Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


Downloaded from GNOVELS.COM.NG




This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG
to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/gnovels

Twitter : https://twitter.com/gnovels

Telegram : https://t.me/gnovels

RABO AJALI ◆◆ 1
ﺑﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺮﺣﻤﻦ ﺍﻟﺮﺣﻴﻢ ﺍﻟﺤﻤﺪ ﻟﻠﻪ ﺭﺏ ﺍﻟﻌﺎﻟﻤﻴﻦ ﻭﺍﻟﺼﻼﺓ ﻭﺍﻟﺴﻼﻡ ﻋﻠﻰ
ﺳﻴﺪﻧﺎ ﻣﺤﻤﺪ ﻭﻋﻠﻰ ﺍﻟﻪ ﻭﺻﺤﺒﻪ ﻭﺳﻠﻢ . .....
Affan... Affan... Affan..
sau uku saurayin dake tsaye a kanshi ya kira sunanshi
amma ko waiwayowa baiyi ba bare ya amsa,, hankalinshi
na kan ruwan dake malale cikin wani katon ramin kiwon
kifin dake cikin gidansu yana kallon yadda suke wuntsil
wuntsil ciki yana girgiza kanshi da jikinshi hakoranshi waje
yana dariya da karfi,
duk wanda ya ganshi yasan hankali sam bai isheshi ba,
dafashi saurayin yayi hade da zama gefenshi ya watsa ma
kifin abincinsu nan take suka kara hautsinewa suna yawo
cikin ruwan gwanin ban sha'awa, ihuu Affan yasa yana
kaďa kanshi yana kokarin kai hannunshi cikin ramin kuma
yana nokesu alamar tsoro, saurayin yayi murmushi ya kara
watsa abincin,,, affan ya cikwikwiyeshi cikin murna yana
fadin yeeehhh Jabeer kara zuba musu yunwa suke ji dama,
jabeer ya shafa fuskarshi cikin tausayin halin da amininshi
yake ciki yace affan lokacin sallah yayi muje muyi sallah
mu dawo sai in cigaba da basu abincin,
affan ya no'ke wuyanshi kamar karamin yaro yace um um
ba yanzu zanyi sallah ba mummy tace ko da yaushe nayi
sallah dai2 ne saboda ni ba a rubuta min zunubi, Jabeer da
idonshi ya fara canza kala dan ya riga ya saba da jin hakan
a bakin affan kullum in yayi mishi maganar sallah,
cikin dabara yace waya fada maka ba a rubuta maka zunubi
Affan,
to bari kaji kasan wutar nan da ake kunnawa mai zafin nan?
Affan cikin firgici yace eh na santa wanda ake dafa min
indomie mai zafi ko,
jabeer yace of course ita ay kasan tafi indomie zafi ma ko,
affan ya gyada kanshi, jabeer yace to wutar da Allah ke
kona waďanda basa sallah tafi wannan zafi sau "dubu
malala gashin tinkiya"
affan ya mike a firgice idonshi zuru2 yace tafi wutar dake
dafa ruwan toilet heater ma wanda yake kona ni in zanyi
wanka,
jabeer yace sosai ma ay wannan ruwan kamar ruwan sanyi
ne akan wutar Allah,
affan ya fara ja baya yace karya kakeyi sai naje na tambayi
mummy,
jabeer ya mike da sauri dan yasan yana zuwa ya tambayi
mummy to fa bazata taba bari yayi sallah ba,
da sauri ya rike hannunshi yace affan ni ke karya,
ya fizge hannunshi yace eh mana kaine kake karya ya juya
ya ruga cikin gida da gudu jabeer na kiranshi yayi banza
dashi,
dafe kai jabeer yayi cikin damuwa sai da yafi minti 5 tsaye
sannan ya wuce ya tafi masallaci,,,,
Jabeer ďinne ya fada maka haka,
affan ya gyada kanshi yana daďa kwanciya jikinta alamun
tsoro yakeji kar wuta ta kona shi,
mummy tace rabu dashi makaryaci ne na fada maka ka
daina kulashi kullum burinshi ya tirsasa maka yin abinda da
bakayi niyya ba kuma ko a musulunce babu takura a addini,
rabu dashi kaji affan din daddy tashi kaje kaci abinci kayi
wasanka kaji,
ya daga kanshi ya mike yana tsalle har ya karasa gurin cin
abinci yana kiran sunan Hansa'u mai aikinsu tazo ta zuba
mishi abinci,
murmushi mummy tayi hade da ajiyar zuciya,
Salma babar diyarta ta ajiye laptop dinta tace mummy
wannan tsinannan jabir din so kawai yake ya ruguza miki
plan dinki, kullum shi kenan maganar sallah sai kace wani
sallau,
mummy tayi dariyar mugunta ta kalli gurin da affan ke cin
abinci duk yayi kaca2 da gurin amma ko digo bai diga a
rigarshi ba saboda tsananin tsaftarshi,
tace barni dashi ummu, jabeer yana wuce gona da iri
tabbas zan san duk yadda zanyi in rabasu da affan in ba
haka ba wata rana zai sa kwaba ta tayi ruwa,
Fareedah tace wallhy I so much hate him sai ya dinga wani
ďadďaga kai kamar kadangare shi a dole ga kyakykyawa
mtsww taja tsaki,
mummy tace ku barni dashi dani yake magana in yasan
wata ay bai san wata ba.....
