Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


Downloaded from GNOVELS.COM.NG




This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG
to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/gnovels

Twitter : https://twitter.com/gnovels

Telegram : https://t.me/gnovels

[7/17, 3:17 PM] Asmabaffa: https://www.arewabooks.com/chapter?id=6683ec1256566fe605af16a3


🪸MUMMUNAR DABI'A🪸




1-5




Official


By
AsmaBaffa




SADAUKARWA NE GA 'YATA TASNIM




Page naki ne
UMMEETAH MUHAMMAD








BISMILLAH


ALLAH YA KAWO MU FANS, ALLAH YASA MU FARA LAFIYA MU GAMA DA RAI DA LAFIYA.


INA KAUNAR KU MASOYANA INA KUMA GAISHE KU.




JAN KUNNE GA MASU AUDIO,DUK WANDA YA JUYA MIN LITTAFI YA KOMA AUDIO SAI YA SAUKE SHI DAGA CHANNEL DINSA.



*ZINARIYAR MACE⚡*
*Wai shin 'yar'uwa menene matsalarki? zubewar nono, ko kuma rashin kwankwason juyawa a falo maigida ya shiririce ya manta da tibi da matan tictok, menene matsalarki ne? rashin ni'ima ko kuma mugun sanyin da ya yi miki katutu, shin rashin taushin fata ne ko kuma kuraje da tabbani, ko bala'in ramar da ta addabeki kuma babu rashin ci ba rashin sha a gidan auranki, gwaigwayewar gashi ce matsalarki ko kuma kaushi da faso na tafin kafa da bushewar fata, kina bukatar fatarki ta yi glowing kalarki ta fita kuraje su mutu, ko kuma kina bukatar azababbun turaruka da humra tare da turarukan wuta. Na san dai kuna da yawa matan da tumbi ya yi musu karan tsaye ina nufin ya katse muku hanzarin yi wa maigida gwalli da muskuce-muskuce a falo😃 Nesa fa ta zo kusa AL-KUTUBIYYA ISLAMIC MEDICINE sun tanadar muku da nau'in magungunan da suke magance kowace irin matsala da izinin Allah. Babban burinmu shine sha'ani na aure ya inganta a samu daidaito. Muna da.*
Na gyaran nono.
Na sanyi.
Dilka tare da hadin sabulu.
Duk Wani nau'in maganin mata.
Humra turarukan wuta perfumes, original miski tahra 3in1, ciccibi budurwar kaza. Had'addun supplement irin wad'anda ba su da matsala. Maganin Sliming wato narka tumbi. Abubuwan da muke sayarwa suna da yawa, kuma babu asarar dukiya. Muna garin kano kuma muna tura kayanmu kowane gari fad'in Najeria da Nijar har ma da kasashemn ketare. Kai tsaye a tuntu'bemu ta lambobin wayarmu domin karin bayani.
*08089965176*
*07084653262*








Labari
England


Baturiya ce kyakyawar gaske ajin karshe ta zauna tare da zuba uban tagumi tana hawaye da kuka,yara ne maza guda biyu da alama 'yan biyu ne, kyawawan gaske kana ganin su kaga ruwa biyu,hasken su bai kai na turawa ba kuma ya wuce ace na yan Africa ne,haka gashinsu ma da komai nasu gaba daya,zaune suke suna wasa.


Wayarta ce tayi kara" ai da sauri ta daga cikin harshen turancinta tace kazo kasar? wanda ta kira ya tattabar mata cewar nazo yanzu zaki gani,murna tayi tace mutum ya huta da wannan masifa ko na kaisu gidan marayu,yara sun hanani sakewa,ko club bana zuwa dama ni a club ya tsince ni muka yi aure,yazo ya sake ni ya tafi da yaransa Nigeria bazan iya ba.
Tana zaune taji Door bell,da gudu ta mike ta bude kofar ranta a bace,wani matashi ne kyakyawa shima wankan tarwada me suffar kamala da alama musulmi ne,Sunansa ta kira Ali ga yaranka na gaji ka sake ni irin sakin ku na musulmi,bazan iya ba,wannan yaran na gaji da su,ka dinga kawo su hutu,Ali dama ya gaji da wulakancin da baturiyar take masa tunda ta haihu yake fama,nan take ya sake ta, divorce paper ta mika masa yayi signing nan take itama tayi,ya duka gaban yaransa 'yan biyu ya dauke su daya a hannun hagu daya a na dama ya fice daga gidan.


