Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kuma shaida masa ranar da ita zata tafi


"Ke kuma sai yaushe zaki tura taki gudunmawar hajjaju,naga jidda wannan karon ta rigaki bayarwa" ya fada yana saka hannunsa a aljihun babbar rigarsa yana ciro kudi.


Baki ta tabe tana duban wani barin


"Dama haka takeso ace,tayi qoqari,amma ni bana abu don a fada ko kuma saboda gasa,Allah sarki raihana.......har batason ace tayi wani aikin alkhairi,takan ce tayine saboda Allah,kuma shi take bida ya mata sakayya"


Wani kallo ya yiwa hajiya qaraman,tayi zaton abunda ya saba shi zaiyi a yanzun ma,saidai ga sabanin tunaninta sai taga ya dauke kai ba tare da yace komai ba,yaci gaba da irga kudaden daya debo din.


Miqewa yayi yana ajjiye mata kudin


"Wannan ki riqe a hannunki,nasun kuma zan saka a tura musu su cire ta banki" baki ta sake tabewa


"An gode,Allah ya qara arziqi ya rabaka da sharrin maqiya da munafukai" ya saba da jin wannan addu'ar daga bakinta,itama kuma tasan cewa an kawo qarshen hirar shi yasa daya miqe ma yana mata sallama ma bata damu ba.


Da kaltum hajiya qarama taso tafiya azaren,saidai kuma abun yazo da akasi,don randa xasu tafin ita da yaranta guda uku da jikokinta shida ranar kaltum din tana da sauran jarabawa guda uku,hakan yasa dole hajiyan ta barta suka wuce ita da yaran,da kuma jawahir banda najwa da ita tace sai ana ya jibi daurin aure zata je,ba zata iya zuwa azare ayi sati ba tana da schedules da yawa.


Jin cewa samir bazai samu tafiya ba sai ana ya gobe daurin aure tace ta zauna nan gidanta tunda masu aikinta suna nan,ya taho mata da kaltum din itama taga jama'a.


Hakan ya yiwa kaltum din,saidai jawahir bataso hakan ba


"Don Allah idan kin gama exams kafin ranar ki gayamin,Allah zan yankar miki ticket da kudina ki taho bauchi a ranar" murmushi kawai tayi mata,itakam banda ma hajiya nason taje da babu abinda zata,zatafi farinciki ace qauyen dinya akace taje,taje ta gano ummanta,don a yanzu bata da burin daya wuce haka.


Su amiru kuwa washegarin randa su hajiya suka tafi shima yabi bayansu,saboda akwai abota sosai tsakaninsa da angon fiye da samir,don yafi samir ma zuwa azare,hakan yasa professor ya sakashi ya tattaro ya dawo gidan hajiyan,saboda yace kada a bar mata gidan babu wani babba namiji sai masu aiki,dama kuma yana da niyyar hakan,saboda gyara daya bayar ayima sassansa,har mummy na tsokanarsa gyaran me?,shi daya kusa tafiya yabar gidan gaba daya?.




Ko daya kaltum batasan yana gidan ba,don ba shigowa ciki yake ba,iyakarsa sassan da suke zama yawancin lokuta shi da amiru idan suna gidan,hakanan da safe yake ficewa sai dare yake shigowa bayan ya gama sabgoginsa.




Yau tunda ta tashi takejin mararta babu dadi sosai,duk kuwa da cewa tun sanda ta gama shanye magungunanta dama takejin wani iri a mararta,amma na yau yafi na kullum,a haka ta samu ta rarrafa taje makaranta ta dawo,sai tayi lamo tun la'asar a bargo tana karatun novel tare da daukan darusa masu yawa,saboda jarrabawa biyu suka rage musu,kuma dukkansu masu sauqi ne,bata da wata matsala ko fargaba akansu,hankalinta kuma na rabuwa kashi biyu,saboda yadda mararta ke sake daurewa.


