Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ya koma sarinsu da yawa yana shigowa
dasu yana siyarwa, a duk cikar kasuwar gwal dake
cikin garin kano babu wani wanda yakai Alhj
Basheer kawo ingantattun gwalagwalan da babu
mixed a cikinsu, wannan dalilin ne yasa duk wanda ya tashi siyan gwal to fa a gurinshi zai siya
dan shagunanshi sun fi karfin goma a cikin
kasuwar, Alhj Basheer ya auri matarshi ta farko
kuma yar uwarshi Zeenatu, auran zumunci akayi
musu wanda ganin girma da kuma karamcin rik'on
da iyayen zeenatu sukayi mishi yasa ya yarda da auren amma badan yanaso ba, shekararsu uku da
aure suna zaman lafiya saboda irin biyayyar da
take mishi, a cikin wannan shekarun ne ya dakko
ta suka dawo Nigeria da zama kwata2 sai dai suje
cameroon hutu, a shekararsu ta biyar da aure ne
hankalinsu yayi matukar tashi saboda rashin haihuwa, babu ma kamar alhj basheer da yake
ganin madarar kuďi babu maciyansu sai dai yan
uwa da makota, ya kosa matuka yaga yana da
ya'ya barin ma ďa namiji dan wani lokaci har
mafarkin gashi nan an haifa mishi ďa kuma namiji
yakeyi, a wannan yan lokutan ne ya fara tunanin k'aro aure duk da a lokacin ba mazauni bane
saboda bai fi yayi sati a nigeria ba sauran kwanakin
duk a kasar waje yake yinsu yana turo kaya, Wata
ranar asabar ya baro airport cikin tsananin jin
yunwar da ta bashi mamaki, nan ya tsinci kanshi da
tsayawa a wani restaurant dake Jabi dan bazai iya matsawa ko'ina ba tare da yaci abinci ba, cikin
karairaya wata farar ingarmar budurwa ta matso
kusa dashi tace alhj me kake bukata, cikin ruďewar
ganin jar fata gata a cike gaba da baya ko'ina sai
rawa yakeyi a jikinta yace anytn special yanmata
dan yunwa nakeji sosai, ta ďan tsuguno kadan tace an gama ranka ya dade, tayi gaba jikinta na girgiza
alhj basheer ya bita da ido baki sake yana kallonta
har ta bace ma ganinshi, ajiyar zuciya mai karfi yayi
sannan ya gyara zamanshi dan ba karamin tafiya
da imanin shi tayi ba, cikin yan dak'ik'u ta dawo
dauke da plate din fried rice da pepper chicken sai peprsoup din kayan ciki a gefe da drinks, alhj
basheer da bai cika cin abincin restaurant ba sai
gashi ya tsinci kanshi da cin abincin nan sosai,
takardar bill ta kawo mishi yabi kirjinta da ya cika
kamar zai faso cikin rigarta da kallo yace yanmata
duk wadannan kudin ni zan biya, tayi walll da ido tace alhj yayi kaďan ko, yayi wata kasaitacciyar
dariya yasa hannu a aljihu ya ciro rafar dari biyar
yace ya daiyi yawa ni kinga abinda zan iya biya
nan, tayi murmushi tasa hannu ta karba haďe
tsugunawa, tace to an gode yallabai, tayi gaba ya
bita da kallo yana lasar baki kamar tsohon maye, tashi yayi bayan ya gama goge bakinshi da tissue
yana sakace ya yafito wani yaron da yaji an kirashi
da John, da sauri yaron yazo ya tsuguna yace alhj
any problm, alhj basheer ya ďagoshi yace no
young man ina bukatar taimakon ka ne,, john cikin
mamaki yace taimakon me alhj, alhj basheer ya jashi waje yace wannan yarinyar da take kawo
abinci nake son sanin sunanta, john yayi dariya
yace OYIZA kake nufi, alhj basheer yace ban sani ba
