Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

right"tace tana cigaba da kukan ta."owk gani. Nan zuwa"yace tare da katse kiran.cikin Saudi ya diro daga kan gadon ya fito parlour a Dari.duk da yaune farkon hawan shi sama bai sha wahalan gane kwatacen taba.yana taba kofan yaji ta a bude,Shiga yayi ya ganta kwance kan gado sai juye juye take duk gashin kan ta ya barbaje ya rufe mata fuska.a rude yq karaso gare ta yana mata sannu tare da tambayan ta ko akwAi magani a dakin ya dauko mata.

Tashi tayi ta zauna tana masa murmushin gefen baki,kamo hannun Sa tayi tana shafawA a hankali tace"kace min mai donkey head but u re a dump ass if not how can u come to my room at this time?naji Hiran ka da abokin ka last 9t wai Ashe ni make fooling.zan nuna maka u re nothing a tafin hannu na kake har ni zaka wulakanta a cikin gidan mu,kasa iyaye na suka fifita ka akaina dan haka yau zan kulla maka sharrin da har ka mutu baza manta dani ba kuma a yAu ba sai gobe ba za ka bar gidan Wanda za a mAka Koran kare tunda kaki tafiya ta girma da arziki...dole a koma kauye
.."tunda ta fara magana farhan ya bushe a wajan ko motsi ya kasa balle ya Iya kwace hannun Sa.kuma lalle ya yarda he is d biggest fool in d world tunda har ya karamar yarina kaman farhat Zata Iya maida shi kwar kwar ko tunanin ya akayi ta samu no shina bai tsaya yi ba.

Zuciyar sace ta wani irin bugawa ganin Ammi ta shigo dakin ladi na bite da ita a baya.farhat tana ganin Ammi ta kara rushewa da sabon kuka.farhan na kokarin kwatan hannun Sa amma ya kqsa,jikin Sa ne ya fara rawa ganin Ammi ta tukaro su gadan gadan fuskan nan nata kaman anyi mata mutuwa.

Hmmmm farhan cikin tsaka mai wuya pls kuyi masa add Ua
[11/26, 5:35 PM] Ummee Yusuf: πŸ’₯πŸ”₯πŸ’₯πŸ”₯🌹🌹

FARHAT

πŸ’₯πŸ’₯πŸ”₯πŸ”₯🌹🌹

Written by ummee yusuf(Maman Yusuf)


I dedicated this page to my sweet sis Ameena adam.luv u soo much.

Page 18


Farhan ya gama saduda yana jiran yaji hukuncin Ammi tana karasowa bakin bed din tace" haba farhat ke dai bazaki taba canzawa ba?abu qalilan zai saki cika mutane da raki?Allah ma yasa alh baya nan da bansan yanda zakiyi ba.son kai ma ta taso kako?yi hakuri wlh haka take da rakin tsiya dan in bata da lfy haka zata ishi mutanen gidan nan."

Shi dai farhan ya rasa bakin magna sai bin Ammi yke da ido da take gyarawa farhat kwanciya.cire hannun farhan Ammi tayi tace"go and sleep son"har yanzu dai ya kasa motsawa Dan ganin abin yake tamkar mafarki.gefen wani drower Ammi ta wuce dauko mata magani,kallon this is the beginning tayi mai tare da gallawa ladi harara.sum ya mike dan sai yanzu ya dawo daga suman zaune da yayi.bai Iya furta komai ba illa ficewa saga dakin,biyu 2 yake hada steps din saboda sauri.shi bai sAmu natsuwa ba sai da gan shi cikin bedroom din shi.

Zubewa yayi a kan Gadon shi yana maida numfashin wahala kaman wanda yayi tseren doki.allah ya so shi Ammi batayi masa mummunan fahimta ba,if not da ya shiga uku .wace hujja zai bayar wanda zai gamsar da iyayen ta cewa yana da gaskiya.tunani yake ta ina ma ta samu no shi?ajiyan zuciya ya sauke mai karfin gaske dan yanzu kam ya yarda kaidin mata azimun ne."Allah ka raba Mu da kaidin mace"ya furta a fili."I have to leave dis house or dis silly gal will make go crazy"murmushi ya fara shi kadai yana juyi a kan gado da ya tuna yanda ya ganta cikin night wear da lokacin da take wani shafa mishi hannu."she already made me crazy"yace yana lumshe ido.