Bata tashi ba saida akayi sallar magariba,tayi alwala tayi salla,ta zauna saman abun salla kamar yadda ta saba kullum tsakanin magariba da ishaa,saboda lokacine na amsa addu'a,lazumi take a lokacin,idan ta gama kuma ta duqufa da addu'o'i kan ingantar rayuwarta data iyayenta.


Bata tashi ba saida tayi sallar isha'i,daga nan tayi bandaki tayi wanka da brush,kamar yadda yanzu ta sabarwa kanta ya zame mata jiki,ta tsane jikinta tayi oiling gashinta ta hadeshi waje guda tayi masa tufka daya sannan ta dauki wasu riga da wando milk colour masu taushi da kauri da hajiya qarama ra bata su,cikin wasu ragowar tsarabarta zuwanta saudiyya da professor ya kaita shekara biyu baya ranar ta dauko jakar ta gansu a ciki.


Tsaiwa tayi tana kallon kanta yadda kayan suka karbeta,ita kanta a yanzu takan jima tana kallon kanta yadda ta sauya lokaci daya,tasan mutane da yawa idan akace musu wanna kattumen da suka sani ce saisun qaryata kafin su yarda ita dince,abu daya ne yake daqila mata farincikinta,idan ta tuna ummanta da kuma habi,ko a wanne hali suke ciki?,ko habi ta haife abinda yake cikinta?,ko ummanta ta warke?,uwa uba kuma idan ta tuna ko zata karade duniya ba zataga dan uwa rabin jiki bilalunta ba,ita dashi sai a lahira,sai taji hawaye sun sauko mata,dukkan wata walwala tata da jin dadinta sun kau.




Yau a sanyaye ta koma ta zauna,ta jima a haka tana nazari,kafin ta sanya hannu ta shafi mararta dake sake qulle mata,wunin yau bataci wani abun azo a gani ba,abincinta na rana dana dare tasan duk suna kitchen din a ajjiye,kuma ko yanzu bata jin cin komai,bata da matsalar dafa ko cin abinda takeso,kamar yadda kowanne cikin masu aikin gidan hajiyan batayi masa shamaki da cin abinda ranshi keso ba ta hanyar data dace,babu almubazzaranci babu barna ko ha'inci,tana da kyauta da kyautatawa dukkan wanda ya zauna tare da ita,itakam.kaltum ba zata iya lissafa adadin kyautatawar hajiyan gareta ba,ko diyar data haifa a cikinta iyakar abinda zatayi mata kenan.


Komawa tayi ta sake kwanciya tana jawo littafin tana cije labba,wala'alla ko zuwa anjima zata iya jin yunwa ta tashi ta nemi abincin.


Yau da wuri ya dawo,don a nan unguwar ma yayi sallar magariba kana ya shigo gida bayan yadan tsaya wajen masu gadi sun dan taba hirar da bata fi minti biyar ba,duj da cewa ba jimawa yake wajensu ba,amma hakan yana musu mugun dadi,ta yadda baya qyamatarsu,ko kuma nuna banbamci ko fifikon dake tsakaninsu.


Yana fidda kayan jikinsa yana kiran wayar jawahir,yana sone yaji ina yarinyar take,saboda akwai siyayyar da yakeson mata,ya dade yana son mata wasu 'yan siye siye,saboda ko babu komai tunda har agiyarsa ta hau kanta to dukka sharuddan kulawa yahau kansa a musulunce,to amma baisani ba ko tare suka tafi dasu jawahir din,don baisan taqamaimen ranar da xasu gama jarrabawar ba.


Bugu biyu jawahir din ta daga,da qorafi ta fara kamar kullum


"Yaya,ban tabajin azare ba dadi ba irin wannan karon,don Allah yaya kaida kaltum ko taho sooner" murmushin daya qawata fuskarshi ya qara mata kyau ya saki sanda yake zare tie din wuyansa


"Mr qorafi,babu gaisuwa,babu jin ya nake sai qorafi"


"Am sorry yaya"saita fara gaidashi ya amsa mata,yana tambayarta azaren tana bashi amsa,tare da bashi labarin yadda aketa tsara bikin,saboda an dade ba'ayi biki ba a familyn sai yanzu,sannan kuma ma auren zumunci ne tsakanin angon da amaryar.


