Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kawoki?”.
          “Kadai satoni! Kuma ni babu wata kaza daka sayamin”.
        Dariya ta bashi, amma sai ya gimtse yay murmushi kawai. “Ai ke amaryace ta musamman, shiyyasa kaiki gidan mijinki ma ya zama na musamman.”.
      Yay maganar da ɗan kwantowa jikin kafaɗarta yana wani sassanyan murmushi idanunsa akanta. Matsawa taso yi ya tura hanunsa ta bayanta ya riƙo ƙugunta. Cikin marairaicewa yace, “Ki sammin ko kaɗan mana, inba hakaba kuma a daren nan na ɗiba rabona a can”.
        Sam Hibbah bata fahimci a ina zai ɗiba rabon nasa ba. Dan haka ta sake juya kanta gefe tana kaiwa baki da faɗin, “Gara kaje ka ɗiba rabon naka a can amma ba nan ba”.
       Wata ƴar dariyar ƙeta yay da ɗaura hanunsa saman ƙirjinta, “Ina godiya sarauniyar gidanmu”.
     Da sauri ta ture hannunsa har tana neman sakin robar ice-cream ɗin ya riƙo da sauri. Kafin tayi wani yunkuri ya miƙe zaune sosai da fige ɗan spoon ɗin ya juya mata baya. Shaf ta manta da wanda take tare, ta ɗane bayansa cikin shagwaɓa tace, “Ummi kin gansa ko”.
       Ice-cream ɗin ya dinga ɗiba yana kaiwa baki da kakkauce mata. Itako ta maƙalƙalesa ta baya da daura kanta a saman wuyansa tana son amsa amma ta kasa. Master da ke sha da sauri-sauri ya fara ƴar dariya mara sauti da batai zaton ya iya ba. Ganin yasha kusan rabi yasata barin bayansa ta sakko da sauri a kujerar taje gabansa zata warce ya kauce ta faɗa jikinsa. Zaune tai ɗare-ɗare bisa cinyarsa. “Ni wlhy ka bani abuna, ai dai baice naka bane, nawa yace”.
       Master dake murmushi ya sake kaiwa bakinsa da ajiye robar ta gefen kanta batare data sani ba. Ta buɗe baki zata sake magana ya haɗe bakin nata da nasa ya fara juye mata ice-cream ɗin daya gama narkewa a cikin bakinsa. Bata da wata mafita saita shanyewa. Dan ganin tana son ture masa fuska ya sashin toshe mata hanci dole ta haɗiye. Koda ya saki hancin bai saki bakinba ya zarce da kissing ɗin ta. A salon da yake sumbatar natane ya sata nutsuwar dole tana amsar sakonsa. Sai da taji hannunsa cikin rigarta ne tai ƙoƙarin turesa jikinta na fara rawa.
        Matsar da bakin yay yakai saitin kunnenta yana sake rungumota da ƙyau. “Kemafa yarinyar nan na kula fitinanniya za'ai. Dan sosai jikinki ke amsar kowanne saƙo”.
        Hibbah jitai tamkar ta tsala ihu. Tai azamar wuntsilowa a jikinsa, yana son kamota ta zille da gudu tabar wajen.
         Binta da kallo yayi yana sakin murmushi da lumshe idanu.

★★★

       Hibbah bata sake jin ɗuriyar Master ba har tai shirin barci ta kwanta, zuciyarta cike da tunani da kwaɗayin ganin ahalinta. Wani gefe kuma na imagine yanda su Ummi zasuji cewar Isma'il shine master ashe, dan ita kam har yanzu zuciyarta ta kasa gaskata hakan, neman wanda zasu tattauna maganar kawai take a ranta. Dan tambayoyine fal bakinsa amma kunyarsa da nauyin daya aza mata yasa ta kasa masa ko guda ɗaya.
     Tun tana a tsorace da tunanin zai shigo har barci yay awon gaba da ita bai shigo ɗin ba. Sai kusan ƙarfe ɗaya har tamayi nisa a barci sannan ya shigo a matuƙar gajiye da tsananin bukatar barci. Yaji daɗin ganin tayi barcin, hakan na nufin ta ɗan samu ƴar nutsuwa a zuciya da jikinta daya murza a jiya. Shirin barcin yay shima da dukkan abinda yake na al'adar rayuwarsa sannan ya kwanta a gefenta.

