Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

zauna a palo tana kallon tv,sai taji karar takalmi me tsini ana sakkowa daga sama ,Kamshi na mamaki ya mamaye palon.


Zayna ce take sakkowa ta sha wata material gown ready made abinta golden ta tsula kyau,kana gani kasan taji hutu da kudi ba karya,Maheera tsabar tsananin kyawunta yasa duk inda mace takai bata isa ta fita ba sai dai daiku tunda a duniya baka rasa wanda ya fika dole ne wannan.


Zayna wani kallo ta bi Maheera da shi sama da kasa ta ganta sanye cikin material silk black me adon flower pink sai dan mayafi siriri data dora a kanta,takalminta normal dai na talaka me dan kyau gashi nan dai,sai dai kyawun Maheera ya tsoratata amma ganin mijinta yana da class kuma sannan yana sonta gashi ma shi sai me kudi yake kulawa sai kawai ta fuske a ranta tasan itama me kyauce komai da namiji ke nema wajen mace tana da shi.


Maheera mikewa tayi tsaye da sauri tace good day Ma,Zayna ta wuce Dining kawai ta zauna ba tare da ta wani amsawar kirki ba,Ibrahim ne ya fito yayi arba da Maheera ya bita da uban kallo ya dauke kai ya wuce Dining ya zauna,shima tace Good day Sir, har tana risinawa,hannu kawai ya daga mata,Adnan ne ya fito shima yana zuba kamshi ya hade cikin kana nan kaya masu tsada blue, ko kallo Maheera bata isheshi ba ya zauna a Dining,sai ga Sohail shima ya fito sanye cikin gajeren wando da riga singlet da bocket da mopper a ciki ya hada uban zufa.


Hannunsa ya goge da karamin towel ya karaso wajen Maheera yana murmushi yace kiyi serving nasu cikin rada yayi maganar.
Maheera ta karasa da sauri tana cewa kuyi hakuri" nan take ta fara serving nasu har ta gama,suka ga girki sharr tun a ido ga kamshi.
Ibrahim ne ya riko hannun Maheera zata juya yace zo ki canja min Spoon 'yar kauye.
Tsoro Maheera taji akan idon Sohail aka yi,daga haka Sohail kawai idonsa ya canja ya nufi Ibrahim gadan gadan ya sa baki a saitin keyarsa ta baya ya gartsa masa cizo sai da wajen ya fashe,Ibrahim ya saki kara da ihu ya mike zasu yi kokawa da Sohail!
Adnan yayi sauri ya rike Ibrahim yasan yana hada jiki da Sohail sai buzunsa karfinsu ba na mutane bane,yace kyale shi kai zaka biyewa mahaukaci,abin kullum karfi yake fa sun fara duka da cizo nan gaba sai tsince tsince a bola suna bin yara da gudu.
Zayna ta tabe baki tace yo ni da suka ce zasu aure ni su biyu ma.
Sohail yace in Allah ya yarda baza ki haihu ba,mahaifarki ta mutu a haka zaki gama aurenki,Adnan yace ameen da sauri kayi addua me kyau dama ni bana son haihuwa, Zayna kamar zata yi kuka tace da Sohail mahaukaci karya kake,Maheera tana ta kallo ta gaji ta janye Sohail tace relax mana ta jashi suka koma gefe suka zauna,Sohail yace da Sahil ne ya rikeki da sauki bazan damu ba ai wannan ba yi bane,kawai a rike mutum idan kika masa ciki fa,Maheera ta danne dariyarta,tace au ba ma shine zai min cikin ba nice zan masa? Ina ka taba ganin namiji ya haihu?
Sohail yace ke wancen kwarto ne tsaf zai iya haihuwa,tayi murmushi kawai tana boye dariyarta.
Kallonta yayi yace ki dinga rufe wannan chakare din naki ni bana son ganinsa duk sai gani ake ta yi Mama fa Hijab take sawa idan zata fita ba a ganin nata,badan ma mama ce ba ai sai nace miki bata da Chakare din nan.
Amma ke kowa sai gani akeyi haba Allah za a daina ce miki Classy girl me shago kawai yafi dacewa dake,Maheera ta rufe bakinta sabo da dariya.


