Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

filin sai ya damƙashi hannun amininsa kuma malaminsa har sai da suka fara aiki ya basu. Shiyyasa har yanzu Abba da Hajiya Mama basusan da zancen ginin ba........
          “Ummi inje in kwanta?”.
Hibbah ta katse mata tunani. Shafa kanta Ummi tai tana murmushi. “A'a ban gama da ke ba. Dan banji ita autata tana da saurayi ba ko a'a?”.
       Da sauri Hibbah ta ɓoye kanta tana dariya. “Kai Ummi ni banda wani saurayi. Nifa bazanyi aure ba muna tare mutu karaba”.
       “Tab, to auta an taɓa haka kuwa. Muma ai munason zaman gidanmu aka ɗakkomu aka kawo mu naku gidan muka haifeku.” Ummi ta faɗa tana dariya.
       “Ni dai bazanyiba ALLAH Ummi. Banason nesa da ke da su Yaya. Indai zanyi aure sai dai mutafi tare ko mijin yazo ya zauna a gidanmu to”.
       Dariya sosai Ummi keyi, irin wadda ta jima batayi ba a rayuwarta. Tanee ɗinta kayan shirme da wauta kenan. Da ana haka da ƴaƴa da yawa na tare da iyayensu ai.
       Tashi Hibbah tai da gudu ta haye gadon Ummi ta kudundune a bargo ita a dole kunya ta kama ta. Ummi da ke dariya tace, “To shikenan ai ke baki da matsala tunda Junaid ɗan gidan nan ne sai kiyi zamanki tare dam......”
        “ALLAH Ummi bana sonsa. Da na auri mugun nan gara na mutu”. Hibbah tai saurin yaye bargon idanunta na cikowa da hawaye. Yayinda fuskarta ke nuna tsananin tsoro da tsanar Junaid ɗin da Ummi ta ambata.
        “To shikenan naji. Amma ai kina son Isma'il ko?”.
       Idanu Hibbah ta zaro waje a firgice. “Wane Isma'il ɗin Ummi?”.
       “Mai zuwa nan gidan mana”.
   “Ni dai wlhy a'a Ummi. Shi yayana ne dan ALLAH kibar faɗa.”
         “Oh ALLAH, ke kuwa Tanee wa kike so a rayuwarki? To ko wanda yazo dubani a asibiti jiya? Muhammad Shuraim ko?”.
      Baki Hibbah ta turo amma batace komai ba. Ummi ta cigaba da faɗin, “Tanee kinga shima alamunsa sun nuna mutumin kirki ne nutsatstse. Ina ƙyautata masa zaton alkairi insha ALLAH. Amma zansa ai bincike a kansa inhar kina son nasa”.
          Kwanciya Hibbah tai ta juyama Ummi baya. “Ni Ummi ALLAH ya cika iyayi. Gashi baida fara'a. ga shishshigi ”.
        “Duk shi kaɗai?. To lallai tunda kika iya gano waɗan nan kina sonsa kenan, zaki kuma auresa”.
       Da sauri Hibbah taja bargo da cewa, “Nifa Ummi a'a baiminba. Sai naje China na dawo zanyi aure”.
      “Tanee wannan mafarkinki ne. Amma ban fidda miki ran zaki cikashi ba idan kinyi aure mijinki ya kaiki da kansa”.
         Shiru Hibbah tayi dan an taɓo mata inda kuma bata son. Itama Ummi sai bata sake tankawa ba ta cigaba da hidimarta da lissafin ƙullawa da kwancewa.

       Zuwa takwas Ammar ya shigo ya tada Hibbah dansu haɗa breakfast su wuce islamiyya duk da sunyi latti. Hibbah kamar zatai kuka ta bisa. koda sukaje kitchen ɗin suna aikin suna faɗa har sai da Yaya Abubakar ya shigo ya tsawatar musu saboda kuka da Ammar ya saka Hibbah.
     Suna kammalawa sukai shirin islamiyya. karyawar ma a tsaitsaye sukayita suka fice.

