Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

abinda ya shalleta da alama,mamakin jawahir din take,ta yadda batajin nauyi da kunyarsa take gaya masa wannan maganar,duk da tasan halinta dama faranse ce ita,amma ta sanyata jin wata iriyar kunya,wadda ta hanata sakewa har suka isa gidan hajiya qarama.


A falo suka taddata tana zaune tana kallon tafsirin sheik Dr Bashir Usman,gefanta lemo ne da cake a ajjiye,da alama ta fara ci ta ajene.


Da hanzari jawahir ta isa gareta ta zube a cinyoyinta,itama tana dariya ta dora tafin hannunta a gadon bayan jawahir din tana murmushi da murnar ganinta.


A nutse kaltum dake dauke da ledar siyayyar hajiyan tayi sallama a falon,sallamar data ja hankalin hajiyan,ta dago tana amsawa tare da zubawa kaltum idanu harta qaraso,ta zube ledojin a hankali sannan ta zauna ta soma gaida hajiyan.


A nutse cikin yanayi na karantar dan adam ta amsa,sannan ta sake maida kanta ga jawahir kafin samir ya shigo.


Yadda shima ta amsa sallamarsa zuwa gaisuwarsa zai tabbatar maka da cewa ba qaramar qauna bace tsakaninsu shida ita da jawahir din


"Ina waccar mai baqin halin?" Hajiyan ta fada sanda take miqewa zata kawo musu wani abun su taba,saidai da qyar ta miqe din saboda ciwon dake qafarta,kusan kuma shine silar zuwansu gidan su dubata.


"Tana gida hajiya,kema kinsan bazata zo ba"


"Nima bana gayyarta,randa duk taga dama tazo,bari na kawo muku abun sha" sai tayi hanyar kitchen,kaltum ta bita da kallo,wani abu na taba ranta,tana tuna mata da ummanta da nata ciwon dake qafarta,saita lumshe idanunta,tana sauke qaramae ajiyar zuciya.


Batafi minti daya ba ta dawo


"Yau ni nake ganin rayuwa a gidan nan,masu aiki biyu amma babu ko daya a ciki?,dambu fa nace ayi an hada komai amma ya gagara gasucan zube a kitchen?,ke jawahir duba store ki debo muku ruwa da lemo,na fridge dinma ya qare an rasa me zubawa,nikam qafa ta matsamin,bazan iya ba,inajin masu aikin da naqi dai su za'a qaromin din" ta fada tana zama,sai jawahir ta miqe tana cewa kaltum tazo suje,suka miqe dai dai sanda samir ke gyara zamansa yana tambayar hajiyan ina duka 'yan aikin,ya za'ayi a barta haka ita kadai a irin wannan yanayin.


"Baraka dama ta tafi gida tun sheran jiya,ita kuma hansai zata dora girkin kenan akayi kiranta surukarta nakan gwiwa"




Kitchen ne me kyau da tsari sosai,kai baka ce kitchen din babbar mace bane kamar hajiya qaraman.


Tsaye tayi daga kitchen din tana dan kallonsa kallo irin na baqunta,jawahir kuma ta shiga ciki tana debo lemukan


"Zo mu wuce,wadan nan ai sun isa" tace da kaltume


"Jeki kai musu mu dawo nan mu zauna,wala'alla magana zasuyi da ita mu basu waje"


"A nan kuma?,ai akwai wani parlour din,saimu koma ciki" kai ta kada


"Kije dai ki dawo" tunda ta fadi haka tasan da dalili,saboda haka bata sake musa mata ba ta fice,babu jimawa ta dawo


"Tana da couse couse?" Kaltum ta tambayi jawahir


"Eh ba za'a rasa ba" saita gyada kai


"Dauko ko guda dayane na gwada wani ganganci mu gani,naga yana kama da barjajjiyar shinkafa da kuma tsakin masara,ko zaiyi mata dambun"


"Yes,correct.....dama anyin dambun couse couse din ai" jawahir ta fada tana murmushi,sannan ta ake shiga store din hajiyan ta soma laluboshu,babu jimawa ta fito dauke dashi guda biyun ta miqawa kaltum,ta karba ra durfafi inda taga an ajjiye duka kayan hadin ta janyo roba ta fara aikin.