Can gefe kuma su Zayna sai kwasar girki suke yi me shegen dadi suna ta ci,Adnan cikin santi ya kira Maheera da hannu,ta karasa a nutse yace aikinki yayi kyau na daukeki aiki,zan dinga biyanki dubu dari,tana murna tayi ta godiya abinta yace gobe ki dawo nan da zama ki fara aikinki,ga Sohail nan zai nuna miki room dinki,tace na gode Sir na gode ta juya ta fice.
Ibrahim sai duri yake ko kala bai ce ba,itama Zayna haka.

Maheera ta fice daga gidan tana ta murna,Sohail ya biyo bayanta yace dama na fada miki zaki samu baki yarda dani ba gashi kuma,tace na yarda ai yanzu na gode sosai Sohail,yace ki daina gode min ni,muje to ka rakani,yace a'a na gaji ni bacci zanyi,tace to bye,ya juya abinsa ya tafi itama ta wuce gidan da take kwana gidan wata kawar Maman su,matar tana auren me rufin asiri a Abuja,itace ma ta samowa Maheera aiki ganin halin da suke ciki a suleja ta kawota gidanta Abuja ta samo mata aiki,matar yaranta uku yare ce kuma na Igala,tana da kirki ga tausayi.


Gida Maheera ta koma tana murna ta samu wacce suke kira da maman Rahmat a palo,maman Rahmat tace yau ya naga yarinya ta tana murna?
Maheera ta bata labarin samun sabon aikinta da salary dinta,ta bata labarin Sohail,Maman Rahmat tace Alhmdllh sai dai zanyi missing zaki barni na daina cin girki me dadi amma na tayaki murna Allah ya taimaka ya bada sa'a,a kula sosai a tsare mutunci,sai kiyi waya ki sanar da yan uwanki da Mamanki ko?
Maheera tace ae anjima da dare zan kira su,kema ki kira Oga fadlu ki sanar masa ya nemi wani ko wata,Maman Rahmat tace yanzu kuwa zan sanar masa inshaallah,Yaran Maman ma suna tayata murna" tashi tayi ta shige bedroom tana cewa thanks.


Washe gari da safe da wuri Maheera ta hada wasu kayanta a akwati me kyau ta tafi gidan su Sohail,har kofar gida me taxi ya sauke ta,knocking tayi dake Sohail ne ke bude gate basu da me gadi,shuru ba a bude ba sai da ta gaji ta turo karamar kofar ta jikin gate sai taga ta bude kawai ta shugo.
A compound ta hango Sohail yana zaune a kujera ya harde kafa daya kan daya yana ji ana knocking bai kula gate din ba,tana shugowa ya bude idonsa da yake a lumshe ya kalle ta kawai,ta karaso inda yake tace Hey,Hey shima yace sannan ya wani tafi dogon tunani sai da ya jima a haka tana tsaye tana kallonsa sannan yayi zumbur ya mike yace oh wai kece?


Akwatin ya fisge a hannunta yace idan an hanaki daukan heavy abu bakya jin magana kawo muje ciki,ta bishi tana murmushi suka shiga ciki ya nuna mata bedroom hadadde kamar dakin amarya yace ga room dinki,tace na gode Sohail,ya hade rai tare da furta ki daina min godiya ki godewa Allah,tace ai ina gode masa yace wannan ke ta shafa,kije ki ma matar gidan girki kafin 5pm suma su Adnan kiyi musu nasu,Maheera tace to ta mike ta wuce kitchen.