Yana da jumurin sarare,abinda yasa alaqarsu da jawahir keda tsaho da kuma nisa,yasan cewa tana da sauqin kai kamar yadda take da surutu,amma banda daddynsu duk cikin gidan babu mai iya bata attention dinsa yadda takeso,shi yasa yake jumurin biye mata.


A handsfree ya saka wayar,har ya gama shanye yoghurt din daya tsiyayo,zuwa sannan ya soma cire socks dinsa saboda wanka da yakeson yi,ya gama jin cewa kaltum din na cikin gidan,saboda haka yayiwa jawahir bayanin zai shiga wanka,ya katse wayar,ya dauki qaramin towel ya shige bathroom din.


A hankali ta ajjiye littafin hannun nata,ta miqe ta zauna sosai kafin ta janyo dankwalinta me santsi ta daura akanta.


Tunani tayi ta fara samun ruwan dumi sosai tasha ko ruwan lipton ko xata samu sauqin cramping din da mararta keyi,don taga walida qawarta idan tana ciwon mara shi take sha,kuma cikin ikon Allah tana samun relief.


Kitchen ta isa kai tsaye,ta samu daya daga cikin masu aikin ta kammala komai,tana daukar cooler din tata abincin,wanda indai ta dauki cooler din ta shiga dakinta kuma saida safe,saboda tana da saurin bacci ne.


Dukkansu tsakanin kaltum dasu girmamawa ce ga junansu,da dan murmushin qarfin hali kaltum tace


"Har kwanciya baba?" Dariya ta danyi


"Tome zan zauna yi,gida babu kowa hajiyarmu bata nan,ai saida safe kawai kaltume....am.....amma ga abincinki nan tun na rana fa banga kinci ba" fuska tadan motsa kadan


"Yau banajin dadin jikina ne baba shi yasa" cikin fuskar alhini tace


"Ashsha....Allah ya sawwaqe,to ko za'a sanya hasanu(yaron gidan) ya yiwa yallabai samir magana ko dan qaramin dakin shan magani kije?" Kai ta kada tana mamakin dama yana gidan,rabonta da ganinsa tun ranar nan,ranar data tsaye mata a rai,take kuma yawan tuna abubuwan da suka faru a ranar


"Ruwan dumi xansha yanzu,ina kuma saka ran zanji dadin jikina"


"To....to Allah ya qara afuwa" da haka sukayi sallama,baba ta fice da flask din abincinta.


Tana tsaye ruwan ya tafasa,ta dauko cup ta juye ta dawo falo.




Tana daga tsaye take surbarsa saboda tana ganin kamar zaifi tsarga mata,tana gab da shanyewa taji motsi kamar an buda qofar falon,saita waiwaya a hankali tana dan jin tsoro ya kamata,duk da tasan cewa gidan cike yake da tsaro,babu wani abu da zai gifto su har nan.




A hankali yake takowa cikin parlour din,idanuwansa zube kam wayar hannunsa da yake amsa kiran dake shigowa,wanda handsfree ya sanya mata.


Yayi wani sassanyan kyau cikin wasu yellow din Kaya da sukayi matuqar fitar da sigar kyans da kwarjininsa.


Idanu suka hada shida ita,nauyin daya zuba ciki nata idanun ta hanyar nutsa nashi idanun cikin nata ya sanya ta janye kallonta,yayin da shi kuma yaci gaba da kallon nata yana ci gaba da amsa wayar.


