Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da can, washe gari da safe ya sake basu umarnin su bishi. Mahaifina bashi da wata mafita banda ya bisan, da yake lokacin duniya na bacci azzaluman basuyi yawaitar yanzun ba. Sun sake yada zango a ƙasar Niger. Inda sukai kwanaki biyu anan dattijo ya kammala harkokinsa. Koda ya sake tabbatar musu gaba zasuyi basu damu ba, suka nuna masa amincewarsu. Yaji matuƙar daɗin yanda suka aminta da shi babu bincike ko nuna shakku”.
        “Bara dai karna jaku da nisa. Daga ƙarshe Iyayena sun tsinci kansu ne a ƙasar haihuwa ta wannan dattijon. Tun a tarbar da akai musu suka fahimci dattijon nan da ko sunansa bai sanar musu ba ƙasurgumin mai arziƙi ne. Yayinda suka isa katafariyar daular sa kuwa sai mamaki ya kamasu na dalilin zuwansa ƙasarsu, dan kuwa dai ya fito ne da ga gidan sarauta mai faɗa a ji da tarihi. Dattijo yasa an karrama rayuwarsu da basu muhallin zama mai tsafta. Bayan kwana biyu sun huta ya nema jin labarinsu. Mamana taso a ɓoye. amma sai babana yace su faɗa masa gaskiya kodan karamcin da yay garesu. Wannan dalilinne ya sakasu fayyace masa komai na rayuwarsu har barowarsu gida. Ya nuna tausayawa a garesu da ga ƙarshe ya ɗauka mahaifina ya ɗaura akan dukiyarsa. Amana da jarumtar da Abbana ya nuna wajen tsare dukiyar da nuna gaskiya yasa Dattijo yarda da shi, harya maidashi babban yaronsa makusanci, komai ya koma hannunsa. Wannan abu ya baƙanta ran ƴan masarautarsu ƙwarai da gaske. Harma da sauran yaransa da ke hidima ma dukiyar kafin zuwan su Abbana. Ƙiri-ƙiri suka ɗauka karan tsana suka ɗorama Abbana, kullum cikin masa gorin shi din baƙon haurene suke.”
        Rayuwa ta sauyama iyayena. Dan cikin ƙanƙanin lokaci dukiya ta bunƙasa garesu. Basu da wata matsala sai ta rashin haihuwa da tsangwamar mutane. Haka suka cigaba da haƙuri da juriya na tsahon shekaru har ALLAH ya azurtasu da samun cikina. Sunyi matuƙar farin ciki, irin wanda baki bazai misalta ba. Hakama Dattijo Isma'il yayi farin ciki tamkar shi za'aima haihuwar, dan shima bai taɓa haihuwa ba. Bayan cikina ya cika watanni tara aka haifoni, inda naci sunan dattijon nan wato Isma'il. Sai dai kallon mahaifi da babana ke masa yasa sukemin alkunya da suna Muhammad Shuraim.”
      Na tashi ɗan gata a wajen dattijo Isma'il da mahaifana. Yayinda tsiraru a cikin jama'ar masaruta ke sona. Wasu ko yanda suka tsani mahaifana haka suka tsaneni duk da ƙanƙantar shekaru na. Shekarata uku a duniya Abbana ya maido mamana ƙasarmu ta haihuwa saboda bazai juri tsangwamar da ake musu nima aimin ba. Dangi sunyi murna, sun kuma sha mamakin ganin ya kuɗance lokaci ƙanƙani. Dan yama take kakana ya shanye dukiyar da suke ƙinsa a dalilinta. Koda ya ajiyemu komawa yay ya cigaba da lura da dukiyar dattijo. Daga ni iyayena basu sake samun wani cikin ba har na kai tsahon shekaru takwas, kafin mamana ta wayi gari da ciki. Nanma sunyi murna, hakama ƴan uwa, musamman ma ni. Cikin mamana na watanni uku ciwo ya kai dattijo Isma'il ƙasa, wanda ake zargin sammu akai masa. Mahaifina shine ya koma jinyarsa, dan ƴan uwansa kowa ya noƙe, burinsu kawai ya bar duniya suhau kan dukiyarsa har matansa.”