A hankali ta dinga aiki da hankalinta da kuma hasashe na yadda take musu dambu a gida,tanayi tana fagabar kada yaqiyi tunda wannan din ba tsakin masara bane,bayan ta hada komai sukayi tsaye a kitchen din jawahir na mata hira,saidai ita hankalinta duka nakan girkin,da kuma kasadar da tayi daga zuwanta baqon waje,yanzu idan ya lalace baiyi bafa me zatace?.


A hankali ya soma fidda qamshi sosai,qamshin daya cika kitchen din gaba daya,mintunan data bashi kuwa na cika ta duba,saita kira jawahir tazo ta dandana.


Lomar farko ta fiddo idanunta waje


"Wow...wow, you make it kaltum....."sai data sake kai hannu ta debo takai bakinta sannan ta sake cewa


"Kinji dan ubansun dadin da yayi kaltum,ya akayi kika iya har haka?" Murmushi kawai tayi mata tana zaro plate guda biyu,ta cikasu dashi,jawahir ta riqe hannunta


"Haba malama,ya zaki kwashe?,mu kuma fa?"


"Hajiya iya da saura ai,ba duka na debe ba" kaltum ta fada tana mata dariya


"Kikai musu saiki dawo kici" ta fada tana tura mata farantan.


"Wai nikam qamshin girki fa nakeji,ko hancina ne saboda yunwar da nakeji?" Hajiya qarama ra fada bayan ta dakata daga maganar da sukeyi


"Qamshin abinci ne,amma ina zaton iskar kitchen ke kadowa ko,bari na fita nan kusa daku akwai eatery na samo miki wani abun da zakici,kafin a san wadda za'a kawo miki ta zauna miki kafin masu aikin naki su dawo" yana fadin hakanne dai dai sanda jawahir ta fito da plates din a hannunta fuskarta fal fara'a.




Da kallo suka bita har ta iso gabansu,ta ajjiyewa kowa plate din sannan ta bude masa ta sanya masa spoon


"Kuci kuji don Allah" ta fada tana dubansu,duban plate din sukayi hajiya tace


"Meye wannan ne kamar dambu"


"Kici don Allah hajiya.... please yaya kada kace ka qoshi" ta fada tana marairaice masa,basu sake cewa komai ba kowa ya dauki nasa cokalin.


"La'ilaha illallahu....wai dambu kukayi haka a dan wannan lokacin me shegen dadi?" Dariya ta qwacewa jawahir,kafin ta dakata


"Hajiya dambun couse couse ne fa?" Idanu hajiyan ta fitar


"Couse couse dai da nake kallonshi a abun banza shine haka?" Dariya ta basu harda samir daya dan murmusa,dadin abincin shima yana ratsashi,duk da dama shi cimarsa ce couse couse,musamman da vegetable soup liver or kidney soups


"Wallahi hajiya aikin kaltum ne,ni kaina abun ya bani mamaki"


"Ikon Allah,wannan yarinyar dai da kuka shigo tare?" Hajiyan ta fada tana fara kai lomomi bakinta,gardin gyada dana zogale gami da wadatacciyar albasa da kayan dandano na hadewa a bakinta


"Ita"


"Ina kuka samota ne?"


"Na daukota ne daga garinsu" samir ya bawa hajiyan amsa sanda jawahir ke niyyar bude baki tace 'yar aiki ce,kai hajiyan ta kada tana ci gaba da kaiwa cikinta abincin.


Ganin hajiyan ta nutsu da abincin,saita juya ta koma kitchen wajen kaltum don bata labarin yadda ta kaya tana dariyar yadda taga hajiyan na cafkar dambun babu qaqqautawa.




Tana mamakin ta yadda aka sarrafa couse couse haka aka baddan masa da kama.