Kamar kowane lokaci da zai dora idonsa akanta,zuciyarsa ta soma masa lissafe lissafe a kanta,baisan yana mata kallon from head to toe ba sam,koda wani ya fada zai iya qaryatawa,maganar amiru ta soma dawo mishi akan canzawarta,tabbas hakane,shima ya gani,ya hango abubuwa masu tarin yawa,kayan jikinta sunyi matuqar amsarta da haskata,baisan yaushe chocolate colour skin ta fara masa kyau a idanuwansa ba,murya can qasa yace


"Bye" yana katse wayar tare da sokata a aljihunsa,har yanzun kaltum dake tsaye yake kallo,wanda taci gaba da tsaiwar ne saboda a ganinta sam bai kyautu ta ganshi ba ta kuma wuce,duk da yadda takejinta a takure saboda kayan jikinta,wanda suka bayyana albarkatun qirjinta qwarai,don ta dauka daya daga cikin brasier din da jawahir ta sako mata cikin kayan.


"Ina yini" ta fada da zazzaqar muryarta ba tare data juyo ba,sautin ya tafi a hankali cikin kunnensa,yadan rage girman idanuwansa kadan


"Kina lafiya?"


"Alhamdulillah" ta amsa shi still ba tare data juyo ba,hakan ya bashi mamaki,tsaiwar me take ta bashi baya haka?,idanunsa saman hips dinta na wasu sakanni,saiya dauke kai,yana sake matsawa zuwa inda take tsayen,yana jin a ransa kamar akwai wani abu da take boyewa batason ya gani ne.


Koda ya qarasa din sai da yayi dana sanin zuwan,tsigar jikinsa ne ta dinga zubawa,ya dauke idanunsa ta hanyar daukan remote yana lalubar tashar da akace masa yau zasu sanya wasan polo live daga Amsterdam lokaci daya kuma yana bata umarnin


"Ki dauko hijabinki kizo muje" babu musu a tsakaninsu,ko wanne ciwo takeji a jikinta ba zata iya masa jayayya ba,don haka ta ajjiye cup din hannun nata da sauri ta juya ta nufi daki,duk da haka sai daya dan bita da kallo kafin ya sake janye idanun nasa yana sakin ajiyar zuciya.


Bata jima ba ta fito ta hijabin sallarta har qasa,ta sameshi ya bawa tv attention,da alamu yana jin dadin kallon,saita saci kallon tvn don ganin me yake kallo haka,a iya dan zamanta dasu ta karanci yana son doki da wasan dokin ma gaba daya,duk da haka haka ya ajjiye remote din ya miqe ta bishi a baya.


Kamar kowanne lokaci shuru ne ya musu rakiya har zuwa makeken kantin zamani,wanda yake maqare da dukka nau'in kayan amfani.


Yadda suke haba haba dashi ya tabbatar mata ba qaramin customer bane,kuma ba qaramin jin dadin zuwansa suke ba da alama,kujera ya samu nan ya zauna,yace ta shiga ta zabi dukkan abinda taga tana so,sai tayi saroro,saboda sam bata taba zuwa ita daya ba,yawanci da jawahir suke zuwa,daga bisani ta fara takawa a hankali a tana duddubawa har tayi nesa da wajen da yake zaunen.


Tayi nisa sosai cikin babban kantin amma haka taketa shawagi,ta kasa zaben wani abun azo a gani,saboda kome tayi niyyar dauka sai tayi tunanin me tsada ne,ta qyale kada taje a lafta masa kudi,saboda nan din ta fuskanci komai nasu kudi ne tsububu a cikinsa.


"Hey baby" taji an fada daga bayanta,saita waiwaya da hanzari,suka hada idanu dashi yana jifanta da murmushi,matashin saurayine wanda a qiyasce bazai wuce shekara ashirin da biyar ba,sanye da qananun kaya,hannunsa riqe da wayarsa,yana da kyau dai dai misali,hakanan kana kallonsa kasan dan gayu ne


"Bari na tayaki zaben,na fuskanci tun dazu kike yawo kin kasa daukan komai" kafin tace wani abu ya karbi dan kwandon hannunta,ya fara duba kayan mata na amfani yana jefawa a kwandon,yana kuma dan janta da hira ta yadda zata saki jikinta dashi.