           “Dattijo Isma'il ya riga yasan da wannan tun ba yanzu ba, dan haka a wani dare ya zaunar da mahaifina cikin dauriya ya sanar masa ɗunbin dukiyarsa daya tattare ya killace batare da sanin masu jiran ya wuce su hau kai ba. Gaba ɗaya ya mallakama mahaifina wanann dukiya, sannan yay masa umarni da ya bar ƙasar bayan ya damƙa masa fuskokin jabu (Facemask) guda uku yace koda ya dawo ƙasar haihuwarsa ya cigaba da amfani dasu shi da mamy na da ni dan yasa ƴan uwansa zasu bibiyesa bazasu barsa ba. Mahaifina yayi kuka sosai a wanann dare, kuka irin wanda ɗa ke yi yayin rasa mahaifa ko yin nesa da su. Shidai dattijo Isma'il nasiha yayta masa da addu'oin fatan alkairi da gamawa da rayuwa lafiya. ALLAH sarki rayuwa ashe nasihar ƙarshe ce, dan kuwa a safiyar wannan ranar aka wayi gari da rashin dattijo Isma'il. Abbana ya shiga ɗimuwa matuƙa harma ya rasa ina zai saka kansa. Yayinda tsoro ya kamashi ganin yanda matan dattijo da danginsa tun kan akai gawarsa harsun fara rigima akan dukiyar da suke tsammanin ya bari. Ana kai gawar dattijo Abbana ya silale ya baro ƙasar da dukiyar daya mallaka masa bisa umarninsa. Inda yabar baya da ƙura. Dan kuwa dattijo kashi uku ya raba dukiya yabar musu kashi guda kawai. Wannan dalilin yasasu farga da rashin Abbana da wuri saboda sunce a nemosa yay musu bayanin ina sauran dukiyar take.”
       “Abbana ya dawo ƙasarsa ta haihuwa cikin zuri'arsa, sai dai kuma anyi rashin sa'a dangin dattijo nacan na bincike a kansa har suka gano inda yake. A nan kuma ɓangaren Abbana koda ya dawo ni kaɗai suke sakama Facemask idan za'a kaini makaranta ko zan fita waje. Su mutane a tunaninsu baƙon yaro mukai, shiyyasa basu taɓa kawo hankalinsu a kaina ba. komai ya sake canjawa. hankalin iyayena ya kwanta, sunan mahaifina ya sake yin shura musamman akan harkar kasuwanci. A ƙanƙanin lokaci ya zama bashi da abokan mu'amula sai manyan mutane, a ƴan uwa kuwa dama zuwa yanzun iyayensu duk sun rasu, babu wasu shaƙiƙai na jini dan shima tamkar Mamyna shi ɗaya aka haifa a gidansu, baima san mamansa ba.”
     “Lokacin da cikin Mamy na ya shiga watan haihuwa a lokacin komai ya sake canjawa, dan kuwa dai dangin dattijo sun ƙaraso ƙasar nan batare da sanin Abbana ba. Hasalima har sun kammala bincike akansa da inda yake.”. Hannu ya kai ya ɗauke ƙwallar da suka cika masa ido, kafin ya cigaba da faɗin, “Ranar da bazan taɓa mantawa ba. Rana mafi ciwo da zafi, ranar da duk nisan tarihi bazai gogeta ba a gareni itace ranar juma'ar dana rasa iyayena duka. Dan kuwa dangin dattijo da taimakon wasu hatsabibai sukaima gidanmu dirar mikiya. Hankalin mahaifina ya tashi, dan ya tabbatar tamu ta ƙare, amma sai cikin jarumta ya faɗama mahaifiyata duk tsanani karta buɗe ƙofa shi zai fita shi kaɗai, idan kuma zamanta da nawa bazai yuwu ba ta tabbatar ta fita zai janye hankalinsu, ta kuma sakamin facemask ɗin wajen dattijo itama ta saka nata. Mahaifiyata na kuka ta shiga roƙonsa kar yaje amma sai ya lallasheta da bata ƙwarin gwiwa. Ya fita garesu, inda suka zagayesa da mahaukatan makamai tare da basa umarnin fiddo musu dukan dukiyarsa. Gane dangin dattijo da yay ya sakashi yarda zai basu, tare da roƙonsu idan ya basu su barsa da ransa cikin iyalansa. Sun nuna sun amince, dan haka Abbana ya tattara kuɗaɗen ya basu harma da dukkan takardun kaddarori suna kammala amsa ɗaya da ga cikin dangin dattijo cikin bada umarni yace (Master kashe shi). Shigar wannan furuci a cikin kunnena ya sani fashewa da kuka a cikin dakin da muke maƙure ni da Mamy. Na mike a razane da nufin fita Mamy ta hanani. Kuka nake ina fisgewa har na samu damar guduwa na leƙa ta jikin window. A dai-dai wanann lokacin wanda aka kira da Master yasa yaransa suka kama Abbana suka danne yay masa yankan rago cikin rashin tausayi da rashin imani duk da kwata-kwata shekarunsa bazasu gaza ashirin ba a duniya”.