Tana tsaka da girkin Sohail ya shugo sanye da jallabiya wata fara dangalalliya duk kaurinsa a waje fari kal me dauke da kwantaccen gashi me kyau yace yana kallon Maheera ya aikin? Murmushi tayi tace Alhmdllh
Yana murmushi yana sosa gashinsa ya furta ko na tayaki?
tace a'a na gode,zai kara magana tace jeka kawai karka jawo min a koreni a aikin nan suce wani abu muke yi ka rufa min asiri,Okay....okay...ya furta yana kallonta ya juya ya fita ya barta tana aikinta, kamshin girkinta ya cika gidan,tana gamawa ta shirya dining Sohail yana can yana wanke mota.


Maheera sai da ta tambayi Zayna ko za a miki wani abu Hajiya? Zayna tace no sai anjima ki dora abincin Ogana, okay tace,taje kitchen ta kwashe ragowar a plate da Spoon ta fito har inda Sohail ke wanke mota,tace ga abincin naka,yace harda ni? tace ae mana,yace ki daina dafawa dani kar su gani suji haushina ke 'yar aikin su ce ba 'yar aikina ba,to yanzu dan kaci abinci sai ya zama matsala? Yace hmm kawai......Adnan ne ya shigo da motarsa wata benz me shegen tsada,a idonsa yaga Maheera tana mikawa Sohail abinci,mantuwa yayi ya dawo gidan shima.


Fitowa yayi a nutse cikin suits me tsada yana danna waya,yana zuwa inda suke tsaye ya dakawa Maheera tsawa sai da ta firgita,yace ke waye ya dafa abincin da kike bashi? jikinta ya hau mazari tace ni..ni...nice na dafawa Hajiyanka shine da ya ragu na bashi.
hannu Adnan ya sa ya fatalar da plate din a hannun Maheera,abincin ya watse a wajen a kasa ya furta look daga yau ke ba yar aikinsa bace,ni na daukeki aiki ni kadai zaki yiwa aiki tare da matata da kanina,idan ba haka ba zan koreki a aikin,idan yana son yaci abinci ga kitchen ya dafa da kansa.


Juyawa yayi ya kalli Sohail yace ka dakko abin shara ka share nan kayi clearing komai ya ja tsaki ya juya abinsa ya wuce ciki.
Maheera tace ikon Allah haka kake shan wahala? Murmushi Sohail yayi yace rayuwa kenan ya za ayi ko a jikinsa ma taga ya dakko abin shara ya share wajen tas ya tattara plate din ya maida kitchen.


Maheera tana ta kallonsa cike da tausayinsa,yace kina ta kallona zan dafawa kaina karki damu.
Jikinta a sanyaye ta koma ciki gaba daya tausayin Sohail ya kamata duk tunaninta dan aiki ne suka dauke shi a gidan.

Daddy Ali ne ya kira Adnan ya sanar masa cewar zaizo Abuja wani aiki zai kawo shi amma a ranar zai koma kano ba zama zaiyi ba,Sohai ma bai sani ba washe gari Zayna a kitchen ta samu Maheera tace ke Maheera kike ko wa? kiyi abinci lafiyayye da wuri before 2pm surikina zai shigo,Maheera tace Alright ma.
Ta fara girke girkenta Sohail ya sameta yace yau girki da wuri? Wai surukin Madam ne zaizo,Sohail baki ya tabe yace na sani ai,sun fada maka ne? Yace sai sun fada min ma,ko sunanki ai ji kika yi na fada miki to ko basu fada min ba na sani yana hanya yanzu ma.


Maheera bata karyata shi ba,kira Sohail yaji Ibrahim yana kwala masa kamar zai fasa gidan,Maheera tace jeka ana kiranka,fitowa yayi da sauri,Ibrahim yace kawo min glass of juice,Sohail ya koma ya kawo masa lemo glass cup,yana karba yace jeka dakina zaka ga wani note book green ka dakko min shi sauri.
Sohail ya wuce sama da sauri har hadadden dakin Ibrahim yana dubawa ya hango notebooks guda uku daya green,daya blue,daya grey color,Sohail ya dauki daya ya duba yace wanne ne green din a haka ya daga sama yana karewa ko wanne kallo,blue din ciki ya dauka yace yesss....wannan shine green ya fito ya kawo.