Sannu a hankali ya fara cika kwandon da kayyakin amfanin mata,saita ci gaba da binsa a baya,duk da cewa amsar kowacce tambaya tasa daga eh sai a'ah.


Sun kusa qarshen layin da suke ciki,kamar ance ta daga idanu ta hangi samir a tsaye daga qarshen line din kayan turaruka,dukka hannayensa zube a aljihun wandonsa,ya kum tsaya qyam ya raba qafafunsa kamar wani soja,babu digon annuri a saman fuskar tasa,sai idanuwa daya kafesu dashi ita da saurayin........




D/Z
49




Wani mummunar faduwa gabanta yayi,saita dakata da bin saurayin,wanda sam shi baima kula da abinda akeyi ba,saboda ci gaba yayi da tafiya yana zuba kayan,har yakai gab da samir daya soma takowa shi kuma inda take yana ci gaba da kallonta.




Gab da ita ya tsaya,taku kadan zai qara su hade da juna,numfashinta kamar zai dauke tayi qas da idanunta,ta kuma qame waje daya tana runtse idanuwanta sanda taga ya daga hannunsa zuwa gareta,daga bisani ta budesu a hankali lokacin dataji motsin daukar cart din dake ajjiye gefanta.


Kusan lokaci guda kowannensu ya sauke boyayar ajiyar zuciya sanda ya kama tsintsiyar hannunta ya riqe,ya fara takawa a hankali riqe da ita suka fara daga farkon layin.


Mamaki ne ya cikata sanda taga irin kayan da yake zaba,kusan duk abinda ya taba ya daukoshi yayi mata choice dinta ne,kaya yake zubawa kamar baisan mutuncin kudinsa ba,tsoro ya kamata,amma daga bisani saita dan sake data tuna maganar da suka tabayi da jawahir sanda ya taba siya mata wani set na man shafawa


"Allah dai ya biya ya saraki,Allah yaci sunansa,ba don yayana bane da tuni nayi wufff da abina,harso nake mu fita shopping dashi,bayajin komai ko meye zaki zaba,ba kamar mummy ba da zata yita mitan zamu qarar mata da lalitarta,yana da kyauta kaman ba gobe,babu ruwanshi"


Nauyinsa ya cikata sanda ya sakar mata hannu,ya bata damar ci gaba da zabar ra'ayinta,shi kuma yana tura cart din kamar wani me aikinta,ya ilahi,ta kasa gano ainihin halinsa,wani lokaci kamar zazzafan mutum,wani lokaci kuma sai taga sauqinsa da sanyinsa yayi yawa,har yayi kamarma ba kowa bane shi.


Sun gama da inda suke suka shiga bangaren undies,kamar ta nutse a waje taji sanda suke ratsawa ta sakanin panties da braziers,sai ta dinga tafiya da sauri da sauri don sunyi su fice a gun.


Danqo hannunta taji anyi daga baya,ta tsaya cak kana ta waiwayo,idanunsa akanta,ya mata nuni da wani abu,saita maida ganinta zuwa abinda yayi mata nunin dashi.


Brazier ce a hannunsa,daburcewa tayi tana dauke idonta,bakinta na dan rawa tace


"Ni...bana sawa" baisan sanda qaramin murmushi ya qwace masa ba,ya yadda da abunda jawahir ta fada,da gaske pretending takeyi,shi yasa zakayi tunanin bata da komai din.


"Wanne size kike sawa?" Dagowa tayi a dan diririce,saiya lumshe idonsa cikin second daya ya bude,saboda wani kyau da yaga sunyi masa a karon farko,sunyi haske sosai,dama can kuma suna da hasken yasan da wannan,amma a wannan karon sun sake kyau saboda girma da suka dan qara yi.