Tana dab da cinyewa suka fito daga kitchen din,hajiyan ta daga kai tana kallon


"Sannu 'yar nan,sannu da aiki kinji?" Murmushi kawai ta saka,ta qarasa tana daukowa hajiyan ruwan da take yunqurin daukowa hannunta baikai ba,ta bude mata ta miqa mata


"Aini mamaki ne ya kamani,kin samu ladana ba kadan ba" murmushi ta sakeyi tana samun gefe kusa da jawahir ta zauna


"Allah yayi albarka"


"Amin" ta amsa da muryarta qasa qasa,yayin data maida hankalinta ga jawahir dake nuna mata wata drama da ake nunawa.


"Yauwa....yanzu sai nafi fuskantarka,me kake cewa?" Tafin hannunsa yasa ya shafi sumar kansa


"Ba wani magana bane dama,yarinyar da xan aura ne muka daidaita kanmu,so inason shaidawa daddy,nayi magana da mummy sai tace na gaya miki,saiki gaya masa" bakinta ta tabe,kana ta dubi inda su jawahir take,sam hankalinsu baya wajen


"Waini za'a yiwa bariki,da ta zartar kawai ai yadda ta saba....wacece ita ya sunanta?"


"Jauhar ce"ya amsata a nutse bayan yin shuru na 'ya sakanni,tsareshi tayi sosai da idanu


"Jauhar dai,yar wajen murjana?" Ta tambayeshi tana tattara hankalinta a kansa




Kansa ya jinjina mata yana kallonta,saita hade ranta tsaf


"Eh lallai....jidda taci alwashin daga qarshen rauwarka ma kenan itace zata zaba maka mata,to ba zata sabu ba,tunda shi yayan ya zama sai yadda aka juyashi,wannan wacce irin masifa ce ke bibiyar rayuwar raihana har yanzu bata huta ba?"


Idanunsa ya lumshe yana jin sunan har tsakiyar zuciyarsa,yana kuma jin wani abu me daci yana motsa masa,cikin muryarsan nan me cike da nutsuwa yace


"A'ah hajiya...,.ki fahimta mana,babu ruwan mummy a wannan maganar,amma idan baki gamsu ba kina iya tuntubar daddy da kanki" shuru hajiya qaramar tayi tana kuma karantar fuskar samir dake kallonta shima,tsahon wasu sakanni kafin ta gyada kai


"Shikenan tunda har kace haka....idan akwai alkhairi cikin lamarin Allah ya tabbatar,idan kuma babu alkhairi....ina roqon Allah ya watsa abun,ammafa ka sani,wannan ba yana nufin na gamsu duka bane na miqa wuya,daga yanzu zuwa ko yaushe ma,idan na gani ko.naji abinda baiyimin ba,to tabbas babu abinda zai hana a fasa ko a dakatar da komai" kansa kawai ya gyadawa hajiyan,har yanzu baisan me yasa ta kasa so ko jituwa da mummy jidda ba.


Sun dan jima a gidan,don har bayan sallar isha'i,sai da suka jira hajiyan ta kira wadda zata tayata zama,saidai har suka zo tafiya bata qaraso ba.


A sace kaltum take kallon hajiyan,itadai duk yadda jawahir ke cewa mafadaciya ce bata gani ba,hasalima saboda ciwon qafarta sai take jin kamar ummanta,duk wadda ta gani da ciwon qafa saita dinga ganin kamar ummanta


"Don Allah kice ya barni na zauna tunda me zaman bata zo ba" ta radawa jawahir,ta dubi samir ta gaya masa,saiya waiwayo yana dubanta


"Makaranta fa?" Ya tambayeta kanshi tsaye,sai sannan ta tuna


"Kwa dawo gobe" hajiya qarama na murmushi,cikin jin dadin yadda take ta nuna kulawarta a kanta tunda tazo tace


"Allah sarki yarinyar kirki,kada ki damu kinji,mubina na hanya,ba jimawa zaki ganta" da wannan sukayi sallama,bayan ta baiwa jawahir wani abu a leda tace su raba ita ba amfani dashi zatayi ba.


Saida suka shiga motar,samir yana qoqarin tada motar jawahir ta bude ledar


"unbelievable...." Saita saki dariya


"Wlh hajiya nada abun dariya,ta rasa yau kuma me zata bamu sai pad?,to ai wanna ni ta yiwa wannan kyautar,don kaltum ma yaa har yanzu bata fara period ba bare mu raba tare" tayi maganar tana ajjiye ledar gefanta


Kamar motar ta tsage ta fita ta qasanta haka kaltum taji,wai yau me ya samu bakin jawahir ne take ta bare magana haka?


