Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ta fada hawaye yana sulmiyo mata


"Indai da rai da rabo,watarana zaku gana" kalaman umman da sukazo mata kenan,suka kuma fi yi mata kama da kalaman wanda ke sallamar bankwana izuwa qiyama idan anayi.


Idanunta qyar bisa ga mahaifinta sanda yake sallamata izuwa ga hannun baquwar fuskar da bata taba koda magagin cewa wata alaqa zata hadasu ba,riqe da qullin kayanta da ummansu ta hada mata


"Muje ko?" Ta tsinkayi baquwar murya tana bada umarni a gareta,saita daga jiqaqqun idanuwanta ta dubeshi,ta sauke a hakali ta maida ga bigiren da mahaifinta ya wanzu ashi dazu,wayam yake babu kowa,ta sake duban hanyar da ummanta ta rakota,itama babu kowa sai takun sawayenta,saita sake dubansa karo na biyu,karo nabiyun da zuciyarta ta buga mata da wani irin qarfi,saboda yadda taga fuskarsa a tsuke,cike da wani irin kwarjini da bata taba katarin ganinsa a fuskar wani ba.


A hankali ta fara daga qafafunta tana jefasu zuwa gaba,tana fatan dagasun da takeyi yayi da dai da sunan tafiya,zasu turata zuwa gaba kamar yadda ya buqata,tana iya ji da ganin sanda suka zartata a tafiya,shida amirun da a sannan batasan ko waye ba,taga dai ya qara sauri ya kuma cimma wanda aka kira da sunan mijinta,taga ya kama hannunsa da alama magana yakeasa,saidai bata damu da jin me suke tattaunawa ba,idanuwanta sunfi hango mata zaizayayyen gidansu,da ummanta dake cikin dakinta tana kuka.






35
D/Z


*Littafin kudi ne,don girman Allah idan kin gani karki mana sharing,biya naki ta wadan nan numbers din ki karanta cikin aminci*


08184017082
Ko kuma
09134848107








"Saraki....wai me kake shirin aikatawa ne?,are you in your sense?" Aamir daya riqo samir a rude ya furta yana duban qwayar idanun samir din.


Hannunsa ya zame daga cikin ma Aamir yana dubansa shima


"So kake nace bazan karbeta ba?,so kake nace musu na saketa?,so kake na gayawa wannan rarraunar uwar cewa na saki diyarta kwana daya tal da daura mata aure?,wannan uwar data karbi dukkan qaddarar auren diyarta ga wanda bata san ainihin koshi waye ba?,ko kuma so kake na gayawa wannan dattijon kawun cewa na saki 'yar 'yar uwarsa?,aurenta baya nufin komai...hakanan bazai sauya komai ba"


"Duk da haka.....ta yaya zaia fuskanci daddy prof ka gaya masa ka daura aure ba tare da sani ko yardarsa ba?" Qaramin murmushin da iyakarsa lebe ya saki,don shi kansa yasan murmushin bai kai qasan zuciyarsa ba,shi da kansa yake gina tunanin abubuwan tashin hankalin da xasu biyo baya ya kuma yi musu fenti su fito radau kamar gaske,ciki kuwa harda sake tabarbarewar soyayya da fahimtar junan da yake tattali,wanda tayi qaranci tsakaninsa da mahaifinsa,sakamakon bambance banbamce na abubuwa masu yawa a tsakaninsu,wani sabanin ma baya sanin ainihin abinda ya haifar musu da shi,yakan zo ne haka siddan a wadansu lokutan


"Kada ka damu a abinda zan gaya masa, just wait and see what will happen". Kanshi amiru ya dafe


"Me yasa nayi coursing maka wannan matsalar?,why?" Gajeran murmushi ya sake fiddawa


"Bawa baya wucewa qaddararsa,dama qaddarar tawa ce" itace amsar daya bashi,kafin amirun ya juya zuwa bigiren da kaltume ta wanzu akai tana biye dasu,har yanzu fuskarta shafe da hawaye da qananun majina


"Tana bayanmu ne fa saraki"


"Garinsu ne,ba zata bata ba" ya amsa masa a gajarce.