     “Kuka na fasa wanda ya jawo hankalinsu ɗakin da muke. Cikin bada umarnin ɗan uwan dattijo ya ce muma a kashe mu. Hankalin Mamy da ya fara gushewane ya dawo jikinta saboda tuna wasiyyar Abba. Cikin rawar jiki ta kama hannuna muka fita ta ƙofar baya su kuma suna ƙoƙarin buɗe ƙofar. Kasancewar a cikin falo komai ke faruwa muka fice a gidan ina kuka mahaifiyata na kuka jini na zuba a jikinta ga tsohon ciki. Tafiya muke ta ceton rai dan kuwa suna buɗe ƙofa sukaga alamar mun fita ta ɓarauniyar hanya sai suka take mana baya. Fahimtar ana binmu yasa Ummi cikin galabaita ta ce naje kawai. Kaina nake girgiza mata ina kukan ni bazanje ko ina na barta ba. Sanin taurin kaina yasata juriyar cigaba da tafiya batare da mun fahimci inda muke jefa ƙafa ba dan gari yayi shiru kasancewar dare ya tsala. Sosai Mamyna ta sake galabaita, saboda alamar haihuwa data zo mata gadan-gadan, ga jini na zuba mata. Yanke jiki tai ta faɗi, na durƙusa a gabanta ina kuka da kiran sunanta ta tashi, amma ina bazata iya ba. Cikin amincin ALLAH mutumin da muke a ƙofar gidansa yaji kukana ya fito. (Sun kashemin Abbana da Ummina baba sun kashesu) na faɗa cikin kukan daya saka Hankalinsa tashi ya kamani ya muƙar tare da ɗaukar Mamy gaba ɗaya ya shige damu cikin gidan. A daidai lokacin su dangin dattijo da ke binmu suka iso ta ƙofar gidan tare da ƴanta'addan hayarsu. Sai dai rashin tabbatar da muna anan ɗinne ya sasu wucewa dan baban nan daya taimakemu ƙarar tahowarsu ta sakashi sa hannu ya toshen baki. Wucewarsu da kamar mintuna biyar naƙudan mamana ya tsananta. Baba ya rasa yanda zaiyi dan bashi da mata. Haka yanaji yana gani ya sama Mamyna ido harta haihu. A galabaice ta damka amanarmu a hannunsa tare da roƙonsa da cewar ya kaimu gidan marayu dan zama anan gidan bazai bamu tsaro ba tunda ta tabbatar dangin dattijo Isma'il sun gama sanin komai a kammu da kamanina na gaskiya tun kan suzo garemu. Tana gama faɗar haka ta bar duniya.”
        “Na ɗanɗana raɗaɗi biyu na zafin rashi a dare ɗaya a kusan lokaci ɗaya. Ga kuma ƙani Ummi ta haifamin. A taƙaice dai a ɓoye dattijo ya samo maƙwafta sukai jana'izar mamyna a washe gari da safe, bayan wata tsohuwa ta suturtata. Bani da wayo sosai dan shekarata tara kacal. Amma na shiga damuwa sosai. Dan ma kallon jaririn Mamy na ɗan ragen jin zafi. Wasiyyar Mamyna tasa baba ɗaukarmu a washe garin da Mamy ta cika kwana uku mu da shi duka muka koma gidan marayu gudun kar makasan su gano inda muke. Ashe shima bai taɓa haihuwa bane shiyyasa matansa duk suka gujesa.”
         “Mun koma gidan marayu da zama inda baba ya tambayeni sunan da zai sama jaririn Mamy na ce Habib. Babu musu baba yay masa huɗuba da suna Habib. Nine na cigaba da rainon Habib a gidan marayu, tare da matar da ke kula da mu da baba wanda a yanzu shine tamkar mahaifina. Karku manta inada facemask ɗin da dattijo Isma'il ya bama Abbana. Kuma ni kaɗai nake sakawa su basa amfani da ita. A kuma lokacin da zamu fito Mamyna ta ɗauka ta sakamin ita. Kuma koda muka zo gidan marayu ban cire ba na cigaba da amfani da kayana batare da kowa yasan ainahin fuskata ba”...............✍