Ibrahim takaici ya kamashi yace wannan yayi kama da green? shine green din? Sohail yace idonka baya gani wannan ai shine green,wannan color din itace ta dace da green haba Yaya kalli ko idon naka computer ta fara kashe shi,uwarka ce computer din ai.
Sohail ya furta ai kuwa da mun huta sai muyi ta danna ta ba ruwanmu muyi game muyi kallo,computer uwar mu guda ai sai game kawai,tsaki Ibrahim ya ja cike da takaici ya fisge littafin ya tafi da kansa ya dakko abinsa.


Sohail ya bi littafin da kallo yace wannan ne green? blue fa ka dakko,Ibrahim yace Sohail dan Allah tafi ka bani waje just go....
Sohail ya nuna hanya yace na tafi kake nufi?
Ibrahim bakar magana ya fada yace a'a ka zauna nace,Sohail ya dawo palo ya zauna tare da harde kafafu yace na gode Yaya yana dagawa Ibrahim gira kamar dan iska,Ibrahim yace kai Sohail karuwa ka gani a nan a zaune? kana wani daga min gira kamar dan iska yaga karuwa.


Sohail ya sake kashewa Ibrahim ido yace ai mu idan iskanci zamu yi karyar karuwa ta kama kafar mu,dariya Ibrahim yayi ba shiri,yace gaskiya haukarku shahararriya ce, Sohail yana jinsa yace Yaya Ibrahim jiya Allah kaje kayi iskanci da wata mace sunanta Bilkisu,mamaki ya kusa kashe Ibrahim,yace a gidan uwarka?
Sohail yayi murmushi yace Allah kayi Sex da wata kuma shine na farkonka ta rinjayeka,ka cuci kanka tunda kakai wannan shekarun baka taba yin iskanci ba sai jiya,duk shekarun da ka kwashe kana hakuri sun tashi a banza fa.


Ibrahim ya hade rai yana muzurai yace kai karka min sharri zanci ubanka,in nayi ma ina ruwanka? Ku aljanun naku ma munafukai ne,Sohail yace shike nan dama tambayarka zanyi...Adnan ne ya shigo palon,Sohail yace Yaya Jiya Ibrahim yayi zina,dubu dari ya bawa karuwar,budurwarsa ce ta kaishi ta baro.


Adnan ko a jikinsa yace to ina ruwanka munafuki yayi din rayuwarsa ce bazai huta ba,idan ku baku da lafiya shi kalau yake,mu da lafiyar mu,Sohail yace ba a dai kuri da lafiya,mu ko zazzabi ai bama yi sam.
Tashi yayi ya bar wajen nasu,Suka ci gaba da hirarsu shi da dan uwansa.


Ali ne ya karaso da escort dinsa motocinsa da securities dinsa,Sohail ne ya karasa jikin motar Daddy dinsu ya bude masa kofa,Alhaji Ali ya fito ya sha farar shadda,kana gani kasan akwai kudi,Sohail yace Daddy ina kwana barka da zuwa,Daddy yayi dan murmushi bai ma amsa gaisuwar ba kawai tambaya yayi ina Adnan? Sohail yace Adnan kafi kowa? Daddy yace wanne sunane haka sabon nick name ya samu? Sohail yabi Daddy suna tafiya yace to ai kai kace kafi sonsa kaga ai yafi kowa ka sa masa kafi su kawai.


Shuru Daddy yayi suka shiga ciki,Sohail sama ya haura yana kwalawa Adnan kira Yaya ka fisu kazo ga ubanku yazo,da Adnan yazo Sohail ya kara furta ka fisu kaje ubanku ya zo,kai fa banda kai? Adnan ya tambaya.
Sohail yace to gashi nan wa ya sani uban mu ne ko ba shi bane Allah ne ya sani,Adnan ya ja tsaki ya wuce abinsa.


