Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ɗago ido ya dubesa fuska a tamke. “Ince da kai nake magana ko?”.
      Yanda yay maganar aɗan zafafe yasa Habib ɗin girgiza masa kai. “Yaya hakan dazan mata ne kawai zaisa na huce da ga abinda ya faru, itama kuma zata kiyaye sake yin wani yunƙuri makamancin hakan.”
Idanu kawai Master ya zuba masa saboda mamakin Habib ɗin matuƙa. Shiko yaki yarda ya kallesa dan yasan yayi ba dai-dai ba.
        Kansa ya sake maidawa ga takardun, “Hum aure kake buƙata kenan? Ko ka fara neman mata ne?”.
        Da sauri Habib ɗin ya ɗago ya dubesa yana girgiza masa kai. “Wlhy Yaya ni ko ɗaya babu a raina. Kawai dai.....” sai kuma yay shiru bai ƙarasa ba
        Takardun hannunsa ya ajiye ya maida hankalinsa gaba ɗaya garesa yana sake tsuke fuska irin yanda bai taɓa gani ba. “Ƙawai dai me?. ƙarya kakeyi, idan har baka neman mata taya kasan ka sakamin pills nasha dan naje ga mace koda babu niyyar haka a gareni.”
       Habib da idanunsa suka kaɗa sukai jajur ya kai tsugunne gabansa. “Wlhy yaya ban taɓa aikata zina ba ka yarda dani, kamar yanda na faɗa maka kawai nayine dan karta sake tunanin kwatanta abinda ta aikata, sannan inason ku rayu har abada”.
      “Kai da wa kukai shawarar aikata hakan a cikinsu?”.
        “Ni kaɗai ne, dukansu babu wanda yasan abinda ya faru sai Yaya Abdull da ya bani”.
      Idanu kawai master ya zubama Habib ɗin batare da ya sake cewa komai ba. Dama ya zargi babu wanda zaiyi wannan aikin garesa sai Abdull ɗin. Tunda aka ɗaura aurensa da Hibbah kullum cikin masa tsegumi yake su baby suke so da wuri. Habib da yaji yay shiru ya ɗago ya dubesa, shi kaɗai ne ya san ainahin fuskarnan a cikinsu, dan haka bai wani damu da ganinta a yanzu ba. “Yaya dan ALLAH kayi haƙuri. Nasan nayi kuskure tunma kan na aikata hakan. Inason naga kunyi zama irin na kowaɗanne ma'aurata da ita. Bana son ka rabu da ita saboda ƙyawawan halayyarta. Duk da ƙarancin shekarunta tasan kanta matuƙa kuma tanada tarbiyyar da kowanne irin nagartaccen namiji zaiso ta kasance uwar ƴaƴansa. Mu ɗin nan marayune, daga mace tagari kawai muke saran samun zuri'a mai albarka da zamu sake ginawa. Wadda zaka fara ginawa kuma itace ginshiƙin da zata riƙe tamu mu duka bakwai ɗin”.
        Harararsa Master yay, da alamar dai ya huce ya ɗauke kansa. Matsowa Habib yay jikinsa ya ɗaura kansa bisa ƙafafunsa. “Please yaya karka rabu da ita dan ALLAH, inaji a raina idan tasan kai ɗin ko wanene zata sakko ta fahimceka ku rayu tare”.
       Lumshe idanu yay bai tankaba nan ma. Shima kuma Habib bai janye kansa ba. Kusan mintuna biyu yaja ajiyar zuciya da furzar da numfashi, a hankali ya kai hannunsa bisa kan Habib ɗin ya shafa. Habib da wani farin ciki ya mamayesa ya miƙe da sauri ya rungumesa yana dariya. “Thanks you Mastern mu. I love you so much”.
        Karan farko Master ya rankwashi kan Habib ɗin yana murmushi. “Mara kunya tashi mun a jiki tunda ka sadaukar dani ai.”
     Cikin shagwaɓa Habib yace, “A'a Yaya ba duka na bataba fa. Ita rabi mu rabi.”
    Nan ma murmushi kawai yayi baice komai ba. Sai da ya miƙe batare da ya dubesa ba ya nufi hanyar bedroom ɗin da Hibbah ke ciki yana faɗin, “Kaje ka sanar musu kowa ya nemo matar aure nan da wata biyu”.
       Idanu Habib ya zaro, kafin yace wani abu Master ya shige. Wata shaƙiyyar dariya ya saki yana haɗiye sauran maganar a ransa ya juya ya fita da gudu dan kai rahoto.

