da wannan mutumin, tunda kuwa ya sakani kuka ɗazun na rantse da yunwa zai kwana shima mugu dangin su Halilu mtsoww ”.
       Karaf kuwa wannan zance a kunnen Master da ke hauro step ɗin ƙarshe. Cije lip ɗinsa na ƙasa yayi tare da kai dubansa gareta da lumsassun idanunsa da tsantsar gajiya da ciwon kai ya kanainaye. Ya ɗan sake tsuke fuska da nufar inda take batare da ita kuma tasan da shigowar tasa ba. Hidimar ma zuba lafiyayyen abincinsa da baba saude ta haɗa masa na musamman takeyi cike da mugunta. Ta ɗiba gasashen hantar da yaji kayan haɗin salad zata kai baki ya riƙe hannun..............✍



*_Gashi nan harda na gobe idan ALLAH ya kaimu😌🚶🏻_*



TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥

*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*

*_NAJI DADI SHINE GARI......_*

*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*

_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_

*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*

     *NA SABUWAR SHEKARAR 2022*

*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*

*SABBIN LABARAI*

*SABUWAR SHEKARA*

*SABON NISHADI*

*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*

*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*

*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.

*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_

*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_

*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_

*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_

*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*

6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank

Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number

08184017082

*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*

09134848107

Littafi daya

1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).

*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽

#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥



*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*



*_Typing📲_*




*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*


*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*

https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb


_________________________


*_Chapter Thirty_*

...........Saurin kallon hannun tayi, ƙamshin mayen turarensa dake daɗewa jikinsa yana rige-rigen shigaa hancinta, hannunta tai ƙoƙarin fisgewa ya ƙara damkewa. Zafin daya ratsata saboda yanda ya matse tafin hannunta da spoon ɗin ne ya tilastata ɗago idanunta dole ta dubesa fuska a kumbure. Kallon ido cikin ido sukaima juna. Tai azamar janye nata dan harga ALLAH ƙwayar idanunsa mai kama data gawurtaccen bajimin zaki tsoto take bata. Ɗan luuu yay da idanun tare da dafa makarin kujerar da take zaune ya ranƙwafo kanta har yanzu hannunsa na riƙe da nata.
       Gaba ɗaya ta dabirce, ta matse jikinta tana sake ƙoƙarin fisge hannunta amma ta kasa.
       “Bayan satan waya ashe har na abinci kin iya kandala?”.
       Ya faɗa a saitin kunneta cikin wani irin slow voice daya saka Hibba ɗan zabura ta matsar da kanta saboda wani irin harbawa da zuciyarta tayi, yayinda gaba ɗaya tsigar jikinta ya miƙe. “Ni wlhy bana sata, kuma ba sunana kandala ba”. Tai maganar da saurin yunƙurawa zata tashi ya sake tsare ko ina har tana jin fita da saukar numfashinsa.
        Wani ɗan lalataccen Murmushin gefen baki ya saki tare da ɗago hannun nata ya kai spoon ɗin bakinsa batare da ya saki hannunba ya sake faɗin, “Tunda na sameki akan abincin da ba naki ba ai sata ne. Sai shegen handama kin cinye naki zaki haɗa da nawa. Da kin sake ko spoon ɗaya ya shiga wannan bakin mai kama dana akku sai kinyi amansa”. Yay maganar yana sake ranƙwafota da ƙyau cikin alamar tabbatar da zancensa. Sai kuma ya saki hannun nata.
        Da sauri ta yarfar da cokalin tamkar wadda ta riƙe maciji. Shima ɗagawa yay da ga ranƙwafawar da yay kanta ya miƙe tsaye sosai akan kafafunsa. Kujerar kusa da ita yaja ya zauna duk da bai ra'ayin cin abincin ba da farko. Plate ɗin data zubama abincin yaja gabansa, tare da sake ɗaukar wani cokalin ya fara ɗiba ya kai bakinsa. Miƙewa tai cikin fushi ta ture kujerar baya tabar gurin hawaye na sakko mata.
         Yi yay kamar baisan da tashin nata ba. Sai da ta kai ƙofar ɗakinta ya ɗan ɗaga ido ya kalleta yana sakin murmushi da kai abincin bakinsa. (Burum!!!) ta rufo ƙofar ɗakin da ƙarfi. Ƙasaitaccen Murmushin ya sake saki yana miƙewa. Ya ja tissue ya goge bakinsa sannan ya janye idonsa daga ƙofar ɗakin nata. Ɗakinsa ya nufa dan babu abinda yake bukata sama da son jin ruwan ɗumi a jikinsa. Tun kafin ya shige ya zame facemask ɗin fuskarsa ya bayyana a Isma'il ɗinsa.

