Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yabi da saurai suka fita a kusan tare. Kallo ɗaya yay ma su Salis da ke ƙoƙarin fitowa a mota ya ɗauke kansa da cigaba da tafiya cikin izza da ƙasaitarsa tamkar wani jinin mulki. 
       Dai-dai yana isowa inda suke suka haɗa baki wajen faɗin, “Barka da gida Master”.
     Hannu kawai ya ɗaga musu yana nufar motar da Habib ya fita da ita. Da sauri Habib ya buɗe masa motar ta sashin da Hibbah ta ke yana matsawa gefe tamkar yanda sauran suka nutsu.
     Duk da yasan a sume take hakan bai hanashi sake ɗaure fuska ba kafin ya sauke nutsatstsun idanunsa masu kaifin gani a kanta. Sai kuma ya ɗan kaudasu tare da ƙarasa takawa gaban motar da ƙyau yana yamutse fuska. Dai-dai lokacin da yake ranƙwafawa su Habib suka kalli juna, yana ɗagowa ɗauke da Hibbah suka waro idanu waje da saurin maida kawunansu ƙasa.
       Ko kallo basu ishesa ba, sai ma sake tamke fuskar boginsa da yayi ya shiga taku cike da izzarsa da kasaita zuwa cikin gidan ɗauke da Hibbah da batasan wainar da ake toyawa ba.
        Idris ya haɗe yatsunsa waje guda alamar love yana wani cije baki. Sauranma idanu suka shiga kashewa da yin alamar nice👌🏼 cike da shaƙiyanci.
       Tsaf yaga duk iya shegen nasu ta glasess ɗin windows. Ya ɗan ciji lip ɗinsa na ƙasa da tura ƙofar falon da ƙafa. Hakan ya saka su Khalid saurin mara masa baya gudun yin laifi.
        Koda ya shigo falon up stairs ya nufa, anan ma falo ne babba masha ALLAH, wanda babu abinda baijiba na kayan more rayuwa. Sai tashin ƙamshi yake ga sanyin ac mai saka nutsuwa. Kai tsaye ya nufi ɗaya da ga cikin bedroom ɗin da ke a up stairs ɗin. ya shimfiɗeta saman gadon ɗakin yana wani sake ɗaure fuska da yamutseta irin shifa ya gajin nan. Ya ɗan zubamata harara yana janye jikinsa. Wayarsace ta fara tsuwwa alamar shigowar kira.
      Sharewa yay tamkar bazai amsa ba. Sai da ta na gab da tsinkewa ya zarota a aljihun wandon baƙin jeans ɗin jikinsa yana jan siririn tsaki da jingina jikin mirror ɗin ɗakin yana kaiwa kunnensa batare da ya ce uffan ba, sai dai shirun nasa na nuna alamun sauraren mai magana ya ke da ga can. Tsawon minti biyu da wasu sakanni ya ce, “Uhmm” da ɗan gyaɗa kai.
          Dai-dai nan akai Knocking ƙofar a hankali, kasancewar sun san idan yana a irin wanann yanayin duk wata hayaniya baya buƙatarta.
        Cikin ƙosawa da motse-motsen kuwa ya bada izinin shigowa yana janye wayar a kunnensa...........✍



TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥

*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*

*_NAJI DADI SHINE GARI......_*

*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*

_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_

*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*

     *NA SABUWAR SHEKARAR 2022*

*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*

*SABBIN LABARAI*

*SABUWAR SHEKARA*

*SABON NISHADI*

*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*

*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*

*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.

*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_

*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_

*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_

*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_

*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*

6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank

Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number

08184017082

*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*

09134848107

Littafi daya

1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).