    *_Washe gari_* tamkar jiya tare sukai sallar asuba. Hibbah dake ta faman sinne-sinnen kai ma ta gaishesa da tambayar jiinsa. Amsa mata yay da tambayarta nata jikin itama, tace ita dai lafiyarta ƙalau. Murmushi yayi kawai bai sake cewa komai ba harya kammala azkar ɗin dayay zamanyi sannan ya mike ya bita gadon. Harta fara lumshe idanu taji saukar hannunsa a jikinta. Babu shiri ta buɗe tana kai hannu zata ture nashi. Hanawa yay ta hanyar riƙe hanun nata da busa mata numfashinsa cikin kunne.
         Zatai magana yay saurin tareta da faɗin, “Shiiii bake kikace lafiyanki ƙalau ba”.
         “Da wasafa nake ALLAH akwai ciwo”. Ta faɗa da sauri tana buɗe idanunta sai gasu a cikin nasa. Duk kuma yanda taso janyewa ya sarƙesu ta gagara. Wasu mayatattun halittun fitina take gani suna yawo a cikin idanun nasa. A take nata suka fara tara ƙwallar da shi kuma suka sake ɗaga masa hankali.     
         “A ina ciwon yake?”.
Yay maganar da wata kasalalliyar muryar dake tabbatar da ɗunbin begenta dake cizonsa. Sake rikicewa Hibbah tai zata fara ja da baya yay mata runfa da jikinsa yana jan sassanyan numfashi da busa mata akan fuska. Sosai ta rikice, dan irin abinda tagani cikin idanunsa a shekaran jiya da rana yanzunma shine tattare da shi. A hankali ya ɗaura hanunsa saman nata yana sake matso da fuskarsa gab da tatan. Kai ta shiga jujjuya masa laɓɓanta na motsawa alamar son roƙonsa.
     Yasan bazai iya ɗaga mata ƙafa ba, hakan yasashi lumshe idanun nasa dai-dai yana kai laɓɓansa saman tausasan nata, dan dama dauriya kawai yakeyi harya iya ɗaga mata ƙafa da daddare. Rawar jikinta da kukan da take masa yau har yaso yafi na shekaranjiya dan wahalar data sha kawai take ƙiyastowa. Shiko da idanunsa suka rufe bida ita kawai yake ta salo-salon da baisan yama iyaba sai yanzun.

         Kuka take sosai tana lafe a jikinsa, nata jikin na ɗan rawa dan yauma ɗin dai wahalar tasha, duk da dai ta shekaranjiyan tafi ta yau sai dai ta yau ɗin ma babu sauƙi dan famine. Shiko babu abinda yake iya furtawa sai shafa bayanta zuwa gashin kanta.
     “ALLAH yay miki albarka”.
Ya faɗa a fusge yana sake turata cikin jikinsa har saida ta ɗan saka masa kuka ya sassauta mata. Sai da yaji kukan nata ya ƙi tsayawane ya mike cike da dauriya ya kaita toilet. Yau ɗin ma dai da taimakonsa ta gyara jikinta tana faman masa raki da roƙon ya kaita wajen Ummi ita dai karya kasheta.
       Sosai yaji tausayinta dan shima yasan dai yayi gaggawar koma mata duk da wahalar data sha kwana biyu da suka wuce. “Indai wajen Ummi ne zan kaiki, amma sai kin barmin kuka. Kin yarda?”.
     Da sauri ta jinjina masa kai alamar eh ta yarda. Ya sumbaci kumatunta da faɗin, “Good girl! ko ke fa. Kefa yanzun kin girma harkan yara yawane Hibbaty”.
        Da wannan daɗin bakin ya taimaka mata suka fito, koda suka sake komawa suka kwanta lafe masa tai a jiki tana jan ajiyar zuciya har barcin wahala yay awan gaba da ita cikin ƙanƙanin lokaci. Sumbata ya kaima goshinta, a ransa wani nutsuwa da kaunarta na ratsashi. Dan a yau yafi jin matuƙar nutsuwa fiye da shekaranjiya da komai yayisa ba cikin hayyacinsa ba.