     Hibba na shiga ta faɗa saman gado ta riƙe ciki, dan da gaske yunwar takeji sosai. Babu yanda Baba saude batai da ita ba taci abinci bayan fitarsa gidan amma taƙi. Har tea tace ta haɗo mata tace ta ƙoshi. Hawayen da suka ciko mata ido ta share tana matuƙar jin kewar Umminta da su yaya Muhammad. Ga kayan jikinta sun isheta matuƙar har ƙyanƙyaminsu takeji. Miƙewa tai da tunanin bara ta ɗanyi wanka ko zata rage halin da take ciki ma ta samu damar yin tunanin mafita akan azzalumin nan ɗan homo.
      Kusan mintuna sha biyar sai gata ta fito ɗaure da ɗankwalin kayan nata da dudu iyakarsa cinyarta, cinyar ma ko rabi bai rufeba. Da ace zata duka babu abinda zai hana a ga jikinta. Bakin ɗan kwalin ta ɗan sa tana goge gefen kunnenta zuwa goshinta da ƙananun gashi suka kwanta sosai. Dan masha ALLAH hibbah nada gashi yalwatacce. Ga cika ga tsaho gwargwado.
       A dai-dai lokacin ne kuma Master da har yay shirin barci bayan ya watsa ruwa ya iso bakin ƙofar riƙe da plate daya zuba abincin kaɗan sai tab.. Da kaya kala ɗaya. Hannu ya ɗaura bisa handle ɗin yana sake tsuƙe fuska dan kansa ciwo yake masa matuƙa. A firgice Hibba ta juyo jin an buɗe ƙofar. Ta zazzaro idanunta saboda daburcewa ma ta gagara neman mafita.
        A kanta ya sauke mayatattun idanunsa da barci da gajiya suka maidasu fici-fici. Janyewa yay cike da basarwa yana cigaba da takowa cikin ɗakin tamkar ma bai fahimci dalilin ruɗewar tata ba. Hibba da ta samu nasarar jan hijjab ta saka ta haɗe fuska sosai tana hararsa. “Shi dai musulinci ya bada dokar yanda ya kamata mutum ya shiga waje ai. Amma ba'a dinga faɗoma mutane kamar wata kirsimeti (Christmas) ba”.
      Banza yay mata kamar bai jita ba. Sai ma ajiye tarkacen hannunsa da yay saman mirror ɗin ɗakin. Batare da ya sake dubanta ba ya fara magana a daƙile. “Kiyi shopping na duk abinda kike buƙata ta online, idan kika cimin data bayan haka kuma....humm”. Ya ƙare maganar yana watsa mata hararar data hanata sake magana.
     Harya fara tafiya tunanin da tayi yanzu-yanzu yasata azamar zabura tai saurin zuwa tasha gabansa. Wani irin shegen kallon da ya saka hantar cikinta kaɗawa yay mata, amma itama da yake gwanace ta taurin kai da kafiya sai tai ƙasa da kai kawai bata miƙe ta bashi hanyar data tare masa ba.
       Sake raɓawa ta gefenta yayi zai wuce tamkarma bai gantaba. Sai dai yanda ta durƙusa a gabansa hawaye na zirara a kan fuskarta ya sakashi satar kallonta ta ƙasan ido yana ɗan takawa ya wuceta, sai da ya kama handle ɗin ƙofar sai kuma ya ɗan rumtse idanunsa yana cijar lip nasa tare da dakatawa.      
     Jin ba'a buɗe ƙofar ba yasa Hibba fahintar bai fita ba, bazai tanka mataba ne ya sata fara magana cikin raunin murya na drama ɗin data shirya masa cikin ƙanƙanin lokaci, dan halin da Ummi zata iya tsintar kanta a ciki kawai take hangowa. “Na roƙeka dan ALLAH ka maidani ga ahalina. Mahaifiyar mu tana da rauni na ciwo da kan tashi a dalilin damuwa. Rashina kuma yana ɗaya daga manyan abinda zai iya tada mata shi. Indai nice na janye alwashina, bana buƙatar wani TAKUN SAƘA da kai. Da ga karshe ina roƙonka dan ALLAH ku barmin ahalina. Ku duba maraicinmu da raunin mahaifiyarmu🙏🏻”.
      Ta kare maganar da haɗa hannayenta waje guda alamar roƙo kukan gaskiya na suɓuce mata yanzu kam. Jin bai tanka ba yasa ta ɗago idanunta da hawaye ke cigaba da mata zarya a kumatu ta dubesa. Har yanzu idanunsa a rumtse suke, kuma bai juyoba bai kuma saki ƙofar ba, sai dai sarai yana jinta. Amma tsabar ƙasaita da mulki yamayi tamkar bai san da kasancewarta a wajen ba.
     Wasu irin zafafan hawaye ne suka sake ziraro mata na tsananin tausayin yayunta da begen Ummin ta. Tana buƙatar zuwa garesu kodan ta sanar musu abinda taji ga Abbah, shiyyasa ta ƙudiri ɗaukar duk wani wulaƙancinsa, indai hakan zaisa ta dace da fatanta na komawa gida.
      Tsahon mintuna biyu bai tanka ɗin ba, yana dai sauraren kukanta dake ƙara saka jijiyoyin kansa miƙewa. Ganin haƙanta bai cimma ruwa ba ya sata miƙewa da nufin barin wajen, dan ta gama sallama taurin rai da rashin tausayinsa. Takunta biyu ana uku Ƙasaitacciyar muryarsa ta sakata dakatawa.
        “Ni bana magana biyu”.
    Wani irin ɗaci da jin zafinsa ne ya soki zuciyar Hibbah. Ta cije lips ɗinta da ƙarfi tana matso hawayen da suka sake ciko mata idanu. Cigaba tai da tafiyarta wani duhu-duhu na mamaye idanunta.