Waye Ali


Ali dan asalin kauyen Jigawa ne wani gari na fulani,maraya ya taso wanda shi kadai iyayensa suka haifa a hannun kakansa namiji ya taso ya girma kafin Allah ya masa rasuwa shima sai yan uwa na kauye,Ali cikin ikon Allah Cirani ya taho birnin kano ya fara kasa lemo a faranti yana bi makarantu makarantu na yara.


A haka ya samu ya shiga University kasancewar ya gama karatun secondary gashi da ilimin muhammadiyya, cikin ikon Allah ya kammala degree dinsa,yana gama bautar kasa wani abokinsa dan gidan gwamna ya bashi babban aiki a mininstry,daga nan Ali ya auri matarsa ta farko uwar gida Asmau, tunda ya auri Asmau bata taba haihuwa ba,sunje asibiti iri iri ance a ita ne baza ta taba haihuwa ba,sabo da wannan dalili ya kara aure ya auri matarsa ta biyu Nadia, shekarar Nadia daya ta haifo Danta namiji kato kyakyawa da shi,yaci suna Adnan,Asmau ba ruwanta ita ta fawwalawa Allah murna take, mutuniyar arziki ce,ita kuwa Nadia tunda ta haihu sai bakaken magana,bayan ta yaye Adnan ta sake haifo Danta Ibrahim sai yarta mace Amal, tun daga sannan kuma bata sake haihuwa ba itama har aka kwashe shekaru uku.


Ali kuwa Business ya fara gwadawa yana hadawa da aikinsa na gomnati,kamar wasa sai ga Ali ya zama hamshakin me arziki har ta kai bazai iya aikin gomnati ba kawai ya bar aikin,bashi wannan kasa bashi waccen,ya koma hadaddiyar GRA a cikin garin Kano.


Ya mallaki kadarori na gasken gaske,har gidajen mai ne da shi state state,Ali Sa'ad ya shahara wanda duk Nigeria an sanshi,yayi fice sam har iyalan nasa basu fiye zama a Nigeria ba sai dai suzo da yawo, ganin yaransa sun dan fara tasawa sun isa a sasu a secondary school sai suka dawo Nigeria garin kano gaba daya.
Yayin da shi kuma yake fita kasashe a inda yaje club yawon bude idonsa ya hango halley baturiya ce usul kuma ba musulma ba,suka fara soyayya cikin kankanin lokaci aka daura musu aure,shekara daya Halley ta haifo masa yan biyunsa kyawawan gaske suka ci suna Sohail da Sahil.


Sai dai an samu matsala bayan sun shekara sun fara tasawa sai aka gano daya a ciki wato Sohail ba lafiyayye bane daya ne lafiyayye,daya kamar dan ruwa haka yake abubuwansa,gasu bulbul da su kuma kusan kansu daya Sahil yafi tsayi da kadan amma banda wannan basu da banbanci,ba kowa ke gane su ba ma.
Daya daga cikin Dabi'un Sohail kuwa shine idan aka bashi abinci baya ci sosai sai wasa,sannan sai anga ya girma shima kansu daya da Sahil sai kawai a wayi gari aga ya rage girma ya sake komawa yaro,ana sake tashi washe gari sai aga ya dawo ya zama kai daya da Sahil,har suka fara cin abinci da kansu,idan aka zuba musu shi Sohail sai ya dinga wasa da nashi ya juye a kasa yana wasa a haka sai ya zana zero 0 da abincin nasa.


Idan kuma ruwa zai sha sai ya samu wuri me rami ko dan kurmi sai ya juye nasa a ciki ya kafa baki ya fara sha,wannan Dabi'ar ta Sohail yasa baturiya Halley ta gaji ta bawa uban su yaransa baza ita iya ba ita kam.


Bayan sati biyu da yaransa Ali ya sauka a Nigeria Kano driver da escort suka dakko shi motocin da suke take masa baya sunfi biyar har zuwa katafaren gidansa dage wata sabuwar GRA,yaransa suna hannunsa su biyu har part din uwar gidansa Asmau ya taka,cikin shigarta ta alfarma ta sha material me tsadar gaske ta harde kafa daya kan daya tana kallon film,murmushi tayi ganin mijinta ya shigo ta mike tare da karbar yaran su biyu tace yarana sun iso,murmushi Ali Sa'ad ya saki ganin Asmau bata da matsala ko da yace zai karbo yaransa daga wajen baturiya ya bar mata tayi na'am har da murna kamar ita haife su sai zumudi take itama tayi yara har yan biyu.