Shuru ne ya zamar musu babban dan rakiya,har suka riski motocinsa guda biyu dake dakon jiran dawowarsa,tunda taga sun nufi motar ta fara takawa a hankali,cikin tsoro da fargaba,mamaki kuma ya maye gurbinsu gaba daya sanda taga amiru ya bude murfin motar ya shige,shima samir din ya bude daya bangaren da niyyar shiga,sai taga ya fasa,ya waiwayo yana dubanta,xuwa sannan ta tsaya cak maqale da kayanta tana qare musu kallo


"Zoki shiga"yayi maganar yana bude murfin daya motar da tafi kusa dashi,sannan ya sake maida dubansa ga baqar fuskarta,wadda tsabar tashin hankali gami da kuka ya qara mata shining,ga kuma hasken rana dake dukan fuskar tata.


Kanta ta girgiza alamun a'ah,don tanq jin cewa koda sama da qasa zasu hadu ba zata yarda ta shiga wannan abar da taji suna kira da sunan mota ba,hasalima wajen gudu take nema,mutanen da bata taba ganinsu suna yawo dako keke ba a karkarar tasu,amma su suka bude wannan abar mai suna motq zasu shiga?,to shin waima ina suka samota?.


"Ki shiga mu tafi,lokaci yana qure mana" ya fada wannan karon yana dan dava murya.


Da qarfi ta girgiza masa kanta,donta fuskanci kamar bai fahimci na daxu ba,amiru wanda yake kallon duk abinda ke faruwa ta mirror,yana kuma qoqarin boye dariyarsa,kasancewarsa ma'abocin dariya koda yaushe,ya leqo da kansa ta window sanda yaga ta fara takawa da baya da baya alamun barin wajen.


"Saika mata dabara,da alama batasan irin wadan na motocin ba" dauke kansa yayi daga duban amiru,ya maida ga kaltume data fara ja baya sosai da inda suke,ya fara takawa a hankali zuwa wajenta,yana mata bayani ta yadda yake saka ran zata fahinceshi,saidai ko kusa ko alama babu alamun hakan,bisa dukkan alamu ma takowarsa zuwa inda take din qara tsoratata yakeyi,don sai qara hanzari kawai take wajen ja da bayan,daga bisani ma data lura ya fita hanzari,saita juya da sauri zata take,hakan yasa ya rufa mata baya cikin zafin nama.


Taku biyar kyawawa ya cafkota,ya damqi hannunta sosai ya fara tafiya,saita turje tana zubar hawaye tare da roqarsa ya barta ta koma wajen ummanta,kada ya cutar da ita,saiya waiwayo ya kalleta,a yadda tayin,babu wani bayani da zata gane,bata masa lokaci kawai takeyi,ya kalli siriein hannunta,ko ba'a gaya masa ba bazatayi nauyi ba ko na sisin kwabo,saboda haka ya dagata cilak ita da qullin kayanta ya nufi bakin motar yana dauke kai gamida riqe numfashinsa,saboda fargabar kada ya shaqi wani abu da zai sanyashi amai ko ya yamutsa masa 'ya'yan hanjinsa.


Ihu ta saki sanda ya sakata a motar,ya tabbatar idan ya canza mota ya barta a nan hauka kawai zata musu,don haka shima ya shiga bayan ya bada umarnin qara qarfin sanyin ACn dake aiki.


Tsawa ya daka mata wadda ta sanyata curewa waje daya,ya fidda dukka idanunsa waje yana dora yatsansa saman lips dinsa alamun tayi masa shuru,ta kasa koda qwaqwqwaran motsi kuwa,sai kanta data cusa tsakanin cinyoyinta tana rawar dari na tsoro daya cakuda da kuka da kuma sanyin da aka balbalawa motar,tana jin a ranta tata ta qare,ita kuma ta wannan hanyar ce sanadin barinta duniya?,ashe babu nisan tazara tsakaninta da bilalunta.