       Da ƙyar ta ƙarasa saman gadon kuka na sake kufce mata. Tana tsoron rasa Ummi da yayunta, tana takaicin fasiƙi azzalumi irin Abba ya samu galaba akansu. Sai a yanzunne take jin matuƙar takaicin biye masa tun farko harta maida murtani. Dan zuwa yanzu ta fahimci irin wannan mutumin ba'a cinsu da yaƙi ta ƙuru-ƙuru sai ta siyasa da taku. Hakan na nufin kuma sai ka kwantar da kai wajen fara fahimtar su ɗin su wanene kafin ka samu damar kutse a lamuransu. Inama ɗazu shiru tai masa har yayi ya gama. (Dole ne yanzu ta sake sabon shiri), ta ayyana a ranta tana miƙewa zaune. Mamaki ya kamata ganin bai fita ba. Ya saki ƙofar ya juyo hannayensa harɗe a ƙirjinsa ya tokare ƙafarsa ɗaya jikin ƙofar daya jingina bayansa. Sai idanunsa da ke matuƙar hanata sukuni da tsiwa da ya zuba mata yana wani kallonta tamkar a ɗage.
     Kanta ta maida ta duƙar tana share hawayen. Lumshe idanun yay ya buɗe yana ɗaukesu da ga kanta ya maida kansa ga ƙofar ya jingina. Ta ƙasan ido ya koma kallonta batare da tasan yana cigaba da kallon nata ba duk da tanajinta a takure har yanzun.
      “Zan iya baki dama bisa sharaɗi”.
Da sauri ta dubesa jin abinda ya faɗa. Tai saurin miƙewa ta nufosa cikin sassarfa. “Dan ALLAH Yaya kana nufin zaka barni in tafi wajen Ummi na?”.
       Ta faɗa tana matsoshi gab batare da tasan tayi hakan ba saboda zumuɗi. Idanunsa ya buɗe da ƙyau a kanta jin yanda ta kusanta kanta da shi. Yanda ya zuba mata idanun ya sata tura baki tai ƙasa da kanta.
       Warware hannayensa yayi yana miƙewa da ƙyau ya tsaya kan ƙafafunsa. Hakan sai ya sake kusancin nasu matuƙa. Baya ta ɗan ja tana sake ɓata fuska. Takowa yay ya sake matsawa suka koma yanda suke, bayan ta shiga jan ƙafafunta. Shi kuma ya cigaba da takawa yana binta har suka dangane da mirror. Hannayenta duka biyu ta dafe mirror ɗin da su tai ɗan baya saboda yanda ya tsaya mata ƙiƙam tamkar soja. Bakinta ne ya shiga motsawa alamar akwai magana amma babu damar faɗa.
       Fahimtar hakan ya sakashi fara magana a daƙile yana bin fuskarta da kallo. “Zakiyi aiki na wata guda tare da mu....”
       Zabura tai babu shiri, hakan ya sata faɗawa jikinsa saboda kusancinsu. Bai riƙeta ba, dan haka ta sake komawa baya jikin mirror ɗin tana faɗin, “Kana nufin nima na fara sata?”.
       “Itama sana'ace ai”.
Yay maganar yana tura duka hannayensa a aljihu da lumshe ido ya buɗe lokaci guda.
      “Tab wlhy ban yarda ba. Ƴar yahoo fa kenan mai datsan accaunt ɗin mutane, zamb.......?”
      Tai saurin rumtse idanun da bakinta batare da ta ƙarasa ba saboda ganin ya ɗora hannayensa saman mirror ɗin yayo kanta. Saurin maida lips ɗinta tai cikin baki ta matse tana ƙwaɓe fuska tamkar zatai kuka, dan yanda ya kusanto da fuskarsa da tata har yana busa mata numfashinsa sai ka ɗauka wani abu zai mata. Janye fuskar tasa yay ya maida saitin kunnenta yana sake tsuke fuska. Cikin wani irin Slowly voice da ke nuna gajiyarsa matuƙa ya fara magana yana shaƙar ƙamshin da gyararren gashinta keyi duk da ya ɗan mimmiƙe ta gaba dan tun gyaran ranar ɗaurin aure. “Ashe zaki dawwama tare da Master har tsufanki babu ganin Ummi”.
      “ALLAH ya kiyaye na zauna da mai homo, wlhy kota katanga sai na haura”.
       Baki ya taɓe da ɗage kafaɗa irin I don't care ɗinnan. Batare da ya sake ko kallonta ba ya nufi ƙofa abinsa cike da takun ƙasaitarsa da izza. Kukan ƙarya Hibbah ta fashe da shi duk da dai har cikin ranta tanajin raɗaɗi da takaicinsa. Baiko nuna yasan tanai ba ya buɗe ƙofar ya fice abinsa.
       “Mugu danginsu Halilu. Na rantse sai kayi dana sanin satoni wannan gidan naka, dan saina addabi kowa. Da wani idanunsa abin tsoro”.
     Oho shi baima san tanai ba. Dan tuni ya kai downstairs. Kamar yanda ya saba a duk dare sai da ya leƙa ɗakunan su Salis ya tabbatar suna lafiya. Waɗanda basu kashe fitila ba ya kashe musu. Wasu ma har barguna ya gyara musu a ransa yana ɗan mamakin kwanciyar tasu da wuri yau, sai da ya ƙara musu addu'ar barci kamar yanda ya saba sannan. Compound ya fito ya dudduba. Sai da ya tabbatar komai normal ma anan sannan ya dawo ciki ya kashe sauran fitulun ya haura sama. Ƙarasa shirin barcinsa yay ya haye gado yana godema UBANGIJI da ya kaisa wanann lokaci da rai da lafiya bayan wasu na asibiti wasu ko na gida cikin jiyya matsanciya. Cikin ƙanƙanin lokaci barci yay awon gaba da shi dan yayi matuƙar gajiya. Gashi dama yasha maganin ciwon kan.