"What?" Samir dake qoqarin tada motar ya fada bayan ya tsaida abinda yake qoqarin yi din


"Me kace yaya?" Jawahir ta tambaya,bai amsa ba,saiya waiwaya gefansa a nutse,ya dora idanunsa kan kaltum


"Shekararki nawa?" Ya tambayeta kai tsaye,tambayar data bata kunya


"Sha biyar" ta amsa masa a hankali,saiya janye idanun nasa daga kanta


"Akwai matsala" ya fada yana tada motar tashi,sannan ya fiddata daga jerin motocin gidan inda ya ajjiyeta,yana qissima lallai akwai wani matsalan,amma bata tadda za'ayi tana da 15yrs ta kasa period.


A komawan ma shuru tayi,saboda kunyar da jawahir ta gama bata,don damuwar maganar biba ma ta fita a ranta ba kamar dazu ba,bayan ta yankewa ranta yin shurun kamar yadda biban tace da ita.




Washegari ita da jawahir suka sake shiryawa zuwa duba hajiyan,bayan sunyi waya da saraki yace shima zaya biyo daga gurin aiki saisu wuce tare.


A falo suka tadda hajiyan,taji dadin ganinsu sosai,ta amsa gaisuwarsu cikin kulawa da tambayar yadda sukaje gida.


Suna tsaka da gaisawa yar matashiyar budurwar da kadanne bata qarasa sa'ar jawahir ba ta fito daga kitchen,hannunta jiqe da ruwa da alama aiki takeyi.


Qarasowa tayi tana dubansu,da alama sunsan juna ita da jawahir,saidai ba wani sanin can can ba,ta zauna kan daya daga cikin kujerun suna gaisawa da jawahir sannan ta dubi hajiyan


"Me za'a dafa?"


"Idan na gaya miki ma me nakeso quiya irin ta 'ya'yan yau ba lallai ta barki ki iya dafamin ba" duban hajiyan tayi,tadan maida bayanta ga kujera ta jingina bayan tayi luu da idanunta


"Kamar kuwa kinsan na gaji,ga baqi mun sake qaruwa,kawai ayi spaghetti jallope" idanu ta fidda


"Wa?,Allah ya sawwaqe,bama ta shinkafa ba saita taliya,nikam ba dani ba,ni ason raina ma na sami lafiyayyen tuwon dawa da miyar kuka" daga jawahir har mubina dariya suka fashe da ita


"Allah ya sawwaqe,haba hajiya me kika rasa da zakici wani dawa?" Cewar jawahir,mubina ta dora da


"Tayani gani dai,wai makaho yaso gulma" baki hajiyan ta sake,kamar yadda kaltum ke binsu da kallo kawai,tana dan qaramin murmushin da bai bayyana a saman fuskarta ba,tausayinsu take da suka jahilci amfanin dawa da har suke ganin baikenta,gayu da gata suka sanya su hasarar alfanu me yawa,tabbas da sunsan amfani da Allah ya zuba a cikinta wawasonta za'a dinga yi,amma abunda ta fuskanta a rayuwar maraya shine,kawai duk gidan da akaga suna cin tuwon masara ko na dawa,to talauci ne yake damunsu,idan kuma masu wadata ne,tofa la shakka za'a lasafta mai gidan cikin sahun mutane masu rowa qanqamo da dan hannu.