Wata Allah ya bata bata so sun ishe ta ga wata tana murna an bata kyauta wanda ba ita haife su ba,Sohail ne yake ta faman rikida yana wani haske yana duhu kuma,Asmau ta kalle shi sosai tace kai wannan sai kace Nepa ana wal-duf,Ali yace wlh nifa wannan yaron ina tunanin daya dan ruwa ne,Asmau tace haba dai inshaallah ba haka bane,tace bari naje na kula da yarana kaje ka huta yau Amarya ke da kai ni nayi yara,Murmushi Ali yayi yafi so ace kwanan Asmau ne yafi zumudi sabo da Asmau ta musamman ce.


Juyawa yayi ya nufi part dinsa,Asmau kuwa tuni ta wuce bedroom dinta da yaranta 'yan biyu.
A ciki ta shirya abinta ta musu wanka dake sun san da zuwan su komai an tanada har kayan wasa, cikin fararen kaya ta shirya su tsaf abinta sannan ta kawo madarar yara ta hada ta fara basu suna sha,Sahil normal yake shan nasa amma Sohail hannu ya sa ya fisge tasa da karfi,Hajiya Asmau taji kamar babba mutum ne ya kwace sabo da yanda taji karfi sosai an fisga,kallon Sohail tayi tace sai kace Daddy dinku ne ya kwace abu irin wannan karfi haka,tana mamaki a ranta, sai taga yaki sha sam yana ta kalle kallen wurare a palon.


Rarrafe yayi ya wuce yaga babu wani waje me rami ko kwurmi a hankali ya dafa jikin kujera ya mike yana tafiya da kyar ya fice daga palon yana fitowa ya hango wani dan kwari inda akwai flower a wajen a nan ya juye madararsa ya kafa baki yana sha,Haj Asmau tana binsa a baya tana kallo,abin ya fara bata tsoro kuma.


Abinda ya kara girgizata shine bayan wasu kwanaki katsam ta nemi Sohail ta rasa,hankalinta ya tashi matuka ta shiga kitchen tana shiga ta iske shi a cikin bowl din gasarar koko da ta tace yana ta wankansa a ciki,duk inda yaga laima ko danshi sai ya tafi ciki ya zauna.


Kishiyarta Nadia ita kanta tsoron Sohail take gasu kyakyawan gaske,Yaranta sune manya Adnan ya kusa gama Jss3 shi kuma Ibrahim yana Jss 1,Amal tana primary 4.
Gaba daya Adnan bakin hali ne da shi shine wanda gaba daya ya tsani Sahil da Sohail,ko kulasu baya yi sannan ya hana 'yan uwansa su kula su ko da wasa,itama Nadia amaryar Ali haushin yaran yan biyu take ji sabo da ta gama sakankancewa itace kadai zata ci gado idan mijinsu ya mutu tunda Asmau bata haihuwa,ji take kamar ta kashe yaran ta huta sabo da tsana,duk da haka wani dadi take ji da Allah yasa daya dan ruwa ne ba lafiyayye bane,ita gani take yi Dan ruwa ne ma Sohail,shi yasa bata kallonsa a mutum sam,idan ta kalle shi ma sai dai ta dinga tuntsira masa dariya haka kawai.

Bayan wasu 'yan shekaru har Sohail da Sahil suka girma suna magana suna gudu ko ina har suka kai matakin zuwa makaranta,ba karamin wahala Asmau take sha da Sohail ba sabo da barna da wasa tare da lalata waje kamar aljani haka yake, maimakon yana girma aga ya canja sai abin ma ya kara rikicewa inda ya fara dalalar da yawu,kullum cikin dalalar da yawu yake, wannan yasa Mahaifinsu ya fara kaishi neman magani wajen malamai amma ba a dace ba duk sun ce ba aljani bane mutum ne,gaba daya Sahil ya fishi girma shi Sohail sai sun girma tare sosai kawai sai a wayi gari aga ya dawo wani yaro shi kadai.


Yau ma haka ce ta kasance Asmau tana ta murna Sohail ya dawo kai daya da Sahil komansu kai daya,kawai yau da sassafe sai gani tayi Sohail ya dawo yaro tafiyar ma da kyar yake yi ,a haka suka hakura aka sasu a pre nursery, Sahil yana da basira da ganewa shi kuwa Sohail kullum sai bacci yake yi har a gama karatu yana bacci,amma da ance an tashi an kada kararrawa zai tashi a bacci bazai sake bacci ba.