wata fara kakkaura, yace yes itace alhj sunanta
"Safiya" Oyiza ake ce mata ita y'ar mai restaurant
din nan ce, bata cika zuwa nan ba sai in tazo daga lagos kuma I think gobe ma zata koma saboda tafi
1wk anan gurin, ya fara waige2 ya ďan rage murya
cikin gulma yace amma fa alhj bat--- maganarshi ta
katse sakamakon kiranshi da yaji madam dinshi
nayi, da sauri yace alhj bari in tafi sai anjima ya ruga
ciki da gudu, alhj basheer a zuciyarshi yace ko bata dame ya ke so ya fada mishi oho? ya ďaga
kafadarshi kawai ya dawo ciki dan yayi magana da
mahaifiyar oyiza, Guri na musamman maman oyiza
ta bawa alhj basheer ya zauna tana yashe hakori
cikin murna dan taga gurin ďana tarko, cikin
girmamawa suka gaisa, saida shuru ya đan ratsa na kusan 2mins sannan alhj basheer ya fara magana
yace madam naga yarinya a gurinki ne kuma inaso,
wallhy da aure nake sonta ba yaudararku zanyi ba,
ni in kin amince ma a cikin sati biyu a gama komai
na maganar aure, maman oyiza tayi ajiyar zuciya
cikin gurbatacciyar hausarta tana girgiza kai tace anya kuwa gaskiya bazan iya ba bahaushe oyiza
ba, kaiii bazan iya ba alhj hausawa basu cika rik'e
mata ba, yayi murmushi yace wasu dai madam ai ba
duka aka taru aka zama daya ba, tace ummm haka
ne amma gaskiya--- alhj basheer ya katseta yace
madam na barki kije kiyi tunani, zan dawo nan da 2days sai inji abin da kika yanke ya ajiye mata
wasu kudin a gabanta sannan ya tashi ya tafi....

◆◆ RABO AJALI ◆◆ 6⃣
By sulaiman bomboy
Jujjuya kuďin maman oyiza takeyi cikin fargaba dan ita a
tunaninta harka kawai zaiyi da ďiyarta su tatsi kudi su bar
banza,
sai kuma gashi da aure yazo musu, ita kuwa sam bazata
iya aurawa ďiyarta bahaushe ba tafi son kabilarta kuma dan
garinsu wato OKENE, mikewa tayi ta shiga wani ďan lungu
da oyiza ke yawan zama kullum in tazo abuja, waya takeyi
tana dariya cikin murnar da uwarta ta kasa gane daga inda
murnar ta samo asali,
zama tayi kusa da ita tana mata magana, oyiza tayi saurin
katse wayar da takeyi ta kalli mamanta,
maman oyiza ta dafa ta tace sofy mun shiga cikin matsala,
oyiza ta haďe rai tace matsalar me mum, maman oyiza ta
share gumin da ya tsatstsafo mata ta labarta ma oyiza duk
yadda sukayi da alhj basheer, cikin damuwa tace ni bansan
me yasa kika fito har kika kai mishi abinci ba, ke da ko ruwa
bakya kai ma customers in kina gurin nan,
oyiza tayi dariyar farin ciki a zuciyarta tace thank uu
"Chummy lord" ta kalli mamanta tace mum wannan shine
matsala? ay wannan is a blessn to us,
kinsan irin dukiyar da yake dashi ne,
kuma kinsan abun dadin bai taba haihuwa ba,
maman oyiza ta saki baki tace a ina kika san bai taba
haihuwa ba,
gaban oyiza ya fadi amma ta dake tace john ne ya fada
min, mamanta tace koma dai menene ni bana son auren
bahaushe, oyiza ta dafa mamanta tace mum karki fara
wannan maganar ma saboda bazai yiwu ba, kawai in yazo
kice mishi eh mun shirya yazo ayi maganar aure,
maman oyiza cikin bacin rai tace kina hauka ne,
oyiza cikin fushi tace yess am mad in dai akan kuďi ne,
kuma duk wanda ya nemi shiga tsakanina da samun kuďi
ko waye wil fc d consequences,..