Wayarsa ya fidda ya kira amiru ya gaya masa su wuce gaba a wannan motar zai tafi,ya kashe wayar ya ajjiye ya fidda iska daga bakinsa


"Inason mu isa gida da wuri" ya bawa drivern umarni


"An gama yallabai" ya fada yana tayar da motar cikin sauri.


Shuru ne ya ratsa cikin motar,babu abinda yake tashi sai sheshsheqar kukanta can qasa,tsahon wasu mintuna,yaja qaramin tsaki yana gyara zamanshi,saboda yana jin kukan a matsayin wani abu da zai sake takurashi.


Tafiyar awa guda da wasu mintuna motarsu tayi parking a parking lot na gidan,ya sanya hannunsa zai bude qofar motar,saiya tuna da ita,ya waiwaya ya dubeta,har yanzu tana zaune a cure waje guda,saika dauka cewa a saman wuta aka azata


"Fito" ya ambata sanda ya bude mata murfin motar,ta daga kai da sauri,idanuwanta suka kan ginin da idan a mafarki ne,banda a zahiri take sai tace gidanta ne na aljanna,aljannar da ake bata labari,to amma wannan kuwa babu ko tantama duniya ce,cikin gidan masu yanka kan mutane,saita fashe da kuka,ta san cewa kwananta ya riga ya qare


"Don Allah kayi haquri karka yankemin kai,wallahi ba laifina bane" ta fada jikinta yana rawa,idanunsa ya lumshe ganin tana neman bashi wani ciwon kan,wannan wanne irin xallar qauyanci ne,saiya bude idanunsa bayan ya saki dogon tsaki


"Kinga....ki fito nace miki,bakiga mutane ba gasunan suna wucewa?,ta yaya za'ayi yankan kai kamar haka?" Sam taqi yarda da zancansa,har sai da amiru ya qaraso wajen,cikin hikima da hilata irin tasa ya fiddota,tana qanqame da kayanta tabi bayan samir,yayin da amiru ya wuce sashensu kai tsaye.


Duk tafiyar second daya ko biyu sai ya waiwayo ya jirayeta,da qyar take daga qafafunta tana saukesu,kai kace tana tafiya ne saman qaya,qafafunta babu takalmi,duk wani motsi tsoranta yake nunawa muraran.


Kallo daya zakayi mata ka hangi zallar isa izza mulki da kuma iko a tattare da ita,dukkansu sun bayyana kansu ta yanayin shigarta,uwa uba kuma yanayin fuskarta dake a hade.




A zahiri jarida take karantawa,yayin da kuma a badini tayi nisa cikin duniyar tunani da kuma lissafe lissafenta da bata so su kaucewa qa'idarta kosu subuce mata,tayi wannan zaman ne mintuna kadan bayan sun gama waya da mahaifiyar jauhar hajiya na'ima,gefanta najwa ce data nutse cikin luntsuma luntsuman kujerun falon,hannunta dake da wayarta tana latsawa,ba kamar sauran lokutan da zaka sameta dauke da tarin takardu ba,wadanda take jin sune tamkar makwafin rayuwarta.


A nutse daya daya cikin ma'aikatan gidan ta shigo,hannunta dauke da babban tray da aka cika shi da kayan shaye shaye da ciye ciye na qwalam sa maqulashe,ta qaraso cike da wani irin nau'in ladabi gaban najwan,taja mata qaramin teburi gabanta ta dora farantin a kai,ta bude duka qananun farantan dake kai,sanna ta tsiyaya mata lemukan har kala biyu kowanne a kofi daban.


"An gama ranki ya dade" ta fada tana ja baya gami a ranqwafawa,duk wannan hidimar da takeyi najwan bata daga kai ko sau daya ta dubeta ba sai da tayi magana.