*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽

#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥





*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*




*_Typing📲_*




*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*


________________________



*_Chapter Twenty two_*

..........Da sallama Habib ya shigo tare da ƙarasa shigowa cikin ɗakin, leda ɗin da ke a hannunsa ya ajiye saman mirror ɗin da yake jingine.
        “Minene wannan ɗin?”.
Ya faɗa yana zuba lumsassun idanunsa bisa kan Habib ɗin.
       A ladabce Habib ya ce, “Makarin abinda aka shaƙa matane”.
        Kallo ɗaya yayma ledar ya ɗauke kansa. Cikin halin ko in kula ya miƙa masa hannu alamar ya bashi. Ɗakko ledar yay ya miƙa masa, ya ɗan janye hannunsa yana girgiza kansa, Habib da ya fahimci mi yake nufi sai ya buɗe ledar ya ciro handkerchief ɗin da ke ciki ya sake miƙa masa. Amsa yay ya zubama handky ɗin ido tamkar mai nazari, kafin yaja numfashi ya fesar yana ɗago agogon da ke a tsintacciyar hannunsa ya kalla. Ganin lokacin sallar la'asar ya gabato sosai ne ya sashi miƙama Habib Handkerchief ɗin. Batare da yayi magana ba ya nufi hanyar fita ɗakin.
       Sukan fahimci abubuwa masu yawa da ga garesa koda ta kurma yay musu. Hakan yasa yanzun ma Habib ɗin ya fahimta. Handky ɗin shima ya maida a ledar ya ajiye saman mirror ɗin ya bi bayansa.
          Koda ya fito bedroom ɗinsa da ke a saman upstairs ɗin ya nufa, sai dai yana da ga can kusan ƙarshen bangon gabas da falon saman, hakan yasa akwai tazara tsakanin shi da inda ya kai Hibba. Tamkar falukan nan ma komai tsaf, bakajin komai sai tashin ƙamshi da sanyin ac da ya gauraye ko ina. Yanda yake kure sanyin zai tabbatar maka shi ɗin ma'abocin son sanyi ne matuƙa. Dan yanda gaba ɗaya saman upstairs ɗin da ke nuna alamar anan komansa yake ya ɗauki sanyin wani bazai iya jimirin zama cikinsa ba. Shiko ko a jikinsa bai damu ba. Agogon hannunsa ya cire ya ajiye saman mirror ɗin ɗakin, tare da tattare dogon hannun rigar jikinsa sannan ya nufi wani ɗan dogon glass daya ci kusan rabin bangon yana facing ɗin gadon sa. Wani abu ya danna ya zuge kansa, yana shiga kuma ya maida ya rufe.
     Baifi mintuna sha biyar ba sai gashi ya fito cikin sabuwar shiga na wandon jeans da t-shirt. Hakama fuskarsa ta canja zuwa wani daban, gaba ɗaya ƙamshinsa ya gauraye ko ina ya danne na fresheners ɗin da ke tashi a sashen.
      Cikin yanayin kamar fushi-fushi da yake cikine ya ƙarama tafiyar tasa bayyana cikin izzarsa da ƙasaita ta musamman. Ya shiga sauka a steps ɗin cikin salon zafin nama da ALLAH ya azurtashi da shi.
         Daga falon ƙasan yake jiyo hayaniyar su Salis da alamu ya nuna suma shirin massallacin duk sukeyi. Batare da ya ko kalli sashen da suke ba ya zauna a kujerar da ke gab da ƙafar benen idonsa akan wayar sa dake hannunsa.. Saman kunne ya kai wayar tare da ɗaura ƙafarsa ɗa ya kan ɗaya. Ana ɗagawa da ga can cikin bada umarni yace, “Ka sameni kai da baba Saude”. Da ga haka ya ajiye wayar a table ɗin kusa da hannun kujerar ya maida idanunsa ya lumshe.