      ★★★
   
   A yinin ranar su Yaya Muhammad duk a gida sukayisa. Suna tare da Umminsu suna shan hira. Basu sake mata maganar tarinta ba, itama batai musu ba. Sai bayan sallar zuhur suma suka wuce islamiyya. Ganin dai har zuwa yamma babu motsin Abbah da su Hajiya Mama yasa Ummi fita wajen maigadi ta tambayesa ko sunyi tafiya ne.
        Baiyi mamaki ba. Dan yasan kaf yaranta a fusace suke da Abban. Bayanin faɗuwar Abban ya bata da kaisa asibiti da akai. Kuma har yau babu wanda ya shigo gidan tun jiyan. Duk da abinda suke mata bataji tayi farin ciki da tsautsayin daya afkawa Abban ba. Sai ma komawa tai falonta ta faɗa duniyar tunani........

_________________________________

      A ɓangaren Abba ba ƙaramar jigata yay ba kafin safiya. Ƙafafu sun kumbura suntum. hakama fuskarsa tamkar ƙwaɓun fulawar sabon burodi. Sauƙinsa ma allurar barci da likitocin sukai masa ganin yanda yake rusar kuka ƙafarsa na masa zogi.
       Sai kusan huɗu na maraice mai gyaran yazo, a cewarsa sun sami lalacewar motane a hanya. Sai dai kuma a zahirin gaskiya ƙaryama yake bai taho ba sai da safen. Komai likitocin basu ce ba. Sai ma damar yaje yay aikinsa da suka bashi, dan haka suka basu sallama.
      
      Ummi na tsaka da tunaninta taji shigowar motoci, mikewa tai ta leƙa ta windown falonta sai ta hango ana fita da Abbah da ga motar Junaid tamkar gawa. Wani irin faɗuwa gabanta yay. Babu shiri ta fito zuwa tsakar gidan itama. Kusan tare suka shiga sashen Momy da su Hajiya mama da ke biye da mai-gyara da Junaid da suka ɗakko Abba ranga-ranga.
         A tsakkiyar falon momy aka shimfiɗe Abba. Sai dai ganin yana numfashi yasa Ummi batace komaiba tabi layin ƴan kallo. Mai-gyara ya fito da kayan aikinsa. sanin abinda zaije ya dawo ya sashi faɗama Junaid cewar ya samo wanda zasu tayasa riƙe Abba dan shi kaɗai bazai iyaba. Badan Junaid yaso ba ya mike ya fita. Babu jimawa sai gashi tare da mai-gadinsu da na maƙwafta. Sai wasu yaran makwaftansu su biyu sa'annin Ammar.
         “Yauwa kayi farar dabara da kukazo da yawan”. Cewar mai gyara yana gyara zamansa sosai a gaban kafafun Abba da sukai suntum har ƙyalli sukeyi.
        Junaid da mutanen daya gayyato baki ɗaya suka zagaye Abba mai-gyara ya fara aikinsa. Sai dai abin mamaki duk da barcin da Abba keyi ana taɓa ƙafar yay wata iriyar mahaukaciyar zabura da ballara ihu. “Wayyyyyyyoooooo!!!!!! ALLAH na zasu kasheni na shiga uku ni Halilu!!!”.
      Babu wanda ihun Abba bai gigita ba a falon. amma ahaka mai-gyara ya cigaba da aikinsa ko tausayi babu. Ihu Abbah yake da iya ƙarfin iko. Tun yana zufa har takai ga sakin fitsari. Can fa abin mamaki da kunya sai ga kashi.
      Hanci su Ameerah suka shiga toshewa. Su kansu masu riƙon nashi ji suke kamar su sakesa su gudu dan azabar warin kashin. Suma kuwa yayi ya farfaɗo yafi sau uku. Tun yana ihu da murya mai kauri har ya koma siririya. Daga baya ma akabar jinta gaba ɗaya.
       Duk yanda Ummi taso daurewa sai da taji hawaye sun ciko mata idanu. Tai ƙasa da kanta saboda tausayi.