Teburin gabanta ta kalla kafin ta daga idanunta ta watsawa matar wani banzan kallo,saita miqe ta zauna sosai tana jifanta da kallon qasqanci


"Wai wacce irin kidahuma ce ke zuwaira?,da baka gane komai a kanki,tunda muke dake a gidan nan....kin taba ganin an kawo min wannan lemon?" Idanunta ta runtse wadda aka kira da xuwaira din,tana jin ciwon cin mutunci da cin fuskar da jawahir din ke mata,duk da cewa ba wannan ne karon farko ba,cin fuskar da suke mata kusan asali ya samo,banda akwai dalilin dake ci gaba da xaunar da ita agidan,ba shakka da tuni ta aje musu aikinsu ta huta,ta dan dubi sashen da hajiya jidda take,tana da yaqinin cewa daman ba zata magantu ba,koda najwan tayi abinda yafi haka rashin kyautawa da muni


Dannewa gami da daure zuciyarta tayi


"Kiyi haquri,wacan da kike sha din,babu shi a fridge din gaba daya,har store na duba koda saura amma kuma babu".


"Momy.....ya akayi lemona ya qare?,kuma ba'a kawo wani ba?" Ta fada ranta a bace,fuska a narke,rufe jaridar hajiya jidda tayi,sai idanunta suka shiga cikin na zuwaira,take ranta ya baci,ya murtuke fuska kafin ta janye idanun nata zuwa kan diyar tata,a duniya duk sanda zata kallo zuwaira sai taji wani abu game da ita,wanda har yanxu ta kasa tantance asalin meye shi?duk kuwa da cewa,ta san bata da sauran wani abu da zai zama tarnaqi ga duk al'amuranta,tarnaqin ma ta jima da zame masa shima tarnaqi


"Tsarin yayanku ne,yace akwai lemuka da yawaba store,ana kawosu suna lalacewa,so daga yanzu saisun kai rabi ko fiye da haka sannan za'a kawo wasu" ta qarashe maganar tana daukar wayarta dake ajiye gefe,gefe guda tana jin wani abu yana motsa mata dangane da sabuwar dokar.


Cikin yanayi na masifa da bala'i ta zauna sosai saman kujerar tana sauke qafarta wadda ada take daya saman daya


"Wai wannan wanne irin abu ne momy?,ni da gidan ubana?,amma sai anmin gate kan abubuwan da suka shafeshi?sai kace wata agola ko kare re?,idan bani da gado a gidan a fito a gayamin mana fyn?"ta fadi tana huci,daga zuwaira dake duqe gefe daya kanta a qasa,har momy dake danne danne a waya babu wanda ya daga kai ya dubeta,sai da takai aya sannan momyn ta jefeta da wani irin kallo da yasa ba shiri ta maida wuqaqen data waso,ta maida kallonta ga zuwaira


"Kwashe tarkacenki malama ki mayar,baza'a ci ba" sum sum ta miqe tana debe kayan,cikin qunan rai da baqincikin yadda yarinyar data haifa take mata wannan cin kashin.


Saida zuwaira ta nutsa zuw cikin kitchen sannan mommyn ta ajjiye wayar hannunta,ta kuma gyara zamanta


"Duk yadda kika so al'amuranki suyi kyau.....idan kikayi wasa ba zasuyi ba,koda yaushe ina qoqarin......" Bata kai qarshen zancanta ba sallamar saraki ta cika falon.


Lumshe idanunta tayi saboda faduwar gaba data sameta wadda batasan ta mece ba,cikin sakannin da basu wuce uku ba ta saita fuskarta,sannan ta juyar da fuskar tata zuwa direction din da yake,ta miqe tsaye cak don nuna murna da girmamawarta


"Oyoyo son.... welcome"ta fada tana gyara tsaiwarta sosai,wadda zata nuna maka irin alfaharin da take dashi,murmushi ya aika mata dashi kamar kowanne lokaci,saita dora da cewa


"Hala ba zata kaso yi mana ko?,Allah yasa an gama dukkan ayyukan daka qudira zaka aiwatar din" maganartata ta sauka tare da saukar idanunta saman fuskar kaltume,wadda dukkan wata juriya tata ta qare,saboda tsintar kanta da tayi a makeken falon na alfarma,wanda ita a nata hasashen yafi kama da irin kwatancen da malamansu na makarantar asuba suke musu na yanayin yadda aljanna take