posted by
sulaiman bomboy
Wannan yayi kuwa?

RABO AJALI ◆◆ 2 by Sulaiman Bomboy
Da gudu ta shigo gida ta tarar da jarababbiyar
kishiyar
uwarta a tsakar gida tana fiffita,
sannu da gida kawai tace bata jira amsa ba ta wuce
ďakin kakarta Hajja Giďe,
fadawa dakin tayi babu ko sallama ta cire skul Bag
ďinta
tayi wurgi da ita a kan gado sam bata kula da
mutum a kan
gadon ba ta fita da sauri ta shiga toilet, Hajja ta idar da sallah tayi tsaki tace wannan yarinya
saidai
Allah ya shirya yi hakuri jabeer, ya mike zaune yana
murmushi yace zata sani ay bari ta dawo, hajja tace
ay kai
baka iya yi mata faďa sai dai kullum kace zata sani kullum
kai ke kara sangarta ta,
kafin yayi magana ta shigo ta ďane kan cinyar hajja
tace
hajjanah" sannu da gida,
hajja ta tureta tace dalla ni sauka karki karya ni, sai a sannan idonta yakai kan jabeer dake kallonta
baya ko
kiftawa, da sauri ta mike tana murmushin jindadi ta
zauna
kusa dashi kamar zata shige jikinshi tace dama
kana cikin dakin nan,
ta shagwabe fuska tace shine kana kallon hajja
tana tureni
ko kayi mata magana kalli fa hannu na saura
kaďan taji min
ciwo, Hajja tace Allah ya kiyaye dai banji miki ciwon ba
ko, ta turo
baki tace kinso kiji min mana inaga ma dan kinsan
yaya
jabeer na nan ne shiyasa baki ji min ciwon ba,
hajja ta kwashe da dariya tace to yau dai sharrin kaďan ne
ko Allah nagode maka ma yana cikin dakin da
yana zuwa
nasan ce mishi zakiyi yau da kyar na barki da rai,
jabeer ya kwashe da dariya,
ta kwabe baki ta fashe da kukan shagwabe harda buga kai
a gado,
jabeer yace subhallahi me kuma akayi miki, hajja ta
mike
tace tabarar fa,
ni bari kaga in fita dan in ina dakin nan zane yarinya zanyi,
cikin kuka tace kaji ko wallhy bulala takemin
kullum yauma
dan ta ganka ne,
jabeer ya haďe rai yace gaskiya hajja zamu kai
kararki can kotun karshe a yanke miki hukunci,
hajja tayi dariya tace mu fara shariar daga yau ma in
dai
akan AFEEYAH ne,
afiyah ta dago kai ta harareta,
jabeer yayi murmushi ya ciro hndky dinshi yana share mata
hawaye, yace so sorry babynah, ya dago fuskarta
ya kalli
cikin idonta yace baki san kin girma da kuka ba, ta
kara
marairaicewa kamar karamar yarinya tace to baka ganin
abinda takemin, yace to nace kiyi hakuri kinji, ki
daina yarda
suna saki kuka kinaso a dinga ce miki ruwa2,
ta noke wuyanta tace ah'ah, yace to sai kin zama
mai hakuri kin daina yawan kuka kinji,
tace tam zan daina, yace yauwa wifey nah,, ya
dakko ledar
gefenshi ya fito dasu biscuits da chocolates,
rungumeshi
tayi cikin murna ta mishi peck a kumatu tace I love u so
much hubbynah, wani abu yaji yana mishi yawo
cikin
kwanyarshi,
a hankali cikin rashin kuzari yace more than u do
babynah,, ta sakeshi tana dariya, nan suka cigaba da hirah
cikin
jindadi tana shan chocolates,
sai da aka kira la'asar sannan ya fito zai tafi, rakoshi
ta fito
yi bayan yayi sallama da hajja, a dai2 kofar dakin inna
suwaiba kausar ke zaune tana ganinsu ta shiga
wakar
habaici tana fadin Allah wadai da halin yan iska sai
a shige