Maman oyiza ta mike tace to zanga yadda za'ayi ki aureshi
tunda ke baki da hankali kina zuwa 1yr ya koroki in dai
bahaushe ne ki ma cire a ranki dan I swear bazan bari ya
shigo ko gate din restaurant dinnan ba bare yazo jin wani
feedbk ta wuce tana masifa,
Idon oyiza yayi jawur nan da nan fuskarta ma ta rikiďa ta
zama jawur gunin ban tsoro, ta mike kamar walkiya ta wuce
motarta taja tayi gida,
wani jan akwati ta bude ta dakko wani farin kyalle da wata
jar baby kamar sassakar laka,
wani kirari tayi mai karfi da ya girgiza gidan da take ciki,
cikin second uku wata mace ta bayyana a gabanta cikin
jajayen kaya,
"fitsarin tsoro na saki ganin halittar wannan matar jikina
take ya fara rawa idona ya ciko da kwalla a zuciyata nace
duk "Badiyya" ce ta sani wannan bin diddigin gashi na kawo
kaina inda zan halaka" dakewa nayi na fara karanto adduoin
neman tsari, nan na samu kwarin gwiwar kai kunnena da
idona gurin abun da sukeyi, oyiza na hango tayi ma matar
da naji ta kira da "Chummy lord" sujjada (wa'iyazubillah)
chummy tasa ma oyiza wani nannaďaďďen farin yadi a
kanta tace "u are safe wit me by ur side",
oyiza ta ďago kanta zuciyarta a dake tace I found him my
lord, amma mum naso ta kawo min matsala, chummy tayi
dariya mai karfi tace ur mum ko kuma gvn mum,
kin manta u sacrifice her sannan kika samu alhj basheer
yasan inda kike,
cikin faduwar gaba oyiza tayi kasa da kanta tace I love my
mum my lord,
chummy tace I knws dat amma in har kinason jin dadi dole
ki katse numfashin mahaifiyarki, kuma bari in fada miki
kina shiga gidanshi zaki samu ciki so u will be d apple of d
house saboda u bring air to d family, ,
mum dinki ta fara tsufa so let her go ke kuma ki fara
rayuwarki mai daďi,
haka tayita convincn dinta har ta gamsu ta fitar da uwarta a
ranta tayi alkawarin yau da dare zata bada uwarta saboda
komai ya tafi mata daidai,
sun kusa awa suna tattaunawa kafin Chummy ta bace,
oyiza ta mayar da komai na tsafinta ta fito ta shiga kitchen
dan tayi ma innocent mum dinta girki, tsayawa tayi a
kitchen ta kasa komai tana tunano rayuwar da tayi da
mahaifiyarta da irin wahalar da mahaifiyarta tasha akanta
da karatunta, tayi tsaki a zuciyarta tace kuďi yafi min komai
ciki harda ke mum,
am so srry mum u have to go,
ina son sunana ya shiga jerin mata masu arzikin duniya,
girki ta farayi duk da jikinta a mace yake amma ta dake
saboda zuciyarta ta daďe da kangarewa da shan jinin bil
adama,
Oyiza ta shiga cikin kungiyar asiri ne tun shekararta ta farko
a jamiar lagos,
wata kawarta esther Babajo ita tasata lokacin tana shan
wahalar rashin kuďi da abinci saboda mahaifiyarta bata da
kuđi, sannan kuma sun shiga ne dan su dinga samun first
class result a set dinsu,
haka kuwa yake faruwa dasu dan su biyun nan saida ya
zamana babu wanda yake iya bugesu, kuma kuďi ma babu
macen da zata nuna musu shanawa a cikin skull, duk irin
gulmarsu da akeyi babu wanda ko wacce ta isa tazo
gabansu tayi saboda tsabar tsoronsu da ake ji,
jini kuwa su kansu basu san adadin na mutanen da suka
sha ba,
oyiza ta hadu da alhj basheer ne a airport lokacin sun dawo
daga Italy ita da esther, tunda ta daura idonta akanshi da
suka sakko daga jirgi taji sonshi mai tsanani ya kamata,
tun a airport suke bin bayan motar da ta daukeshi har zuwa
hotel din da zai kwana kafin safiya ya wuce kano,
Saida suka bari ya shiga ciki sannan suka samu drivern da
ya daukoshi suka tambayeshi sunanshi, da kyar da kuma
kuďi da suka bashi ya sanar dasu sunanshi da kuma garin
da yake, godiya sukayi mishi sannan suka wuce,
tun daga ranar Chummy ta fara mata aiki akanshi, nan ta
gano irin kudin da yake dashi da kuma wanda zaiyi nan
gaba, ta kuma gano matsalar da yake ciki na rashin
haihuwa ,
jin yunwarshi da tsayuwa a restaurant dinsu 4d first tym
duk aikinsu ne..
dariya oyiza tayi bayan ta gama tunano wadannan
abubuwan sannan ta sauke abincin da ta daura ta kwashe
ta haďa juice ta jere su akan dining ta zauna zaman jiran
mamanta dan suyi hirar karshe....