Bayanin amfaninta hajiya qarama ta fara musu,amma saita fuskanci basa ganewa,jawahir na dariya tace


"Hajiya,abincin dokuna ce fa?,ita naga ana yamutsawa da wani abu ana bawa dokunan ya samir"


"Me yasa dokunan suka fimu qarfi da lafiya?" Kaltum ta jefa musu tambayar ba tare da tasan ta fito a bakinta ba,dukka sai hankulansu sukayo kanta,saboda funda aka fara maganar batace komai ba kallo ne nata,sai taji wani nauyi,amma kuma haka ta daure taci gaba da magana


"Dabbobinmu wani lokacin sun fimu lafiya qoshi da kuma kitse ajikinsu,saboda muna daukan dusar kayan amfaninmu dama tsabar muna basu,da sunan shine abincin daya dace dasu,mu kuma muqi ci saboda muna neman dadi,bamu damu da kyau ko ingancin abinda zamu ci ba,dadi kawai muke yiwa" sai sukayi shuru suna nazari,zuwa can jawahir tace


"Kuma fa hakaneeee kulsum na yadda dake wallahi" yayin da hajiya qarama ta zuba mata ido,tana mamakin fasaharta da kaifin hankalinta a shekraun da take dasu,duk kuwa da cewa.ba wami abun mamaki bane ga duk mutumin daya rayu cikin karkara,wata baiwar basira hikima da fasaha Allah ke musu,wala'alla kyan nature irin nasu da bata baci da hayaqin kamfanoni da ababen hawa bane,da kuma cimar ganyayyaki da zallar abinci masu gina jiki damu muke musu kallon banza da suke ta'ammali dasu


"To kundai ji" hajiyan ta dora da fada musu,ita dai mubina sam bata gama yarda ba,daga qarshe dai kaltum tace suje ta tayata ta dora girkin,sai gashi sun buge da barwa kaltum din girkin,wanda ita kuma ta sauya akalar abinda sukayi niyyar dafawa ta maida tuwan dawar da hajiya qarama keso,dawarta me kyau kuwa,jar dawa wadda tafi kowacce amfani,niqanta kuma yayi laushi yadda ya kamata.


Sanda ta jerewa hajiyan komai bayan sun gama sallar magariba,hajiyan don dadi kamar tayi me,albarka kawai take sawa kaltum din


"Hajiya mu ba zaki gode mana ba" jawahir daketa kai lomomi bakinta ta fada,don ita ba zata iya tuna when last data ci tuwon dawa ba,don haka ta manta dadinsa ma kwata kwata,saidai babban abun mamakin shine,ashe haka kaltum din ta iya girki?,eh tabbas don girki ummansu ta horesu dashi,tun tana da shekara goma take dora sanwa,shekararta biyar tana girki,girki kuma kowanne irin irin dai wanda suke tu'ammali dashi zata yishi fes aci ayita santi,abu daya ne zuw biyu dama bata iya shi ba,girke girken da tazo ta tarar suna yi na zamani,sai kuma kayan dandano dana qamshi kala kala dasu basa amfani dashi,amma zama da take yawan yi a kitchen yasa ta gane amfanin da yawa daga cikinsu,ta kuma iya sarrafasu,amma yanzun data tashi yiwa hajiya qarama girkin ma,dukka ajjiyesu tayi,tayi amfani ne kawai da komai a gargajiyace,nan ta barsu suna santi,tayi dakin da mubina ta sauka don daura alwalar magariba.




*SAƘONE MAI NAUYI,BUDE IDANUNKI DA KYAU KI KARANTA!!*


*_RAMUWAR SALLAH GAME JININ AL'ADA!!_*


*_Shin kinsan cewa,duk sanda jini ya dauke miki,minti biyar kafin rana ta fadi saikin RAMA SALLAR AZAHAR DA LA'ASAR?_*


*_Idan ya dauke miki minti biyar kafin alfijir ya keto,saikin rama sallar magariba da isha'i ta jiya?_*


*_idan ya rage saura minti uku alfijir ya keto ko biyu ko daya,ba zaki RAMA MAGRIBA BA AMMA ZAKI RAMA ISHA'I tana nan a kanki_*


*_idan ya rage saura minti daya rana ta hudo to SALLAR ASUBA TANA KANKI SAI KIN RAMA TA_*


_wadan nan wajibi ne ki riqe ki kuma ramasu,idan ba haka ba zaki tashi a littafin ayyukanki baabu su_