"Komai yazo min ne a qurarren lokaci,inata qoqarin shaida miki tahowata kuma ya gagara saboda yawan ayyyuka"Yakai qarshen maganar yana yiwa kansa mazauni saman kujerar dake daura da qofar shiga falon,ya kuma dora idanuwansa akan kaltum dake shawara tsakanin shigowa ko fita


"Qaraso ciki" ya bata umarni kai tsaye,yana kausasa muryarsa,hada idanun da sukayi bayan umarnin daya bata shiya hanata komawa a guje kamar yadda tayi niyya,ta qaraso daura dashi kadan,ta zame a hankali ta zauna saman lallausan carfet din dake gaban kujerun,tana jin kamar zata nutse saboda tsananin laushi,sai a sannan idanun jawahir yakai ga kaltume,ta zuba mata idanu sosai tana yamutse fuska,ita kuma wannan daga ina?,daga ina yayansu ya debota?,ta yiwa kanta tambayar,saidai babu ikon tambayarsa,saboda tasanshi sarai ba sanin shanu ba.


A nutse momy ta koma ta zauna,saidai har yanzu hankalinta yana kan kaltume,duk da cewa idanunta ba'a kanta yake ba.


Najwa ce ta gaisheshi bisa dole kamar yadda takeji a kullum har cikin zuciyarsa,ya amsa ba tare daya bawa yanayinta muhimmanci ba,ya maida hankalinsa ga momy,ya gaidata ta amsa tana bada umarnin a kawo masa abun tabawa cike da nuna tsantsar kulawa kamar yadda ta saba nuna masa a ko da yaushe,ya tsaida hakan ta hanyar cewa sai zuwa anjima.


"Wannan fa son?" Ta tambaya tana nuna kaltum da baki










36


Hkan ya baiwa najwa damar juyawa zuwa sashen da kaltume ke zaune a rakube,kamar zakace kyat ta zura da mugun gudu


"Mai aiki na qaro muku" ya fada kansa tsaye yana relaxing saman kujerar da yake zaune,yana jin yadda gaba daya ya gaji.


"Me aiki yaya?"jawahir ta fada cikin wani salo me kama da gatsali


"Jawahir......" Momy ta kira sunanta da qarfi
"Na'am" ta amsa tana duban momyn,da idanu ta gaya mata kada ta sake magana,sai taja bakinta ta tsuke,haushi da takaici na cikata,ta taya zai dauko kucakar ya kawo musu gida da sunan mai aiki,gidan ma irin nasu,gidan professor rashid guda,wanda mutane da yawa ke kwadayin yin aiki qarqashinsu,koda an tashi daukar mai aiki momyn nasu saita zaba,ta kuma jarraba mutum ta aminta dashi take dauka,ma'aikatan daba ita ta daukesu ba cikin gidan batajin basu wuce uku ba,shine kawai zai wani kwaso musu kalar qyanqyami,saboda yana taqama da ikon da yake dashi a gidan,qwafa taja can qasan ranta,tana jin sauran qiris ta rushe komai,ta maye gurbinsa,wannan shine babban buri da muradinta,wanda dashi take kwana take kuma tashi.


Da murmushi saman fuskar momyn,tana qoqarin dai daita komai ta dubi samir din


"Banda abinka son....ai kasan tsarin daukan ma'aikata a gidan nan,ko baya ga haka ma professor kasan baya bari a dauki qananun yara kamar haka,banason wannan ya jawo wani sabuwar matsalar tsakaninku fa?".