Malaman dama an sanar musu haka suke kyale shi, tare ake kaisu school da su Adnan a dakko su,kudin makaranta ma Adnan ake bawa a hannunsa ace ya raba musu su yaran kasancewar shine Babba,Adnan idan ya tashi sai kawai ya bawa iya yan uwansa wanda suke uwa daya uba daya ya hana twins nasu,haka zasu je school suna kallo ana ta ciye ciye na kayan yara amma banda su sai dai su zauna a class,gashi shi Sahil baya wasa wani silent ne baya kula kowa,Sohail shine sarkin wasa amma bacci baya barinsa yayi wasan indai a makaranta ne.


Watarana 'yan biyu sun kara wayo suna primary 2 Sahil ya gaji ya samu Mama Asmau ya fada mata yace Mama Yaya Adnan bai taba bamu kudin school ba muna kallo ana siyen alawa mu bamu da kudi,Asmau tayi murmushi tace to kuyi hakuri kunji ta basu hakuri,tun daga ranar take musu abinci suna tafiya da shi sannan a jakar su ta zuba musu alawoyi da biscuits,amma Adnan yana ganewa sai ya dinga kwace jakar yana kwashewa ya bawa kannensa.
Abincin ma ya kwace ya zubar ya basu flasks dinsu haka,nan ma Sahil ya gaji ya fadawa Mama Asmau.
Ranta yayi mugun baci amma ta danne ta basu hakuri ta canja sai ta dinga bude tsakiyar littafinsu tana sa musu kudi a ciki na break a haka suka tsira suke samu suna siyen wani abin.


Gaba daya Adnan da Mahaifiyarsu Ummi Nadia sun sawa sauran yaran tsanar su Sahil basa kaunar su ko kadan shi kanshi Daddyn nasu Ali Sa'ad bai damu da su Sohail ba,ganin kamar ba mutane bane,ba ruwansa da su komai sai dai su Adnan.


Ana wannan har su Sahil suka isa aike sosai ana aiken su su siyo abu a kanti,duk sanda aka aiki Sohail to baza aga dai dai ba,yau Asmau ta fito zata aiki Sahil ta iske jikinsa yayi zafi yana zazzabi tace kai Sohail zo na aike ka,yaje ya karbi kudin,tace kayan miya zaka siyo min,me nace? Yace kayan miya,tace good boy tattasai tumatir da attaruhu na dari biyu saura naga ba dai dai ba sai na zaneka yau.
Har ya fita tana nanata masa kayan miya zaka siyo ya fita yana gudu,amma yana fita bakin gate yaci birki ya fara tafiyar sangaya kamar bazai tafi ba yana wasa da kudin,sai da ya kwashe 30mnt bai je ba,yazo kusa da masu kayan miyar sai ya hango anyi ruwan sama ya kwanta a tsakiyar titi,cikin ruwan yaje ya shige yana ta wanka,kowa in yazo da mota sai dai yayi dariya ya kauce da motar ya wuce a nan ma ya shafe 1hr yana facaka da ruwa wanda duk jar kasa ne jajir da ruwan,sai da ya gaji sannan ya fito ya tafi siyo abinda aka aike shi.


Ance ya siyo kayan miya amma sai ya tafi wajen me abarba da kankana yace a bani kayan marmari,ai kuwa aka yanka masa kankana da yawa a leda aka hada masa da abarba itama a yanke aka bashi ya juya ya nufi gida,a hakan ma a hanya sai da ya nemi bishiya ya kwanta a wajen ga ledar kankana a gefe sai da ya sha sanyinsa sannan ya tashi ya koma gida,lokacin Mama har ta gaji ma tayi shinkafa da wake abinta,sai gashi ya dawo jikinsa jajir da ruwan kasa ga ledar kankana ce da abarba a ciki,bakin ciki ya kama Mama,duk hakurinta sai da ta zane Sohail da tsinken tsintsiya,ranar kuwa kwana suka yi basu yi bacci ba yana ta kuka yaki dainawa kamar an kunna inji,har Alhaji Ali sai da yazo cikin dare yace Asmau ke da yaran naki ne? tace wlh nayi danasanin dukan Sohail wannan masifa har ina kai Allah ya shirya,Murmushi yayi haka suka kwana ba bacci,Sahil ne kawai yayi bacci sabo da yaro ne.