Kai ta sake girgiza masa


"Bana sa......"
Bata ankara ba taji ya fusgota a tausashe,sai gata dan dashi,wanda motsi kadan zatayi ta hade da jikinsa


"Idan na auna da hannuna zan gane ai" ya fada yana daga hannayensa,hijabinta taga ya fara tattarawa tare da qoqarin zura hannayensa ciki,batasan sanda ta cafki hannun nasa ba ta riqe,a rude kuma ta gaya masa number din tana jin yadda mararta tayi wani mugun murdawa,da alamu kuma tsoratar da tayi ya kawo hakan.


Murmushi ya saki ganin yadda gaba daya ta wani rude,sai ya janye hannayen nasa ,amma duk da haka baija baya ba,saiya qara ma matsowa,hakan yasa ya hade gap din dake tsakaninsu,jikinsa na gogar nata,baisan sanda ajiyar zuciya ta kubce masa ba


"Na zaci kinmin qaryar size ne......but ki daina takurewa haka,suna iya lalacewa ko su zube tunda wuri.... brazier is necessary for you tunda kinkai shekarun"




Ji tayi inama qasa zata tsage ta shige ciki ta huta,jikinta ya dauka rawa ta rigashi ja da baya tana dafe mararta data sake murdawa kamar ta tsage,har sai data dan sunkuya


"Are you okay?" Ya tambayeta muryarsa na shaking kadan,dagowa tayi yana gyada masa kai,saiya juya yana duba size din data gaya masan,ya saka iya yanda ya kamata,tana kallonsa ya hada harda pad.


Da qyar take takawa zuwa motar,ta bude seat dinta ta zauna,tana jin sanda ya qaraso shima ya bude ya shiga,baya an saka musu kayan a booth ya tada motar suka fara tafiya,saita cure waje daya,tare da dora fuskarta saman cinyoyinta,tana jin yadda pain ke tasowa daga mararta har zuwa qafafuwanta,wanda dauriyarta ta fara qarewa,harta fara motsi kadan kadan wai ko zataji sauqin radadin.


"Are you okay?"ya sake tambaya karo na biyu,bayan ya fuskanci yadda taketa motsawa,saita gyada masa kai,saidai suna gab da isa gida juriyarta ta qare ta soma fidda qaramin sautin kuka.


"Marata" ta amsa masa


"Ya salam" ya fada yana tsaida motar


"Kin gama shan magungunanki?" Kai ta gyada masa


"Ok...." Ya amsa yana dauko wayarsa,number din dr labaran ya laluba ya kirashi,cikin sa'a kuma ya sameshi,ya masa bayani


"Babu komai,dama hakan na iya faruwa saboda motsawar mahaifa,zata fitar da jinin dake cikinta ne,zan tura maka pain reliever tasha,zata samu sassauci,sai kuma hot or cold water therapy,amma fa,zata iya samun kamar bleeding haka,so she needs somebody else close to her"


"Okay dr, thank you for your help"


"Ba komai" suka kashe wayar,ya maida dubansa ga kaltum wadda batasan ma bayanin da akeyi ba,saiya tada motar yasa kafin su isa bakin pharmacy din ya turo da maganin.


A gaggauce ya karbo magungunan ya dawo ya sake tada motar suka wuce gida,kokaci lokaci yana juyawa yayi mata sannu.


Da kansa ya zagaya ya bude mata murfin motar,yadan matsa gefe don ya bata damar fitowa.


Kasa motsawa tayi,sabida a jikinta take jin danshi,wanda batasan na meye ba,data duba kadan sai taga kamar jini,don haka ta sauke idanunta qasa,ta kuma kasa motsawa.


"Taso" taji ya fada,sai taga hannunshi yake bata,rau rau tayi kamar zata saki kuka,sai kuma ta hadiye ta miqa masa hannun nata a hankali ya dagota,qin motsawa tayi,don tana ji a jikinta ta bata masa seat,tana kuma kunyar ya gani,amma ba yadda zatayi haka ta motsa.