TATATTUN FITATTUN LABARAN ZAFAFA BIYAR NA 2022*🔥🔥🔥🔥🔥🔥

*ALSHIRINKU MASU KARATU!!!*

*_NAJI DADI SHINE GARI......_*

*KINA DA BUQATAR TSAFTATATTUN LABARAI DAKE CIKE DA*

_ILIMI_
_NISHADI_
_TSUMAMMIYAR SOYAYYA KUMA MAI TSAFTA DA ZATA SAKI SHIGA SHAUQIN SOYAYYA DA DUKAR DARUSSA KALA KALA A FANNIN ITA SOYAYYAR DA RAYUWA?_

*MAZA GARZAYO KI NEMI LITATTAFAN ZAFAFAN MARUBUTA GUDA BIYAR*

     *NA SABUWAR SHEKARAR 2022*

*WADANDA SUKA ZAUNA,SUKA TACE LABARANSU,SUKA MUSU ADO DA SABUWAR FASAHA!!!*

*SABBIN LABARAI*

*SABUWAR SHEKARA*

*SABON NISHADI*

*_FARINCIKIN KASANCEWA DA MARUBUTAN CIKIN SASHEN DA AKE GWABZA RUWAN SHARHI DA MUSAYAR RA'AYI NA DABANNE_*

*MAZA 'YAR UWA SIYA NAKI KI SHIGA SAHUN WANNAN TAFIYAR,TARE DA SAMUN DAMAR SHIGA SASHEN COMMENTS NA MUSAMMAN MALLAKIN MARUBUTAN*

*_TAKUN SAAƘA!!_* _Bilyn Abdull_.

*_SO DA ZUCIYA_* _Hafsat (miss xoxo)_

*_DEEN MANSHAL_* _Mamu gee_

*_ƊABI'AR ZUCIYA_* _Safiyya huguma_

*_HALIN GIRMA_* _Hafsat Rano_

*ta hanyar tura kudin littafinki zuwa ga wadan nan lambobi dake qasa*

6019473875
MUSAA ABDULLAHI SAFIYA
keystone bank

Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number

08184017082

*IDAN KATI NE KUMA KO VTU,SAI KU TURA ZUWA GA*

09134848107

Littafi daya

1____300
2____400
3____500
4____700
5____1,000 (1k).

*INGANCI DA NAGARTAR RUBUTU,BABU NADAMA KO DANA SANI*🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽🤞🏽

#team ZAFAFA BIYAR🔥🔥🔥🔥🔥

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*


*_Typing📲_*




*Albishirinku mata💃.*

shin Ina ma'abota ado da kwalliya🗣️? Ina team no makeup🗣️? Mata gareku ina mai tabbatar muku dacewa duk wanda takeneman kayan gyaranjiki walau matsalan fata kike fama dashi kamarsu pimples, tabo, sunburn,nankarwa, knuckle ko Mai Kika shafa yabatamiki jiki Dama sauransu walau Kuma kawai kinasan kigyara fatarki kizamto tauraruwa abarso abar marari agurin kowa😍Mata inamai tabbatar muku dacewa kujaraba kayan mg's skincare Koda gudane dg cikin kayansu kuga abun mamaki🧚🏻‍♀️ domin kayansu kankat ne Koda iya sabulunsu Kika Dana saikinfita zarra cikin Mata domin ynd fatarki zaikoma Shar kamar Madara kidinga kyalli kina haskakawa duk inda kikayi se ankalleki😘Kuma wani abun jindadin ma shine duka kayansu organic ne Babu na bleaching kawai zaigyaramiki jikine yafiddomiki d ainihin natural beauty dinki inma NASA haske kikasiya natural ne kawai bn bleaching b💁‍♀️mekike jira hjy maza garzayo kinemi naki acikin farashi merahusa kigyara jiki kiyi fes abinki baruwanki da sekinyi kwalliya inzaki fita😃kifita aganki da zallar kyawunki hjy😍kanawa mutanenmu ina godiya Kuna nunama mg's one luv tnx for ur patronage dama Yan sauran state mg's na godiya may your pocket never lck azo asiya Kaya hilis karnakoma kauyenmu🥺Yar shawarmannan karta gagareni🤧😂
Henajiku lvs🤭
Meso should chat
08062991549
07046881166
Call 08064532391
Soap:3k, beauty kit:11k,bridal kit 18k
Instagram:glow_with_mgs
Facebook:mg's skincare