         Mintuna biyu kacal tsakani Khalid ya fito da ga wata ƙofa bakinsa ɗauke da sallama.
     A saman laɓɓa ya amsa masa batare da ya buɗe idanun nasa ba. Sai da baba Saude tai sallama a ƙarshe sannan ya buɗesu a hankali.
       “Babana an shigo ashe? Sannunku da dawowa”. Dattijuwar tsohuwa mai cikar kamala ta faɗa tana ƙoƙarin kaiwa zaune ƙasan tattausan carpet ɗin dake a tsakkiyar kujerun.
        Kujera ya nuna mata yana girgiza kansa cike da bata girma. Kafin ya buɗe baki tamkar bayaso ya fara magana. “Tun ɗazun na shigo ai. Na zata kina barci ne baba”.
        Murmushi tayi dai-dai tana kaiwa zaune. Ta ce, “Eh barci ya ɗan figeni kam sanda suka shigo. Nima motsinsu ne ya tadani”.
        Kansa kawai ya ɗan jinjina mata, tare da duban baƙin agogon fatar da ke ɗaure a tsintsiyar hannunsa. Cikin rashin son hayaniyarsa ya maida kallonsa ga Khalid da ke tsaye har yanzun. “Tsayuwar zaka cigaba da min a kai. Ko kiransu ku wuce masallaci!”.
       “Ayi haƙuri boss”. Khalid ya faɗa yana ɗan shafa ƙeya da komawa ciki domin kiran ƴan uwansa.
       Master ya janye idanunsa da ga kallon Khalid da yayi ya maida kan baba Saude. “Baba Saude zaki dawo nan da zama. Akwai yarinya zata kasance da mu anan na wani ɗan lokaci ne, ALLAH yasa bamu takuraki ba”.
       Baba Saude ta ɗan wawwaiga falon, dan ita bama ta lura da kowa ba. Amma sai ta ce, “Babu damuwa Babana, sai na dawo nan ɗin tunda ba wani abu nake acan ɗin ba, ba kuma wanine tare da ni ba balle nai tunanin barinsa. Kwana ne dama kawai ke kaini ai. Sai ina neman lamunin tahowa da ƴar marainiyar yarinyar nan dake wajena”.
      Kansa ya ɗan jinjina mata, kafin a takaice yace, “Nagode”.
      “Ai nice ya kamata nai godiya da karamcinka gareni babana. ALLAH ya saka maka da alkairi ya jiƙan iyaye da rahama. ALLAH ya bani tsahon rai da lafiyar kaiwa ran aurenka”.
      Wani ɗan ƙasaitaccen murmushi ya saki da kaɗan ya nuna akan fuskarsa. Batare da ya ce komai ba ya maida dubansa ga su Habib da ke fitowa da shirin tafiya masallaci.
           “A gyara mata ɗaki a nan ƙasa”.
     Ya faɗa yana miƙewa.
Cikin rashin fahimta Habib ya ce, “Auntyn ko Baba Saude?”..
       Wani malalacin harara ya zubama Habib ɗin tare da nufar hanyar fita. Batare da ya amsa masa tambayar ba yace, “Kaje da ita ta duba abinda babu zuwa anjima a faɗa min idan kun dawo salla, dan zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu nake son ta dawo gaba ɗaya”.
        Cike da jin daɗi su Habib suka juyo suna duban baba Saude fuska a washe. “Finally baba Saude zata dawo kusa da mu gaba ɗaya”.
        Ƴar dariyar jin daɗi tayi itama cike da so da ƙaunar yaran tana miƙewa domin yin salla. Suma suka fice cike da murna wannan zance na dawowar baba Saude kusa da su saɓanin da da zuwa kawai take tai musu girki ta wuce da yamma.
      