      Master da ke jiyo dariyar Habib ɗin baima san murmushi ya kufce masa ba shima. Ya ɗan girgiza kai yana ƙarasawa cikin ɗakin da sallama a bakinsa. Shiru babu motsin komai alamar barci Hibbah keyi har yanzun. Ya zare jacket ɗin jikinsa yana ƙarasawa gaban gadon ya zauna ta gefenta. Babu abinda yafi buƙata a yanzu kamar kwanciya. Sam bayajin ƙarfi da daɗin jikinsa dauriyace kawai. Dan bashi da burin daya wuce ya tattare aikin nan ya ɗauki matarsa suje su huta. Bargon da take ciki ya ɗan janye da kai hannunsa saman goshinta. Zazzaɓin ya sauka, a yanda numfashinta ma ke fita kawai ya isa tabbatar da hakan. Yaji daɗi har cikin ransa, fasa tashinta yayi dan karya takaloma kansa wata rigimar, ya ɗauka ledar daya shigo da ita ya sake fita. Babu jimawa ya dawo ɗauke tea. Zama yay yasha tare da maganinsa. Shima yay shirin barci ya haye gadon yana sauke ajiyar zuciya............✍🏻


TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥

*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*

*_NAJI DADI SHINE GARI......_*

*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*

_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_

*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*

     *NA SABUWAR SHEKARAR 2022*

*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*

*SABBIN LABARAI*

*SABUWAR SHEKARA*

*SABON NISHADI*

*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*

*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*

*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.

*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_

*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_

*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_

*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_

*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*

6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank

Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number

08184017082

*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*

09134848107

Littafi daya

1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).

*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽

#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥





*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*

 