daki afi karfin awa wai da sunan ana hira, ran Afiya ya baci matuka jabeer ya lura da hakan ya
rike
hannunta gam ta fisge, tace da uban wa kike ,
kausar ta
mike tace da ubanki nake kinji na kira sunanki, in
ba tsarguwa kikayi ba meye na jin haushi shegiya
marar
kunyar banza,
Afeeya ta kuma hassala tayi kanta da sauri jabeer
ya riketa
da iya karfinshi ya jata da kyar suka fita, kukan bakin ciki ta fashe mishi dashi tana ta tirje
hannunta,
murmushi yayi dan yasan in bata tsaya ta mayar da
martani ba bazata taba hucewa ba,
hakuri ya shiga bata amma ko kalma daya bata iya
rikewa ba saboda zuciyarta cike take da bakin ciki gani
take idan
basuyi fada da kausar ba yau sai tayi ciwo mai
tsanani,
matsowa sosai yayi kusa da ita yace haba afee nah,
ba nace kiyi hakuri ba, kinaso inyi fushi ne, ta turo
baki tana
kuka tace ko zaka fashe yau bazanyi hakuri ba,
ya hade rai yace to ni kuma in bakiyi hakuri ba mun
bata
garin ma zan bari gaba daya, cikin dakewar zuciya tace ka
tafi gaba da birnin sin ma dan wallhy bazan hakura
ba,
sakin hannunta yayi yace ni ko? Ta juya mishi baya
tace eh
ďin, yace to shikenan bye yasa kai ya fita,
ko ajikinta a lokacin saboda zuciyarta na azalzalarta
taje
gurin kausar.......

11 hours ago Sulaiman Bomboy [7:00am 08/11/2016] .: ◆◆ RABO AJALI 3
By Sulaiman Bomboy
Tana shiga ta tarar da kausar na buga k'ullun alale,
sam
kausar bata kula da shigowarta ba sai saukar wata
sanda taji akanta da karfi, zafin ya gigita ta sosai tasa ihun
da ya
fito da inna suwaiba da hajja daga ďaki,
cikin rudewa inna suwaiba ta kama kausar tace
kausar
meya faru, kausar ta kasa magana sai kuka takeyi hannunta
rike da gurin jini na fita,
hajja ta kwace sandar hannun Afiya tace yanzu ke
saboda
tsabar mugunta wannan murďaďďiyar sandar kika
buga mata,
Afiya ta turo baki tace hajja fa baki san abinda tayi
min
bane shiyasa,
inna suwaiba cikin fushi ta saki kausar tace uban
me ta miki, Afiya ta murguďa baki tace gata nan ki
tambayeta,
inna suwaiba tace lallai yau za'a haifi ďa mara ido a
gidannan wallhy,
Afiya tace a haďa harda mara hanci ma a haifa,
hajja ta bige bakinta tace ke wai wace irin yarinya ce da
baki jin maganar kowa,
Afiya tace to wai hajja ita baki tambayeta me tace
mana ba,
ce mana fa tayi yan iska, inna suwaiba tace ay kunfi
karfin ya'yan iska saidai na guguwa, wallhy yau saina
miki shegen
duka a gidan nan sai na tabbatar wannan
tsinannan bakin
naki yayi laushi,
Afiya tace Allahn da halicci baki na shi kadai zai iya sashi
yayi laushi ba wata ca--- hajja ta toshe mata baki
tace na
shiga uku ni Giďe, yanzu ke Afiya bazan miki
magana kiji
ba, inna suwaiba tace hajja ki wuce daki ki barni da yarinyar nan wallhy yau sai na mata lahani a
gidannan,
Hajja tace kiyi hakuri suwai--- karki bani hakuri ki
cuceni
hajja kullum mu kenan a cuce mu a taushe mu, to
wallahi bazan dauka ba,
ji yadda jini ke zuba a kan kausar ay dan tasan
kuna daure
mata gindi ne ke da malam shiyasa take abinda
takeso, in
ba ta raina mutane ba ay kausar ba sa'arta bace, hajja tace kiyi hakuri dai nace suwaiba, Afiya ta
harari hajja