       A cikin wannan halin su Hibbah suka fara dawowa gidan. Ihun Abba ne ya ringa jan hankalinsu suka dinga nufo sashen duk da sun manta shekarar karshe da suka shiga sashen. Su kansu tsoro ya kamasu ganin yanda Abban ya koma. Badan sun so ba dole suka dinga toshe hancuna suma saboda wari.
     Mai gyara ya ɗora kafa da hannun Abba. Sauran raunikan ma aka gyara. Ya shafa magani ya bada wanda za'a cigaba da masa amfani da shi. Kafin a cake masa ƴan kuɗaɗensa masu nauyi. Aka kuma kaisa masauki dan yace sai da safe zai wuce yamma tayi.
          Sai lokacin Hajiya Mama ta farga da su Ummi da yaranta. Ido ɗaya ta kanne ta shiga zazzaga bala'i wai sunzo ganin ƙwaƙwaf. Cikin subutar baki Hibbah taja wani wawan tsaki da faɗin, “Kaɗan ma ya gani. Ummin mu yaso gani a wanann kwatankwacin bala'in sai shi ALLAH ya tsundumasa. In takamarsa zalunci wataran ƙafar za'a guntule.....”
     Wata muguwar cafka Hajiya mama ta kaima Hibbah ta ko kwasa a guje tabar sashen. Zata bita Junaid ya riƙota cikin masifa. “Barta kakus. Nine nan zanci uban uwarta, wancan bakin nata mai kama da na reza yau sai na ɓaɓɓarkasa wlhy. Shegiyar yarinya mai bakin akku. Idanma an sakata tazo ta faɗa ne to ina dai-dai da kowane shege a gidan nan. Wama ya sani ko kada mana shi akaiyi. Kai bama zan yardaba ALLAH sai munje kotu”.
        Tsaki Ammar yaja tare da kama hannun Ummi suka fice. Su Yaya Muhammad ma kai kawai suka girgiza sukai gaba abinsu da barin su Hajiya mama da takaici. Dan so sukai su tanka su kwashe komai sukai wajen ƴan sanda. Daga nan a wuce kotu har ALLAH yasa sukai gaɓar da suke fata. To sai akai rashin sa'a yaran Ummi masu lurane suka manna musu hauka.
      Koda suka koma sashensu basuga Hibbah ba. Sun san ta boye kanta a daki ne saboda tasan tayo laifi, tunda suma suna hanata rashin kunyar. Alwala ma duk sukayi suka fice masallaci. Ummi ma ta nufi ɗakinta gabatar da tata duk da tana jiyo hayaniyar su hajiya mama daketa zage-zage har yanzun.
       Koda suka dawo bayan sallar isha'i Hibbah bata yarda ta fitoba har suka ci abinci sukai hira kowa ya tafi makwanci. Babu kuma wanda ya nemeta dan a tabbatar mata batai dai-daiba.

      Tun a daren maƙwafta ke shigowa duba Abba dan sunji ihun da yayta zugawa. Duk wanda ya shigo sai su hajiya mama suce yaran Ummi ne suka jima Abban ciwo. Da yawa ba yarda suke ba, saboda sunsan halin matsi da Ummi ke fuskanta a gidan da yaranta tun suna kanana. Dan tunkan ma Hajiya mama ta dawo gidan da zama idan tazo da ga ƙauye haka zataita zubda tujara wa Ummi kala-kala, tunda kuwa mijinta ya rasu ta dawo da zama baki ɗaya sai Ummi ta shiga uku ta lalace itada ƴaƴan ta, gashi nan har yanzu basu huta ba.

  *_______________________________*

               Shiru kakejin Master da yaransa tamkar basa ƙasar. Babu kalar takalar da jami'an tsaro basu masa ba a kafafen ƴaɗa labarai yay kunnen uwar shegu da kowa. Ko randa zancen kai matar gwamna koto ya fito da ga hukumar yaƙi da ta'annatin kayan gwamnati babu wanda yaji ko tarin master. Shi dama ba sanin taka mai-mai accaunt na duka handles nashi akai ba. Dan kullum cikin canja salo yake.
Sun cigaba da saka idon ganin kozai tanka amma shiru, dan haka suka cigaba da shirya masa tarkuna ta ƙarƙashin ƙasa dan sunsan tabbas zaije kotun.