Ammi sai mita take har ta bata magani,sannan ta sassauta murya tace "haba mana habibty kin fa girma yanzu ya kamata ki rinka hakuri watarana haibuwa fa zakiyi,so pls ki rinka daurewa.kinji?"kai kawai ta Iya dagawa,Ga wani hawayen takaici da take zubarwa.anytime zatayi Abu amma shine da nasara.shiru tayi tana sauke ajiyan hrt.ammi tacewa ladi ta zauna a wajan ta tana zuwa.tana ganin fitan amni ta taso a zuciya ta kwashe ladi da wani wawan mari cikin takaici tace mata"me nace miki?magana nake kin wani zuba min ido kaman ki cinye ni.ke da nace miki ki taho da ammi bayan kinga ya shigo kaman da 20mins ba.duk kin rusa min plan.pls ki fita min a daki kamin in miki wani mugun abun."sum sum ladi ta fice mata a daki.komawa tayi bakin bed ta zauna tana tuna yanda yau ta zauna ta tsara abinta tun safe kuma Allah ya taimake ta ta samu no shi cikin sauki a lokacin da ya bar way an Sa a parlour. But bari Abba ya dawo I know what to do cos nasan da shine yazo ya gan shi haka toh tabbas sai ya kore shi a Daren nan kuwa.ta wani bangaren kuma hankalin ta ya kwanta Dan taswn ya tsorata Iya tsorata cos taga hakan a kwayar idon shi.haka tayi ta nazari da kyar bacci yayi nqsaran daukan ta


Da washe gari da yamma Abba ya dawo daga abj.and yanzu jikin farhat da sAuki sosai.on Friday morning sunq zaune a dinning suna break fast ,fa rhan duk haΓ±kalin na kan farhat da ko kallln inda bata yi.can ta ciko bakin ta da potatos ball tana taunawa.dago idon da zatayi suka hada ido da farhan daya zuba mata ido.kashe mata ido 1 yayi yana mata alama da wai loman yayi yawa,murguda mishi baki tayi tare da kauda kai gefe.murmushi abba yayi yacigaba da cin abincin sa dan duk abinda suka yi kan idon shi aka yi.

Wannan ne karo na uku da yake dago kai ya kalli Abba da niyan mgn amma sai kuma sunne kai kasa yana murmushi,Abba ne ya lura dashi yace"ya dai farhan kaman bakin nan naka akwai magana"..

Sunne kai ya karayi yana murmushi sannan yace"Abba ka tambaye lil sis tasan abinda zan fada maka Dan wannan wani babban burin ta ne nake son cikawa,ta Dade tana gaya min tun farkon zuwa na gidan nan.ni kuma a matsayi na,na Dan uwan ta naga ya kama ta in cika mata wannan burin Dan ta samu farin ciki da kwanciyar hankali.da dai banyi na am da zancen ba amma da naga ta dage shiyasa nima na bata goyon baya.

Wani irin sanyin dadi ne ya lullube farhat lokaci daya da taji furucin farhan,sai dai kuma tana tsoron me iyayen ta zasu ce.but koma menene zata Iya daurewa tunda finally ya yarda zai bar musu gida da kan Sa,dama tasan za ayi haka Dan yanda rannan ta tsorata shi.

Abba ne ya katse mata zancen zuci da take yace"mama na ki fada min wani irin buri ne haka da ni ban sani ba,bayan a baya ni ke fara sani"ta budi baki da niyan magana kuma tayi shiru.a ranta take cewa ta ina zata Iya gayawa abba cewa bakon sane bata so,ta Yaya zata fada masa cewa talakawa da yake ja a jiki ne bata so?ta San in yaji daga bakin ta hukuncin da zai yi mata sai yayi sauri dayawa.wannan dalilin yasa taja bakin ta tayi shiru.tana sunne kai itama.