     A ɓangaren Hibbah kam sai da ta gama sharce-sharcen ƙwallarta ta cire hijjab ɗin bayan taje ta murzama ƙofar key. Kayan daya ajiye ta warware. T-shirt ɗinsa ce mai gajeren hannu da three quarter wando sai mayen ƙamshinsa sukeyi. Ta ɓata fuska tana cillar da kayan. “Ni bazansa kayan ƴan homo da yahoo ba”. Tai maganar tamkar zatai kuka.
     Abincin da ya ajiye ta ɗauka da bottle water ɗin da suma ya ajiye ta zauna a bakin gado ta fara ci dan da gaske yunwa takeji. Taci sosai tasha ruwan sannan ta miƙe. Kayan ta sake harara dan harga ALLAH tana buƙatar saka sutura a jikinta. Bazata taɓa iya barci da guntun ɗankwalin dake ɗaure a jikin nata ba. Hakama kayan data cire ƙyanƙyaminsu take bazata iya maidasu jikinta ba. Wando da rigar data gama mita a kansu ta ɗauka ta saka. Sai ga three quarter ita ya zamar mata dogo, dan kaɗan ya rage ya rufe idon sawun ƙafarta. Hakama rigar tai mata burun-burun tamkar kaita mata dariya. Baki ta taɓe da yamutsa fuska tana duban kanta a mirror, dan ba karamin addabarta ƙamshin turaren nasa yayi ba.
   Idonta ne ya sauka akan tab ɗin daya ajiye mata. Ita sam tama manta da ita. Ɗauka tai da saurin tana faɗin, “Stupid me. Wai mima ya kaini masa magana bayan ga maganin kukana anan”. Ta ƙare maganar da ƙyalƙyalewa da dariya. Ta dira tsalle ta ɗane gado ranta fal farin ciki. Babu lock a tab ɗin, hakan ya bata damar sauke idanunta akan hoton su Habib su bakwai sai shi na takwas a tsakkiyarsu, duk sun wani kanannaɗe masa jiki tamkar tata. Shima ya shafo fuskar Adam da Khalid dake gefe da gefensa yana ɗan murmushi. Daga ƙasa Habib da Idris suna zaune sun ɗaura kawunansu bisa ƙafarsa ɗai-ɗai sun kwantar. Sai bayansa Musbahu, Zaidu, Salis suna akan kafaɗarsa suma. A kallo ɗaya zaka fahimci tsantsar ƙaunar da sukema juna. Ta ɗan taɓe baki da faɗin, “A haka dai kamar mutanen kirki, sai dai ALLAH kaɗai yasan tsiyatakun da kuke aikatawa.”
       Kauda hoton tai da nufin shiga inda applications suke taci karenta babu babbaka sai taga saɓanin haka. Dan kai tsaye ga shagon da zatai sayayya ya kaita. Cikin takaici tai ƙoƙarin fitowa amma hakan ya gagara. Tamkar zata fasa kuka dan haushi. Har tayi niyyar ajiye tab ɗin sai kuma ta tuna bata da sutura kota yin salla. Da bai taimaketa ya bata waɗan nan ba ma da batasan yaya zatai ba. Kaya ta fara zaɓa harda underwears tanata faman ƙunƙuni. Yanda taketa zaɓar abubuwa zaka fahimci harda mugunta a ciki. Dan sai faman taune lip take tana murmushi. Sai da ta gama yayar kaya san ranta sannan ta dangwarar da tab ɗin tana hararta ta koma ta kwanta duk da bata tunanin zata iya yin barci saboda kewa da damuwar rashin ahalinta a tare da ita.