Karon farko ya hangi inda ta bacin,saiya sake mata hannu,ya zagaya ya bude booth din ya zaro ledar siyayyar ya sake dawowa inda take tsaye.


Tafin hannunta ya sanya cikin nashi ya hade yatsunsu waje guda,abinda yasa wani shock a jikin kowannensu kamar haduwar wutan nefa da ruwa,sai yaci gaba da takawa zuwa cikin gidan sannu a hankali tana biye dashi.


*BAYAN AWANNI*




A hankali ta bude idanunta daga nannauyan baccin da yayi awon gaba da ita,wanda batasan yaushe ya dauketa ba.


Ci gaba tayi da bude idanuwan,har sukayi tarwai,saita dan dakata tana duban dakin,take abinda ya faru awanni uku da suka shude suka dawo mata,ashe komai a gaske ne ya faru ba mafarki ba yadda ta tsammata


A hankali ta juyar da fuskarta muhallin daya zauna a dazun kafin bacci yayi awon gaba da ita,wayam yake wajen babu kowa,da alama ya fice ne daga dakin,saita dora hannunta saman shafaffen cikinta zuwa mararta,tana iya jin yadda hannunsa ke yawo har yanzu a wajen,tsigar jikinta ta zuba,saita runtse ido tana girgiza kai,abinda bata taba kawowar faruwarsa ba,wai wani namijin da taba jikinta ba tare data iya hasala komai ba.


A hankali idanunta suka doru kan agogon dake dakin,qarfe shida na safe saura minti daya,da sauri ta miqe,saboda yau din suna da jarabawa,kuma qarfe takwas invigilator din zaizo,sai kuma ta tsaya cak tana wara idanu,saboda canjin da taji a jikinta,sai a sannan ta tuna cewa itama yanzu ta fara period kenan kamar yadda sauran mata keyi,hakan yasa ta fara takawa a hankali ta nufi bandaki.


Tana gab da qarasawa taji an tura qofar dakin,batakai ga waiwayawa ba,hakanan baikai ga magana ba ta gane cewa shine ta hanyar sassanyan qamshinsa,baice komai ba ya koma da baya,a hankali ya mayar mata da qofar ya rufe mata.


Ajiyar zuciya ta saki da taji ya koma din,don nauyinsa ma bazai bari ta iya hada ido dashi ba


"Yanzu bakan kalar pant dina da brazier din da nake boye masa duka ya gani,innalillahi" ta fada tana dafe qirji,bayan tayi tsaye a gaban mudubi,saita kauda tunanin,ta fara cire kayan jikinta.


Wanka tayo gaba daya,sosai taji dadin jikinta,tana shiryawa tana tuna yadda ya dinga treating nata jiya with care,saidai kuma ya haifar mata da feelings da wasu abubuwa masu wuyar mantawa cikin zuciya,saboda wannan shine karon farko da suka taba zama kusa da juna very close irin haka,wannamn shine karo na farko data taba kallon fuskarsa sosai,fuskar da take cike da kwantaccen saje mai duhu sosai,wanda ya qawata ta ya kuma qawara labbansa masu tudu da suka yiwa fuskarsa kyau.




Tsaf ta gama shirinta kamar ba ita tayii fama da ciwo jiya ba,tayi cas cikin uniform din da akullum suke mata kyau kamar kayan gida,tsai tayi gaban madubi tana kallon fuskarta,sai ta sanya hannu tana shafar gefan fuskarta tana jiya yadda yayi.mata jiya,idanunta ta lumshe murmushi yana qwace mata,sai kuma ta bude idanun da hanzari sanda taji alarm na agogon ya buga qarfe bakwai.


A kitchen ta samu su baba,suka gaisa a gurguje,ta karbi wani daga cikin breakfast din daya zama ready ta soma karyawa dashi,baban na tambayarta ya jiki tace mata aita samu sauqi,don babu wanda yasan ma ciwon da tayin a jiyam cikin gidan daga ita saishi.