tace wai hajja hakuri kike basu ni baki bani hakuri
ba sai su
da babu abin ma da nayi musu,
inna suwaiba ta hassala sosai tayi kan Afiya ta cakumota,
hajja ta riketa tace wallhy suwaiba karki taba min
marainiyar Allahn nan,
wallhy kika kuskura kika sata kuka sai ranki yayi
matukar
baci, inna suwaiba tace ay ko sai dai ya baci ta kaima
Afiya duka
ta goce tana kicikicin kwacewa,
kausar dake jin kanta kamar dutse ta mike tazo ta
bayan
Afiya ta kai mata duka, Afiya tayi kukan kura ta kwace
jikinta a gurin inna suwaiba ta haye kan kausar
inna
suwaiba na jibgarta ita kuma tana jibgar kausar,
hajja na
gefe tana kuka ita sam bata ma ga dukan da afiya kema
kausar ba ita dai tafi jin dukan da akema Afiya,
dakyar da taimakon shigowar malam faďan ya
rabu kowa
na maida numfashi, kausar bayan inna taje ta boye
tana kuka sosai saboda taji jiki, Malam Atiku cikin bacin
rai yake
ma inna faďa itama cikin fushi take mayar mishi,
yace yanzu in banda ke babbar kwabo ce meye na
shiga
faďan yara, wai ke in an barki ga mai ýa ko, kin gama zubar
da mutuncinki a idon karamar yarinya, inna cikin
fushi tace
faďa min mai mutunci a idon wannan shegiyar
yarinyar,
hajja ta fashe da kuka tace wallhy ba shegiya bace, Danbaba ni na gaji da zaman gidan nan kullum sai
sun
tsokani yarinyar nan ita kuma Allah bai ďiga mata
hakuri a
ranta ba gara muyi nesa dasu su zauna su kadai a
gidan, malam Atiku yace babu inda zaku hajja, baku da
inda yafi
nan, zan dauki tsatstsauran mataki akan wannan
alamarin,
inna suwaiba tayi tsaki ta hararesu tace ka daďe
baka ďau mataki ba, wannan yarinyar wata rana saita dauko
muku na
barin gari, ta kama hannun kausar suka wuce ciki
tana
masifa zuciyarta na ķuna saboda Afiya, ta rasa
dalilin da yasa ta kasa samun nasara akan Afiya,
zama tayi bakin gado idonta yayi jajur dan ba
karamin caza
mata kwakwalwa Afiya keyi ba,
Can kuma dakin hajja fada sosai suke ma Afiya
akan rashin hakuri, malam atiku yace ni wallhy na rasa inda
yarinyar
nan tayi gadon wannan halin hajja ko kadan bata
da hakuri
komai aka mata tace saita rama kuma rayuwa
bazata taba tafiya haka ba,
Allah na tuba kayi hakurin ma ya ka kare a wannan
zamanin
bare kuma bakayi ba, hajja tace ay ni yanzu inaga
nawa ido
tsakanina da Afiya dan gani sukeyi kamar goyon bayanta
nakeyi ni take ďaura ma bakin jini dan kawai taga
banason
abinda zai bata mata rai shiyasa takeson a dinga ci
min
mutunci, Afiya ta fashe da kuka tace dan Allah hajja kuyi
hakuri in
shaa Allahu ko duka na zasuyi bazan kara tanka
musu ba,
hajja tayi tsaki tace ke ďin ce zaki faďi magana in
yarda, malam atiku yace hajja muyi mata addua babu
mamaki
bazata kara ba,
Afiya tace Allah abba bazan kara ba,
hajja tace to Allah yasa da gaske kikeyi, duk suka
ce ameen, nan suka cigaba da yi mata nasiha akan
rayuwar
duniya cikin dabara suke mata nuni da illar rashin
hakuri,
Afiya jinsu kawai takeyi dan ita bataga rashin
hakurin da aketa ikirarin tana dashi ba ita dai tasan ko manzon
Allah
s.a.w yace in aka bata maka ka rama dai2 yadda
akayi
maka, to ita kuwa akan me zata yarda tanaji tana
