Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

hudu,kuka take sosai tana kakkarwa,har zamu gota tausayinta ya tsargamin saboda irun kukan da take,na saka driver yayi parking,na fita na sameta.


Ta dan tsorata da farko da ganina,amma daga baya saita saki jiki,na tambayeta ta gayamin labarinta kan cewa,su ba 'yan garin nan bane,bata da kowa a duniya,saida kakarta ta rage mata,ita ke riqonta,to itama kakar tata sai Allah yayi mata rasuwa,sai wata mata dake siyan quli da daddawa wajen matar ta dauki riqonta,ashe matar magajiyar karuwai,data kaita gidanta tayi tayi da ita kan ta shiga harkar neman maza amma taqi,dalilin da yasa ta dinga gana mata azaba kenan,data gaji shine ra gudo.


Sanda na dauketa zuwa gidana banji komai a raina ba,hakanan ban kawo komai ba,kawai na saka a raina cewa,duk wanda ya taimaki wani Allah zai taimakeshi.


Amma tunda muka zo gidan muka tattauna da xuwaira naga rashin gamsuwarta da lamarin,abun ya dan bani mamaki,saboda nasan cewa ba halayyar zuwaira bace,tana da kirki tana da tausayi,abinda yasa muka jitu kenan tamu tazo daya,saidai duk da na karanci hakan ga fuskarta,bata fito fili ta gayamin ba,har sai dana tuntubeta da cewa


"Naga kamar xaman hauwa dana yanke tare da mu baiyi miki ba ko?" Murmushi kawai tayi sannan tace


"Ba haka bane,rayuwa ce yanxu ta canza,duniya ta zama abar tsoro,taimako ya zama shima abun tsoro,kawai dai inaga ya kamata kisan ainihin wacece ita kafin ki xauna da ita" a lokacin murmushi nayi


"Banda abinki zuwaira.....ta yaya zansan wacece ita?,bayan bata da kowa?" Kai zuwaira ta kada


"Bazaiyu mutum ace kaf danginsa babu mutum ko daya ba,ba'a rasa saura,idanma babun,can inda ta zauna ita da kakarta kafin rasuwarta ya kamata ki tambayi halayyarsu kiji" a lokacin gani nake kawai hasashe ne irin na zuwaira,amma kamannin jidda basuyimin kama dana wata mai mummunar dabi'a ko halayya ba,don haka nabi zuwaira da cewa zan bincika na share zancan kawai,jidda taci gaba da rayuwa damu.


Abun kamar hadin baki haka hafsa tace min,da yake tana da zafi ma har sabani mukaso samu da ita,tace nikam bani da wayo ne ko bansan ciwon kaina ba,da zan dauka mutum rana tsaka na kawoshi rayuwata ban bincika ainihin wayeshi ba,nace mata babu komai,Allah na nufa,kuma ina fatan ya sanyawa nufina albarka,tun tana mita da qananun maganganu har ta haqura ta zuba idanu,saidai a yadda take kallon jidda da yadda take mu'amala da ita zakasan kwata kwata bata kwanta mata a rai ba,don ba haka take mu'amala da sauran masu aikin gidan ba.


Ta bangaren rashid ban samu matsala ba,saboda a sannan din jiddan da girmanta,budurwa ce,ta haura shekara ashirin ma,saboda haka ta haura shekarun da baya daukar masu aiki a cikinsu,yace dai kawai idan ina ganin dai daine shikenan,ta zauna din tare damu.


Maganganun zuwaira da hafsa suka sanya naqi sakin jiki lokaci daya da jidda,na dinga karantarta a nutse,amma banga wani aibu ko mummunan hali tattare da ita ba,sai hidima da soyayya da take nunawa samir,fiye d wadda ni uwarsa nake nuna masa,hakanan fiye da wadda su zuwaira ke nuna masa,idan tana gidan samir baya kuka,babu me tabashi,babu me masa fada,baya neman abu ya rasa,kai hasalima idan kaga samir a wajena tun a lokacin nono kawai zai sha ya koma wajenta,ko yaye dana tashi ita ta karbeshi ta yayeshi,a lokacin hafsa ta tada ballin bala'i kan ita tace zata yayeshi ai,zata hadashi da yaronta amiru,wanda suke sa'anni,tsiran kwana biyu ne haihuwarsu,jidda na kuka tana bata haquri ra tattara samir ta kai mata,don ko sau daya bata taba nuna ta gane hafsa bata qaunarta ba,hakanan bata taba nuna damuwa kan rashin qaunar dake idanun hafsa ba,kullum girmamata take da nuna mata qauna.