Allahu akbar,,,
tabbas mun tsinci kanmu a zamanin da kuďi suka fi
wadanda suka kawo mu duniya daraja,
kuďi sunfi ďan da ka tsuguna ka haifa saboda a cikin 100%
85% zasu iya bada komai nasu dan su samu kuďi dattin
duniya,,,
tabbas a wannan zamanin da muke ciki masu karancin
imani da tawakkali zasu iya aikata komai saboda kudi,
Ya Allah ka tsarkake mana zuciyarmu da ta yan uwa
musulmi baki ďaya,
Allah ka azurta mu da baye bayenka kayi mana rowar
talaucin da zai kaimu ya baro mu,, ameen thumma
ameen....

[7:00am 11/11/2016] ◆◆ RABO AJALI ◆◆7
By Sulaiman Bomboy
Daren ranar bayan sun gama hirah da mamanta
ta nuna
mata ta hakura da maganar alhj basheer, mum ta
yi murna
sosai dajin hakan daga bakin oyiza,
sai gurin sha ďaya taga mum na hamma ta
dafata tace
mum bacci kike ji, mum tace eh bacci sosai
nakeji bari inje
in kwanta, oyiza ta mike tace bari in kara gyara
miki ďaki
saboda kiji dadin bacci da kyau,
mum tayi murmushin jin dadin ganin yadda yarta
ke
tarairayarta, dakinta oyiza ta wuce ta yaye
shimfiďar zanin
gadon tasanya mata wani fari kall a kasa sannan
ta ďaura
nata akai,
idonta yayi ja lokacin da ta dauko wata kwalbar
farin
magani zata yayyafa a gadon, sai da ta ďan
zubar da
hawaye sannan ta yayyafa maganin ta fita taje ta
taso mum
da ta fara bacci,
har ďaki ta rakata ta rufo kofar ta koma ďakinta
tayi tagumi
tana jiran dare ya raba ta tafi gurin meeting, ,,
2:45am
Tsugune suke gaban "CHUMMY LORD" cikin
jajayen kaya
su kusan goma sha biyar maza da mata masu
neman arziki
da mulki,
jini ne a kwarya wani bakin mutum ya ďauko ya
mika ma
wacce take gaba ta sha ta mika ma sauran duk
suka sha
sannan suka ajiye kwaryar, wani irin kirari haďe
da ihu
"chummy" tayi akan wani farin kyalle sai ga wasu
yara
yanmata basu wuce shekara 14 ba sun bayyana a
gabanta
cikin night gown, yara ne farare kyawawa masu
kama da
juna da ganinsu yan biyu ne,
a firgice yaran suka fara waige2 suna kankame
junansu,
chummy tayi dariya sosai tace Alhaji Sambo
aikinka yayi
kyau lallai ka tabbatar kana son cin wannan
kujerar,
da sauri yaran suka fara kallon mutanen gurin ko
zasu ga
wanda aka kira da sunan mahaifinsu, jikinsu ya
kara rawa
lokacin da idonsu ya sauka akan babansu mai
kaunarsu
dare da rana wanda a wannan daren kafin su
kwanta bacci
saida yayi yawo dasu cikin garin abuja da
kewayenta ya
kashe musu makudan kudi na ban mamaki, cikin
rawar
murya suka ce PA--PA,
alhj sambo ya sunkuyar da kanshi kasa,
daya daga cikinsu tayi karfin halin zuwa gabanshi
ta
dafashi dan gani takeyi kamar mafarki takeyi,
jin da gaske shi ďinne yasa ta rusa ihu ta kalli
yar uwarta
tace "Fanne" ba mafarki nakeyi ba wallhy papa
ne, meyasa
zaka mana haka, yanzu ashe neman duniya zai
iya saka ka
bayar da ya'yanka na cikinka,
papa sanda zaka bada damu bakayi tunanin
bazaka kara
ganin mu ba,
cikin fushi dayar tace "Fanna" meye a ciki dan ya
bada mu
an kashe,
kika san iya adadin mutanen da ya kashe saboda
neman
duniyarshi,
kukan me kikeyi? Saboda bazaki kara shakar
iskar duniya
ba kome?