gani a taka ta, bazai yiwu ba,, har suka gama nasiharsu
Afiya tana
gyada kai kamar taji abinda suka ce sai gab da
magriba
malam atiku ya fita suma suka tashi suka je yin
alwala... Tun daren ranar take zuba idon ganin jabeer shiru
har kofar
gida ta fito ta tsaya tana kallon kofar gidansu ko
zata ga
fitowarshi amma ko giftawarshi bata gani,
kullum ta dawo skull sai ta tambayi hajja ko yazo, in hajja
tace bai zo ba nan zata fara sababi tace hajja kawai
ki
fadamin ko kin fita yazo baki nan ko kuma kina
baccinki
bakisan yazo ba, hajja saidai tayi tsaki tayi banza da ita ta cigaba da
abin da
takeyi,
Afiya ta damu sosai da rashin ganin jabeer ji takeyi
kamar
ta mutu saboda rashin ganinshi haka kawai zata zauna taki
cin abinci tayi ta kuka hajja bata ko kallonta bare ta
rarrasheta..
Yauma kamar kullum a cikin sati biyun da tayi bata
ga
jabeer ba tana zaune ta haďa kai da gwiwa tana rero kuka
hajja ta ajiye mata abinci a kusa da ita ta zauna
gefenta ta
kira sunanta, bata dago ta kalleta ba ta cigaba da
kukan da
takeyi, hajja tace to shikenan tunda bazaki saurareni ba
dama jabeer ne,,, ta ďago kanta da sauri tace me ya
sameshi hajja,
hajja tace yana nan cikin koshin lafiya baki ga
yadda yayi
kyau ba, dazu kina makaranta yazo yace in faďa miki yana
gaisheki in ya samu lokaci nan da wata daya bayan
kin
gama jarabawa zai zo ku gaisa,
idonta ya ciko da kwalla tace hajja wata daya? Hajja
tace eh mana, ba yace kince ya tafi gaba da birnin sin
ba,
to ba wasa nake mishi ba afiya ta faďi haďe da
fashewa da
kuka, hajja tace ay ko shi da gaske ya ďauka,
Afiya ta maida kanta cikin gwiwoyinta cikin kuka tace
shikenan kar ma yazo din dama nasan so kawai
yakeyi ya
kasheni,
hajja ta gimtse dariyarta tace kull kar na kara ji, duk
laifinki ne meyasa in yayi miki magana bakya ji,
Afiya tace to ba nace na daina ba kema shaidace
yau sati
biyu kenan banyi fada da kowa a gidan nan ba
kuma suna
tsokanata meyasa baki faďa mishi haka ba, da wani abun
nayi da yana zuwa zaki fada mishi amma saboda
nayi abun
kirki shine kika ki fada mishi,
Hajja dariya taci karfinta sosai ta mike ta fita tana
dariya ita kaďai, Afiya ranta ya kara baci ta kwanta tanata kuka
harda
sheshsheka tana tausayin kanta dan tasan in bata
ga jabeer
ba nan da kwana biyu to tabbas zata iya mutuwa,,,
muryar hajja taji tana kwalawa Mahmud kanin kausar kira,
ya taho da gudu yana buga ball yace hajja gani,
tace Gidan
Alh Bara'u zan aikeka,
Afiya ta mike zubur ta dakko hijab dinta ta fito tace
zanje hajja, hajja ta kalleta tace da wannan kumburarren
idon
zaki shigar musu gida,
Afiya tace eh dashi zan shiga ni dai ki fada min
sakon,
hajja tace to ay sai kije ki shiga din mu gani zonan mamu
kaji ta miko mishi kullin magani tace kace a aikawa
Asiyah
nayi mata bayanin amfaninsu,
ya karba yace to hajja, bin bayanshi Afiya tayi ta
hađe rai tace bani, jikinshi na rawa ya mika mata hajja tace
Afiya
karki fita gidannan haka ko uniform baki cire ba,
bata
saurari hajja ba ta fita dan so kawai takeyi yau ko ta
halin k'ak'a taga jabeer....