    ★★

      Yau da yamma Hibbah na makaranta ta fito class cike da gajiya da yunwa. Fatanta kawai ta samu motar komawa gida da wuri dan su Hafsat tuni sun wuce saboda ba department nasu ɗaya ba. Su kuma yau duk lecture ɗin safe sukayi. Ita kaɗaice tayi na yamma.
          Ta samu da yawan ɗalibai dake ta tutsutsun shiga motar da duk tazo wucewa. Dan haka tai gaba saboda kanta dake ciwo. Cikin sa'a kuwa tana matsawa gaban sai ga wata taxi ta faka gabanta. Batare da tunanin komaiba ta afka ciki bayan ta sanarma direban inda zai kaita, shi kuma ya faɗa mata kuɗin. Ko ragi bata nema ba dan buƙatarta kawai taje gidan da wuri. Saboda tana tsoron abinda zaije ya dawo ne musamman akan dangin Abbansu dake cike da gidan nasu dubiyar Abba. Dan zuwa yau da yake cika kwana uku jikin nasa da sauƙi.
      Ƴan can asalin kauyensu ne sukazo mota guda duba shi. Sai dai hakan ya bama Ummi mamaki da su kansu, dan sam da ga Abba har hajiya mama bason mu'amula da ƴan ƙauyen sukeba yanzun. Shiyyasa har ƙasan ranta takejin akwai wata a ƙasa da suke ƙullawa.
        Wasu hawayen tausayin Ummi da su kansu ya cika mata ido. bayan hannu tasa ta share tare da kwantar da kanta jikin sit ɗin ta lumshe idanu ko kanta zai sassauta sara mata.......

         Ummi nacan na dakon jiran dawowar Hibbah itama, dan yau da kanta ta soyama Hibbar wainar filawa da tasan tana matuƙar so. Yayinda can ƙasan ranta ke cike da fargabar taruwar dangin mijin nata da nata a gidan. Dan tasan akwai abinda suke ƙullawar da gaske. Sai dai kuma ta saka a ranta komi zasu ƙulla insha ALLAHU ta gama shirya musu a wannan karon. dan itama tun a jiya data fita ta gama tsara komai akan makomar ƴaƴanta. Nasu kawai take jira yanzu ta ɗora da ga inda ta tsaya. 