Numfashi ya fidda
"Babu komai momy,a bata wajen zama,zanyi magana da dadyn"


"Shikenan....."ta fada tana mutstsuka hannaye ta,tana jin wani abu nason kutsawa cikin zuciyarta amma tayi gefe dashi,ta dubi jawahir


"Kuje da ita ki bata daki"


"Kaman zuwaira ke kaisu boys quarters din" jawahir ta fada,sai momyn ta tsuke fuska sosai


"Ba cikinsu zata zauna ba,a bata daki nata na daban" idanu jawahir din ta fiddo,kamar zatayi magana sai kuma ta fasa,mamakin abinda momy ke nufi ya kamata,kamar wata 'yar gida za'a bata daki guda?,miqewa tayi da hanzari ranta a bace ta soma yin gaba


"Tashi ki bita.....meye sunanki ne?" A hankali samir ya bude baki zai amsawa mommyn,sassanyar qaramar muryarsa ta maye gurbin tata
"Kaltume" ta fada da qaramin sauti mara amo.


"Tashi kije ta baki masauki" kamar wadda ciwon paralyze ya kamawa qafafu haka ta dinga ji sanda ta miqe,tsoro baqunta rauni da kuma firgici sukayi mata qawanya gaba daya,tana riqe da qullin kayanta taci gana da bin gurbin da jawahir kebi har suka isa wani kebantaccen corridor me dauke da dakuna manya guda hudu.


Muqullin jiki ta murza ya bude ta soma shiga,tayi tsaye sanda kaltume ke takowa sannu a hankali,kamar wanda ke shiga wuta


"Dalla malama ki shigo,nan ba bukka bace ko rumbu" ta fada cikij tsawa,tsawar data razana kaltume din,saboda haduwa da tayi da tsoro da kuma ganin yanayin dakin da bata taba katarin ganinsa ba,hakan ya sanya qullin hannunta faduwa saman qafafunta,jawahir ta bisu da kalllo kana ta tabe baki


"Ga daki nan,amma ki sani,ba qyaleki za'ayi ba,duk abinda kika barnatar saikin biya,don haka kibi a hankali" ta qarasa maganar tana galla mata harara,sannan ta kewayeta ta fice,ta bita da kallo har zuwa sanda taja mata qofar.


Zafafan hawaye suka sauko mata,wannan rayuwar kuma itace yanzu zata fuskanta,su waye wadan nan da zata rayu cikinsu ne?,me zata tarar,shi kansa wanda aka kira da sunan mijinta wayeshi?,bata da tabbas a kansa bata da tartibin wata amsa guda daya gamsashshiya game dashi,ta juya ta kalli gabas da yamma kudu da arewa na dakin,ta yaya ma zata iya rayuwa a wannan wajen me kama da gidan aljanu?,ko ina glass,da wani abu mai santsi da qyalli,shiba daben sumunti ba,hakanan ba ledar tsakar daki ba,saita zame taja da baya a hankali ta zauna a qasan da batasan na meye ba,kuka na balle mata.




A zafafe jawahir ta koma falon,ta tadda saraki ya fice sai mommyn


"Mommy,ta yaya......" Bata kai ga qarasawa ba mommyn ta daga mata hannu


"Babu abinda kika sani ko kima kika iya sai shirme,wadansu lokutan ina raina hankali da wayonki....." Daga wannan bata sake cewa sa ita komai ba, taci gaba da kankare farcenta data taras tana yi,saita juya ta kwashe wayarta da headphone dinta ta yi dakinta fuuu,mommyn ta bita da kallo,daga bisani ta dauke kanta tana girgiza kai,nan da wasu mintuna tasan zata dawo da kanta,don haka taci gaba da gyaran farcenta.




Sai daya gama sharce kansa sannan ya lalubi undies ya feshesu da turare ya fara sakawa,sai daya gama sawa ya dubi Aamir


"Zamu leqa wajen hajiya qarama,amma sai zuwa anjima,zan leqa company yanzu kafin lokacin tashi yayi,akwai abubuwan da zan dudduba"


"Ba damuwa,inason na leqa mutuniyar" ya fada yana dan kashingida


"Saika nema kuma abokin rakiya,badai muhammad samir ba" ya amsa masa yana qoqarin bude katafaren ma'adanar kayanshi.