Kowa sai daya tausaya mata sanda samir ya tafi yaye wajen hafsa,ta koma sukuku babu wani walwala,har rashid ya gane,a sanna magana ta soma hadasu,ya tsokaneta da maman samir,yace kuma zai lallaba hafsan ta dawo mata dashi.


Wannan shine silar fara magana tsakaninsu,saboda mahaukacin son da rashid yake nunawa samir,kamar an gaya masa cewa shi kadaine abinda zai haifa a duniya.


Na riqe jidda cikin martabawa da girmamawa,na bata suttura irin wadda nake sawa,na bata irin abincin da muke ci,na bata makwanci tamkar na matar gida,na kula da buqatunta fiye dana kowa,saboda a lokacin ina ganin tafi sauran ma'aikatana quruciya,inaso ta tsare kanta da mutuncinta har tayi aure.


Cikin hakan na duba certificate na secondary dinta,banyi qasa a gwiwa ba na samar mata gurbin karatu cikin jami'ar da nake koyarwa,ba matsala ko wahala ta samu saboda muqamin da nake dashi a sannan, course me kyau na samar mata,saboda dukka ina duba gobenta.


Tafi tafi jiddan ta soma sakewa damu,ba jimawa ta koma kamar 'yar gida,a hankali sai duk wata sabga ta gidan ta fara komawa wuyanta,bayan tsantsar kulawa da samir,wanda wani lokaci tare suke zuwa lactures su dawo,har wasu ma na tsammatar danta ne,wanda sukasan bata da aure kuma sun dauka qanwata ce,dukka ina ce musu eh,saboda nima inajin dadin zama da hauwa,tana da matuqar ladabi da biyayya,hakanan tana yabawa sosai da dukka hidimar da nake mata,saboda babu abinda zan siya ban siya mata ba,don a lokacin dan dai Allah ya hadani da mutane masu tsarkakakkiyar zuciya ne,daba shakka a sannan babu abinda zai hana hassada da qyashi shiga zukatan su zuwaira akan jidda,amma Allah baisa sun nuna komai ko sun damu ba.


Cikin qanqanin lokaci ban farga ba na fara ganin wasa da dariya sun fara shiga tsanin rashid da jidda,na danju kishi kadan,amma abun ban wani bari yayi tasiri sosai a raina ba,saboda naga dukka akan samir ne,fiye da rabin hirar tasu ma duk kan samir ne da abinda zasuyi yaji dadi,rayuwarsa ta inganta,don haka sai na saki raina,da zuciyata daya naci gaba da sabgata.


Kwatsam ban ankara ba sai sabo da shaquwa ya fara gittawa a tsakaninsu,hira raha da wasa da dariya,tun ban damuwa har na fara jin kishi sosai a raina,amma na rasa ta yadda zan yiwa rashid qorafi,saboda yadda jidda ke bani girma tana kuma sake bada himma wajen kula da samir da nuna masa soyayya da kulawa.


Wasa wasa abu yaci tura,har takai ta kawo rashid zai dauki jidda da samir su fita shopping ni ina zaune,koda abu ne wani lokacin idan bana kusa saidai ya bawa jidda ta riqemin kota ajjiyemin,idan nayi magana sai yace,ai yaga na aminta da jiddan ne,kuma yarinyar nan tana da hazaqa da qoqari,komai.naki dana yaron nan ita ke muku shi,haushi ya cikani,na tsuke fuska nace


"Ai ba gazawa taga nayi ba ko bare ka gayamin haka" dariya ya fashe da ita


"Kai raihana,ban sanki da wannan ba,kishine kawai yake damunki hala,amma jidda ai hutu ce a wajenki,kaf masu aikin gidan nan babu wanda yake aikatuwa irinta" gaskiya ne abinda ya fada,amma abinda na gani shine,babu wata sabga data zama wajibina dana gaza,komai na kula da mijina ban fasa ba,aikina bai sanya na rageshi da komai ba,kuma shi dinma harkokinsa sun sanya ba mazaunin gida bane.