*_YAYA KIKE QARA KWANAKIN AL'ADA IDAN KIKA LURA DA QARIN KWANAKIN DA JINI YAKE MIKI KAFIN DAUKEWARSA???_*
πŸ‘‡πŸΎπŸ‘‡πŸΎπŸ‘‡πŸΎπŸ‘‡πŸΎπŸ‘‡πŸΎπŸ‘‡πŸΎπŸ‘‡πŸΎπŸ‘‡πŸΎπŸ‘‡πŸΎπŸ‘‡πŸΎπŸ‘‡πŸΎπŸ‘‡πŸΎπŸ‘‡πŸΎπŸ‘‡πŸΎ






45


*_KIJI TSORON ALLAH,ki biya ki karanta cikin aminci,ba tare da kin taba haqqin kowa ba_*


08184017082
Ko
09134848107
_______________________________


Ana gama sallar magaribar daga masallacin layin gidan hajiya qaramar gidan yayo,a qasa yake tattakowa cikin nutsuwarsa har ya kawo gidan.


Sanda yayi sallama falon dukkaninsu ke qoqarin amsa mishi sallamar,amma banda mubina da tayi suman xaune,tana jin jinin jikinta kamar ya daskare ne waje daya ya dauna zagayawa yadda ya kamata.


Babu wanda ya fahimta halin da take ciki,shima duba daya yayi mata ya ganeta,amma bataga alamar haka ba,saiya samu waje ya zauna yana duba hajiya qarama da jiki,yayin da jawahir ke masa sannu da xuwa,gami da yunqurin miqewa da gaggawa tayi ciki itama don tayi sauri tayi sallar kafin yace su fito su tafi,don tasan bayason jira.


Da wata shaqaqqiyar murya mubinan ta gaidashi,tana jin wani iri babu dadi da ganinsa qalau da tayi,don ta gwada kiran wayarsa yafi a qirga amma baya dagawa,ta rasa wacce irin rashin sa'a ce irin wannan,ta mallaki number dinsa cike da fata da burin samun soyayarsa,sai kuma ya datse hanyar da take fata da burin tabbatuwar hakan.


Ganin babu kowa a falon sai ita ya sanya dole itama ta miqe tabi bayansu,saidai dukka wanda ya kalleta yasan jikinta a matuqar sanyaye yake


"Kicewa kalsum tazo ta bawa yayansu abinci....yauma dai ita ta ciyar damu,wadan nan iyayen qyuyar ba abinda suka iya sai abincin bature mara inganci bare qara lafiya" hajiya qarama tace da mubina tana kuma yiwa samir bayani,gami da yunqurin miqewa itama don taje tayi salla.


Sanda take gayawa kaltum din taje takai abincin sai jawahir ta bi mubinan da kallo ganin yadda lokaci daya tayi laushi sosai,yanayinta ya canza.


Miqewa kaltum tayi daga saman abun sallar data kafu a kai tana addu'o'i,kwanakin nan kawai daurewa takeyi tana mazewa,amma ranta damuwa ce fal,tayi kewar gida kamar hauka amma babu wanda ta nunawa,bata kuma da yadda zatayi,kullum da tunaninsu take kwana take kuma tashi,uwa uba kuma ita din asalan da wuya kaga bata kwana gida kusa da ummansu ba,bako ina take zuwa ta tarda ta kwana ba,sai gashi yau wani qaddara ta kawo silar rugujewar zamansi,ta nesantata da gida zuwa wani waje me nisan da tunaninta bai taba dauko mata wannan ba.


Daga nan dakin kitchen din kawai ta wuce ta hado kayan abincin dai da yadda ya dace,don tasan qila samir dinne ya iso.


Tun kafin ta qarasa ta hangeshi yana amsa waya,sai tayi qas da kanta tana takawa a hankali zuwa inda yake zaunen.


"Barka da yamma" ta fada cikin wani yanayi fa batasan yadda akayi tayi magana a hakan ba,wala'alla kodon idanunsa daya zuba mata ne da sukayi mata nauyi?.


Zare idanun nasa yayi daga kanta,don baima san yana kallon nata ba,saiya amsa mata daka yana ci gaba da amsa wayarsa,shida jauhar ne,a yanzun tana jinta kamar tafi kowacce mace sa'a a duniya,ta fara sarewa daga samun samir din kwata kwata,duk kuwa da yadda yayi mata,saiga albishir kwatsam na dukkan dama ta samun mallakar tasa,wannan dalili yasa ta buse wutar mallakar zuciyarsa babu qaqqautawa.