    
★★★★★

         A can gidan su Hibbah kuwa zuwa yanzu ƴan uwanta sun fara shiga ruɗani, dan kamar wasa babu ita babu alamarta a cikin gidan. Lungu da saƙo sun zagaye har sashen su Hajiya mama da basama tunanin zataje. Tun sunayi su kaɗai har mutane da suka farga suka fara tayasu. Da ga cikin gida takai har an fito waje amma babu ko mai kama da ita. Babu ma wanda yace ya ganta bayan wanda suke a falon Ummi.
     Yaya Muhammad ne ya tuno kiran da Shuraim yay mata. Wanda a dalilinsa ya sakata fita waje dan ta amsa. Kuma tabbas daga haka bata dawo ba har suka fita massallaci.
       Kansa ya dafe yana ambaton “innalillahi....”
      Gaba ɗaya suka maida dubansa gareshi a ruɗe. Ya cigaba da faɗin, “Tabbas Abubakar kayi gaskiya yaron nan hatsabibine na gaske. indai har hasashena yana kan dai-dai tun kafin a ɗaura auren nan ya ɗauke Hibbah.”
      “What!?”.
Yaya Abubakar ya faɗa a razane, illahirin jikinsa sai tsuma yake.
            Yaya Muhammad da ke jin juwa na kwasar sa cikin raunin murya yace, “Ƙwarai kuwa Abubakar ya ɗauke mana ita. Dan shine ya kirata lokacin da muke ɗaukar hoton nan amma sai taƙi ɗagawa, nine na korata waje akan taje ta ɗaga. Na tabbatar da ga lokacinne ya sace mana ita”.
     Saurin riƙosa Isma'il dake a bayansa yayi ganin yayo baya zai faɗi. Yaya Umar kam ai dole ya kai zaune dan ya tabbatar ya cigaba da tsaiwar faɗuwar zaiyi shima. Yayinda tuni idanun Usman da Ammar sun fara kawo ruwan hawaye. Sauran abokansu kam da ke wajen kowa ya shiga halin taraddadi da tausayin su Yaya Muhammad. Dan kallo ɗaya zakai musu ka fahimci tsananin ƙauna da sukema ƙanwar tasu.
      Komai ya kwance musu, tunani ma sun gazayi na neman mafita. Ammar da ke kuka ya nufi cikin gida da zummar sanarma Ummi dama tunda suka dawo sallar la'asar basu koma ciki ba. Saurin riƙosa Isma'il yayi yana girgiza masa kai. “Ammar ba yanzu ba. Ummi bata cancanci sanin wannan tashin hankalinba yanzu. Inaga muɗan jinkirta har a samu mafita”.
         Kuka sosai Ammar ya fashe da shi, hakan yasa Isma'il ɗin rungumesa cike da lallashi.
      Yaya Abubakar da zancen Isma'il yaja hankalinsa cikin gamsuwa da ƙarfin hali ya ce, “Shawararka tayi Isma'il, dolene mu jinkirta sanarma Ummi wannan batun duk da cewar zuwa yanzu tasan babu Hibbah a gidan. Sai musan mi zamu sanar mata dan hankalinta ya kwanta”.
          Cike da gamsuwar jawabinsa duk suka kaɗa kansu. Suna nan tsaye suna tattauna yanda zasu ɓulloma Ummin suka juyo sabuwar hayaniya ta ɓalle a cikin gidan, har takai wasu na fitowa a guje. Da sauri suka shiga, dan tun daga nan suna jiyo kururuwa da ihun Hajiya mama.
      Da ƙyar suka iya kutsa kai cikin falonsu. Inda ke cike da ƴan biki da ke zagaye da Hajiya mama da Abba da Junaid wai zai daki Ummi. Hajiya mama nata zagin Ummi akan itace ta tsara komai akan auren su Yaya Muhammad. Abba ma yana zazzaga tasa masifar da tattaro duk laifin Shuraim (ko nace master) yana azawa kan Ummi. Duk da kuwa sarai yasan gadar zaren da ya ƙulla ce ta rufta da shi. Yayi iya hasashensa kuma ya gagara kamo bakin zaren da dalilin Master na juya shirin nasu zuwa tsarinsa daban, shiyyasa yazo sauke haushin da takaici akan Ummi marainiyar wayonsa. Harda yo gayyar ƴan tayo..
         Isma'il ya finciki Junaid ta baya yana ƙoƙarin riƙe katakon da ya ɗaga wai zai bugama Ummi da ke zaune ta dafe kanta tana jiran saukar katakon. A take mutane suka dare saboda yanda ya zubar da Junaid ɗin a ƙasa ya take masa wuya. Riƙesa Yaya Muhammad yay ƙoƙarin yi amma sai ya fisge jikinsa, da ƙarfi ya daka katakon da ya kwace a hannun Junaid ɗin a ƙasa saitin kansa, jikinsa sai wani irin tsuma yake tamkar mafaraucin zaki. Duk yanda Junaid ke kakarin mutuwa yaƙi ɗaga ƙafarsa a wuyansa, sai ma sake murzawa yake cikin tsananin taurin zuciya.
       A matuƙar firgice Abba ya ƙai hannu wai zai ture Isma'il. Sai dai ko motsi bai yiba. Sai ma waiwayowa da yay ya duba Abban da wasu irin jajayen idanun da suka bama kowa matuƙar mamaki. Dan gaba ɗaya ya birkuce musu da ga Isma'il ɗin da suka sani zuwa wani daban.
          “Idan jikinka ya ƙara gigin taɓa nawa saina ɓallaka yanda ko uwar data haifeka bazata sake gane kamaninka ba.”
        A wani irin zabure Abba ya waro idanu yana nuna kansa, “Da ni kake?”.
      Ƙafar da yake murza wuyan Junaid da ke kakarin mutuwa ya ɗaga. Yay wani irin tsalle tamkar ɗan ƙwallo zai buga ball ɗin daga kai sai mai tsaron gida ya halbi hakarƙarin Junaid. Wata irin wahalalliyar ƙara Junaid ya saki tare da jan numfashi tamkar zai shiɗe sai ga aman jini.
       “Innalillahi... Isma'il!”.
Yaya Muhammad ya faɗa da sauri yana kawo hannu zai riƙesa. Saurin ɗagama Yaya Muhammad ɗin hannu yayi idanunsa na kan Abba da gaba ɗaya ilahirin jikinsa tsuma yake. Dan yanda Isma'il ɗin ke tunkarosa sai yake ganin tamkar zai haɗiyesa da idanunsa masu suffar na Zaki ne.
      “Yaya Muhammad barni na kartama wannan shashashan dattijon warning na ƙarshe. Dan inhar ya sake koda kallon Ummi da wata manufa to lallai saina maidashi abin kwatance. Kai bama shi ba. Ko karen gidan nan ya sake mata kallon banza lallai ni Isma'il zan daddatsa shi gunduwa-gunduwa na cinye namansa ɗanye dan uban da ya haifesa”. Ya ƙare maganar idonsa akan Abba. Yatsansa na nuna Hajiya mama da ta koma jikin bango ta maƙure jikinta na rawa kar-kar-kar. Ga fitsarin da ya cika mata mara tuni ya ɓalle ya fara bin kafafunta yana sauka saman tiles.............✍


TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥

*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*

*_NAJI DADI SHINE GARI......_*

*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*

_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_

*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*

     *NA SABUWAR SHEKARAR 2022*

*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*

*SABBIN LABARAI*

*SABUWAR SHEKARA*

*SABON NISHADI*

*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*

*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*

*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.

*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_

*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_

*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_

*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_

*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*

6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank

Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number

08184017082

*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*

09134848107

Littafi daya

1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).

*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽

#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥




*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*




*_Typing📲_*




*_Zafafa biyar na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki saya kafin ki karanta. Muna haɗaki da ALLAH idan kin saya karki fitar mana saboda hakan cutarwa ne a garemu da ke kanki da kika saɓa mana alƙawari ta hanyar zalintarmu da son ruguza mana kasuwancinmu._*


______________________


*_Chapter Twenty Three_*

.............“Kaga wani salo kamar a film”.
Ammar ya faɗa dariya na kufce masa a bazata. Dan haka kawai wasan yay matuƙar birgesa da ƙayatar da shi.
        Su yaya Abubakar kam da gaba ɗaya mamaki da al'ajab ɗin Isma'il ɗin ya daskarar da su a tsaye da ƙyar suka iya fisgo numfarfashinsu sukai azamar zuwa suka sha gabansa ganin Abba ya ke nufa gadan-gadan. Dan su gaba ɗaya abinda zukatansu ke basu lallai Isma'il yana tare da wani bahagon aljani ne ƙila.
      Idanunsa ya rumtse da ƙarfi ganin sun tare sa. Cikin wata irin murya mai ƙaraji da saka firgici ga ma'abocin saurare yace, “Minti uku na baku a fitar min da wanann sauran gawar anan. Kar kuma na sake ganin ƙafar waninku anan. Inba hakaba.... Ya ƙyalƙyale da dariyar da ta saka su Yaya Abubakar sake zama turus a gabansa.
       Jiki na rawa Momy ta kama ƙafafun Junaid ta fara ja tana kuka. Yayinda tuni Hajiya mama ta fece da gudu har tana cin tuntuɓe zata faɗi. Su kawu Garba da ke gefe a maƙure suma ne sukai karfin halin matsowa suka taya Momy ɗaukar Junaid da zuwa yanzu ya sume sabida azabar murzar da wuyansa yasha da haƙarƙarinsa.
        Da gudu Ammar ya taho ya rungume Isma'il ta baya yana dariya da hawaye a lokaci ɗaya. Hakan yasa Ummi ma da tai mutuwar zaune tana kallon Isma'il ɗin ta miƙe zuwa garesu. Hannun Isma'il ta riƙo cikin nata hawaye na sakko mata saman kumatu. Jawo hannun nasa tai ta zaunar da shi akan kujera tare da ɗaukar goran ruwa da ke a saman centre table da aka ajiyema baƙi ta ɓalle murfin ta ɗora masa a baki tana shafa kansa.
      Babu musu ya hau sha yana jan ajiyar zuciya. Sai da ya shanye shi tas ta janye goran tana cigaba da shafa kan nasa.
     A hankali ya lumshe idanunsa da komawa baya ya jingina jikinsa da kujerar, numfashinsa tun yana sauka da zafi-zafi har ya koma sauka a hankali alamar zuciyarsa nayin sanyi.
     Ummi ta share hawayen fuskarta tanayin murmushi da duban su Yaya Usman da har yanzu ruɗani da al'ajabin mamakin Isma'il ɗin ya gaza barinsu. Matsowa sukai gareta. Yaya Umar da yaya Usman suka rungume Isma'il ɗin. Yayinda Ammar yazo ya zauna gabansa ya ɗaura kansa a saman cinyarsa fuskarsa washe da dariya tamkar gonar audiga.