        Barci sosai sukayi batare da wani ya takura musu ba. Dan su Habib ma tun safe suka bar gidan. Baba Saude kuwa da ba sanin mike faruwa tayi ba ita duk ɗaukarta ma Hibbah bata gidanne. Dan tun randa sukazo bata sake ganinta ba master ya kasa ya tsare.
      Kusan a tare suka farka. Sai dai jin motsinsa yasa Hibbah ƙin buɗe nata idon. Idanunsa ya zubama fuskarta yana ƙare mata kallo, yanda yaga idonta naɗan motsawa yasan ta tashi. Baiyi magana ba, sai yatsansa daya ɗora saman rumfar idon yana wasa da shi. Dole ta buɗe idanun da ture hannunsa tana kumbura fuska. Murmushi yayi da saƙalo hanunsa ta bayanta ya matso da fuskokinsu dab da juna yana kai mata sumbata.
       “Nifa kwana biyu naga harma kin nutsu autan Ummi”.
       Yay maganar cikin raɗa tamkar mai tsoron ajisu.
     A ranta tace, (ba dolena ba. kana min wannan muguntar nacika magana kace na maka rashin kunya ka fake da hakan ka maidani machine). A fili kam saita marairaice masa fuska tana mar-mar da idanu. “Dan ALLAH yaushe zaka kaini wajen Ummin?”.
          Yasan dama shine matsalarta. Maimakon ya bata amsa sai ya lumshe idanunsa yay shiru tamkar bai jita ba. Idanunta ta buɗe tana kallon fuskarsa har batasan ta shagala ba. Sosai yaji idanu na yawo masa a jiki, amma ya dake harda sauya saukar numfashinsa tamkar mai barci. Tunaninta barcin gaskiyarne ya ɗaukesan. A hankali takai hannu bisa girar idonsa ta ɗan gyara, sai kuma ta murza goshinsa kaɗan duk dan son ta tabbatar ba facemask ya saka ba. Sake kumawa tai kan laɓɓansa nan ma dai taji, ta cigaba da shafa kumatunsa da siririn gashi na saje ke kwance har zuwa kunnensa ta ɗan murza nan ma zuwa bayan kunnen da ƙeyarsa. Yanda take masa gaba ɗaya tsigar jikinsa miƙewa take, ganinfa da gaske neman firgita masa jiki takeyi sai da ya shammaceta ya buɗe idanunsa da suka fara sauya kala. Aiko karaf suka faɗa cikin nata. Saurin janye hannunta tai a fiskarsa amma ya riƙe ya dannesa da nasa. Gaba ɗaya ta daburce, baya ta juya masa murmushi na kufce mata dan taji kunya harga ALLAH.
           Shima murmushin ya saki da kwantowa bayanta yana son leƙa fuskarta. “Ki kalli mijinki nakine auta, yanda kike auta a gidanku insha ALLAH kece ta fari kece auta a zuciyar Shuraim ɗinki. Karkiji komai, kiyi komai ba komai baby luv”.
       Fuskar ta cusa a cikin filon, duk yanda yaso ya janye taƙi. Dole ya haƙura ya miƙe yana dariya da take mamaki. Tanaji ya shiga toilet ta sauke nannauyan ajiyar zuciya. Jin motsin ruwa ya sata tabbatar da wanka yake dan haka ta miƙe ta fara gyara gadon, fatanta ta fice kafin ya fito. Tana cikin gyaran takardun daya ajiye idanunta ya sauka akan wadda ke sama da tsautsayi yasa file ɗin ya ɗan goce suka zubo. Tsugunnawa tai tana tattarosu sai taga tamkar sunan Abbansu a jiki. Duk yanda taso hana kanta dubawa ta kasa, ɗaya bayan ɗaya ta dinga dubasu sai taga duk takardun kaddarorinsu ne da ta taɓa jin su Yaya Muhammad na maganar suna hannun Halilu. Mamaki ya kamata ta cigaba da dubawa har zuwa na ƙarshe da ke rubuce da dogon bayani. Ƙofar bayin ta ɗan kalla jin har yanzu akwai motsin ruwa yasata zaman dirshan ta fara karantawa a nutse..........✍


TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥

*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*

*_NAJI DADI SHINE GARI......_*

*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*

_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_

*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*

     *NA SABUWAR SHEKARAR 2022*

*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*

*SABBIN LABARAI*

*SABUWAR SHEKARA*

*SABON NISHADI*

*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*

*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*

*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.

*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_

*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_

*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_

*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_

*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*

6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank

Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number

08184017082

*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*

09134848107

Littafi daya

1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).

*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽

#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥



*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*

 

*_Chapter Forty Three_*



...........Bayanine tiryan-tiryan daya shafi takardun da harƙallarsu, harda kuɗaɗen daya kwashe na Halilun da yanda akai ya amshesu, da masu mallakin dukiyar da alaƙar dake tsakaninsa da su A.G. A yanzu kam Hibbah ta sake tabbatar da Master baya tare da su A.G ɗin, duk da ya mata bayanin komai ta yanda ya shiga jikin nasu da tunanin shaiɗaninsu ne shi. Wasu irin irin hawaye suka gangaro mata saman fuska zuciyarta na tunano mata randa Isma'ill ya karyama Abba ƙafa akan abinda yay ma Ummi.....
       Zare takardar da akai ta bayanta da ɗisowar ruwan wankan jikinsa ne ya sata juyowa da sauri. Master daya tamke fuskarsa matuƙa kamar bashine ya gama tarairayarta yanzun ba, ya ɗan harareta yana ɗaukar sauran takardun ya maida cikin file ɗin. Ya ajiye ya juyo kawai yaji ta faɗa masa jiki a bazata ta rungumesa da sakin wani marayan kuka. Babu shiri ya dafe towel ɗin daya ɗauro a ƙugunsa dake neman faɗuwa. Dama ba wani rigan arziƙi bane a jikin nata, hakan sai ya bashi damar jinta bisa fatarsa dake ta faman raɓar ruwa yanda ya kamata. Ya lumshe idanunsa  yana riƙota da ƙyau shima da sakin nannauyar ajiyar zuciya.
        Baice komai ba sai yatsun ɗayan hanunsa daya tura cikin gashinta, ɗaya kuma yana shafa bayanta a hankali, zuciyarsa sai wani irin zallo take da tsalle-tsalle kamar zata fito waje. Ganin kukan nata bana ƙare bane yajata suka zauna a bakin gadon tana jikinsa. Fuskarta ya ɗago dasa babban yatsansa yana share mata hawayen.
       “Miya faru kuma?”.
  “Ka yafe min”.
Wani ƙasaitaccen murmushi ya saki yana ɗan ɗage gira sama, idanunsa na yawo akan fuskarta. “Ni baki min laifin komai ba”. Yay maganar yana ɗan sumbatar laɓɓanta.
       Kanta ta girgiza masa hawayen na sake rige-rigen sakkowa. “Nasan na maka laifi, na fahimceka a bai-bai, amma wlhy karkaga laifina nima inada hujjata. Nagode, ALLAH ya saka maka da alkairi, ya cigaba da baka kariya a dukkan motsinka da al'amuranka. Abinda naji wajen su Abba da shegen jami'in nan yasa nake maka kallon bai-bai. Kuma koba niba duk wanda yaji tunda baisan gaskiya ba zaiyi komai kamar nine”.
       “Na sani Muhibbat, shiyyasa naita miki uziri. Duk da kin hasalamin zuciya a ranar, dan kaɗan ya rage ki buɗemin dukanin aikina da zai iya sa harsu Ummi su rasa ransu ma. A hakanma kaɗan ya rage ki jefa rayuwarsu a haɗari, ALLAH ya taƙaita. Ina ƙaunar Ummi Muhhibat, hakama su yaya Muhammad. Bayan yaran nan da kike ganina da su a yanzu ahalinki sune ahali na biyu da nake kallo mafi kusanci dani a duniya. Tun bayan rasa mahaifiyata Ummi ce ta fara dafa kaina taimin addu'a cike da soyayya. Taya kike tunanin bazanyi yaƙi a kan zuri'arta ba. Taya bazanso haɗa jini da ita ba.” ya ɗaura hannunsa saman cikinta “Ina fata da addu'ar ALLAH yasa wannan cikin nayi ajiyar jinina da zai miki rakkiya zuwa wajen Ummina”.
       “Nidai ba yanzu ba”.
Ta faɗa tana tura baki da kwantar da kanta a kafaɗarsa.
       “Haba baby luv kiji tausayina mana, Su uncle Habib mafa shi suke jiran gani”.
        “Waɗan nan na daina kulasu a gidan nan ai, dan suma haushina sukeji”.
      Ƴar dariya yayi mara sauti da kamo hannunta ya ɗaura bisa fuskarsa. “Kefa kikai musu laifi, kika sa aka harbar musu Yayansu. Ba dole suyi fushi da ke ba. Amma nasan da sunga kin ɗan fara amai sun samu ɗa zasu daina ai”.
          Baki ta tura tana ƙara cusa kanta a wuyansa. “Ni dai nace ba yanzu ba”.
         “To ai ya riga ya shiga insha ALLAH, dan ban buga ƙwallona da wasaba tun a farkon fari”.
        Tashi tai zata bar jikinsa da faɗin, “Nidai babu ruwana wlhy inada kunya”.
         “Nima ai inada ita. Bakiga tun shekaran jiya kunyarki nake ji ba”. Yay maganar yana binta da kallo.
        Juyowa tai ta kallesa da ɗan waro idanu tana riƙe haɓa “Kai ɗinne kake wani jin kunyata?”.
       A yanda tai maganar da waro idanun da bage bakin ya bashi dariya, amma sai ya gimtse baiyiba, yay ɗan murmushi kawai da ɗage gira ɗaya. “Baki yarda kin kalleni ba yazaki gani. Idan kina son tabbatarwa zoki gani”.
     Kafinma ya rufe baki ɓurum ta faɗa toilet da sauri. Murmushin fuskarsa ne ya sake faɗaɗa. Ya miƙe domin shiryawa yana godema ALLAH da wannan farin ciki daya bashi a lokacin da bai zata ba. Harya kammala shirinsa tsaf cikin ƙananun kayan nasa na fama Hibbah bata fito ba. Yasan inhar tanajin motsinsa a ɗakin kota gama bazata fito ba. Dan haka ya tattara wayoyinsa da lap-top yayo falo.