Abu daya ne da ban ankara dashi ba sai sannan,jiddan tana da azarbabi,wasu abubuwan na rashid ko na samir duk sanda na tashi xanyi saina tarar tayi wuf tayishi,koda baqi nayi kafin nace ayi musu kaza tayi,duk wanda yazo gidan saiya tafi da kirkin jidda a bakinsa,duk sanda muka hadu ya dinga tambayar ina jidda?,yarinya me kirki,musamman dangin rashid,cewa suke nayi dace da yarinya me kirki,ranar da family na daga sudan sukazo kuwa,zaka ce wajenta suka zo,duk wata hidima tasu a wuyanta take har suka tafi,da na dan motsa zatace aa na zauna miyi hira da baqina.


Randa na hada undies din rashid xan wanke a toilet dina,nayi baqi na fito muna gaisawa bayan ta saukesu a wannan lokacin na fara taka mata burki kan ta daina shiga hurumin daba nata ba,tana hawaye ta bani haquri,idan raina ga baci nayi haquri,ita batayi don wani abu ba,tayi ne saboda taga jiya iwar haka ina kwance bani da lpy ina fama da zazzabi,yadda naga tanata kuka tana bani haquri sai naji babu dadi,naga kamar ban kyauta mata ba,tunda kulawa ce tasa haka,amma komai kulawa bai kamata ta taba kayan da suke sirrin mijina ne,nace mata ya wuce amma ta kula.


Kwana biyu haka ta dinga rayuwa sukuku a gidan,har samir sai daya koka saboda yadda ta koma ba kuzari,rashid ma ya fuskanci haka,ya kuma sameni da maganar.


Fada sosai na dinga yi,ta inda nake shiga ba ta nan nake fita ba,saboda raina haka kawai naji yana quna,bugu da qari kima yaron cikin dake jikina,wanda ya qaramin zafi,baice komai ba harna gama,sannan ne ya amsa min da


"Kada dai kije kishi ya rufe miki ido ki batawa wanda yake qoqarin kyautata miki" lafazin da ya sanya jikina yayi sanyi kenan,na rage daurewar dana fara yi mata.


Yan kwanaki tsakani laulayi ya sakani a gaba,sai komai ya sake komawa hannun jidda,ni kaina a sannan na yaba mata,yadda take hidima damu kan jiki kan qarfi,bata xama ta huta kona minti daya,ga makaranta tata data samir wanda ya fara zuwa ba jimawa,ban samu kaina ba har sai da nayi barin cikin,taci gaba da hidima da ni har na warke na koma kan harkokina.


Ban jima ba na sake samun wani,shima dai itace komai.namu,wannan ya qara kusanci me qarfi tsakaninta da samir dama rashid,shima dai cikin sai da ya fita na samu sauqi,bayan na warke saina sake ganin canji sosai tsakanin rashid da jidda,idan nayi magana yahau fada,yace duk kyautatawar da takemin bana gani?,sai shi don ya kyautata mata?.


A wannan lokacinne rigima kusan taso barkewa tsakanin hafsat dashi,ta shiga maganar,ya hadamu duka yace bamu da kirki kuma bamu da halacci,kamar yadda na gaya miki,hafsat tana da zafi,saita qyaleshi kamar anbar maganar,tafiya tana kamashi tazo ta sanya jidda tattara kayanta tace lallai sai tabar gidan.


Yadda jidda ke kuka tana roqon tayi haquri ya karyarmin da xuciya,ina qoqarin cewa ta barta,amma hafsa ta hada harda ni,haka nan tasa jidda ta tattara tabar gidan,ta gama kin bambamin fadan na zauna lusaranci,idan baiyi wasa ba zafa qwace rashid a hannuna,tayi ta gama ta fita.