Zama suka yi suka gaisa da Daddy suka fara hirar aiki da harkokin kamfani da yanda kudade suke shigowa,Zayna tana cikinsu a zaune suna ta hira abinsu,Sohail kuwa yana dakinsa sai da ya gaji ya fito ya wuce kitchen ya samu Maheera tana fitar musu da abinci,tayata yayi suka shirya abincin a dining,Daddy Ali yana kallo ko a jikinsa sai ma murmushi da yayi yace Sohail akwai aiki wai ina Sahil? Sohail yace yana Lagos,Ali bai ma san dansa ya tafi Lagos ba,Ali yace amma baku fada min ba?
Wanda kafi so din naka basu fada maka ba?
Ali ba kunya yace wallahi basu fada min ba, Kai Adnan me yasa banji labari ba?


Adnan yace wata harka ta samun kudi Sahil ya samu wacce zai tsaya da kafafunsa,aiki ne me tsoka kuma shi yasa muka amince ya tafi,duk wani kudi da komai mun bashi yana can ya fara aikinsa ba matsala yana samun kudi,Daddy ba bincike yace to ai hakan yayi amma Sahil zai iya tsinana wani abu kuwa a duniya? Kar ya zubar min da mutunci ina so zan fito takarar gomna next year, Adnan yace to wa ya sani ne zanje na bincike shi naji.
Daddy yace kayi gaggawar hakan bana son abinda zai taba min siyasa ta.


Maheera dai tana jinsu Daddy ta gaisar sannan ta koma kitchen tana tsaye ta lula tunanin abinda akewa Sohail wai dama baban su ne? Mamaki ya cika ta,Sohail ne ya shigo da fara'arsa ya manta sam yace ki kaiwa Daddy tissue,tace wai da gaske babanku ne? Sohail yayi murmushi yace ae mana ai babanmu ne nida Sahil shine ya haife mu,ba ina ta cewa zan baki tarihina zan fada miki matsalata sai ki nuna bakya son jin labarin.


Amma baban mu ne mahaifi, Maheera ta tuna sanda yake zuwa shagonta yace zan baki tarihina,zan fada miki wata magana,sai ta dauka shirmensa ne kawai zai mata sai tace baza taji ba ita ya kyaketa.


Idonta ne ya ciko da hawaye tace kayi hakuri ban sani ba wlh,yanzu ina Mamanku ko itace ta mutu? Sohail yace ni ban sani ba tunda ni ban taba jin labarinta ba amma dai ance tana England sannan arniya ce itace tace bata son mu shine Daddy ya kawo mu wajen Mama Asmau itace ta raine mu har muka shiga University sai ta rasu bayan ta rasu kuma shine aka cire mu daga makaranta muka dawo nan da su yaya muna musu aiki,suna dan bamu 1k 2k,Daddy kuma shike daukan nauyin cinmu da shan mu sai sutura ana siya mana sai dai muga an kawo mana,ba a bamu ko sisi mu siyi abu da kanmu,sabo da mu bamu da amfani ance.


Maheera tana ta hawayen tausayi tace wlh kuna da amfani kuna da kyawun hali da hankali kawai su basu gani ne amma ni na gani kuma na sani na yarda da kai Sohail,Sahil ma haka you are the same kuna da hankali wlh,kunfi su Adnan hankali da kyan hali,Sohail yace Allah? Ke kin yarda muna da hankali? Maheera tace sosai ma Sohail na yarda da kai.
Kin yarda dani? Ba wanda ya taba cewa muna da hankali sai mama Asmau sai ke,kin yarda da mu? Maheera tace ae.
Zamuyi magana bari na gama aikina,yace to ya juya ya fita sai murna yake da farin ciki yau an samu wacce tace suna da hankali.