    Hannu ya kai a hankali bisa kan Ammar yana shafawa. A karon farko ya saki murmushi da ɗago kansa ya na kallon Ummi da su Yaya Muhammad.
       “Kiyu haƙuri Ummi, lamarin mutanen nan sai da over acting. Na fahimci wannan ce kawai mafita a garemu. Inba haka ba sai wata fitinar ta kaure har akai ga jima wani ciwo”.
     Yanda yay maganar cikin sanyin murya tamkar yanda suka sanshi ne ya saka su Yaya Usman sakin ajiyar zuciyoyi.
        “Amma Isma'il ka bani tsoro matuƙa wlhy, har mun fara tunanin ko baka da lafiya ne”. Cewar Yaya Muhammad yana murmushi.
     Ɗagowa Isma'il yayi zaune sosai yana saki ƴar dariya. “Yayanmu lamarin tsohuwar nan ne sai da haka. Sai dai fa nasan wlhy ba haƙura sukai ba, dan da alama na jima wancan wawan yaron Junaid ciwo a haƙarƙari. Ummi inhar shirinku na barin gidan nan na nan to lallai dole ne ki tafi kema a yau ɗin nan. Kamata yay ma ace yanzu kawai. Kinga sai ki tarbi amare da kanki”.
       Yaya Abubakar da har yanzu shi dai yake kallon Isma'il ɗin cike da nazari da wasiwasi ya gyaɗa kansa cikin gamsuwa. “Wannan mafita ce mai ƙyau. Dan Abba kam ba kanwar da za'a lasa bace aji kaifi kawai. Ummi kamar yanda Isma'il ɗin ya faɗa barin gidan nan yanzu shine mafita kawai”.
       Sosai itama Ummi ta gamsu da zancen. Dan duk abinda zai ɓata mata taron auren yaranta bata fatansa. Sarai kuma ta fahimci abinda su Hajiya mama ke burin yi kenan. Sai dai kuma cikin damuwa da rauni ta ce, “Tanee ɗin fa an ganta?”.
         Da sauri Yaya Umar ya gyaɗa mata kai. “Eh karki damu tana tare da ƙawayenta ashe. Zuwa anjima nasan zatabi masu kai su can kawai”.
        Duk da zuciyarta a raunane take hakan bai hanata gamsuwa ba. Ta mike tana warware mayafinta da dama tana tare da shi tun ɗazun ta sake yafawa. Dama ba wani muaten bane sosai a sashen. Makwafta da suka shishshigo sukai mata ALLAH sanya alkairi duk sun fita saboda yamma tayi sosai. Sai ƙawayenta na kusa sosai irinsu Hajiya Mardiyya. Suko sunsan da shirin barin gidan. Dan dama sune zasuje amsar amare acan. Jin hukuncin da su Yaya Muhammad ɗin suka yanke ne ya sakasu mimmiƙewa suma suka hau kimtsawa.
     Su Ummi basu da matsala da komai na sashen dan sun tsince masu muhimmancin sun killace sauran. Su hajiya mama nacan akan Junaid cike da ruɗani suka samu suka fice dan dama gari ya fara duhun magrib da ake ta faman kira a masallatan anguwar. Mutanen da ke a tsakar gida kuwa gulma da tsugudidin da suka haɗa kai sunayi group-group yasa basu hankaltu da su Ummin ba. A tunaninsu kawai ƴan biki ne zasu wuce gida.
         

★★★★★

        
           A can L.E street kuwa cike da farin ciki da ƙaunar yaran har cikin rai baba Saude ta mike domin gabatar da sallar la'asar ɗin itama. Tana idarwa ta fito ta hau shirya musu abincinsu na rana da basu ci ba.
           Kasancewar yunwar kuwa na ƙwaƙular cikinsu ana idar da sallar la'asar ɗin suka dawo gidan. Sai dai su kaɗai suka shigo falon banda Master da yay zamansa a ƴar runfar bunun da ke a gefen swimming pool ɗin gidan. Dan yasan tunda suka dawo gidan shegen surutinsu ba zai barshi ya huta yanda yake bukata ba.
        Suko da ga can cikin zalamar kayan daɗin da baba Sauden ta baje musu a babban dining ɗin suka baje da fara ɗurama cikinsu. Yayinda kowa ya fara kai lauma sai sabon surutu ya ɓalle, baba Saude na gefe na musu dariya kamar yanda ta saba har suka kammala. Sune suka zaɓar mata ɗakin da zata zauna anan downstairs ɗin. Hundred percent kuwa ta gamsu da ɗakin, dan yana ɗan nesa da ɗakunansu ga shi kuma gab da kitchen.
      Sune suka shiga gyara mata komai duk da bama

Please Login or Register in order to submit comment