Tunda jidda ta fita duka sai tausayinta ya kamani,na kasa nutsuwa,musamman idan na tuna cewa bata da kowa,to ina zataje?,itace tambayar data dinga damuna,na tsaya gaban madubi na dubi kaina,sai naji bana ji sam bana tsoron zama da jidda,banjin zata iya qwacemin rashid,duba da irin halaccin da na yiwa rayuwarta,halaccin da nakejin ya isa yasa jidda taji kunya da nauyin aikata min ba dai dai ba,uwa uba bata ko kama qafata wajen kyau da diri ba?,to meye zanji tsoro?,wannan tunanin ya sanyani fita neman inda jiddan tayi.






57


"Tun ba'ayi nisa ba aka sameta rakube gefan gidana zaune ita da kayanta,taci kuka ta godewa Allah,nasa aka shigo da ita ciki,kafin ma ta qaraso ta soma roqata na rufa mata asiri na barta ta zauna,nace kada ta damu,taci gaba da zama damu,saidai na kafa mata wasu qa'idoji tace zata kiyaye in sha Allah,a baya ma duk abinda ya faru nayi haquri,nata dauka zan zaci wani abu ba. Da wannan mukaci gaba da zama da jidda lafiya qalau,wanda bayan 'yan watanni saita nemi na barta ta koma zama a hostel,ta dinga zuwa gida weekends,ban musa ba na barta,saboda ina ganin nima hankalina sai yafi kwanciya da hakan,data koma din kuwa sai naji tsarin ya yimin,har zuwa sanda na sake yin bari na uku,a sannan naci wuya,su zuwaira da samir ke kira bibi wato baba,bai iya fada ba a sannan saboda yarinta,har ya soma wayo kuma ya bita a haka,su suke komai,saidai na fuskanc sam rashid baya ganin qoqarinsu,bashi da aiki sai mita,bini bini yace da jidda tana nan kaza za'ayi,na zauna tsaf naga babu ta inda suka gaza,duk abinda jidda keyi sunayin ma fiye da hakan,ina fama da ciwo saina tattarashi na watsar kawai shida mitarsa.


Ban tashi gane cewa komawar jidda hostel wani babban illa ta shirya yimin ba sai bayan wani lokaci da soyayya tayi nisa tsakaninta da rashid ba tare dana ankare ba,nayi kuka nayi kuka na godewa Allah randa na ganshi cikin school ya dauketa sun fita cikin shauqin soyayya,na dawo gida nasha kuka son raina,na zauna na yiwa kaina hisabi,na kuma binciki kaina tsafff...naga me na rasa?,me kuma na gaza dashi?,saboda gudun yanke masa hukunci kan kuskure,babu itace amsar dana lalubo,saboda ado da gayu da kuma tsafta dukka a wajena jidda ta koyeshi,kyau kuwa ko gefan takalmina nasan cewa jidda ba zata iya riqewa ba da suna karawa dani,iya kula da miji ta wannan fannin ni malama ce,mata da yawa na neman sani a wajena,wajen gyaran shimfidarmu kuwa.....sam bana yarda ma nayi amfani da kayan qasar nan,saina tantance masu kyau na qasarmu dana wasu qasashen da suke da qwarewa ta fannin.


Ganin na gagara gano dalilin.....saina azawa raina cewa,kawai dabi'ar maza ce,a haka kuma Alla ya haliccesu,komai kyanki ko iya gayunki idanunsa basa kasa gane masa wata da zai dinga jin ta fiki,jidda halal dinsa ce,saidai hanyar da suka bi tana da ciwo,yarinyar dana riqa kamar qanwata saboda kyautatawa?,to amma kuma.....babban abun mamakin ma shine,ta yaya har ta iya janye hankalin rashid?,tambayar dana kasa baiwa kaina amsa,na kuma kasa hutawa har sai dana samo amsarta,saboda ina tsoron kada ya zaman tana bin malaman tsubbu ne,na zauna ta cimmani,gwara nasan a wanne mataki nake?.