        Ilai kuwa hasashen Ummi yayi dai-dai, dan tana tsaka da wannan tunanin akai kiranta sashen Abba ɗin. Hijjab ta saka har ƙasa ta tafi. Tun a falo Maomy ta sakar mata wani habaicin da ya tsaya mata a rai. Sai dai batace komai ba ta ƙarasa falon Abba.
        Su kawu Bello ta samu da wasu a dangin Abban. Sai hajiya mama. Bayan ta gaishesu ta nema waje ta zauna duk da ba dukansu suka amsa ba. 
            A gadarance Kawu Ayuba ya fara bayani. “Hasiya basai mun sake ɓata lokacin tisa magana ba. Nasan kema tunda kika ganmu anan kinsan zancen. Kamar yanda su Yaya Ballo sukazo kwanaki akan maganar auren ƴaƴanki da yaran wajen Alhaji Halilu yanzu batun saka rana ne ya tashi. Saboda tsabar halacci da hangen nesa irin nasa yace kawai tunda munzo dubasa a saka. Shi baya wani bukatar ƴan kunji-kunji tunda batun tuwona maina akeyi. To a yanzu haka dai ga kayan saka rana nan ma duk ya saya dan yace shine uban anguna shine na amare, kuma koma bai faɗa ba dama shine, tunda tun suna kananunsu shiketa wahala akansu. Koda kuwa mahaifinsu na raye shine mai bada auren nasu ai dama. Basai na jaki da nisa ba. Yanzu haka dai an yanke ranar aure wata biyu kacal. Batun kayan aure na akwati da kukeyi anan binni duk yace zaiyi baya buƙatar komai da ga yaran nan. Ita kuma Muhibbatu tunda kun saka yarinya ta nuna bata bukatar wannan haɗin, da azo ta bijire bayan auren kota illata yaro kawai za'a fasa. Za'a bata shi wanda ta kawo ɗin ALLAH ya basu zaman lafiya.....”
      A firgice Ummi ta dago ta dubi Abba. Wani shegen murmushi ya sakar mata tare da kashe mata ido ɗaya. Zatai magana yay saurin katseta cikin marairaicewa. “Hakan ai shine yafi kwanciyar hankali Kawu Ayuba. Kaga da alalata zuminci gara dai abi komai a sannu zaifi. Kuma ita mace ce. Banason a cuta mata akan abinda bataso. Dan yarinyace mai hankali da nutsuwa. Duk da damuwar da Junaid ɗin ya shiga nace ya haƙura kawai tunda tana da zaɓinta. Kuma zaɓin nata ma naga mutumin kirkine sunansa Muhammad Shuraim. Ɗan gidan Alhaji Aliyu ne mutumin kirki. Inajin kunyar ma nace bazan bashi jinina ba”.
        Harga ALLAH Ummi ta shiga ruɗani, ta kuma ji ɗan sanyi ta wani fannin. Dan tana mamakin ta yaya shi Abban yasan da zancen zuwan Iyayen Muhammad Shuraim ɗin? Kodai su masu kawo kuɗinne sukai mistake ɗin zuwa nan kawo kuɗin maimakon gidan Sheikh Aliyu Abdul-ra'uff Maina? Lallai akwai abinda bata sani ba. Dan akwai manufa da dalilin yin hakan ga Abba, saboda halin makircinsa da ta sani. Hakanan salin alin bazai hana ɗansa ba ya bama wani.........
          “Wannan shaiɗancin dai nasan ita ta kitsashi. Duka yarinyar nawa take da tasan wani bijirema zaɓin iyaye. Ni wlhy dan Halilun yace a barta ne da baza'a bari ba. Sai dai idan an aura mata Junaidun ta mutu”. Sababin Kawu Bello ya katse ma Ummi tunaninta.
      Cikin makirci Abba ya amshe da faɗin, “A'a kawu bello ba'ayi hakaba ai. shima wnanan ɗin mutumin kirki ne wlhy. Dan yamafi Junaid nagarta. Muyi fatan ALLAH yasa haka shine yafi alkairi”.
     A take duk ƴan falon suka shiga yabon Abbah da jinjinama ƙoƙarin sa, Ummi kam anata zaginta wai bata da godiyar ALLAH akan ƙoƙarin da Abban keyi tun bayan rasuwar mahaifin su Ammar. Tare da yi mata gugar zana na habaicin asalinta.
     Ita dai uffan batace da su ba. Hasalima hankalinta ya rabune gida biyu. Duk sauran bayanan da suka cigaba dayi sai tama koma bata fahimtar komai. Jinsu kawai dai take da kunne da binsu da ido har aka tashi a taron ko nace suka sallameta.