Dariya suka bawa abba ya Dan dara yace"ina sauraron ki mama na"abba in fa na bar zancen tuntuni amma tunda shi ya tado ta sai ya fada maka"tace tana kallon kasa.dariya ya karayi yana kallon Ammi da tayi shiru kaman bata wajan,yace"yau kuma ni ake kunya kuma mama na?"juyowa yayi saitin farhan yace"kaga kanwar taka ta kasa fada Dan haka kai ya kama ta ka daure ka fada ko.......?"

Da kyar farhan yace"ammmm dama.......Dama....
Dama me kayi magana mana INA jinka"abba yace yana kallon Sa.kara sunkuyar da kai yayi sannan yace"abba dama mun daidaita kan Mu ne ni da farhat......."sai yayi shiru yana murmushi da Sosa keya.

Masha Allah!!! Abinda abba yake maimaitawa kenan kana ganin fuskan Sa zaka Ga Balkan farin ciki daya kasa boyuwa"shiken nan tuwo na main a,hjy kinga ikon Allah ko"?itama cikin tsananin farin ciki tace"wlh alh inaga na fika jin dadin wannan hadin".

Bin kowa take da kallo Dan bata San Inda zancen Nash ya dosa ba,ita da take jiran taji an rufe ta da fada amma gani tayi ma suna ta farin ciki.muryan Ammi taji tana cewa"Ai biki zamuyi na ban mamaki a Maiduguri,da nawa ya tawa".zuciyar ta ne yayi wani irin bugawa Dan sai yanxu ta gane inda zancen nasu ya dosa.cikin kidima da tashin hankali ta mike tace.

Tab farhan ya debo da zafi.muje zuwa yanzu aka fara wasan.
[11/27, 7:04 PM] Ummee Yusuf: πŸ’₯πŸ”₯πŸ’₯πŸ”₯🌹🌹

FARHAT

πŸ’₯πŸ’₯πŸ”₯πŸ”₯🌹🌹


Written by Ummee yusuf(Maman Yusuf)

Gaskiya ina jin dadin comments da mahawaran da kuke ,yana kara min karfin guiwa.gaisuwa ta musamman ga MUSLIM IBRAHIM, ina yin Ku sosai masoyana.

Page 19

"Wlh Abba karya yake min,yaushe mukayi haka da kai?"jikin ta har rawa yake,idon ta kuwa sai ambaliyan Hawaye suke.kana ganin ta kasan tana cikin matukar tashin hankali .farhan kanshi sai da ya firgita ganin yanayin ta kuma ya tabbatar tsanan da take masa ya wuce misali amma yayiwa kan Sa alkawari zai koya mata zazzafan soyayyar Sa in dai aka aura masa ita.fargaban shi daya kar iyayenta su gane karya yake suki bashi ita.

ihun tane ya dawo dashi daga zancen zuci da yake sanadiyan buge mata baki da Ammi tayi.

Cikin fushi Ammi tace"bana son zancen banza,ca nake da amincewar ki ya fada kuma shekaran jiya da daddare da baki da lafiya wa kika kira?INA tare nazo na iske ku".

Cikin kuka mai tsuma zuciya tace"ni......Ammi ba wannan maganan nace ya fada ba".toh me kike son ya fada mama na?"Abba ya jeho mata da tambaya,fuskan shi dauke da murmushi.ta ina zata fara fada musu kudirin tq akan farhan?shiru kawai tayi tana shesshekan kuka.

Abba yace "borin kunya ne haka mama na uhum?Ai ba wani abin damuwa bane Dan ya ce ke kika fara ra ayinsa Dan ko ba komai Ai Dan uwan ki ne.nima kuma shaida ne"yace yana dariya kasa kasa"dazu da ido na,na gan Ku kuna ta soyayyar ku ,har kun manta ba Ku kadai bane a dinning din".