Bayan su Sahil sun gama primary school abin mamaki ba abinda Sohail ya iya amma a jarabawa shine yake zuwa na farko komai sai ya cinye tas sai dai Sahil yazo shi na biyu duk kokarinsa,tun ana mamaki ma har andaina.
A haka suka shiga secondary school lokacin Adnan yana university a England can aka kaishi,Ibrahim ma yana shirye shiryen Tafiya can,Amal kuma Alhaji Ali yace mace ce kawai tayi karatunta a Nigeria ita da kasar waje sai da yawo.


Nadia Amaryar Ali idan taga Sohail kawai sai ta dinga sheka masa dariya haka kawai,har baya so ma ya ganta yaron ganin yana dalalar da yawu da girmansa dan secondary guda amma yana haka,gasu Iya kallonka baka taba hango muninsu sai dai Sohail rikida yake yau sai a wayi gari aga yayi dan duhu ko aga ya koma kamar bature sak ko watarana kawai aga ya dawo wani yaro sosai.


Sai da suka shiga ss1 yau suna aji malamai sun gaji da baccin Sohail gashi sai ya dinga cinye jarabawa sai suka daina daga masa kafa da anzo ana koyar da su kullum sai an masa tambaya an tashe shi komai baccin da yake amma ana masa tambaya sai yace shi ai bai dade da shiga school din ba jiya jiya aka kawo shi.
Yau ma wani malami ya gaji yana zuwa ya tashi Sohail ya mike tsaye yana murza ido,yace what is a Noun? Sohail yace ai sabon zuwa ne ni jiya aka kawo ni,malamin ya fara masifa yace tun pre nursery kuke a makarantar nan kace jiya aka kawo ka? yace ae ni wlh jiya aka kawo ni ya kwabe fuska zaiyi kuka,dole aka kyale shi.


A cikin class din kuma farin jini ne da su Sahil sabo da kyawun su ana mugun kaunar su duk makarantar, akwai wata yarinya Zayna a class din ba wanda take so ita sai Sohail a duniya,har tissue take zuwa da ita kullum ta gogewa Sohail yawun bakinsa watarana idan yana dalala,Sahil kuwa bashi da sakin fuska ma gani yake yafi uban kowa a duniya duk da yana da kyawawan dabiu haka Allah yayi shi sai ka rantse girman kaine da shi.

Ana haka a ss1 Sohail ya tsiro da wani abu duk macen da ta fara irgen dangi ko jinin Haila sai kawai aji a bakinsa ya tona asiri ya fada da karfi a class din sai kowa ya sani, budurwarsa Zayna ita ba abinda ta fara na nuna alamun balaga a tare da ita sai gashin hammata,yau tana zuwa aji kowa yayi shuru ana jiran shigowar malam tazo ta zauna a kusa da kawarta,Sohail ne yayi magana da karfi kuma da Zayna Isma'il ta fara gashin hammataaaaaa.....aji aka barke da dariya ana kallon Zayna,kunya ta lullube Zayna ta fada kasan sit ta buya,Sahil yana jinsu ko magana baiyi ba.


Malam ne ya shigo nan take Sohail ya fara baccinsa abinsa har aka tashi yana bacci,sannan Sahil ya tashe shi suka wuce driver yazo daukan su,Amal yayar su tana motar tana wani daure fuska suka shiga ciki driver ya ja suka tafi,Amal ta samu Sohail ta talla masa mari haka kawai tace shegu yan iska kunki fitowa da wuri muna ta jiran ku,Sahil kuwa ransa ya baci ba zato ya saukewa Amal mari a fuska,kumatu ta dafe tace Sahil ni ka mara? Yace an mare ki so what? Who do you think you are? ko yaushe sai dai ku zage mu ku dake mu,me muka yi muku,idan kin yiwa Sohail ya kyale ki ni bazan kyale ki ba,Sohail yana kallon su yace ku chasu arna ku chasu,shi da ake tare masa amma ko a jikinsa.


Suna Isa gida Amal ta fito ta samu saurayinta na university dinsu yazo wajenta shima dan gidan me kudi ne,suna fita wajensa ta wuce,Sohail yana zuwa zai wuce su yace saurayin Aunty Amal ai Auntyn m Jinin haila take yi yau ya wuce abinsa,Amal ranta ya baci kuma da gaske Sohail yake tace wlh idan na dawo ciki sai na lahira ya fika jin dadi,ciki suka wuce aka barta nan saurayin yana murmushi ya zaci lafiyayye ne Sohail yace ashe kina off,ya aka yi yaro ya gani,kwana nawa kike yi? Amal duk taji kunya ta share zancen.