RABO AJALI 4 ◆◆ By Sulaiman Bomboy Tana fitowa
tayi tafiya kadan ta fada gidansu
jabeer,
gaisawa tayi da Ado mai gadi, yace yar lelen jabeer
kwana
biyu kinyi wuyar gani, tace wallhy baba ado mun kusa fara jarabawa ne,
yace au too to Allah ya bada sa'a, tace Ameen ta
wuce ciki
idonta kan motar jabeer tasan tabbas yana ciki,
kai tsaye ta wuce dakin Ummi ta murda ta shiga
hade da sallama, amsa sallamar yayi haďe da ďago kanshi suka
haďa ido,
kallonshi ta tsaya yi idonta cike da kwalla shi kuwa
murmushi yake mata yana mai jin dadin ganinta,
girgiza kanta tayi ta wuce kitchen inda taji
buruntun ummi, ummi na ganinta ta fadada fara'arta tace Afee yan
matana,
Afiya ta tsuguna ta gaisheta, ummi ta amsa haďe da
ďagota tace kin gujeni kwana biyu ko ďan girki kin
daina zuwa tayani, afee ta sunne kanta tace wallhy
ummi jarabawa zamu fara yanzu bana fita amma ay nazo
ran
Saturday bakya nan,
ummi tace eh kwarai naje daura, ya hajja, afiya tace
tana gida ita ta aikoni wai gashi a kaima anty
Asiyah, ummi ta karbi maganin tace Allah sarki kice mata
an gode
sosai kinji,
afiya ta gyaďa kanta sannan tace bari in tayaki
wanke wanken, ummi tace aiko nagode kamar
kinsan na gaji, ga
dayyaba har yanzu bata dawo ba, Afee ta fara
wanke2 tace
ummi Amirah fa, ummi ta wanke hannunta tace
tana can kaduna gidan Asiyah har yanzu bata
dawo ba, Afeeyah tace Allah ya dawo da ita lafiya, ummi tace
Ameen
yar albarka ta fita ta tarar da jabeer zaune yana
latsa waya
tace au ashe baka fita ba, yace walhy ummi nagaji
ne sosai, tace ay da gajiya ni bari in ďan kwanta kafin la'asar,
yace to ummi Allah huta gajiya tace Ameen ta wuce
ciki,,
saida ya tabbatar ummi ta kwanta sannan ya mike
ya shiga kitchen ďin,
tana tsaye tana goge kwanukan da ta wanke tana mita tana
girgiza kai,
dariya ta bashi a zuciyarshi yace yau ya shiga uku
da masifarta,
karasawa kusa da ita yayi ya dauki plates din da ta
goge zai jera tayi saurin rikesu tace malam ka ajiye ni ban
sa ka
ba, yace ay nasan baki sani ba tayaki kawai zanyi,
tace to
banaso ko dole ne,
yayi murmushi yace dole ne mana in ban tayaki aiki ba wa
zan taya,
tayi tsaki tace wacce ka samu a cikin sati biyu nidai
ka fita
kawai, da nasan ma zan sameka a gida da ban
shigo ba, yayi dariya haďe da rike kafadunta yace
makaryaciya dan
ki ganni ne ma kika yarda aka aiko ki, tace God
forbid, in ganka inyi maka me, yace kiji
daďi mana
in kuma bakiji dadin ganina ba kalli cikin idona ki faďa min,
ta ďago a tsiwace zatayi masifa suka haďa ido tayi
saurin sauke kanta saboda wani abu da ta gani a
cikin
kwayar
idonshi, yayi murmushi yace nasan kinyi missing ďina,
cikin muryar shagwaba tace ni banyi missn dinka
ba, yace um um fa karki sani in tafi gurin da bazaki
kara
ganina ba,
muryarta ta fara rawa tace me ya rage kuma tunda har ka
iya yin sati biyu baka neme ni ba, ya dago kanta ya
kalli idonta da hawaye ya fara zuba a cikinsu yace
bake
kikace
in tafi ba, ta dunkule hannunta ta buga a kirjinshi da karfi
tace to ba