Mikewa farhan yayi yana Sosa kai ya fice da sauri, irin wai shi yaji kunyan nan.Ammi da abba suka bishi da dariya.

Kara volume din kukan ta farhat tayi,yanda take jin zuciyar ta kaman ya fashe.har wani daci daci take ji a bakin ta,farhan ya gama da ita wai ita ta fara cewa tana son shi,Ga iyayen ta sun yarda da karyan da ya tsula musu.Ammi tasan sarai karya farhan yayi amma taji dadi Dan ba Wanda zaki farhan a matsayin surki saboda kyawawan halin Sa.and above all da alamu ya nuna zai Iya zama sanadiyan shiriyan ta.

Cikin lallashi ammi ta bata baki,tashi tayi da gudu tayi banyan stairs tana cigaba da kukan ta.

Abba ya dubi Ammi fusakan dauke da tsantsan damuwa yace"anya swthrt ba kya ganin kaman mama na da gaskiyan ta?ban taba ganin ta cikin wannan yanayi ba.kema kin San bans son bacin ran ta cos ita daya gare ni".Ammi da har yanzu fuskan ta dauke yake da zallan farinciki tace"haba dear kasan fa habibty har yanzu kuruciya na damun ta,a yanayin da na fahimta itama tana son shi kawai dai taurin kai ne irin nata.and beside farhan ba zai taba yi maka karya ba,da anyi auran zasu sasanta kan su.just mu taya su da addu a tare da fatan alkhairi.

Abba ya sake fuska yana murmushi tare da gyada kai alamun gamsuwa da jawabin matar Sa,yace"hakane allah ya sanya alkhairi.ameeeen....."

Farhan na fita kiran Umar yayi yaji ko yana gida yaje ya same shi,Umar yace"bana gida inama kusa da anguwan Ku,ina cikin government house bari in karaso "OK"farhan yace tare da fitowa bakin gate ya tsaya.baya son su shiga ciki su hadu da farhat Dan yau yasan ya tsokono tsuliyar dodo.shiyasa zai bar gidan ba zai dawo ba sai ya tabbatar tayi bacci cos in ya tsaya haduwar su bazata yi kyau ba ko kuma ta rusa masa plan.yana nan tsaye har Umar yazo ya tsaya a gaban shi.bude gaban motan yayi ya shiga ya zauna,Umar yana zolayan shi da in jerry sa."tana ciki muje in baka lbrn abinda ya faru.kai man me kayiwa yar mutane?"Umar ya tambaye yana shan
Kwana"muje zan fada maka ".

Farhat tana kwance kan bed din ta sai rusa kuka take kaman ranta zai FIFA,mesa akan farhan kwata kwata bata da Sa a ne?zagi da asshar ba Wanda bata durawa farhan ba sai sumbatu take.

Chak kukan nata ya tsaya kaman an dauke wutan nepa."wat did I just do?"tace tana tashi zaune tare da goge hawayen ta."I rise my voice to him in front of my parent,I cried in his present.oh shit"tace tana kaiwa pillow ta duka kaman shi ya mata laifin." abinda nake son yayi a gaban abba shi yasa nayi daga yau baxan kara kuka a gaban shi ba balle ya raina ni.I know by now he is celebrating ya sani kuka.kaman yanda ya sani na zubar da hawaye na,I promise sai yayi Wanda yafi nawa sai yayi nadaman taro wasa da yayi tare dani.I promise"tace tana kara goge hawayen ta.

9:30pm Umar ya sauke shi a cikin gidan yana cewa"dude wats ur next step?kasan fa ka debo da zafi"dariya yayi ya bude kofan motan ya leko ta window suna kallon juna,yace" don't worry I will handle it,I knw by now tayi bacci and zan San yanda zanyi Mu rage haduwa da ita"its impossible u know since a gida daya kuke."I know and I will try"yace yana juyawa cikin gida,"gud 9t"Umar yace yana Jan Motan shi.