          Tun a ƙofar fitowa yaja ya tsaya saboda cin karo da baƙon dake zaune a falon ƙafa ɗaya kan ɗaya yana kallo. Abdull da ya ɗan ɗago ya kallesa ya ɗauke kansa yana wani shaƙiyin murmushi. Hararsa Master yayi da cigaba da takowa cikin falon. Ya zube kayan hannunsa saman centre table ɗin da fisge remote ɗin hanun Abdull ɗin ya rage ƙarar tvn.
      “Banza ɗan nanaye ko ina ake sai an nuna hali”.
      Murmushi Abdull ɗin ya sake saki har da ƴar dariya. “Ni da kai a tantance ɗan nanaye ai ayanzun. Mutumina kafa samu lafiya da alama. Na wani tada hankalina a banza harda baro canada babu shiri”.
        “To ubanwa yace kazo mai kan gwanda kawai.”
      “Zakako cika baki yanzun tunda harbi yayi sauƙi, tsabar zalama ma ga ciwo sai da ka tafi kwaɗayi filin ball”.
            Murmushi master yayi dan Abdull ba ƙaramin tasa rayuwarsa yake gaba ba. Shima mutum ne mara son hayaniya da yawan magana, dan harma yafisa miskilanci. Amma inhar suna tare to bakin Abdull cau-cau akansa.
        “Wai yaushe ka shigo haka dan ALLAH?”.
      “Tun randa aka harbeka. Daddy (I.G) ya sanarmin naji bazan iya kwana a canada banzo naga rabin jiki ba.”
        Dariya Master yay yana gyara zama. “Shine sai yau nake ganinka, kazo kuma kanamin iskanci anan. ”
            “Tun randa kasha harbi ina gidan nan, kai ne dai kai wahalar gani saboda kana daga lungu kana tsinkar fure.”
       “ALLAH ya shiryeka to”.
Master ya faɗa yana murmushi.
       “Amin ya rabbi tunda addu'a kaimin. Ina madam ɗin tazo na ganta, dan na huce zuwa yanzu tunda nasa an rama mana harbinmu”.
         “Mara kirki, ALLAH zai saka mata ai”. Master ya faɗa yana miƙewa. Dariya Abdull yayi yana binsa da kallo, “Eh lallai ka shiga hannu ɗan gimbiya. Da alama dai ƴar shilar nan taka tauraruwa ce cikin taurari”.
        Master da ke haɗo musu coffee yay murmushi kawai batare da ya bashi amsa ba. Sai da ya kammala ya dawo falon ya ajiye a centre table ya zuba musu sannan ya zauna bayan ya mikama Abdull ɗin nasa.
      “Bestie ya yarana da madam?”.
   Abdull ya ɗan ɗage kafaɗa da faɗin, “Lafiya lau suke, sunata gaisheka.”
       “Ina amsawa, nayi kewarsu da yawa gaskiya”.
     “Karka damu suna gab da dawowa kusa da kai insha ALLAH. Ya gwagwarmaya? Daddy nata bani labarin ayyukanka da jajircewarka. ALLAH ya saka da alkairi ya ƙara girma”.
        Master dake murmushi ya kai kofin coffee ɗin bakinsa ya ɗan kurɓa. “Uncle baya gajiya da yabona, shi baya tsoron kar wataran naci amanarsa”.
    Harararsa Abdull ɗin yayi ya ɗauke kansa. Zaiyi magana Hibbah da batasan da zaman Abdull ɗin ba ta fito cikin shirin son zuwa gaida baba Saude yau. Ganin Abdull ɗin na kallon hanyar bedroom ɗinne yasa Master juyawa ya kalla wajen shima. Numfashi ya ɗan ja a hankali ganin yanda kayan sukai mata ƙyau, baiyi zatonma zasu mata ba a lokacin daya sayesu. Ganin ta ɗan daburce kamar zata juya yay mata alama da idanu tazo. Babu musu ta gyara ƙaramin gyalen data yafo saman wando da rigan parkistan ɗin ta nufosu cike da nutsuwa tamkar ba ita ba. Abdull da tuni ya ɗauke kansa da ga kallonta ya maida ga tv yace, “Amarya baƙya laifi ko kin kashe ɗan masu gida”.