wasa nakeyi ba, shine ka daina bari in ganka baka
ma
damu da halin da zan shiga ba kasan ko kwana
ďaya ne in ban ganka ba banajin daďi ni nasan yanzu ka
daina sona
tunda har ka iya yin sati biyu baka ganni ba kuma
ka zauna
la-fiya ta karasa fadi cikin kuka mai tsanani,
kwantar da kanta yayi kan kirjinshi dake bugawa da sauri
yace am so sorry Afee nah kece bakya ji in na miki
magana, tace wallhy na daina kaje ma ka tambayi
hajja Allah
ko sun
tsokaneni bana tanka musu, jabeer yace to yi shuru na yadda ki daina kuka
kinji,
ta gyada kanta tace promise me bazaka kara yin
bacci baka
ganni ba,
yace I promise baby in dai da rai da lafiya bazan kara ba
kinji, tayi murmushi tace Allah ya kara maka
tsawon rai da kuma lafiya in dinga ganinka har
karshen
rayuwata,
ya ja kumatunta yana murmushi yace Ameen my queen,
tayi dariyar jindadi suka cigaba da kife kwanukan
suna hira har suka gama,
a parlor suka zauna yake tambayarta karatun
jarabawa,
tace tanayi sosai saidai maths ke dan bata wahala, yace
baki da matsala zamu dinga yi kullum kafin ku fara
exams
tashi ki rakani gidansu Affan,
ta turo baki tace nidai bazan shiga ba,
ya harareta yace yau sai kinzo munje kin gaisheshi rabonki
da shiga gidan tun kafin ya fara ciwo saboda haka
yau sai
kin shiga, ta marairaice tace ni fa ba ruwana in
wadannan
masu kama da iyamuran sukayi min wllhy ramawa zanyi
saidai kace bani da hakuri, ya murďe bakinta har
saida tayi kara yace suwaye
masu
kama da inyamurai,
tace oho ni nasan sunansu ne, yayi dariya yace bazaki taba canzawa ba afee sai
dai addu'a, tace wallhy zan canza amma fa baza a
dakeni a
hanani kuka ba,
yace to naji tashi muje bazamu daďe ba, tace too ta
mike suka fita suka shiga gidan Alhj Basheer,, Yana
zaune as usual a gurin kifaye yayi kasake
yana
kallonsu kamar me nazarin wani abu,
jabeer ya dafashi ya juyo a firgice ganin jabeer yasa
shi washe hakori sosai yana kaďa kanshi cikin murna,
jabeer yace Affan abokin jabeer kuma abokin kifi,
Affan yayi dariya cikin maganar dolaye yace jiya
baka zo
ba inata kallon can kofar mota har dare baka zo ba,
jabeer yace kayi hakuri na danyi wata tafiya ne, Afiya
dake tsaye fuskarta dauke da tausayin halin
da affan
ke ciki tace ina wuni, ya ďago kanshi dake rawa
yana
washe hakori yana kallonta baya ko kiftawa, duk maganar da jabeer ke mishi bai kalleshi ba idonshi
na kan
Afeeya
kanshi yaki tsayawa guri daya,
jabeer ya kalli afeeya da ta rabe tana jin tsoron
kallon da Affan ke mata yayi murmushi yace affan baka gane
Afeeyah ba, affan ya girgiza kanshi ya runtse
idonshi kamar
yana son tuno wani abu can ya bude idonshi yace
na
ganeta amma na manta a wani cartoon na taba ganinta, jabeer ya kwashe da dariya haka shima
affan suka
dinga
dariya tare saida jabeer yayi shuru sannan affan ma
yayi,
jabeer ya kalli afeeya da ta cika tayi fam ya maza ya mike yace Affan ka jamin bala'i,
affan ya mike shima ya matso kusa da afiya sosai
kamar
zai shige jikinta yasa hannu ya shafi fuskarta wani