Sahil kuwa bacci ya sha sai yamma ya fito palon su Khalisat ya same su gaba daya a palo suna kallon film, Dukkansu suka zuba masa ido kamar mayu ko wacce tana sha'awar su har uwar tasu,Islaha dai tana kitchen tana aiki sai gata ta fito tana shirya Dining,Sahil ya kalleta da muguwar tsana suka hada ido,jikin Islaha ya hau rawa,tsoronsa take ji sosai,kanta ta dauke ta shirya dining,Khalisat tana ta jan Sahil da hira yana sharewa.
Islaha ce ta shiga kitchen,yace kitchen ne can? Aunty ta karbe zancen tana kwarkwasa tace ae kitchen ne zaka iya zuwa ka dauki abinda kake so,feel free ka zama dan gida.


Mikewa yayi ya shiga kitchen din,ba zato Islaha ta ganshi tsoro ya kamata ta fara rawar jiki,Sahil yace kyayi rawar jiki ai, wajen maza kuma kin iya cire pant a sauke shi kasa,Munafuka me fuska biyu na tsane ki.


Islaha muryarta na rawa tace wlh ni ba yar iska bace ban taba iskanci da namiji ba,tsawa ya buga mata enough....a mota muna tafiya haka kika ce ke ba yar iska bace harda cewa cinyata ba safe waje bane,har na miki gata na zame miki uwa da uba na doraki a precious cinyata safe waje irin wannan,harda ce min dan iska to gashi an tsinci iskanci a wajenki,na rainaki ma wlh,akan kudi a tafi a bankadewa maza Taskira shame on you, Allah yasa Sohail yayi mana kawar mu Maheera ta ishe mu useless girl.


Islaha ta fara kuka da hawaye ita bata san me tayi masa ba ya tsaneta,ya juya zai tafi tace wlh ban taba zina b....kafin ta karasa yace rufe min baki makaryaciya na ganki da idona to,Allah ya nuna min gaskiya anje an bankade taskira,ke kuwa nawa za a baki haka?


Islaha tace wlh idan ka kula su Khalisat wallahi a gidan nan sai anyi yaki ai dai nice nan na fara saninka,lalataka zasu yi,
Indai ina gidan nan babu wacce ta isa ta lalataka Sahil yace au fashi da makami na zaki yi? Tace ae? Baza su tsinci komai a jikinka ba face wahala,sai na fito da bad character dina da nake dannewa a gidan nan,za a ga bad character, sai nayi fashi da makami,Khalisat ce ta samo ka to sai nayi fashinka,yace to nidai abar nan tawa daya ce ina kuke so na sata,kai ku tsaya sai na fadawa Sohail ya fada muku gaskiya ni ba dan iska bane,wannan iskancin da zinace zinace na zamani bama yi,bamu iya bude taskirar mata ba.


Daga fadan da yake yi kuma sai ya koma hira yace da na sauka ruwa ya zaneni ranar da muka zo,Islaha tayi dariya tace sannu ai na tambayeka tun farko ina zaka je kaki kulani,kasa kasa yayi da murya yace ya kike fama da aiki a gidan nan tace uhm ba a magana ina shan wahala a rayuwa.
Sahil yace ai wahala yanzu kika soma gani tunda kike bada Taskira ana saka mazari a ciki kin gama yawo,ke da albarka har abada a haka zaki kare,karshen ki bazai kyau ba,bayan sun gama hira kuma ya koma masifarsa.
Ki daina kulani na fada miki na tsaneki ya bata rai ya fice yana huci.
Su Aunty duk tunaninsu Sahil me hankali ne murna suke ganin ya tsani Islaha gaba daya,yana fitowa yace wannan wacce mahaukaciyar me aiki kuka samo ne? Na tsaneta bana sonta,Aunty tace uhm yar gidan yar uwata ce ta ishe mu muma,tsaki ya ja ya sake mikewa yace bari na koma wajenta sai na mata rashin mutunci ni zata raina,Su Khalisat har wani dadi suke ji Islaha duk kyawunta baza ta kwace musu Sahil ba.