        Murmushi Hibbah tai da kaiwa zaune a kujerar da ke kusa da ita. Cikin girmamawa ta shiga gaida shi. Shima amsa mata yay da kulawa yana kallon Master da ya cigaba da shan coffee ɗinsa yana saurarensu.
      “Amarya yaya kina kulamin da bestie na sosai ko?”.
      Murmushi tayi, dan gaba ɗaya jitai kunya ta dabaibayeta. Sai take ganin kamar kowa zai iya fahimtar halin da take ciki tsakaninta da Master yanzun. Shi dai Abdull ya cigaba da tsokanarta ne. Yayinda ita kuma ta kasa amsawa dan kunya. Sai da ya gaji dan kansa ya barta. Master dai bai tanka musu ba har sai da Abdull ɗin yay shiru sannan ya duba Hibbahn, saboda nutsuwar tata yay masa daɗi.
      “Muhibbah!”.
Ya kira sunanta a hankali. Ɗan ɗagowa tai ta dubesa da amsa masa. Ganin ita yake kallo ya sata sake maida kanta ƙasan.
     Ya ɗan sake kwantar da bayansa jikin kujera yana kallon nata. “Wannan sunansa Abdul-Hakim. Aminina ne kuma ɗan uwana. Likita ne a yanzu haka yana zaune a canada tare da iyalinsa da yaransa biyu”.
       Jin yayi shiru ne yasa Hibbah jinjina masa kanta. Tace, “Masha ALLAH Yaya sannu da zuwa. Ka baro su lafiya?”.
           Abdull da Hibbahr ta birge ba kamar yanda yake tunanin ganintaba yay murmushi, “A lallai na samu ƙanwa kenan. To ina godiya sosai Muhibbat. Suna lafiya, suna kuma gaisheki”.
      “Nagode ina amsawa”.
  “Nima nagode sosai da samun tarba daga gareki”.
        Kanta kawai ta jinjina masa tana miƙewa. Rasa madafar ina zata dosa ya sakata nufar kitchen, a yanda ta samu kitchen ɗin sai kawai ya birgeta taji sha'awar yin abinci a ciki. Ƙofar baya ta fita ta kitchen ɗin, wadda daga nan babu nisa da sashen su Habib. Babu wani tunani ta nufi can. Sai dai bata samu kowa ba sai baba Saude da taji daɗin ganinta. Dan sai tambayoyi take mata akan yaya take? Ina ta shiga? Yaya jikinta?.
     Hibbah da itama tai kewarta harsu Habib ɗin ma da Sharifat ta amsa mata cike da girmamawa. Daga nanne suka ɗan taɓa hira har Hibbah ta sakko zancen sonyin girkin amma ta duba a can sashen babu kayan abinci.
     Karan farko da baba Saude taji aranta kodai akwai alaƙa ta aure tsakanin Master da Hibbah ne? Kamar zata tambaya dai sai tai shiru. Sai ma sanar mata da tai cewar gama breakfast ɗinsu nan tun ɗazun take jiran shigowar su Salis sukai amma babu wanda ya shigo tun fitar safe da sukayi.
       A nutse Hibbah ta amsa mata har baba Saude na mamakin yanda ta canja mata a ƙanƙanin lokaci. Sai dai ta danne a ranta ta bita da kallo harta fice.