Qaramin murmushi kawai Aamir ya saki,yasan halin kayanshi dama,abu daya da bai yarda dashi ba yayi rakiyar zance,yace shiba yaron kowa bane,baiyi,kuma shima ba wanda zai nema yayi masa,kowa ya iya allonsa ya wanke,rakiyar zance ko gulma.


Cikin kayansa ya dudduba,ya fitar da wani lallausan yadi butter color ya sanya,a nan yabar Aamir yayi ɗai ɗai,shi ala dole ya gaji,ba yadda samir din baiyi ya tashi su fita tare ba yaqiya.


Tun tana kasa kunne ko zataji motsi ko gilmawar wani,harta saddaqar da cewa an kawota qare kukanka,inda babu wanda zata ji,babu kuma wanda zai jita.


Duk sanda agogo ya kada saita daga kai ta kalleshi,duk da cewa batasan qarfe nawa yake bayarwa ba,yanayin shigowar hasken rana dakin kuwa bashi da banbanci daga shigowarta zuwa yanzun da take zaune a jikin bago kamar wata qadangaruwa,ya kamata ace taji yunwa,amma tunanuka dake cunkushe cunkushe cikin kanta ya hanata taji yunwar arziqi,sannu a hankali lokaci ya dunga motsawa zuwa gaba,cikin jikinta ta dinga jin yakamata ace tayi salla,koda lokacinta baiyi ba,bare tana ji a ranta ma lokacin yayi qila ma har ya gota,saidai batasan inane zata nufa don daura alwala ba.


Zagaye ta dinga da idanunta harta hangi qofar toilet,ta miqe zuwa qofar sannu a hankali ba tare da tana da tabbacin wane waje bane nan,sai a sannan tasan lallai tana buqatar abinci,saboda jinta da tayi fayau iska na dibarta,ga sanyin wajen da taketa jin ya mata yawa.


Tsaye tayi a bakin qofar,ta jima tana qiyasta ta yadda zata budeta,kafin daga bisani tayi shahada ta soma gwada budewar na wasu mintuna kafin ta samu nasarar turata ta bude.


Bin bandakin tayi da kallo,wanda yafi mata kama da daki,don kaf karkararsu bata taba ganin mai kya makwanci kwatankwacin nan wajen ba,take ranta ya bata cewa wani dakinne mai zaman kansa,kenan babu wajen zub da ruwa bare ta daura alwala?,idan kuma tace zata fita ina ta nufa?,ba zata iya maida kanta inda ta baro dazu ba bare ta koma wajensu ta tambayesu.


Sake qudundunewa tayi a yadda take zaunen,sanyin tiles dana ac na ratsata,wanda batasan sanyin meye ba,sai dan banzan takura matan da sukayi,zuwa wani lokaci cikinta ya sake buqatuwa qwarai zuwa ga abinda zai sarrafa ya bawa jikinta kuzari.


Mamaki qwarai ya mamayeta,wadanne irin nau'in mutanene wadan nan?,masu qarancin karamci?,iya rayuwarta da yadda suka ga ummansu nayi akan baqi sam ba haka bane,duk da kasancewarta mai qaramin qarfi,wadda itama idan aka bata da farincikinta zata karba,amma duk sanda baqo ya shigo gidan,nata ko ba nata ba,saita zuba ta miqa mishi,koda bangaren kawu iliya yazo ba nasu ba,ta riga ta saba da ganin hakan,sai gashi yau ta fada hannun wasu mutane,an yasar da ita a wani daki dake mata kama da qiyama.


Qarfe shida da mintina ashirin ta shigo gidan a gajiye daga makaranta,mintuna goma kenan a gaba suka rage a kirayi sallar magariba,duk da cewa kaita ake a daukota amma hakan bai hanata jin gajiya a jikinta ba,tayi mita tayi qorafi kan a bata mota,amma saraki yace ba yanzu ba,yasan yadda jawahir keda tarin qawaye,kasancewarta mai faran faran da son jama'a,ta haqura da tsarin yayan nata,saboda tasan cewa kome ya tsara a gareta baiyi don ya cutar da ita ba,sai don amfanin kanta,bata kuma damu da kalar motar da najwa ke hawa ba,ta tattara ta barwa lokacin da yayan nata ya zaba mata.