*_Chapter Forty one_*



.............*_WASHE GARI_*

       Da asuba Hibbah ta rigashi tashi, dan cikin barci ya dinga jiyo motsinta a bayi. Tashi yay da ƙyar yana ambaton sunan ALLAH. Alhmdllhi jikin ya masa daɗi, dan magungunan da yake sha sun matuƙar taimaka masa. Koda ta fito kallo ɗaya tai masa ta ɗauke kanta. Shima baice komai ba ya mike zuwa bayin yayo alwala. Koda ya fito shine yaja musu sallar, yana lure da yanda Hibbah taƙi yarda ta kallesa bai nuna ya damu ba. Bayan sun idar tana ƙoƙarin miƙewa ya riƙota ya zaunar a jikinsa. Kanta ta kauda gefe tana ƙoƙarin haɗiye ƙwallar da suka ciko mata idanu.
       Hijjab ɗin jikinta ya cire, tare da riƙo fuskar tata cikin tafin hannunsa ya juyota garesa. “Nikam wai har yanzu ba'a huceba”. Yay maganar yana ɗaura kansa bisa goshinta”.
       Duk yanda taso ƙwace fuskar tata hakan ya gagara. Dole ta nutsu waje guda, gashi tanason yin magana amma babu dama. Ta tabbatar datayita kusancin laɓɓansu zai iya sawa ya haɗu da nasa.
       Fahimtar hakan da yayine ya sashi ɗaura laɓɓan nasa saman nata ya ɗan sumbata. Sai kuma ya janye goshinsa yana kallonta da ƙyau. Duk yanda yaso su haɗa ido ko tayi magana taƙi. Sarai ya fahimci borin kunyane kawai. Dan haka ya saketa yana murmushi.
       Zumbur kuwa ta miƙe tabar wajen, har tana cin tuntuɓe da ƙafarsa.
       “Ni dai kar amin asarar ɗan tayi na”.
      Ya faɗa cike da shaƙiyanci yana binta da kallo. Cikin tunzura baki gaba ta haye gadon taja bargo ta rufe har kanta tana ƙunƙunj. Duk da dariyar dake son kufce masa dai ya danne abinsa baiyi ba. Sai ma ya miƙe shima ya hau gadon dan barci yake son ƙarayi. Hibbah data ƙudundune waje guda tai saurin buɗe idanunta a tsorace. Zata miƙe ya riƙota yana daidaita fuskarsu waje guda. Yatsansa ya ɗaura saman laɓɓanta ya shiga zagayawa dashi a hankali. Tsigar jikintane ya fara tashi amma sai ta danne taƙi nunawa.
Cikin ƙasa da murya sosai tamkar mai raɗa yace, “Mikike faɗa da banaji?”.
Hannunsa ta ɗan ture daga bakinta tana kumbura bakin kamar zatai kuka, “Ai dai ALLAH ya sani bance komai ba”.
Ganin zata juya masa baya tana maganar yay azamar tareta, laɓɓansa ya matsar gab da nata yana wani narke idanu, “Ni nasan kince ai”.
Kafin ta samu damar cewa wani abu ya rufe bakin nata, cikin shauƙin dake ɗibarsa ya shiga aika mata da sumbata a nutse data saka zuciyarta shiga tsoro harta fara tsuma. Duk da yaji a yanda jikin nata ke ɓari bai saketa ba ya cigaba da abinda yake har sai da ya tabbatar tayi laushi. Hagitsatstsun idanunsa da suka kaɗai sukai jajur ya ɗago yana kallon fuskarta, idanunta dake hawayen tsoron ya sumbata da jan nannauyar ajiyar zuciya.
         “Nasan ni mai laifine a gareki ta kowacce fuska Muhibbat, sai dai inason kisani kece kika faramin laifi.”
     A karon farko Hibbah ta buɗe idanunta ta kallesa, ga hawaye shaɓe-shaɓe. Sai kuma cikin sauri ta sake maidawa ta rufe, dan batason ganin idanun nan nasa da fuskar nan ta yaya Isama'il da ya saka, ga matsananciyar kunyarsa dake matuƙar cizon ranta da ɓargo. Batare da ya damu ba ya tura yatsun hanunsa cikin gashin kanta da sake matsota jikinsa. “Inason ki nutsu a yau kisan kowanene Muhammad Shuraim (Master). Asalin sunan shine Isma'il Aliyu Hikima”.
       Cikin sauri Hibbah ta sake buɗe ido har yawu na sarƙe ta. Ganin ta miƙe zaune shima ya miƙe, ruwan dake a bedside ya ɗakko ya ɗora mata a baki. Babu musu tasha tana kallonsa tamkar idanunta zasu zubo a karon farko wajen kallonsa.
        “Tabbas Isma'il shine sunan, kuma shine a gabanki yanzu haka da fuskar zahiri bata bogi ba Muhibbat.”