Inda zamu tafi nan zai zo yau ko gobe ko jibi in
kwananshi
ya kare shima,
gara ma su kashemu da zama karkashin zalunci
da cin
kudin haram da na kawunan mutane,
wani mugun mari aka dauketa dashi ta waiga ta
kalli bakin
mutumin zuciyarta ta kara zafi tace ba mari nake
bukata ba
kashemu zakayi mu huta,
"chummy" tayi dariyar kusan minti uku sannan
tace ai dama
kun mutu ruhinku ne anan,
in naso zan iya barin ruhinku yayita yawo shi
kadai a duniya
gangar jikinku kuma tana rami,
Fanna tace ki so din,
fanne tayi saurin cewa dan Allah dan annabi ku
maida mu
gurin mammi ta waiga ta kalli mahaifinta tace
papa kaji
tsoron Allah,
Oyiza cikin Fushi tace chummy lord yaran nan na
bata
mana lokaci gashi har asuba ta gabato ga kuma
mum can
daure gara ayi mata abinda za'ayi in wuce gida,
Fanne ta waigo ta kalleta a hankali tace mum? U
mean
mum dinki kika bayar saboda--- wannan karan
chummy ce
da kanta ta kai mata duka a baki,
chummy tace bazan kashe yaranka yanzu ba alhj
sambo
dey wl be under my control, zan watsasu duniya
saboda
naga za'a dama dasu,
fanne tace karya kikeyi jininmu ne yafi karfin ki,,,
chummy tayi murmushi tana girgiza kai,,
Alhj sambo cikin tsoro yace my lord ina tsoron
kar suyi min
illa, chummy tace babu kai babu su saboda zaku
binne
gangar jikinsu a grave so ka kwantar da
hankalinka, yayi
ajiyar zuciya yana kallon hararar da fanne take
musu shi da
oyiza,,,
dafa kansu chummy tayi da wata sanda mai
kyalli nan da
nan suka bace,,
Mum din oyiza kuwa kuka ta dingayi ganin
ďiyarta ce ta
bada ita, gaba daya magana ma kasa fita tayi a
bakinta sai
girgiza kai kawai takeyi tana tunano rayuwar da
tayi da
yarta,
cikin minti goma aka gama da maman oyiza suka
gama
shaye shayensu sannan kowa ya bace, ,,
Kuka oyiza takeyi a bakin gadon da mum ke
kwance tana
ihu makotan da ta aika mai gadinsu ya faďa
musu suna
kanta suna bata hakuri,
ta kira can kauyensu ta fada musu suma suka
dinga ihu
suka shirya suka kamo hanyar abuja,
Guraren karfe biyu akayi mata sutura da kyar dan
yan
uwanta sunce saidai su kaita can okene a binneta
ita kuma
oyiza ta kafe saidai a binneta anan saboda
tsoron kar
asirinta ya tonu dan tasan kakarta na ganinta
zata san abin
da ya kasheta dan itama mayyar kanta ce,
saida malamai sukayi ma yanuwanta nasiha
sannan suka
yarda akayi mata sutura aka kaita gidanta na
gaskiya...