Sallama yayi ya shiga parlour kaman yanda yayi expecting ba kowa sai t.v da yake ta ihun Sa shi kadai.dakin shi ya wuce yayi kwanciyar shi zuciyar Sa wasai,tsabanin farhat da ta kwanta zuciyar ta a cunkushe.

Cikin sati 2 abba da Yan uwan farhan suka tsaida magana akan nan da 2weeks za a sha biki.farhat na dawowa saga sch Ammi ta tare ta da zancen,aiko abin sai ya dawo mata sabo cos har ta manta da batun wani farhan sbd Rabon da tasa shi a ido tun ranan da ya shirya wasan sa.kuka ne yake son kubce mata amma haka ta daure ta shanye da ta tuna alkawarin da tayi,she will never drop her tears for him.murmushin dole ta kakalo ba tare da ta ce komai ba tayi hanyan stairs.

Zama tayi a bakin gadon ta,tare da rafka tagumi da hannu 2.tana son bawa farhan mamaki amma ta yaya?Dan bata son shawaran kowa shi yasa bata fadawa frnds din ta ba.

Cire tagumin tayi ta mike tana murmushi tace"yessssss.....hakan zanyi..."

Nace toh me farhat take shirin yine?😳
[11/28, 7:24 PM] Ummee Yusuf: πŸ’₯πŸ”₯πŸ’₯πŸ”₯🌹🌹

FARHAT

πŸ’₯πŸ’₯πŸ”₯πŸ”₯🌹🌹


Written by Ummee Yusuf (Maman Yusuf)


Page 20

Zaune suke a parlour dukan su bayan sunyi dinner amma har yanzu farhan bai dawo ba.in bata manta ba,kusan a week kenan basu hadu ba."what is he planing?ya kamata in San me yake shiryawa next b4 nima in nuna masa salon wasan".tace a ranta.

Sallama yayi a kofan parlour, Ammi ta amsa ya shigo ciki.dan razana yayi ganin ta a zaune parlour dan baiyi tsamanin ganin ta ba a wannan lokacin.amma da yake wayeyen guy ne sai ya mazge.gaishe dasu Abba yayi sannan ya samu waje ya zauna.

Fada Abba ya Fara masa kan ddadewa da yake a waje kwana 2nan,kamin ya amsa mishi sai jin muryan ta yayi tana cewa"Abba ba laifin shi bane,laifi na Dan muyi waya kuma ya fada min ya ba zai samu daman dawowa da wuri ba."ke fa wani sa'in shasha ce,mesa baki fada min ba?"Ammi ta katse ta tana hararan ta."mantawa nayi fa Ammi"tace a shagwabe."ya isa haka,ke meye naki na sai an fada miki?tunda ya fadawa kanwar Sa Ai shikenan"Abba yace da smiling face.sunne kai suka yi dukan su suna dariya kasa kasa.Ammi ma dariyan tayi tace "Ai shikenan kuwa na daina magana daga yau.

Farhan ya jinjinawa farhat a zuciyar Sa cos a zaton shi zata dauki wani mummunan mataki a Kansa shiyasa ma yake zuwa gida late kawai Dan kar su hadu but yasan yanzu ma she is up to some thing.

"Ya farhan ur food is on d table"tace tana masa kallon kasan ido.mazgewa shima yayi ya mike ya nufi dinning, cikin sauri itama tabi bayan shi tana "let serve me u"Abba ya bisu da ido cike da sha awa.

Ita ta ja masa kujera ya zauna,plate ta dauka ta cika mishi da tuwon semovita yasha miyan kuka Wanda aka burge naman kaza a ciki said kamshin man shanu yake.wani plate kuma ta cika shi da kammoniye Wanda yasha spices,ta tura masa plates din duka 2gaban Sa tana murmushi,ta xauna a kujeran da yake opp da nashi.wanke hannu yayi ya fara aikawa cikin Sa.har wani lumshe ido yake saboda santi.ita kuma sai wani yatsina fuska take Dan kyankyami miyan take.