      Wani irin bugawa ƙirjin Hibbah ya sakeyi. Cikin rawar jiki da son ƙin gaskatawa takai hannunta saman fuskarsa tana rumtse ido. Sake buɗe idon tai da sauri taja baya jikinta na sake ƙarfin karkarwa. “M....master kana nufin kaine Yaya Isma'il?”.
        Kansa ya jinjina mata yana lumshe idanunsa ya sake buɗewa a kanta.
        “Na shiga uku ni Muhibbat wane irin rikitaccen mafarkine wannan nake a ciki?. Impossible hakan ta kasance”.
     Tai maganar tana ƙoƙarin sauka a gadon. Saurin riƙota yay ta dawo jikinsa. “Shiyyasa nace ki nutsu ki saurareni”. Ya faɗa a cikin kunnenta da wata murya mai taushi tamkar bashi ba. Batare da ya bata damar sake cewa komai ba ya cigaba da maganarsa. “Sunan mahaifina Aliyu..........” tiryan-tiryan ya cigaba da bata labarinsa tamkar yanda ya bama su Ummi. Sai kuma ya ɗora da “A farkon shigata tawagar su Master an taɓa kamamu, lokacin ina farkon shiga aji shida na sakandiri. Tunda aka kawomu police station wani babban jami'i keta kallona har kallon ya gundireni naji haushi. Fahimtar hakan da yay yasashi ɗauke kai yana murmushi. Bansan yaya akai ba bayan kamar awa guda aka fiddani ni kaɗai kuma babu wani bayani. Hakan ya tsayamin a rai, daga baya kuma saina watsar na cigaba da harkar gabana.”
        “Bayan na kammala jami'a na kaima wanda ya ɗauki nauyin karatuna result ɗina dan ya gani, tare da sake masa godiya, sai naci karo da jami'in nan da yayta kallona a station, abin ya ɗauremin kai, na kuma sha mamaki amma sai na danne. Yaji daɗi ya kumayi farin ciki a take anan kuma yaymin tayin aiki saboda ganin yanda nake da matuƙar ƙwazo da kaifin basira akan harkar kimiya da fasaha. Babu musu na amsa cikin farin ciki da murna dan kuwa aiki ne na jami'an tsaro. Na miƙe cikin farin ciki zan tafi ya dakatar da ni ta hanyar faɗin, (dakata yarona ai bamu gama magana ba). Komawa nai na zauna ina basa dukkan hankalina.”
        “Yarona zaka zama jami'in ɗan sanda amma na sirri, dan haka zakai aiki kafaɗa da kafaɗa ne da mu ƴansanda amma a sirrance batare da kowa yasan wannan ba sai ni. Inada abubuwa masu yawa dake cimin rai da zuciya, sai dai ina matuƙar jin tsoro da shakku akan wanda zan ɗora yaymin. Wannan yasa a randa na fara ganinka a station naji a raina zaka iya. Hakan yasani komawa na biya maka kuɗin karatu dan a cikin idanunka na fahimci da gasken zaka iya. A yau zan sanar da kai wani abu, duk tsahon shekarun nan daka ɗauka kana karatu ina biye da kai, hatta shiga cikin ƴan daba da kakeyi wanda na fahimci kanada wani dalili duk ina sane da kai).”
       “Nayi matuƙar razana dajin zancensa. Dan haka na miƙe ina girgiza masa kai. Saurin riƙoni yayi shima yana girgizamin nasa. cikin taushin murya kuma ya shiga lallashina. (Yarona zaka iya, ni na tabbatar zaka iya insha ALLAH. Wannan Master da kake ƙarƙashinsa ko kasan gawurtaccen ɗan ta'addane da muke fako tsahon shekaru. Sai dai a bincikenmu ya nuna yana tare da manya-manyan masu faɗa ajin da ko kamashi mukai munyi a banza zai fito kamar ko yaushe. Daga ƙarshe ma wanda ya kamasan shine zai rasa aikinsa ko rayuwarsa. Jami'anmu sun halaka da yawan gaske a dalilinsa. Sai dai a yanzu haka akwai yarona a cikin yaransa shine duk ke bani bayani game da kai, dan shima ya shiga jikinsa ne domin mana cid. Inason dan ALLAH ka sanarmin miyasa ka raɓu da shi kai?).”