     Koda ta dawo sashen nasu a yanda ta fito ta kitchen da babban tray ɗin sai Abdull yay tunanin ita ta haɗo musu abincin, Master dai da kallon mamaki ya bita amma sai baiyi magana ba harta kai trayn ajiye saman centre table. Ɗan ɗagowa tai ta dubesa. “Ko akai muku dining?”.
       Tsabar mamakin daya rufesa da ƙyar ya iya kaɗa mata Kansa. Kafin ya iya motsa laɓɓa da ƙyar yace, “Nan ma yayi sannu da ƙoƙari”.
      Kanta kawai ta kaɗa masa tabar wajen, kitchen ta koma ta haɗo duk abinda zasu iya buƙata ta ɗauraye ta sake kawowa, kafin ta koma ta ɗauka ledan jiya data gani cikin fridge. Chocolates ne a ciki sai naman da ko taɓashi basuyi ba. Sai roban ice-cream guda ɗaya data rage. Chocolates ɗin ta ɗiba guda uku ta ɗauka naman ta koma sashen su Habib.
         Yanzun kam ta iske sun dawo, dan tana shiga suka haɗa baki wajen gaisheta da kiranta aunty Queen kamar yanda suka saba. Harararsu tayi itama kamar yanda ta saba ɗin, kafin takai zaune kusa da baba Saude tana ɓare ledan chocolate ɗaya ta kai baki. Koda suka cigaba da hira sunsha matuƙar mamakin yanda take amsa musu a nutse tamkar ba ita ba, hakan yasasu fahimtar dama tsiwa ce ke damun bakinta kawai badan batasan komaiba ko bata da nutsuwa ne. Habib ma tun yana ɗan basar da ita harya saki jikinsa kuma. Itako tayi mirsisi tamkar ma

Please Login or Register in order to submit comment