Tea din data kurba ya tsaya mata a wuya sanda taji tattausan muryarsa na magana cikin kitchen din,cikin girmamawa baba ke bashi haqurin rashin kammaluwar abincin da wuri


"No,no need to worry.....zanyi break a waje" ya furta maganar yana sauke idanuwansa akanta,duk da baya ganin fuskarta yasan cewa itace.


Ajjiye cup din tayi,ta juyo a hankali,kallo daya tayi masa tayi qas da idanunta,yau shigar ta fari ce,suit ce wadda ta amsa sunanta three in one,saidai komai nata fari ne kamar yadda shima duk abinda ya saka a jikinsa yake fari,wataqa hakan yana da nasaba da kasancewar ranar juma'a ce,ba qaramin zama shigar tayi a jikinsa ba,itakam ba zata iya cewa ga wasu kaya da ya saka basuyi masa kyau ba,ba tare data bari sun hada ido ba tace


"Ina kwana"cikin rusunawa


"Lafiya lau" ya amsa mata yana juyawa tare da fadin


"Muje na saukeki,ya kirani ya gayamin bazai samu zuwa yau ba" da sauri ta bi bayansa bayan ya fice tana yiwa baba sallama.


Cikin motar saukar numfashinsu gami da qamshin turarukan jikinsu,jinta take gaba daya a takure,wani kwarjini yake mata matuqa


"Ya jikin naki?" Sai data dan qwato numfashinta sannan ta amsa


"Na samu sauqi" shuru na second biyu ya sake cewa


"Ma sha Allah,but idan kikaji ko kikaga wani abun daban kiyi magana,yace a gaya masa zai duba"


"In sha Allah,na gode" ta furta qasa qasa,kansa kawai ya gyada yana ci gaba da tuqin,amma kuma wani abu yana dawo masa a kansa shima,wanda daga jiya zuwa yau mutuwar jikin da yakeji bata sakeshi ba,har i yanzu babu wani qwaqwwaran kuxari tattare da shi,har ya sauketa makarantar,ta jawo jakarta ta rataya,sai kuma tace dashi


"Don Allah inason inje gidan mummy....." Dubanta yayi


"Kiyi me?,suma daxu sun tafi azare,su biba kawai suka rage"


"Abubuwana na manta nakeso na dauko" kamar ya tambayeta wanne abu sai kuma ya fasa,ya gyada kai yana cewa


"Is okay" hannu ya zura aljihun gaban motar ya ciro kudi ya miqa mata,kudin ta kalla ta kalleshi,ta girgiza kai alamun a'ah,yadan matse fuska kadan yana dubanta


"Jawahir ta gaya min bakya karbar wani abu cikin kudinki na wajenta....me yasa?" Kai ta kada,tana jin zuciyata na karyewa,duk sanda tatuna da cewa ummanta nacan cikin tsananin buqatarsu,sai taji tamkar taci amanarta idan ta karba tayi amfani dasu taji dadi alhali umman nata nacan a wani hali da batasan wanne iri bane


"Ohhhh....na manta fa,bakyason sababbin kudi kudi ko?,to amma fa.....wannan mijinki ne ya baki su ko?" Furucin nasa ya sanyata daga kai da hanzari zuwa gareshi,cikin sa'a suka hada idanu,kunya ta sanyata sadda kai tare da kubucewar murmushin da bata shirya masa ba,sai yaji dadi a ransa,yayi hakanne don yaga murmushinta kuma haqansa ya cimma ruwa,a taqaice yace


"Take it" hannu biyu ta saka ta karba


"Na gode,Allah ya biya" tayi maganar sanda ya sake kunna motar yana gyada mata kai,ta juya ta nufi ajujuwansu.


"Mijinki" kalmar data dinga yi mata amsa kuwwa kenan cikin kunnuwanta,da qyar ta samu ta kori sautin muryar sanda aka

Please Login or Register in order to submit comment