         “Ina ganin kima da mutuncinsa. Dan ya ƙyautata rayuwata na samu ilimi a gaɓar dana yanke ƙauna da samun hakan. Dan haka babu musu na zauna na zayyane masa koma na rasa iyayena a dalilin Master da dangin Dattijo Isma'il suka saka. Na kuma tabbatar masa da fansa zan ɗauka dan bazan bar Master ba. Har hawaye sai da yayi domin tausayina. Ya kuma tabbatarmin burina zai cika cikin sauƙi amma saina zama jami'in sirrin da yaymin tayi. Na amince a lokacin. tare da bayyana masa ainahin fuskata ta Isma'il Aliyu Hikima. Yasha amamaki kwarai da gaske, musamman da yaji cewar tun ina yaro nake ɓoye fuskata ta zahiri, bayan iyayena shine na biyu daya ganni a hakan. Hakama da yaji nike haɗa dukkan Mask ɗin wa kaina yaji daɗi ya kuma yabama fasaha ta. Domin abune daba kasafai ake samunsa anan yankunanmu ba.”
      A dalilin ganin zan iya ɓoye fuskata yace babu damuwa ma zan iya aiki kafaɗa da kafaɗa da su kamr kowane ɗan sanda a zahiri, a baɗini kuma aikin sirrinmu, sai dai zan cigaba da ɓaddabamin ɓoye ainahin fuskar Isma'il zuwa wani lokaci. Na amince da hakan. Na kuma shiga cikin tawagar horaswa da fuskar Muhammad Shuraim, cikin amincin ALLAH na fito a jerin jami'ai masu matuƙar ƙwazo. Sai dai ana kammalawa na sake ɓacewa ɓat bisa umarnin I.G. Na sake komawa cikin su Master da zuwa yanzun dukkan sirrinsa a tafin hannuna yake, dan dukkan abokan mu'amularsa a cikin manya da ƴan ta'adda irinsa na sansu nasan inda suke, nasan makamar harkokinsu. Na iya maganarsa. Na iya salon tafiyarsa na iya abubuwa da dama irin nasa wanda inhar na juye maka shi baka isa cewa bashi ɗin bane musamman idan na saka mask na fuskarsa. Indai taƙaice miki zance a wani dare batare da sanin kowaba a cikin yaran Master na ɗaukesa, zuwa safiya na maye gurbinsa, yaransa kuma duk nabi hanyoyi daban-daban aka kamasu ɗaya bayan ɗaya ta yanda babu yanda ubannin gidansu zasu iyama ganosu balle cetonsu. A gefe kuma ina aikina a zahiri tuƙuru game da dukkan abinda ya dace”.
         “Duk da kasancewana normal ɗan sanda, nayi ayyukan sirri da yawa bisa umarnin I.G ni da ɗansa Abdull da ya zama aminina tun a jami'a. Efcc Chairman da General abokaine na I.G tun ƙuruciya, hakanne yasasu sanin ayyukana a wajen I.G har suma suka fara jana jikinsu dan halayyarsu ɗaya da I.G akan ganin ƙasarmu ta dawo hayyacinta. Sai dai rashin mabiya na ƙwarai yasa basa iya tufƙa sai an warware musu. Nasha kawo musu information da yawa daya shafi ayyukansu a dalilin bincike na. Hakanne yasa a wasu lokutan nakanyi aiki kafaɗa da kafaɗa dasu tamkar yanda akasan jami'an tsaro da yawa sunkanyi hakan a sirrance a tsakaninsu. Kin shigo rayuwata a dai-dai gaɓar da nake gab da kammala tattara bayanai akan duk wasu masu hannu bisa ta'addancin Master. Naso hukuntaki, dan kin kusa ruguzamin aiki, amma sai labarin ya canja salo a dalilin I.G, shine yasa akai masa bincike akanki da ahalinki harya gano bakida wani dalili na harata tsiwace kawai da rawan kanki. Babu wani kwanakana ya bani shawarar aurenki. Ban iya cemasa komai ba dan yanada mutunci da girma a idanuna. Sai dai na dauka ɗammarar shiga jikinki nima dan tabbatarda ƙwazonki da yaketa yabawa harda kwaɗayin na aureki. Dukkan abinda su A.G sukai miki mun sani, musamman daya kasance ni suke ɗauka Master ɗinsu a halin yanzun. Muhibbat a yau na gama aikina daya shafi wancan Master ɗin, zan kuma damƙashi ga hukuma shi da su A.G, zan kuma bayyana fuskar Isma'il ma duniya, shiyyasa na fara nunata gareki bayan iyayena, baba, Habib, I.G, da kuma su Ummi. Sai dai kafin hakan inason ki sani tun randa na fara ganinki a asibiti kikaima zuciyata shigar sauri. Kece kika ruguza dukan yaƙinina akan ƙin yarda da mace, kece kika ɓata duk wani alwashina akan soyayya. Da gaske nake ina sonki”.
          Hibbah da gaba ɗaya hawaye suka gama wanke fuskarta tun fara bata tarihinsa ta matsa jikinsa da sauri ta rungumesa tare da fashewa da sabon kuka, sai kuma ta ɗago tana kai masa kananun duka a ƙirji kukan na sake kufce mata..........✍
      



TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥

*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*

*_NAJI DADI SHINE GARI......_*

*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*

_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_

*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*

     *NA SABUWAR SHEKARAR 2022*

*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*

*SABBIN LABARAI*

*SABUWAR SHEKARA*

*SABON NISHADI*

*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*

*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*

*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.

*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_

*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_

*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_

*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_

*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*

6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank

Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number

08184017082

*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*

09134848107

Littafi daya

1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).

*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽

#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥


*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*

 


*_Chapter Forty Two_*

...........Har cikin ransa sai da yaji shock dan bai zaton hakan ba da ga gareta cikin sauƙi. Sai dai idan yayi dubi da tarbiyanta da yanda ta tashi za'a iya mata koda wayone da yaudara ta amince. Idanunsa ya lumshe tare da riƙe hannuwan nata yana murmushi, ya rungumeta da ƙyau shima yana jerama UBANGIJI godiya, dan jinsa yake tamkar ya sauke wasu kaya masu nauyi dake bisa kansa.
         Muhibbat da gaba ɗaya ta kasa tsaida kukanta ta sake yunƙurin barin jikin nasa.
        “I'm sorry Hibbaty”.
    Ya faɗa cikin kunnenta yana sake matseta da busa mata iskar numfashinsa cikin kunnen dake tada mata tsigar jiki..
      “Ni ka sakeni, wajen Ummina zanje, karka sake shiga sabgata kuma. Karka sake zuwa mana gida.”
         Cikin gimtse dariyarsa ya ɗagota da riƙe fuskarta cikin tafukan hannunsa. “Buɗe idanun mana ki kalli cikin nawa ki faɗa. Kefa kikace da Isma'il zaki zauna, taya kike tunanin kunnen Isma'il yaji wannan zance yay sakacin barinki kiyi nesa da shi kuma?”.
          Sake matse idanun tayi hawaye na zirarowa. Batare data iya buɗesu ba tace, “To na fasa. Yanzu bazan zauna da kai ba”.
        “Shi kuma babyna kimin yaya da shi? Dan bazaije ko ina ba a gidansu zai tashi”.
         Babu shiri ta buɗe idanun sai dai bata kallesa ba. Cikin motsawar sakarcin nata tace, “Ni yaushe naga wani babyn ka balle na rakitama kaina har yaje gidanmu”.
      Hannunsa ya ɗaura a saman cikinta yana ƙasa da shi a hankali, cikin muryar raɗa ya ce, “Gashi anan insha ALLAH, zaki gansane kema soon”.
             Hanunsa ta ture da faɗin, “ALLAH ya kiyaye”.
      “Na yanzu kam ya faru sai dai ya kiyaye na gaba kuma”. Ya bata amsa yana kwantar da ita shima ya kwanta a gefenta. Duk yanda taso tashi kuma ya hana dole ta haƙura. Sai dai ta masa shiru bata sake tankawa ba. Shima gajiya da suruntunne ya sashi rufe idanunsa da fatan samun barci.