"A villager will never change,yuks!look at u so disgusting".dagowa yayi yana kallon ta with his smiling face,yace"my future wife,I like ur style.da alamu kin Iya kula da muji and nasan u accept d defect".wajan su Abba ta kalla,taga sun Dade da barin parlourn.kallon banza ta mai tana nuna shi da yatsa cike da tsiwa tace"future wife indeed,huh! Sai kayi nadaman taro wasa da kayi dani,run wuri kuma tun dare baj maka kaje kace ka fasa auran da bakin ka b4 is too late 4 u.kaima kasan ko a matsayi driver baka isa ka shigo gidan nan ba,balle ka dubi tsaban ido na kace wai ni zaka aura.wlh wlh in har baka jenye ba akayi auran nan,kasani duk abinda ya biyo baya kayi kuka da kan ka bcs I have already warn u.

"Wow!miss ego yace yana tafa mata"irin wannan long lec haka?gaskiya zaki Iya lec a ko wani sch.but kin San me?da farko nasa zuwa gun abba in ce na fasa auran ki.dama naso taimaka miki ne sabida naga tunda nazo gidan nan ko kare ba zo gidan nan da sunan yana son ki ba,dan hallacin da Abba ya min shiyasa nima naso in danyi manage dake,cos baki da qualities da nake so matan da zan aura ta kasance da su.but furucin ki na yanzu da kike cewa akwai abinda zai biyo baya,toh gaskiya kinsa min kwadayin ganin ko menene.Dan haka ki fara shiri na fasa janyewa."yace ya mata murmushi kaman ba shi yayi furucun ba.

Farhat ta matukar fusata,tunda take ba a taba ci mata mutunci haka ba.ita da take gara maza shine wannan poor bagger yake cewa zai manage da ita.ita da take ganin duk guys din maid bata ga Sa an auran ba.a fusace ta dauki warmer mai cike da miyan kuka ta watsa mishi a fuska,in ba Dan yayi saurin rintse idon shi ba da ya shiga masa ido.

Cike da karaji tace"karya kake,kai din banza waye kai a garin nan?kai da kake karkashin mahaifina matalauci mabaraci har kake da guts din Dada min magan........."

Katse maganan nata tayi ganin ya nufo ta gadan gadan.fuskan nan nashi a murtuke kaman bai taba dariya ba,sai da yazo dab da ita har suna jin numfashin juna.wani kallo yake mata da yasa ta firgita"repeat wat u have just said now"yace idon shi cikin nata.a matukar tsorace take da yanayin shi amma ta daure tace"dallah matsa min in wuce duk ka cika ni da wari ,a rinka wanka pls"kara matso ta yake tana baya,yana binta har ta kai jikin bango.hannayen Sa duka 2 yasa ya mata rumfa har yanzu fuskan a murtuke take.duk a rude take tasan ko tayi ihu su Ammi ba jin ta zasuyi ba,balle ma ba zata yi ba Dan kar ya raina ta.


"Ina ruwan ki da wari ko kamshi na jiki na?ina ganin sai na koya miki yanda ake kula da miji,tunda naga dai sauran ki".yace yana goga mata fuskan shi Wanda ta bata da miya kan nata fuskan.runtse ido tayi tana cize lebe sakamakon zafin jajin miyan da shiga mata ido."let's share it wife"yace yana murmushin mugunta Dan sab yasan yajin ya shiga mata ido amma ta matse ita ala dole kar ya raina ta.bai barta ba sai da ya goga mata miyan tas a fuska da jiki,tana ji tana gani saboda ya tare ko ina ko kwakwaran motsi bata iyawa.