Washe gari ta kira john a waya tace yaje ya buďe
shago in
alhj basheer yazo ya kawoshi gidansu,
haka kuwa akayi yaje ya bude shago amma har
dare babu
alhj basheer, washe gari ma haka,
oyiza hankalinta in yayi dubu ya tashi tana ta kai
kawo
saboda rashin zuwan alhj basheer gashi har an
kusa sati
daya,
a daren ranar ta bayyana gaban chummy da
matsalolinta,
chummy ta gama incantation dinta tana girgiza
kai tace
yana karkashin kulawar matarshi,
ta nuna mata wata kwarya,
bakar mace ta gani a ciki sanye da hijab tsaye
gefen gadon
mijinta dake bacci tana sallar dare in ta idar sai
tayi adduoi
ta tofeshi dashi sannan ta mike ta kara tada
kabbara,
chummy tace kin gani da idonki ko? Oyiza ta
haďe rai tace
na gani amma ay ni babu ruwana da wannan,
mum na
bayar saboda haka so kisan duk yadda zakiyi,
chummy tayi dariya tace dadina dake wutar ciki,
trust me
Oyee cikin satin nan za'a daura miki aure da alhj
basheer,
cikin farin ciki oyiza tace yanzu naji magana.....

◆◆ RABO AJALI ◆◆ 8⃣
By SULAIMAN BOMBOY
Alhaji basheer tsugune yana gyara canvas din kafarshi cikin
shigar blue nd white track suit,
mikewa yayi bayan ya gama ya kalli matarshi zeenatu dake
gyaran gadon da ya tashi yace to ni na fita training, tace to
a dawo lafiya yallabai,
yace Allah yasa sannan yasa kai ya fita,
Zagaye ya dinga yi yana jogging cikin farin ciki saboda
yadda sanyin safiyya ke kaďashi,
yayi zagaye na tara yana yi yana hutawa, a zagaye na
goma ne ya hango wani shima jogging din yakeyi dai2 gurin
wata katuwar kwata kafarshi ta gurďe ya tafi zai faďa alhj
basheer yayi saurin rikoshi yana fadin subhanallah sannu,
mutumin ya ďago yana gyara kafarshi yace yauwa nagode
sosai gaskiya ka taimake ni, alhj basheer yayi murmushi
yace mu gode ma Allah, mutumin ya mika ma alhj basheer
hannu yace sunana Bara'u ina nan zoo road, "BB close" opp
gidan alhj Basheer Balarabe,
Alhj basheer yayi dariya yace ni kuma sunana Basheer
Balarabe (BB) nima ina zaune a zoo rd BB close cikin gidan
Alhj Basheer balarabe,
Alhj Bara'u yayi dariya sosai yace ikon Allah alhj basheer,
kaga yadda Allah ke abunshi ko, .
alhj basheer yayi dariya yace kai gaskiya bamu fitar da
hakkin makobtaka in ba haka ba ga gida ga gida ace bamu
san juna ba,,
Alhj bara'u yace ko 1week banyi da tarewa ba kuma nasa
ayi min magana da duk makota na kai kaďai ne Allah baiyi
zamu hadu ba saboda ance min baka gari,
alhj basheer yace kwarai kuwa ban daďe da dawowa ba, to
ya unguwar tamu da fatan dai baka samun matsala,
Alhj bara'u yace walhy babu matsala unguwar cike take da
mutanen kwarai naji dadin kasancewata cikin ku, Alhj
basheer yayi murmushi suka fara tafiya yace to ya iyalin fa,
Alhj bara'u yace tukunna dai har ansa rana jiranta nakeyi ta
karasa skull zuwa nan da 3monts sai ayi in shaa Allah,
Alhj basheer yace Allah ya nuna mana kai kadai ne a cikin
gidan kenan, alhj bara'u yace eh ni kadai ne amma
weekends a daura nakeyi saboda rashin iyali, alhj basheer
yace hakan yayi Allah ya taimaka yace ameen har suka
karaso gida suna hira cikin kankanin lokaci suka saba da
juna, a dai2 kofar gida sukayi sallama kowa ya shiga gida,
kanshi tsaye yake tafiya cikin gidanshi yana amsa gaisuwar
masu musu hidima, yazo gab da shiga parlo yaji wata
muguwar faďuwar gaba,
juyawa kanshi ya fara yi sosai ya dafeshi ya karasa parlon
dakyar ya zauna kan kujera, zeenatu na can kitchen bata
san halin da mijinta yake ciki ba,
runtse idonshi yayi siffar Oyiza ta dinga mishi yawo a cikin
kwakwalwar kanshi, buďe idonshi yayi da sauri da ya tuno
da oyiza gaba daya yaji wani abu ya tokare mishi kahon
zuciyarshi, ga wutar son ganinta da ta ruru a zuciyarshi
kamar wacce aka iza da petur,
mikewa yayi da sauri ya shiga bayi yayi wanka sharp2 ya
fito ya shirya da gaggawa ya feshe jikinshi da turare ya debi
kudi a sv dinshi na gida masu yawan gaske sannan ya wuce
kitchen ya sami zeenatu,
Cikin rashin fahimta tace tafiya weekend kaiko ina zaka,
yace abuja zeena alheri ne yake kirana,
tayi murmushi tace to Allah ya kawo mana alkhairin tare,
yace ameen yar matata sai na dawo, tace to Allah ya tsare
ya kuma kiyaye hanya, yace ameen ya fita da sauri,
biyoshi tayi da gudu tace na manta ban fada maka ba, dan
Allah zan shiga gidan Malam atiku gurin Ma'u tayi min
kitso, yace to adawo lafiya tayi miki mai kyau fa, tace karka
ji komai in dai kitson ma'u ne, yayi murmushi ya fita ya
tafi...