     Koda suka tashi wajen sha ɗaya duk yanda Hibbah taso zillewa hanata yayi tare sukai wanka. Ta gama ƴan koke-kokenta na shagwaɓa ta bari. Breakfast ma tare sukayi, tanason taje gaida baba Saude ya hanata. Dole ta haƙura tanata faman sinne kai dan sam bata buƙatar su haɗa ido. Sai dai dukan motsinsa saita bisa da kallo, har yanzu zuciyarta na kaikawo akan kasancewarsa Isma'il kuma Master. Sarai yana lure da ita amma sai ya basar yanata aikinsa tana gefensa. Lokaci-lokaci yakan sakata tai masa wani aikin.
      A yau dai komai yinsa take babu musu ko tsiwa, dan idan ka ganta bazaka taɓa ɗauka Hibbahn Ummi da su Yaya Ammar bace. Haka suka kasance har yamma salla ce kawai ke tashinsu. Abinci ma da aka kawo na rana catai ta ƙoshi. Shima kuma baici ba dan bayajin daɗin bakinsa tamkar ita. Har dare bai fita ko inaba yanata aiki, sai bayan sallar isha'i ne Habib ya shigo musu da ledar kayan kwaɗayin da suka fita yawo suka siyo. Koda ya shigo falon Hibbah na kwance a doguwar kujeran da Master ke aiki kanta a saman cinyarsa. Dan ta kwanta tai filo da hanun kujerar ya taso daga inda yake zaune ya ɗagota yasa kan nata saman cinyarsa. Duk yanda taso tashi kuma bai bata fuska ba dole ta haƙura ta kwanta ƙamshin turarensa na mamaye kwanyarta a hankali. Aikinsa yake ita kuma tana kwance idanu a rufe ta lula duniyar tunani.
      Koda Habib ɗin ya shigo bayan ya amsa masa sallamar da bashi iznin shiga kallo ɗaya yay musu ya ɗauke kansa zuciyarsa na masa wani fari fat. Kayan ya ajiye yana masa sannu da aiki.
          Amsawa yay yana ɗago idanu ya kalli ledar, sai kuma ya maida dubansa ga Habib ɗin.
         Da sauri Habib yace, “Na aunty Queen ne, sai da safe”.
       Kafin ma master yace wani abu tuni ya fice. Kansa ya ɗan girgiza da maida dubansa ga Hibbah da duk take jinsu amma tayi luf. Ganin bata motsaba komai baice ba ya cigaba da aikinsa. Sai zuwa can da yaga barci na meman dibarta ne ya ajiye aikin yana buɗe ledan. Gasashshen namane mai romo da ice-cream. Sai Haɗaɗɗun chocolates masu daɗi. Roban ice-cream ɗin ya ɗauka ya buɗe. Dan shima ma'abocin sonshi ne. Batare da yayi magana ba ya ɗiba yakai baki.
       Hibbah dake sauraren taji yace ta tashi ta hadiye yawu da ƙyar. Jin alamar ya ƙara kaiwa baki yasata buɗe idanunta da miƙewa zaune. Hannu tasa ta warce roban tana ɗan hararsa ƙasa-ƙasa da ƙunkuni.
      “Ai nidai banji ance nakaba amma ka hau kai da sha”.
         Gira ɗaya ya ɗauke yana sauke mata wani shu'umin kallo. “Naga kamar baki da ra'ayine shiyyasa nace bara na maida jinina da kika tsotse jiya da wanda kikasa bindiga ta zubarmin”.
        Baki taɗan murguɗa gefe da kai cokalin ice-cream ɗin zata sha ya kai hannu zai riƙe ta tura da sauri.
     “Humm rowa ko?”.
  Kumburarrun idanunta ta ɗan juya masa “Kai da baka da rowar ka taɓa siyamin ne?”.
       Master daya shagala a kallonta har tana saka tsigar jikinsa tashi ya ɗan waro idanu kaɗan. “Aunty Queen kiji tsoron ALLAH ban sayo miki kazan first night ba randa aka

Please Login or Register in order to submit comment