       Koda ta fito a sashen taso zuwa gidan malam sai dai gudun abinda zaije ya dawo da fitar tata yasa ta haƙura. Dan haka tai kiran numbar wayar matarsa da yake ƙawarta ce suna zuminci sosai duka biyun. Sai dai tasan uwargidan Maimunatu yanzu haka tana Oman da autan gidan dake karatu acan.
     Bugu biyu Malama Jiddah ta ɗauka. Bayan sun gaisa da ɗan barkwancin ƙawaye Ummi take tambayarta ko Malam na nan kuwa?.
        Malama Jiddah tace, “Eh yana nan, sai dai yana tare da kamar baƙin da naji kunyi magana ranar zasuzo yau ɗin. Lafiya dai ko?”.
        “Tofa, kaji wani kuma ruɗanin. Umm Muhammad! Lafiya dai ba lafiya ba. Akan baƙin dama na kirasa ban samu ba......” (Komai Ummi ta zayyane mata da ya faru yanzun anan gidansu).
         “Bara muga baƙin su wuce to sai na sanar masa. Duk da dai inaji a raina ko duk shine ya tsara hakan dan mijin nan naki sai da siyasa ake iya kamasa a hannu. Ya riga ya zama mai fuska biyu inba ka saniba babu mai cewa zai iya sheɗancin da yake zubawa shi da uwarsa Umm Abubakar. Amma ki kwantar da hankalinki dan ALLAH, ALLAH yana tare damu”.
        “Shikenan Umm Muhammad ALLAH yay mana jagora. A gaishe da yaran sai na jiki”.
     Sallama sukai da ga haka zuciyar Ummi fal waswasi da saƙe-saƙe.

*__________________*

             Ido Hibbah ta buɗe a ɗan yanayin razana saboda barcin da ya figeta. Gabanta ya faɗi lokacin da idanunta ke kaiwa waje ta windown motar da aka sauke gilashi baki ɗaya. Mazaunin direban ta kalla tana haɗiyar yawu da ƙarfi saboda bushewar da maƙoshinta yayi lokaci guda. Tai saurin ɓalle murfin motar ta fito domin tabbatar ma kanta inda ya kawotan fa ba anguwarsu bane...............✍




*_Tofa. Ina mai taxi ya kai Hibbah?. Wane ruɗanine ya shiga kan Ummi game da kawo kuɗin auren Hibbah da ga gidan su Shuraim? da alama ta nuna tasan da zancen. Shin malam Aliyu Abdul-Ra'uff Maina ne ya fara aika iyayen Shuraim ga Abba kokuwa yaya abin yake ne? Wane shiri Ummi keyi akan yaranta da takejin ƙarfin gwiwar nasarar kubutar dasu ne haka? Minene shirin Abba shima game da fasa bama Junaid ɗansa auren Hibbah ya yarda ya bama Muhammad Shuraim? Shin kodai dama shine ya turosa batare da ita Ummin ta farga ba?. 🤔tambayoyinfa da yawa. Yayinda ni kaina amsarsu nake nema🚶🏻😩._*


________________________

TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥

*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*

*_NAJI DADI SHINE GARI......_*

*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*

_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_

*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*

     *NA SABUWAR SHEKARAR 2022*

*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*

*SABBIN LABARAI*

*SABUWAR SHEKARA*

*SABON NISHADI*

*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*

*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*

*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.

*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_

*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_

*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_

*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_

*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*

6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank

Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number


08184017082

*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*

09134848107

Littafi daya

1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).