Yadda taga jawahir na masa,saita duqa tayi serving dinsa,bayan ta gama ta yunqura zata miqe sai ya dakatar da ita da hannu yana ci gaba da amsa wayarsa,hakanan ta koma gefe ta zauna tana,ta takure waje daya tana wasa da yatsun hannunta,jinta take wani iri,saboda babu kowa a falon daga ita saishi,sai take ganin kamar ya cika falon shi kadai.


Batasan me yasa a duk sanda zasu kebe daga ita saishi ba saita dinga jin wani nauyinsa,tana auna hakan a ma'aunin girma da nauyin alkhairin da yake shigowa dashi a rayuwarta.


A hankali kunnuwanta ke dauko mata wasu daga cikin wayar da yakeyi,ta fuskanci da mace ne,haka kawai sai takejin wani abu mara dadi a qirjinta,amma tafi ta'allaqa hakan da ajjiyeta da yayi tana suraran sirrinsa,saita qara tsumewa a waje daya,tana ta faman murza yatsunta kamar wadda aka baiwa wannan aikin.


Shi da kansa ya gimtse hirar ta hanyar daukar excuse din zaici abinci,saboda bayajin wani dandano nata ko armashi,ya sauke wayar idanuwansa na sauka kan zara zaran yatsunta wanda ke nuna dukkan alamu na laushin da fatarta keda ita.


Sai da yayi bismilla alamun fara cin abincin sannan ta farga ya gama,a hankali ta gyara zamanta ba tare data iya kallonshi ba.


Hankali kwance yake cin abincinsa,tare da mamakin yadda girkin yayi dadi,dama can ta iya girki ne ko zuwanta ta koya,tunda tazo basu taba wata doguwar hira tsakaninsa da ita ba,saiya jefa mata tambayar


"Ya akayi kika iya girki?"
Ka ta jinjina masa sannan ta bude baki da 'yar qamar muryarta ta amsa masa da eh


"Waya koya miki?"


"Ummana ce" ta amsa masa


"Madalla da umma,tayi qoqari sosai" maganarshi ta sanyata daga kai ta dubeshi,sannan murmushi ya qwace saman fuskarta.


Karo na farko da yaga wadataccen murmushinta irin haka,fuskarta ta qawatu matuqa,ta sadda kai murmushin taci gaba da wanzuwa kan fuskarta


"Na gode" ta fada tana jin dadin yadda ya yabi ummanta,sama sama yake kallonta,yana kuma karantar farincikin dake zuciyarsa dangane da yabon mahaifiyarta da akayi,sa yaji wani abu yana taba ransa sosai akan hakan,harma yaji ya qoshi,duk da dadin da abincin yayi masa,don bazai iya tuna yaushe yaci irin wannan tuwon ba,gidan hajiya qaraman yake samu dama,to ita kanta kwana biyu daya zamana yau lafiya gobe babu sai ta sakarwa masu aikin girkin duka,su kuma bason tuwo suke ba,kamar yadda ya fuskanci mummy bata sonsa,hakan ya sanya ba'ayinsa sam a gidan.


"Tunda kike baki taba period ba dama?" Ya tambayeta kansa tsaye,tadan daga ido ta kalleshi,sai tayi saurin sakewa,nauyi da kunya suka cikata,saita cure waje daya kamar mejin sanyi,ta kasa amsa masa tambayar,murmushin gefan baki ya saki,sabida ganin yadda tayi daga yi mata tambayar,saiya tuna sanda take bala'i lokacin da zata amsa haqqin dan uwanta,duk yadda suke hasashen bata da kunya ashe ba haka bane,abu daya ne zuwa biyu kawai,ita din bata bari a danne haqqinta indai tana da ikon karba,sai kuma zamantowar mutum me qaunar mahaifiyarta da yan uwanta.