*_WASHE GARI_*

         Kamar yanda ya saba shine ya tashesu suka wuce massallaci duk da kuwa bayajin daɗi, dan ciwon kan har yanzu bai sakesa ba duk da yayi barci. Koda suka dawo su kaɗai suka shiga ɗakin motsa jiki shi sama ya dawo. Bai ko kalli ɗakin da Hibbah take ba. baima nuna ya tuna tana gidan ba ya shige abinsa.
       A ɓangaren Hibbah ma ta farka dan ta saba. Sai dai tana idar da salla ko azkar batai ba ta haye gado ta koma barci. Barci sosai ta sha har kusan goma saura. Tana buɗe ido da ledoji taci karo manya-manya guda uku. Fahimtar kallo daga nesa bazai mataba ya sata sakkowa taje garesu. Ɗan bubbuɗewa tai sai taci karo da kayan datai shopping jiya da dare ta online. Babu shiri ta shiga sungumar ledojin duk da akwai nauyi tana kaiwa saman gado ta dinga ɗagasu tana zazzagewa.
      Mamakine ya bayyana a saman fuskarta ƙarara. Dan duk abinda ta zaɓa ɗin an sako mata. Harma da wanda bata zaɓa ba na fanin kayan shafa, sabulai, kayan gyaran gashi, da kayan yan kunne sai takalma. total na kuɗaɗen da aka sakko ta shiga dubawa mamaki na neman halakata. “Anya mutumin nan yana da man kai kuwa? Koda yake ina ɗan yahoo ma yasan zafin kuɗi tunda wasu suka tara ya wawasa. ALLAH ya gani naidai tunda badani ya sato ba ko naci banda zunubi”. Ta faɗa cike da yarda da kai.
       Dama azababben ƙamshin turaren kayansa ya isheta, dan haka ta faɗa wanka. Bata wani jimaba ta fito dan dama bata daɗewa a wanka, da sabbin kayan shafanta

Please Login or Register in order to submit comment