Jidda tayi amfani da zallar KISSA ce,wadda hausawa sukance TAFI MAGANI,ta shiga rayuwar rashid ne ta hanyar amfani da abinda yafiso duk duniya wato dansa samir,tayi amfani da duniyanci da gogewa,wadda bansan ina ta samota ba?,da ita na daukota na kawota gidana?,ko kuma.bayan shigarta makaranta ta hado harda karatunta?.


A lokacin nayita qoqarin shanyewa,ban nuna masa na gane komai a tsakaninsu ba,saidai deep inside ina karantarsa,ina karantar duk wani motsi nasa,saina fahimci wasu abubuwa da ban fahimta ba a baya,kamar yawan yin adonsu ranar juma'a,suyi anko shi da samir yace zaya kaishi gidan hafsa,ba zasu dawo ba sai magariba,wani lokaci nakan gansu tare da jidda,sai yace min suna tahowa suka gamu da ita ya qaraso da ita,to amma ban taba kawo komai a raina,saboda bana zarginsu shida ita.


Ranar data dawo gida duk qarshen sati kamar yadda takeyi itama ban nuna mata komai ba,saboda inason na gama karantarta,mamaki ya dinga cikani saboda yadda suke pretending wa junansu,saidai idan har kayi tsaiii da ranka zaka iya shinshino akwai wani abu a tsakaninsu,abun yayi masifar baqanta min rai,wato ni suka maida wawuya kenan tsahon lokaci?.


Lamarin kishi abune da ba kowacce mace ke iya cinyeshi ba,musamman kishi da irinsu jidda masu yaqar mace da takobin kissa,naso na danne amma sai naketa ganin canje canje,kaf hankalin rashid yana kanta,lokaci daya ta canzashi kamar asiri,shine tashi cikin dare yaje falo suyi waya,shine fitar yammaci ko dare,shine zaman charting shi daya baya so kowa ya rabeshi.


Ranar dana kasa jurewa.....randa ya tashi tsakar dare,ya shiga toilet yana waya,ga zatonsa bacci nakeyi,na tashi na zauna na jirayi fitowarsa har kimanin awa daya,yana ganina mamaki da 'yar razana ta nuna kan fuskarsa,amma da yake namiji ne saiya fuske,yana tambayata ya tsaremin bandaki ko?,shiga zanyi?,kaina girgiza masa


"Jira nake ka gama wayan da jiddan,inason yin magana da kai" sosia fuskanshi ya nuna shock,sai ya zauna jikinsa a sanyaye,cikin nutsuwa na fara masa maganar mamakin da ya bani kan boyemin da cij amanata da suke shirin yi da jiddan,na fitittike masa,ya tabbatar min soyayya suke da jidda,kuma aurenta yakeson yi,abinda yasa ranar bamuyi kwanan dadi ba,don ya bani mamaki,abun kuma ya dagamin hankali duk da na sani,amma tabbacin da na samu daga bakinsa ya sake sani cikin qunci da baqinciki.


Wasa wasa zamanmu ya hargitse,rigima har wajensu yadikko,hafsa ta shiga ta fita yadikko ma tace bata yarda da auren ba,saidai idan har ni na amince,abinda yasa rashid ya tattare ya dawo min,ya dinga roqona na barshi ya auri jiddan,da farko na kafe,amma bayan na dauki wayarsa rannan naga irin saqonnin da jidda ke tura masa,na tabbatar da cewa koda su yadikko sun tsaya min auren bai yiwu ba bani da wani sauran kwanciyan hankali a gidan,don haka na zubda makamaina nace masa na amince.


Aranar naga zumudi da farinciki da soyayyar da zan iya cewa rabona da ita tun lokacin da muke zaman lafiya lumana ni da shi,hawaye ne kawai ya dinga sauka a idona,tun a sannan nasan cewa tawa jarrabar kenan,don haka na duqufa da addu'a,ina gayawa ubangiji na. Tabbas naga tasirin addu'a,saboda sai Allah ya ragemin damuwa sosai cikin raina,duk yadda na zaci abun sai ubangiji ua huwace min shi,har ya zaman Hafsa ta fini shiga damuwa da tashin hankali,daga qarshe ma take ganin nice na daurewa rashid baya,tsanar data yiwa jidda ta ninku. Tun daga lokacin jidda gaba daya ta daina dawowa gida na weekend,banace ga a inda take ba,amma dai tabar dawomin. Ba'a dauki wani dogon lokaci ba rashid ya hada lefe,wanda ya kusa fin nawa ma,saboda a sannan ya fara siyasa,wadda ta karbeshi sosai,saidai ta sake taka rawar gani wajen canza masa halaye da dabi'u,bamu da rashin ci ko sha ko suttura,hakanan bana rasa kudi a hannuna,amma abubuwa da yawa sun canza.