Ai kuwa tana gama sallamar bako part din Mama Asmau ta nufa a fusace,Mama ta kalleta suna palo tare da yaranta tana biya musu karatun Qur'ani gobe suna da hadda,lafiya ke Amal ko sallama babu? Zuwa nayi naci uban yaran naki ta furta da tsiwa tana fisgo Sohail,Mama ta janye Sohail tace wlh kina taba min yaro saina kwashe ki da mari tunda baki da kunya.


Ae bani da ita ai bake kika haife su ba juya ....karaf a kunnen Alhaji Ali Daddy me shirin shigowa yana jin haka ya karaso ya cafke Amal babu bata lokaci ya hau jibgarta sai da ya mata lilis babu wanda ya kwace ta,yace idan uwarki ce zaki fada mata haka? Matata ita ba uwar ku bace? Amal tana kuka tana bada hakuri, da kyar ya hakura ya kyaleta ta fice da gudu kuwa.
Matarsa Asmau ya bawa hakuri,tayi murmushi tace ba komai fa Allah dai ya shirye su,duk Adnan ne ya koya musu.

Bayan shekaru biyu Su Sahil suka gama Secondary school dinsu,sun wani tasa sun girma sun kara kyau,lokacin kuma Sohail Allah ya yaye masa dalalar yawu tuni,ya daina abubuwa da yawa duk ya daina ya zama cikakken mutum amma fa akwai shirme,kana ganin yanda yake abubuwansa kasan kansa yana fisga, sai dai an daina wasu abubuwan manya wanda hakan ba karamin dadi yayiwa Asmau da Ali ba, idan yana abubuwa a rikice zaka san lallai fa wani abu na damunsa,a hankali shima Sahil kawai rana tsaka kansa ya fara tabuwa irin na Sohail,yanda Sohail ke shirmen shima haka yake yi, iri daya suke shiriritar su da Sohail,Asmau ta damu sosai tayi tayi Alhaji Ali ya tsaya a nema musu magani sosai amma yaki sam,ganin ma a haka basu da kokari basu san komai na duniya ba sai dai result kawai a school me kyau sune suke daukan na daya,amma idan ka tambaye su abu daya baza su iya fada maka ba,har shi Sahil din duk kokarinsa yanzu babu ya gudu bai san komai ba,shi yasa sam Alhaji Ali mahaifinsu bai damu da su ba.


Yana ganin ba abinda zasu iya tsinanawa a rayuwa kawai dai a basu ci da sha,ganinsu yake kamar ma ba mutane ba,komai baya sawa da su sai dai yaran Nadia sune mutane,ya dauki su Sohail ba wasu mutane ba,Asmau tun tana fada masa gaskiya har ta gaji,zai basu sutura ci da sha shike nan,su Ibrahim kuwa har kasuwan ci yasa ake koya musu suna gama school zai basu company guda shi da Adnan.
ita kuwa Nadia dan dalalar yawun ma da Sohail ya daina sai bacin rai take da Sohail ya samu lafiya,duk shirmen da suke bugawa shi da Sahil a haka cewa take lafiya suke.


Yau ma Mama gani tayi sun sha wankan kana nan kaya abinsu abinka da kuruciya,sun sha kyau kamar a sace su,tace ina zuwa kuma? Sohail yana daura agogo shi a dole shege yace filin ball zamu kalli wani match yana yarfe hannu,Sahil kuwa turare ya fesa yana wani jiji da kai,Mama dariya tayi kawai tace to a dawo lafiya manyan yara,suka amsa da Ameen,tace banda driving driver ya kaiku please,suka ce to sannan Sohail harda yiwa Mama kiss a kumatu ta make shi suka fita suna dariya,amma yanda suke kalle kalle da wuri wuri kasan ba lafiya kansu da tabi.


Driver ne ya kaisu har gidan su Zaynah suma katafaren gida a hadaddiyar unguwa,tasan da zuwansu ta sha gayunta,yanzu tunda sun gama secondary ana barinta tana zance,fitowa tayi sanye cikin doguwar rigar material,har ga Allah bata gane waye Sohail ba waye Sahil ba yau ta kasa ganewa sai taje ta rike hannun Sahil,Sohail yayi murmushi yace ke kin ganni nan tunda kema bakya iya

Please Login or Register in order to submit comment