Team glow✅

munayin makeup Yan kaduna gamai bukata ze iyazuwa nd munazuwa gida shima in anaso

08062991549

_________________________

*_Chapter Twenty Nine_*

..............“Ina da son yara matuka, duk da ban son yawan hayaniya da yawan magana. Sannan kuwa nima yaro ne, hakan yasa a koda yaushe zaka ga yara zagaye da ni musamman saboda Habib da wasu jariran biyu da mama mai kula damu take raino tare da Habib. Wannan dalilin yasa suka taso tamkar ƙannena a gidan marayun, idan sukai laifi nike hukuntasu na musu faɗa, sannan nine ke kula da karatunsu dan mun cigaba da zuwa makaranta musamman ma ni dana fara secondary a wajen gidan marayun da baba ke kaini da kansa kullum bayan na ƙarasa shekara ɗaya a primary ɗin gidan marayun. Mama mai kula damu ce ta sakamin suna Master duk da bana so banƙin amsa mata. A hankali sai sunan ya bini a gidan kowa ya koma kirana da Master har su Habib”
          “Ina girma sunan Master daya kashe Abbana na ƙara zama a ƙwaƙwalwa ta fiye da karatu, a gefe kuma da an tashi a makaranta nake tafiya talla batare da sanin baba ba da hukumar gidan marayu. Kai wani lokacin ma bana zuwa makarantar gaba ɗaya. Da kuɗin sana'ar nake sayoma su Habib sweets, biscuits da kayan kwaɗayi na yara. Tun kowa bai farga ba har suka farga dani. Baba ya dinga min faɗa, sai dai da ga ƙarshe kuma da kansa ya bani kuɗaɗe da bawani yawane da su ba na cigaba da sana'ar dan ya fahimci inaso. Saboda tunda aka hanani saina ɗauka ƙunci da fushi na sakama kaina.”
      A lokacin dana kammala secondary su Habib suka shiga na fara tunanin kutsa kaina cikin ƴan jagaliya, dan na gama nazarina kaf ta wannan hanyarne kawai zan iya nemo Master daya kashe mahaifina. Anan ɗin ma batare da sanin Baba ba na faɗa cikin ƴan daba tare da zama da kaina naima facemask ɗina wasu gyare-gyare saboda ni mutum ne mai fasaha matuƙa tun ina da ƙarancin shekaru, sai dai ALLAH ya tsareni bana shan komai na maye, duk sanda kuma zasu aikata tsiyatakunsu nasan ta yanda zan zille musu. Dan na shiga cikinsu ne kawai dan neman ilimi da kuma neman Master. A gefe kuma na takura baba akan mubar gidan marayu, dan na tabbatar zan iya rikemu mu duka da sana'ata da zuwa lokacin tayi ƙwari na daidai talaka mai neman cin yau da gobe. Da ƙyar baba ya yarda muka dawo cikin mutane da zama a gidansa ɗin nan da muka bari shekarun baya. Ni na cigaba da buga-bugar karatu akan su Habib duk da lokacin dai da ɗan saukin wahalhalu akan mai karatun secondary. Yayinda niko a dalilin ƙoƙarin da ALLAH ya bani wani bawan ALLAH ya ɗauki nauyin karatuna na jami'a a ranar taron tshoffin ɗalibai da akai na makarantarmu.”
        “Na cigaba da kutsa kai cikin ƴan daba ina neman Master a sirrance har ALLAH yasa na dace na kasance ɗaya da ga cikin yaransa, dan zuwa yanzu ya matuƙar gawurta. Cikin ƙanƙanin lokaci na zama amintacce a wajensa, dan ina bala'i-bala'in kwantar masa da kai har sauran yaransa najin haushi da takaici na. Ban damu ba, dan tunaninsu da nawa dabanne suke haukarsu. A zahiri ina cigaba da karatun jami'a. Baɗini ina karantar kowanne motsi na rayuwar Master, gefe kuma ina kasuwancina da ALLAH ya sakama albarka mukeci muke sha ni da waɗan da nakema kallon ƙanne kuma ahalina bayan Habib. Bayan kammala jami'ata na shirya takanas na kaima wanda ya ɗauki nauyin karatuna result ɗina dan ya gani, tare da sake masa godiya. Yaji daɗi, ya kumayi farin ciki a take anan ya bani jari mai kauri da zan iya riƙe kaina harma da ƙannena.”