Da kyar ya gane restaurant din, yana isa ya fito cikin farin
ciki,,
tsayawa yayi turus saboda ganin gurin da yayi a rufe,
jingina jikin motarshi yayi ya rasa me ke mishi daďi yanzu
wa zai fara tambaya inda take anan gurin, ya kusa 30mins
kafin ya shiga motarshi da niyyar tafiya,
kamar daga sama ya hango john yana bude gurin,
fitowa yayi da sauri kamar wanda akayi ma albishir da
gidan aljanna, karasawa yayi yana kiran yaron, john ya juyo
rai a bace saboda yadda yaji ana kiranshi ganin alhj
basheer yasa john jindadi ya fito da gudu ya tsuguna a
gabanshi ya gaishe shi,
alhj basheer ya amsa suka shiga ciki,
ya kalli john yace ina madam dinku, john ya raunana fuska
yace madam is no more alhj tun ranar da kazo washe gari
ta mutu, alhj basheer ya girgiza kanshi cikin tausayin oyiza
yace Allah ya jikanta to ina yarta oyiza,
john yace tana gida dama tace idan kazo in kaika can gida,
alhj basheer yaji dadi sosai a ranshi dan a tunaninshi kafin
mahaifiyarta ta rasu tayi mata bayanin komai, tashi yayi
suka fito shi da john suka shiga mota suka wuce gidansu
oyiza...
Bayan ya gama yi mata gaisuwa yana rarrashinta saboda
kukan munafurcin da take yi ita a dole tayi rashin uwa,
tausayinta sosai ne ya ratsashi ya tambayeta ko
mahaifiyarta tayi mata bayaninshi,
tayi kasa da murya tace eh a daren ranar ta fada min komai
kuma tace in ka dawo zata yarda ka aureni, ta fashe da
kuka tace ashe bazata ga auren ba,
alhj basheer zuciyarshi ta kara narkewa yace kin yarda to
zaki aureni, tayi kasa da kanta tace ko banaso zan yarda
tunda shine last will din mahaifiyata, alhj basheer yace haka
ne naji dadi sosai da kuka amince dani, yanzu ina son cikin
satin nan a gama magnar komai muyi aure in tafi dake,
wani daďi ya ratsata tace to ba matsala bari in turo maka
kanin babana kuyi magana, mikewa tayi ta shiga ciki ta turo
mishi kanin babanta da wan mamanta,
Kudin da alhj basheer ya wankesu dashi da kuma nuna
yanason ya auri oyiza saboda yana tausayinta shi kadai
yasa suka yarda da auren suka sa rana ya biya sadaki da
komai, sannan ya tafi cikin farin ciki,
A daren ranar ya fita da oyiza yawo ya siyo mata duk wani
abu da mace zata bukata na aure,, sun daďe tare har suka
saba sosai kafin su rabu,
Tana shiga gida ta dinga tsalle tana murna nan ta shirya ta
wuce gurin chummy yin godiya....