irin
laushi yaji haďe da sanyi mai fisgar zuciya ya maza ya cire
hannunshi yana tsalle yace bari inje in fada ma
mummy
yau na taba fuskar cartoon, jabeer ya janyoshi yace
karka
kara ce mata cartoon, Affan ya bata fuska yace to mecece in ba cartoon
ba kalli fa
idonta kato irin nasu, kuma ka taba fuskarta kaji,
jabeer yace idonka ne ya ga cartoon wannan
Afeeya ta ce,
ka tuna ta, Afeeya mai kyuiya mai kukan banza ya faďi yana
mata kallon tsokana,,,
affan ya kara rufe idonshi ya bude yace mai kuka
irin na
mage, Afiya tayi tsaki cikin fushi ta fara tafiya, affan
yace jabeer kace ma cartoon ta dawo dama bani da barbie din
wasa,
jabeer yabi bayan afeeya yana cema affan jeka
kace ma
mummy ta siyo maka wannan barbie din tawa ce,
Affan ya bata rai yace sai na fadama daddy in ya dawo ince
kaki bani barbie,
jabeer bai kulashi ba shidai hakuri kawai yake
bawa afeeya,
suna kaiwa gate zasu fita shima affan yasa kafa zai
bisu yaji wani irin tsawa mai firgitarwa sannan gabanshi
yaga
kamar namun daji suna so su biyoshi,
a sittin ya ruga ciki yana ihu yana kiran sunan
mummy, jabeer sam bai lura da yanayinshi ba ya
ďauka shirmenshi
ne dan baya taba wuce kofar mai gadi yauma yayi
mamakin
da ya biyosu har gate saboda barbie,,
Har cikin gida ya rakata yana rarrashinta da kyar ta
sauka da alwashin ta
gama shiga gidan Alhj basheer har ta koma ga
Allah dama
sam jininta bai haďu da flowers din kofar gidan ba
ma bare a kai ga mutanen cikinshi gara ma daddy
da shi affan din
suna gaisawa in jabeer ya kaita gidan, ta saki ajiyar
zuciya
tace yaya jabeer haka Yaya affan ya dawo rabona
da ganinshi tun ina js3,
Amma wai wane irin ciwo ne wannan, hajja dake gefensu tace au ke yau kin shiga kin
ganshi,, ay
a unguwar nan babu wanda ake bari yaje dubashi
ko meye dalili oho,
jabeer yace hmm babu wani dalili hajja kawai dai
matar gidan ce bata yarda a ganshi ni ma dan ta rasa
yadda
zatayi dani ne shiyasa ta barni,, ga daddy ba
mazauni ba
dan sai yafi wata bayanan,
hajja tace to Allah dai---- sai bakinta ya sar'ke kamar a
datseshi da gum...
wannan itace babbar jarabawar da Allah ya
daurawa AFFAN
ta hanyar kishiyar uwa babu wani mahaluki a
doron kasa da zai iya yi mishi addu'ar samun sauki,
jabeer shi ne kadai yake iya ganinshi har yayi
yunkurin sanyashi a hanya amma saboda karfin
iko da
lokacin da
Allah ya ara ma mummy, daga affan ya fara jin maganar
jabeer kamar kiftawar walkiya sai ya mance abinda
yace ya bijire mishi,
duk yadda taso rabasu ta kasa saboda amintar su
mai karfi
ce wacce zaiyi wuya kasamu labarinta a kasar hausa,
Bari in baku takaitaccen tarihin gidaje ukun...

◆◆ RABO AJALI ◆◆ 5.
A unguwar "zoo road" dake cikin garin
"kano" ta dabo tumbin giwa nan zan ďan tsakuro
muku tarihin gidajen makota ukun, Alhaji Basheer
Balarabe dan asalin k'asar Cameroon ne, sana'ar
Gwal ita ta shigo dashi kasar nigeria tun yana saro kaďan2 yana siyarwa har Allah ya sanya wa abin
albarka

Please Login or Register in order to submit comment