*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽

#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*





*_Typing📲_*




*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*


*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*

https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb


*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*

https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS


*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*

https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw


_________________________


*_Chapter Sixteen_*

.........Da sauri ta dafe kanta da ya sara mata da ƙarfi. Cikin ɗacin murya da zafin da takeji a zuciyarta tace, “Wai nikam mina muku ne na laifi? Dan ALLAH kubar rayuwata ta cigaba da tafiya a yanda take karku sakamin ahali a masifa. Wancan karon kunce dan na bibiyi wanine. Wannan karon kuma mina aikata zaku kawoni nan?”.
            “Duk bani da amsoshin tambayoyin nan naki. Aikina kawai shine ɗakkoki na kawoki nan wajen. Gashi kuma na cika. Amma idan muka shiga da ga ciki harma abinda baki tambaya ba za'a baki amsarsa na sani”.
          A fusace Hibbah ta dubesa zatai magana aka katseta......
      “Gaskiya ya faɗa miki, bashi da amsar da zai baki. Dan haka bismilla ɗiya ta”. Dattijon wancan karon da aka kaita office ɗinsa ya faɗa dai-dai yana ƙarasowa inda suke. Dan tun shigowar taxi ɗin cikin station ɗin yake kallonsu ta window. A fahimtar da yay mata na tsiwa da rashin tsoro da kafiya ya sashi yanke shawarar sakkowa da kansa ƙila tafi jin shakkarsa ta shiga.
     Sai dai kuma ina. Shima a fusace ta kallesa wasu hawaye masu zafi suna sakko mata. Ganin tana motsa  laɓɓanta alamar sonyin magana ya girgiza mata kansa. “Nan ba muhallin da ya dace ki cigaba da cewa komai bane ɗiyata. Ina mai tabbatar miki wannan kiran yasha ban-ban dana farko. Dan kai tsaye ke zai taimaka bamuba Muhibbat. Bakomai yasa nace hakaba sai ƴan uwanki dake gab da shiga haɗari”.
       “Ƴan uwa na?!”. 
Hibbah ta faɗa ƙirjinta na wani harbawa. Uffan jami'in dattijo A.G baice ba ya juya zuwa office ɗinsa. Da sauri tabi bayansa har tana haɗawa da ɗan gudu. Dan ba ƙaramin hargitsa tunaninta maganarsa ta ƙarshe tayi ba. Duk da yanajin tana binsa da gudu bai tsaya ba sai da ya isa har office ɗinsa. Kusan a tare suka shiga da Hibbah. Tai saurin zuwa gabansa ta durƙusa.
       “Uncle dan ALLAH karku cutarmin da ƴan uwa. Ku daina tursasani yi muku abu ta hanyar yimin barazana da su. Kunsan kuwa mi kuka nema haddasama rayuwata a wancan karon? Saura kaɗan na rasa Ummi na, gatana ni da yayuna. Farin cikinmu madubin rayuwarmu. Miyasa kuke son saka alkairi da sharri? Miyasa kuke son yin amfani da ni saboda ku haskaka kanku ma duniya? Miyasa ku ke........”
        “Ya isa ɗiyata. Duk yanda kike tunani ba haka abin yake ba a wannan gaɓar. Yanda kiɗan ya sauya itama rawar zata sauya ne dole. Inason ki nutsu ki bani dukkan hankalinki nan, domin haɗa hannu wajen tabbatar ma mutanenmu abinda suke ganin bazai yuwu ba saboda rauni da ƙarancin shekaru da suke kallo kai tsaye”.
       “Ni bazan nutsu ba, bazan taɓa nutsuwa ba dan ku taurarine masu wutsiya. Dan ALLAH ku daina saka rayuwata data ahalina cikin *_TAKUN SAƘAR KU_* da bawan ALLAHn nan. Bani da alaƙa da komai nasa kamar yanda kuma bani da alaƙa da ku. Indai harkar computer ce na barta har abada duk da kuwa itace burina, itace mafarki na, itace zummata, itace kaifina. Amma saboda cigaba da rayuwar ahalina cikin salama na tattarata na ajiye. Na manta kaina cikin waɗanda suka iya koda kunnata. Please na roƙeku ku barmin rayuwa data ahali su huta. Ku barni naji da damuwar cikin gidanmu ita kaɗai ta isheni”.
      Yanda ta haɗe hannaye tana roƙonsa hawaye na kwarara a kumatunta duk sai tausayinta mai tsanani ya kamashi. Idanunsa suka kaɗa sukai jajur. Kansa ya shiga girgiza mata yana ƙoƙarin kamo hannayenta dake haɗe har yanzu waje guda alamar rokonsa🙏🏻. Sai dai yana kawo hannu ita tai azamar jan nata baya.
        Da sauri yace, “Shike nan naji zan barki ki tafi. Amma ki tabbatar Tabbas kinada alaƙa da Master Muhibbat, saboda wannnan ɗin kasarki ce, kuma a ƙasar taki yake aikata dukkan ɓarnarsa. Sannan rayuwar yayunki da mamanki na cikin haɗari a hannun ƙanin mahaifinku da shi wanda kike ganin baki da alaƙar komi da shi. 1Mu kaɗai ne kawai

Please Login or Register in order to submit comment