◆◆ RABO AJALI ◆◆ 9..
BY SULEIMAN BOMBOY
Cikin satin aka ďaura auren alhj basheer da Safiya
oyiza a
okene, shiri na musamman chummy tayi ma oyiza
ta
haďata da special kayan tsafi a cewarta su zasu
taimaketa
ta zauna lafiya saboda wannan matar tashi mai
yawan
addu'a,
Washe garin daurin auren ne ya dauki matarshi
da
kawayenta biyu suka kamo hanyar kano,
tunaninshi ďaya
shine yadda zai fara tinkarar zeenatu da maganar
ya auri
oyiza saboda sam duk wainar da ake toyawa bata
sani ba,
ita dai taga ana ta aikin gyaran part din gefenta
sama da
kasa amma sam bata kawo aure yayi a ranta ba,
sai gurin
bakwai suka shigo garin kano, kallon garin oyiza
da esther
keyi har suka kawo kofar dankareran gidan alhj
basheer
dake zoo road,
a kofar gidan alhj bara'u ya hango su tsaye shi
da malam
atiku suna hira, ganin motarshi yasa suka mike
suka karaso
gurinshi da saurinsu, ya leko ta cikin glass cikin
fara'a suka
gaisa, yace ga amarya fa ku gaisa,
alhj bara'u yayi dariya yace wace amaryar kuma,
alhj
basheer yace amaryata da aka ďaura min aure da
ita jiya,
malam atiku yace shine ko labari ranka ya daďe
to Allah ya
sanya alkhairi sannu amarya,
oyiza ta gyara gyalenta tace yauwa, alhj bara'u
ma yayi
mishi addu'a suka ja suka tsaya shi kuma ya
danna kai
cikin gida kirjinshi na duka sosai, parking yayi
suka fito
duka su ukun suna mika gasu ďirka2, sannu alhj
basheer
yace musu sannan ya fara tafiya suna binshi a
baya,
yana buďe kofar main parlon yayi arba da zeenatu
cikin
kyakykyawar shigar material dinkin stone work
fatar nan
tata sai kyalli takeyi ga wani kamshi da sanyin
dadi ko'ina a
cikin parlon, da sauri ta karaso tana mishi sannu
da zuwa,,
gabanta ya faďi sosai da ta hango su oyiza
amma sai ta
kara fadada fara'arta tana musu sannu da zuwa,
karasawa
sukayi cikin parlon suna yabawa da kyau da
tsarin parlon
ga kuma kula da yake samu ta musamman,
zeenatu ta nuna musu guri suka zauna ta wuce
kitchen cike
da tambayoyi a zuciyarta, kayan shaye2 ta kawo
musu da
snacks tanata yake,
ta kalli alhj basheer da ya dafe kanshi tace
yallabai gajiyar
ne, tashi muje ciki kayi wanka,
oyiza cikin kishi ta watso ma zeenatu harara,
alhj basheer yace zauna zeena akwai maganar da
nakeso
muyi dake,
ta nemi guri kusa dashi ta zauna,
a hankali ya fara magana yace sai kuma kika
ganni da baki,
tayi murmushi tace eh,,
yace dafatan zaki fahimceni zeenah, kinsan komai
nufi ne
na Allah kuma matar mutum duk inda take sai ya
aureta,
ya nuna oyiza yace wannan matata ce jiya aka
ďaura min
aure da ita bawai dan inci mutuncinki ko kuma
dan bana
sonki ba, "a'a" wannan auren ki ďaukeshi
kaddararre ne
daga Allah kuma babu mamaki safiyya na tafe da
alkhairai
masu yawa cikin gidan nan,
zeenatu da tayi mutuwar zaune tayi maza ta
saita kanta ta
kirkiri murmushi tace kaii barka Allah ya sanya
alkhairi nayi
maka murnar samun karuwa,
ay aure cigaba ne yallabai Allah ubangiji ya
bayyana
alkhairan dake cikin wannan auren kuma
alkhairan ya
wanzu a tsakaninmu,
yace ameen yar albarka zeenatu nagode sosai da
kika
fahimceni,
tace ba

Please Login or Register in order to submit comment