A lokacinne hafsa ta dire tace sam batasan zance ba,yadda ya yiwa jidda kaya haka zaimin,bai musa ba,saboda ganin bana ce masa ko uffan kan dukka lamuransa,na kawo idanu na zuba masa. Abubuwa da yawa sun faru,akayi biki kai kace lokacinne zaiyi auren fari,saboda irin abubuwan da yakeyi,hafsa kamar zata zauce saboda baqin ciki,tace ita bata yarda ba,ba shakka jidda asiri tayiwa rashid,ni kuma nasan ba asiri bane,kirsa ce ta gwanaye,mummunar kissa da warwareta sai Allah da malaman gari.


Fadin ma irin amarcin da akayi da rayuwar dana fuskanta bayan aurensu da jidda bata baki ne,saidai na tattarashi gaba daya na sallamashi,saboda komai nayi bana burgeshi,hankalinsa gaba daya baya kaina,wani abun ma idan yayi sai inga kamar wanda aka yiwa dole yake zaune da ni.


Ta fannin dangi da 'yan uwa kuwa,dai daikune basa yi da jidda,duk da cewa bawai sun juyamin baya bane,nima ban canza dukkan halayyata da mu'amalata dasu ba,haka nan ban fasa yi musu alkhairin da aka sanni dashi ba,amma suna matuqar sonta dayi da ita.


Tafi tafi rayuwa ta dinga garawa,na zama tamkar nice asalin 'yar aikin jidda,cikin ruwan sanyi da wani salo na kissa me kama da siddabaru ta qwace komai daga wajena,gidana mijina d'ana,kowa cewa yake jidda kamar kece kika haifi samir?,shi kansa yaron akwai shaquwa me girma tsakaninsu,saboda yadda take shagwabashi,saidai wani lokaci abun yana min ciwo,don abubuwa da yawa daya kamata ace ta kwaba masa bata kwaba masan,ina tsoron kada ya lalace,shi kuma mahaifinsa idanunsa ya rufe da soyayyar ta,baya ganin ba dai dai dinta ba,komai tayi dai tayi.


A sannu a sannu jidda ta fara fiddomin da muna nan halayenta muraran a fili,bayan ta tabbatar da cewa ta qwace komai ya koma hannunta,saidai fa a bayan idanun kowa,daga ni sai ita kadai take gwadamin wanna fuskar.


Ni kadai ni da mata irina ke kadai zasu fahimci irin jahannamar da nake ciki,don kowa yabonta yake,kowa cewa yake na dace da abokiyar zama,jidda batayi butulci irin na sauran mata ba,batayi butulcin da aka zatar mata zatayi ba,da yawa kan tambayeni....me yasa nake rama?,bayan ban rasa komai ba?,wasu kawai saidai na bisu da murmushi,saboda duk yadda naso yi musu bayani ba zasu gane ba,ba zasu taba fahimta ba,ba zasu gane quncin da zuciyata take ciki ba.




Cikin wannan yanayin rayuwa ta dinga tafiya damu,yau fari gobe tsumma,tuni jidda tayi aminai,masu bata shawara,cikinsu babu kamar hajiya shuwa,wadda na jima da sanin cewa hatsabibiya ce,kusan da gudunmawarta komai yake sake wanzuwa yake dada tabarbarewa cikin gidan,itama yarinyar macace,kusan sa'ar jiddan,saidai a sannan ita yaronta guda daya fawwaz. A haka a irin wannan rayuwar har ta haifi najwa,tsirar shekaru uku ta sake haifan jawahir,a hakan nake haquri nake zaune,ina duba abubuwa masu yawa,ina duba cewa komai yayi farko zaiyi qarshe,ashe qaddarar tawa me tsaho ce,ashe banyi komai ba cikin tafiyar qaddarata......