Kallon yanda take fama da idon ta yake,"so tell me something good b4 I go to bed"yace yana dariya kasa kasa.cikin dauriya ta dake ta bude idon ta daya canza launi daga fari zuwa ja,harara ta watsa masa tace"ban taba ganin talaka mai ji da kai irin ka ba,kana ganin har ka Kai matsayin da dani zan Iya gaya maka wani magana?any way I can say poor bagger stay.........ouch..."race tana Sosa bakin ta sanadin Dana mata yatsan Sa manuniya da yayi a baki kuma shi yayi sanadin katse maganan da ta fara.kallon Sa take cike da takaici,ji take inama zata Iya rufe shi da duka da tayi ko zata huce haushin ta.Ga radadin ido gana bakin duk a lokaci daya."next tym try and find a nice name to ur hubby ko kuma inta hukunta shi wannan somin tabi ne sauran sai a bedroom din Mu"yace yana kashe mata ido tare da shafa gefen fuskanta da miyan kuka har ya fara bushewa.juyawa yayi yana dariya cikin takun kasaita ya nufi dakin shi ya bar ta nan tsaye da kunan zuciya.

A zuciye tayi dakin ta,direct bathroom ta fada tana mai jin haushin zuciyar ta da take yaudaran ta na jin dadin yanda suka kasance tare a yau take Ga kuma hancin ta da yaki daina jiyo Mata daddan kamshin Sa.

Wanka tayi sosai wai duk Dan ta daina jin kamshin but still tana ji.sleeping dress tasa ta dauki turarenta ta kama fesawa sai da ta kusan feshe rabi tukun ta ajiye ta kwanta a gado tana tunanin yanda zata kuntatawa poor bagger a haka har sarkin barayi ya saceta.shima farhan haka ta kasance a wajensa ,sai wani murmushi yake tunda ya fito daga wanka Ga laptop yasa a gaba amma ya kasa tabuka
a komai.ganin bazai ya ba yasa ya rufe laptop din yayi kwanciyar Sa yana tuna moment din such na yau
A haka shima baccin Ya kwashe shi.
[11/29, 7:16 PM] Ummee Yusuf: πŸ’₯πŸ”₯πŸ’₯πŸ”₯🌹🌹

FARHAT


πŸ’₯πŸ’₯πŸ”₯πŸ”₯🌹🌹


Written by Ummee Yusuf(Maman Yusuf).


Zan rayu da Ku zan mutu,Abadan dani da kuzo Mu zauna masoya na.

Page 21~22

Washe gari ya kama Saturday ba aiki Dan haka gidan shiru kowa na bacci in ka cire mutum 2,farhat dama al adan tane every weekend tana motsa jiki.sai farhan kuma da yaki komawa bacci yana jiran yaga fitowan ta.fitowa tayi cikin shirin ta yanda ta saba wato 3 quarter black colour,white top and white facing cap.tayi matukar kyau tana rike da ball dinta while ladi tana rike da sauran kayan bukatun ta


A kan idon shi ta fara wasan yau yana nan tsaye a bakin window da phone dinsa a hannu, kawai sai ya tsinci kan shi da mata video yana smiling. yana nan tsaye har ta gama,yaga ta nufi
cikin gida.da sauri shima ya matsa daga window ya ajiye wayan ya fito tsokana.

Sauri sauri take tafe tana goge ruwan jikin ta,bata lura da shi ba sai da tazo dab dashi sannann ta ankara da mutum a gaban ta.ta taso da rashin mutunci taga ladi ta kusan isowa inda suke, rabawa tayi ta gefen shi ta wuce ciki ba tare da ta kula shi ba Dan bata son ya bada ita agaban masu aiki.murmushi yayi ya bita da ido Dan sab ya ya gane dalilin rashin kula shi da tayi.bedroom ya koma ya kwanta yana kallon videon da ya mata yana murmushi.

Sai 9 suka sauko Dan yin break fast,sun Dan jima kan dinning amma farhan bai fito ba.Ammi tace"habibty je ki kira yayan kj muyi break".bata so ba amma ba yanda ta iya ,haka ta daure ta nufi bedroom shi.

Knocking ta fara yi,jin shiru yasa ta bude kofan dakin ta shiga.wani irin kamshi mai dadin gaske ya mata maraba,kallon dakin ta faryi komai neat a tsafta ce.tabe Baki tayi irin dakin bai mata ba.karasa shigowa ciki tayi tana dube dube.ganin kan gadon ba kowa yasa ta juya da niyan fita, jin karan bude kofan bathroom yasa

Please Login or Register in order to submit comment