A falo ta zube tana ajjiye takardunta,mommy dake shirin shigewa shiyyarta don shiga wakan tarbar mai gidan da bai mata tsufa ta dubeta


"Yanzu nake shirin daga waya na kiraku,yau dadewar tayi yawa"


"Wallahi momy,yunwa da gajiya,bamu zaci muma zamu kai hakan ba"


"To barkanku tunda kun dawo,saiki shiga ki saka a kawo miki abinci"


"Sai nayi sallah momy,saura 'yan mintuna a tayar,idan naci yanzu kasa tashi zanyi nayi sallar akan lokaci" ta amsa mata tana qoqarin miqewa saman doguwar kujera abinta.


Ganin falon babu kowa saita dauka remote tana canza channel din dake aiki saman screen din tvn dake falon,tare da maida hankalinta ga channel din data sauya.


Sosai program din da take kallo ya dauki hankalinta,har aka tayar da sallar aka idar bata sani ba,motsin shigowar samir da fitowar mommy cikin shigar alfarma ya sanyata miqewa ta zauna,kamar ko yaushe fuskarta qunshe da murmushi takewa samir din murnar dawowa


"Yaya,bari naje nayi salla na dawo naji nasarar da aka samu wannan karon,bamuyi waya sosai ba tunda ka tafi"


"Au,dama bakiyi sallar ba tun daxun?" Tana zura takalminta cikin sauri tace


"Wallahi momy bansan an idar bama" ta hada da mayafinta tana yin bangaren dakunansu da hanzari.


Kayanta duka ta aje sama madubi ta nufi bandaki,saidai ta taras da heater din bandakin nata babu ruwan zafi


"Ya salam" ta fada tana fitowa daga bandakin,ta nufi daya daga cikin dakunan da tasan ko yaushe a gyare su,ba zata rasa ruwan zafi a cikin toilets dinsu ba.


Kanta tsaye ta tura qofar dakin data lura shi daya ne a bude ba tare da wani zato ku tunanin ganin kowa ba,kacibus tayi da kaltum dake kwance a qasa a cure waje guda,tana fidda sautin kuka ta cikin hijabinta.


A matuqar tsorace taja da baya tana shirin bada iska,amma sai tayi ta maza,ta tsaya tana kallon kaltumen gami da karantarta,saida zuciyarta tadan samu nutsuwa sannan ta soma takowa zuwa ciki,ta tsugunna a gabanta a hankali ta dan tabata.


A firgice ta miqe,da alama itama a tsorace take,saita tsaya suna yiwa junansu kallon kallon,tsahon wasu sakanni kafin kaltume ta gyara zamanta ta lumshe idanunta hawayen da suka cika mata idanu suka sake gangarowa


"Me kike a nan?,daga ina kike?" Jawahir ta tambayeta tana ci gaba da dubanta cike da mamaki,kasa bata amsa tayi,saboda mugun qullewa da cikinta yayi


"Keda wa kuka zo?" Ta kuma tambayarta


"Nida wanine,daga qauyenmu" maganar ta daurewa jawahir kai,amma sai tayi gajeran tunani daya sanyata miqewa ta koma zuwa falo.


"Daddy ya saba lokacin shigowarsa yau,ko wani abun ya tsaidashi?" Samir ya tambayi momy.


Fuskarta qunshe da fara'ar nan tako yaushe tace


"Eh....yace min suna da taron jam'iyya,amma tunda na kirashi naji bai daga ba,basu gama bane" agogon hannunsa ya kalla


"Ok"ya fada,yana shirin sauke idonsa daga kan agogon muryar jawahir ta bayyana


"Momy....wace yarinyar ce acan dakin take kuka?,tacemin ita da wani sukazo daga qauyensu,shi

Please Login or Register in order to submit comment