          “Koda na dawo na nunama baba ya sanyamin albarka, ya kuma bani shawarar maida hankali akan kasuwa basai na jira aiki ba, na amince da shawararsa dan haka na ƙara jari akan kasuwancina, UBANGIJI mai rahama dan-danan harkoki suka buɗe na canja mana gidan zama, na kuma koma makaranta nima. Domin cigaba da karatuna akan computer a wajen ƙasarnan. Tunda na tafi ban dawo ƙasata ba sai da na kammala karatuna. Amma koda yushe ina sanin motsin su Habib. Tun kafin na dawo na gama tsara yanda an tunkari master, dan kuwa na samo horo na musmman akan abubuwa masuyawan gaske.”
“Yarana sunyi farin ciki da dawowata nima kuma nayi farin ciki da ganin sun zama manya sun kuma sake hankali. Sai dai kuma na iske baba babu lafiya. Hankalina ya tashi matuƙa dan ina sonsa hakama su Habib, duk muna masa kallo ne na uba. Kwanana biyar ALLAH yay ma baba rasuwa. Tabbas munji wannan mutuwa dan su Habib kuka rurus suka dinga yi suna sake ɗaga hankalina. Sai da na dage matuƙa suka dawo hankalinsu. Da ga lokacinne na fara basu horaswa ta musamman da basu san manufarta ba. Na kuma sake komawa cikin su Master da zuwa yanzun dukkan sirrinsa a tafin hannuna yake, dan dukkan abokan mu'amularsa a cikin manya da ƴan ta'adda irinsa na sansu nasan inda suke, nasan makamar harkokinsu. Na iya maganarsa. Na iya salon tafiyarsa na iya abubuwa da dama irin nasa wanda inhar na juye maka shi baka isa cewa bashi ɗin bane, musamman idan na saka mask na fuskarsa. Indai taƙaice muku zance a wani dare batare da sanin kowaba a cikin yaran Master na ɗaukesa, zuwa safiya na maye gurbinsa, yaransa kuma duk nabi hanyoyi daban-daban aka kamasu ɗaya bayan ɗaya ta yanda babu yanda ubannin gidan Master zasu iyama ganosu balle cetonsu.........”
       “Kenan yanzu duk kuɗin da ake sata a banki da sunan Master wancan ne ba kaiba Yaya Isma'il”.
    Ammar ya faɗa cikin katsesa da zaƙuwar son jin yaya take ne.
        Wani ƙasaitaccen murmushi Master ya saki. tare da kai hannu ya shafa kan Ammar. “Da ga shekara biyu zuwa yau duk nine”.
     Kai Ammar ya jinjina cike da gamsuwa. Sai faman murmushi yake dan shikam jin wata sabuwar ƙaunar shi yake har cikin jini da ɓargo duk da har yanzu bai faɗi dalilinsa na wawasar kuɗaɗen ba bayan dalilin kama Master daya kasance mai laifi a garesa.
       Master ya cigaba da faɗin, “Na shigo rayuwarku ne a dalilin Muhibbat, sai dai labarin ya sauya adalilin karamcin Ummi da ku kanku. Sai kuma randa na jima Halilu ciwo saboda ranar na fara ganinsa a gidanku, na kuma sansa a matsayin yaron su Alhajin Mande. Wannan dalilin ne ya sani yin bincike akanku sosai harna gano mummunar manufar da yake da ita a kanku. Cikin sa'a kuma abinda yake shiryawa a kankun sai aikinsa ya faɗo hannuna duk da dai nina saka A.G yay hakan batare da shima ya sani ba. Shiyyasa na koma ta bayan fage nazo ma Muhibbat matsayin Muhammad Shuraim. A lokacin da naita bibiyarta nine da kaina. Sai dai kuma ƙanina Musbahu shine yake zuwa gareku da fuskar Shuraim. Yayinda shima kansa baisan niɗin nine Isma'il ba, na kuma cigaba da ɓoye musu zahirina saboda wani dalili nawa daban. Dan basu taɓa sanin ainahin fuskata ba duk da kuwa tun suna ƙanana suke tare dani. Sannan basu taɓa sanin aikin dana tsundumasu a ciki munayi tare ni miye dalilinsa ba. Tsabar biyayya da soyayyar da sukemin ce kawai tasa basu taɓa min musu ba akan komai da nace suyi. Domin gaba ɗayansu na horar da su akan harkar Computer.”