Domin kuwa shekara daya tal da haihuwar jawahir.....na sake samun wani cikin,shima dai mai wahala kamar wancan,ni kadai nake wahalata nida zuwaira da harira,amma a gaban idanun mutane kuwa,ciki harda rashid.....tsinke jidda bata bari na daga,abun ya zame min jiki,ba baqona bane,don ta qware wajen iya wannan.


Kwatsam rana tsaka ina zaune da wani yammaci saiga rashid ya fadomin afujajan,jidda na biye dashi a baya cikin tashin hankali tana qoqarin riqeshi,tare da neman ya tsaya,amma yana qwacewa yana sake yin gaba,ina zaune a inda nake ban motsa ba har ya iso gabana


"Waye uban wannan cikin na jikinki?" Itace tambayar daya jeho min,tambayar data rudani har na miqe tsaye ba tare dana sani ba,saboda ban taba kawo fitar irin wannan tambayar daga bakin rashid ba,ko wanne irin xama kuwa muke,na maida masa da amsar cewa.....bashi da uba daya wuceshi,saiya jefomin takardar hannunsa,wadda ban iya dauka na duba ba,shima bai iya tsaiwa na duba din ba ya shiga bayanin


"Tun bayan buguwar da nayi watannin baya da suka shude aka yimin gwaji,wanda bai fito ba sai cikin satin nan,suka kuma shaida min akwai jijiyoyina da suka tabu,wanda bazan sake samun haihuwa ba sanadiyyar hakan,a ina kika samo wannan cikin?" Maganar data sanya jiri ua debeni ya maidani kan kujerar dana tashi a kanta,innalillahi wa inna ilaihi raji'un na dinga maimaitawa,ta inda yake shiga ba ta nan yake fita ba,ya kuma barmin gargadin cewa lallai ne na samo uban cikina.


Wannan shine abunda ya kusan tarwatsa rayuwata,ya kuma kaini kabari tun jidda bata gama shirin kaini ba,cikin gidan ya zame min tamkar sansanin yaqi,duk wani sauran farinciki da walwalata da nake tattali gaba daya suka yi nasu waje,babu mai kusantata da zuwa inda nake,hatta dasu bibi,duk da cewa su din jidda ce ta kafa musu dokar,matuqar suna son ci gaba da aiki a gidan,amma bibi da harira basu yarda ba,don suna biyo dare suzo su ganni,su kuma kawomin abinci,don bana iya ci,jidda kuma bata damu a bani ba,a sannan nayi burin akwai isassun kudi a hannu na,da babu shakka saidai a wayi gari a ganni a sudan cikin mahaifata,wadanda basu san halin da nake ciki ba,sakamakin bacewar wayata lokaci guda sama ko qasa,ni kuma ba fita nake ba a sannan,ko lecturing din da nake ban iya zuwa saboda azabar ciwo daya hadu da gagarumin baqinciki.


Duk wannan yanayin nida hafsa muke karbar takaicin,a haka ma ina boye mata wasu abubuwan bata sani ba,saboda banason na bata kyakkyawar alaqa da kuma dangantakar dake tsakaninta da dan uwanta,wadda dama tun aurensu da jidda yau shiri gobe fada,kuma duka a kaina ne,ya kuma koka da hakan shi kansa,kan cewa ina shiga tsakaninsa da 'yar uwarsa.


A irin wannan yanayinne wata rana ina zaune,na gama rubuta kan wani mummunan furuci da jidda tayimin daren shekaran jiya,makomata,da kuma hasashen abinda zaizo ya sameni nan gaba muddin naci gaba da irin wannan rayuwar......gidan babu kowa,don ko dama samir yana nan,zanga yana yawan kallona,amma yaqi zuwa inda nake,abun yana daya daga cikin abubuwan da suka sake kassaramin ruhina,gani nan ni ba mutun ba

Please Login or Register in order to submit comment