"Ki dauko takalminki muje,yanzu zamu dawo,ki gayawa jawahir ta zauna" bata iya tambayarsa ba,sai kawai ta miqe kamar zata harde ta nufi daki,binta yayi da kallo kafin ya janye idanuwansa,yana tuna ganin da yayi mata a dandali ne,a sannan halayyarta ce ta gaskiya kenan?,kansa ya shafa yana ture tunanin gefe guda tare da duban hajiya qarama dake dawowa falon.


"bazan boye miki ba,sonsa nake kuma yayimin.......zaki iya taimakamin?" Wadannan ne kalaman da suka shiga kunne kaltum sanda take shiga dakin,duka sai suka juyo suka kalleta,kanta ta dauke tana nufar inda ta ajjiye takalmanta,ba tare data sak dubansu ba tace


"Yaya yace ki jirashi,zamuje mu dawo"ta fadi mata tana nufar qofa


"Ok,saikun dawo" ta amsa mata tare da maida hankalinta ga mubina,wadda gaba daya ta koma kalar tausayi,bisa kuma dukkan alamu zuciyarta a karye take sosai.


Ta cikin hasken gidan yake hangota yana zaune daga cikin motarsa sanda take fitowa,ya fuskanci bata da wani zafi ko kadan,komai nata tana yinsa ne cikin sanyi,saiya buda gida gaba kafin ta qaraso,ya kuma janye idanunsa ya maida ga wayarsa da tayi qara alamun shigowar saqo.


Sai data zauna sosai sannan ta rufe qofar,ya ajjiye wayar gefansa ya tayar da motar sannu a hankali suka fice daga gidan.


Tafiyar mintuna ashirin suka iso wani guri da tun daga waje yafi mata kama da asibiti,da suka shiga ciki ta daga kanta tana duba rubutun dake maqale a qololuwar ginin wajen,a nan ta tabbatarwa kanta a sibiti ne,tana jin sanda yayi waya da alama da wanda sukazo wajensa yake,kana ya bata umarni suka fito,yana gaba tana biye dashi har cikin asibitin.


Kai tsaye reception suka tsaya,wanda ke dauke da files na marasa lpy a tsare cikin wata kanta,sai tarin computers da suke amfani dasu wajen karbar kudi da bada receipt.


Da mutane a wajen don haka suka dan tsaya daga baya,hankalin samir na ga wayarshi yana qarasa duba saqon da ya samu dazun,daya hannun nasa kuma riqe da key na mota yana dan kadashi.


Tunda suka shigo wajen hankalinta ya dauko a kansa,ta juyo ta kalleshi yafi sau shurin masaki,saidai shi baisan abinda ke faruwa bama.


Kaltum kuwa duk abinda ke faruwa tana kallo,har zuwa sanda tadan matsa kusa dashi,da wata maqalalliyar muryarta dake nuna gayunta tace


"Hi" sai a sannan ya daga kanshi ya dubeta


"Hi" ya mayar mata yana qoqarin maida kansa ga wayarsa,ta yunqura zata sake magana muryar receptionist din ta katsesu


"Sir.....kaine muhammad samir?" Kai ya gyada mata


"Sorry sir.....Dr labaran yace ka shiga office dinsa ka zauna,zaka ha sama ne,daga hannun damanka daki na qarshe a nan zaka samu office dinsa"


"Thanks" yafada yana yin gaba,kaltum tabi bayansa,saidai koda bayan sun gota ta din sai data waiwaya ta kalleta,itama su take kallo,ta sakarwa kaltum murmushi tare da daga mata hannu,saita dayke kanta tana tabe baki,itakam koda a karkararsu tana ganin baiken irin wannan zub da kan,ashe har a nan ma da ake ganin matansu sun waye suma suna irin wannan dabi'ar?.


Tana biye dashi tana mamakin me ya kawosu asibiti?,waye baida lafiya?,kuma.taji ana zancan dr,koshi za'a duba?,duka bata da amsa,saita haqura taci gaba da binsa tana zubawa sarautar Allah ido.


Har suka shiga suka zauna yana duba wayar hannunsa,shuru yaci gaba da ratsa office din,lokaci lokaci tana satar kallonsa,abinda ke fado mata a rai kawai shine....maganar mubina data tabbatar tana da alaqa

Please Login or Register in order to submit comment