      “Kune mutane na uku da kuka san ainahin fuskar Isma'il bayan iyayena da baba. Wanda da farko naje asibiti da wata fuska ne daban, a dalilin Ummi naji bazan iya zuwa mata a baɗinina ba shiyyasa na sake komawa na biya kaso ɗaya bisa ukun kuɗin aikinta bayan na biya duka a farko. A yau kuma na zaɓi bayyana muku zahirin gaskiya ne a dalilin Ummi. Banason ta shiga wani hali akan rashin Muhibbat, sannan ya kamata kusan wane ƙudirine a zuciyar Halilu kar yabi ta wata hanyar ya cutar da ku idan yaga ban masa aikinsa yanda yake so ba. Dan na tabbata zai binciko gidan nan yanzu hakama dan a rikice yake kuma shi mutum ne kamar sauna idan ya ƙwallafa rai akan abu.”
         “Na ɗauke Muhibbat ne saboda bin bayan Halilu da tai ranar ɗaurin aure batare da kun sani ba, yayinda ta jiyo sirrikansa masu yawa. A ranar ɗaurin aure yawan mutane yasa bazaku fahimci bana tare da ku ba. Amma kuma nazo, sai dai ganin fitowar Muhibbat da duk da ta saka hijjab da Niƙab na ganeta ya sani fasa bin ƴan ɗaurin aure nabi bayanta. Sai da na tabbatar da inda ta nufa sannan na  koma gida a hanzarce, amma tunkan na ƙarasa na kira Habib ya sameta a wajen, hakama maigadin gidan halilun, saboda duk gidajensu na sirri da suke aikata tsiyatakunsu akwai yarana a ciki, amma ba cikin su Habib ba. wasu masu gadi, wasu masu musu aikin gidan batare da sun sani ba. Aurenku kuwa da yaransa dama can na shirya wargazashi tsaf. Dama na tsara sai an kai Muhibbat gidana zaku san nine master, a gefe kuma na cigaba da kasancewa daku matsayin Isma'il. To sai akai rashin sa'a autar Ummi ta buɗemin aiki saboda rashin jinta”.
       Murmushi Ummi tayi da kai hannu ta share hawayenta. Suma su yaya Muhammad duk murmushin suke da sauke ajiyar zuciyoyi.
      “Kuyi haƙuri da fuskokin yaudara dana zo muku daban-daban. Ni kaina inaji haushin yaudarar Ummi, shiyyasa na zaɓi zuwa na bayyana muku kaina dan ku kanku ku sami nutsuwar shiga sabuwar rayuwa a yau. Hakama Ummi hankalinta ya kwanta kar garin neman gira a rasa ido dan bazan yafema kaina ba idan wani abu ya sameta adalilina. Auta na tare dani tana zubamin tsiwa da tsaurin ido Ummi, sai dai banason ta san niɗin wanene yanzu har sai nan gaba. Aiki akan Halilu kuwa ita daya raina itace zatayi komai da kanta insha ALLAH”.
         Dariya duk sukayi, Yaya Abubakar da gaba ɗaya ya tsunduma tunani da nazartar labarin Isma'il Master yay ɗan murmushi, “Ai ni auta kamar ba'a gasa mata baki wajen wankan jego ba. Dan wannan bakin natane ya jefata a tarkon jami'an tsaro su A.G sukaso yin amfani da ita. To ashe wanda suke bulayin neman shi tuni ya gama neme su”.
        Nanma dariyar suka sanya. Yaya Umar ya karɓe da faɗin, “Ai bakin auta ya mana rana. Tunda gashi ya jawo mana Master har cikin gida batare da mun saniba. Sai dai muna son sanin ƙyaƙyƙyawar manufarsa kodan mu cirema ranmu zarginsa a jerin na ɗan ta'adda ɓarawo da kowa ke kallonsa da shi.”
      “Wannan gaskiya ne yaya Umar. ALLAH ya jikan su Mamy yay musu rahama ya saka musu, amma ya kamata musani kam”.
  Cewar Yaya Usman da hawaye suka ziraro masa na tausayin Master ɗin. Gaba ɗaya suka amsa da amin, sannan suka shiga ƙara jero sabuwar addu'a ga mahaifansa. Ummi kam tama gaza

Please Login or Register in order to submit comment