Kitchen din Sahil ya koma,ya kalli Islaha yace kina da saurayi wai? Mutumin da yace yar iska ce ita tana kula maza tana Zina amma yanzu kuma yana tambayar saurayi,Islaha ita kanta mamakinsa ya isheta,tace a'a bani da shi,yace yafi miki mutunci mu maza da kike gani ba 'yan goyo bane mu,ko an goya mu sai an sauke mu,Islaha tana dariya kasa kasa tace harda kai yace ae mana harda ni da Sohail karki sake ki goya mu,Islaha tace wai wanne aiki kazo yi nan? Kujera ya ja ya zauna yace bariki nazo yi,zobo me sanyi Islaha ta zuba a cup ta mika masa,yace mu a baki ake bamu bama cin abu da kanmu,har yaushe aka haife mu yara ne mu fa,Islaha duk wasa ta dauka yana yi shi kuwa da gaske yake fadar komai,tace to bari na baka a baki.


Su Khalisat suna palo shuru shuru sun ga Sahil shuru yaki fitowa tsoro ya kama su,Khairat tace bari na leka ta mike sadaf sadaf tace dole abi sahu bako ne ba a san halinsa ba,Islaha tana ta bashi zobo a baki yana shanye abinsa sai da ya kusa gamawa ya tankade cup din ya fadi kasa ya tarwatse yace da girmana,nifa ba dan iska bane irinki me neman maza yaja tsaki ya juya sai suka yi karo da Khairat.


Khairat ta matsa da sauri taga Islaha tayi zugum ga cup a tarwatse bata sani ba Sahil aljaninsu fada musu abu suke yi iya tsiyarka watarana baza ka iya kure su ba,kafin kazo sun sani,Khairat ta harari Islaha tace stay away from him yafi karfinki,gashi nan kin jawa kanki sai ki gyara wajen.


Sohail yana komawa wajen su Khalisat kamar munafukin miji yace yawwa ni gaskiya indai itace kar ta dafa min abinci a gidan nan,kar ta yi min komai,Aunty tace karka damu girkin ma da hannunmu zamu dinga yi maka har wanki da komai,yace yafi muku,Khalisat tace bari nazo mu fita a mota na kaika yawo,Aunty tace da kin bari tunda zan fita na fita tare da shi,Khalisat taji haushi da kishi tace ai na shirya,Khairat tana jinsu tace ni na kaishi next week.
Sahil yace ayi haka? Kunki sharar masallaci zaku yi ta kasuwa,ko girki bakwa yi ga me yi can bakwa wanki duk yi muku akeyi yanzu da kanku zaku yi min nawa? Aunty tace laaa ba komai ai bakonka annabinka,Sahil yana kallonsu dai dai yace alright ku kuka ga zaku iya ai! ya furta kai tsaye ba ko darrr.



Free page
400 ne




0175487861
Asmau Garba Muhammad
Gtbank


'Yan Niger
+22790795939








AsmaBaffa
08061929616
[7/17, 3:17 PM] Asmabaffa: 🪸MUMMUNAR DABI'A 🪸


16-20






Official


By
AsmaBaffa




SADAUKARWA NE GA 'YATA TASNIM




Page naki ne
Baby Ak






MASU AUDIO BAN YARDA A SATAR MIN NOVEL BA A JUYA BA,DUK WANDA YA DORA A CHANNEL DINSA SAI YA SAUKE.




*ZINARIYAR MACE⚡*
*Wai shin 'yar'uwa menene matsalarki? zubewar nono, ko kuma rashin kwankwason juyawa a falo maigida ya shiririce ya manta da tibi da matan tictok, menene matsalarki ne? rashin ni'ima ko kuma mugun sanyin da ya yi miki katutu, shin rashin taushin fata ne ko kuma kuraje

Please Login or Register in order to submit comment