Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

dawo Islaha tace dalla jeki mu ba wanda zamu kyale, gidane baza mu fita ba wallahi bana tsoron kowa rayuwar lagos nayi iskanci ne kawai bana yi amma indai da baki za ayi magana ba wanda ya isa naji tsoronsa.
Zayna ta juyo a fusace da matukar mamaki tace ke......a gidan mijina? Gidan aure na kizo kina daga min murya an dauke ki aiki amma kizo ni kina daga min murya? Islaha tace miji manya muma zaman wasu muke duk da ba a daura ba zaman su muke,Zayna tace to kuwa sai nasa kin bar gidan nan bari Adnan din ya shugo,Islaha tace shima adnan din naci ubansa ai ta kansa na fara baki sani ba,inci uban mijin inci na matar duk na gama da ku,Maheera tace Islaha kiyi shuru,Islaha tace ke kike jin tsoron su wlh.


Zayna sama ta wuce tana huci.
Maheera bedroom ta koma tana yiwa Islaha fada gidansu fa muka zo cin arziki muke,kuma kin san biyana akeyi ina da matsala a gidanmu nima indai rashin kunya ce na iya amma sabo da Iyayena da yan uwana nake hakura ina biyayya.
Amma ni duk layinmu ma tsoro na ake ji amma rayuwa da yanayi yasa na sakko,ki dain jansu da fada ki bari mu cimma buri sai mu fara bude musu munanan halayen mu,dariya Islaha tayi tace ina da hot temper bazan iya shuru ba kiyi hakuri amma zan fara mugunta a gidan nan,zaki ga tsiyar da zan dinga yi musu inda kika ga bera haka zan dawo


Wayar Maheera ce tayi kara ta duba taga kanwarta ce Juwairiyya ta daga tace yan university ya aka yi? Juwairiyya tayi dariya tace Alhmdllh Aunty kayan abincina ya kare sannan akwai wani kudi zamu biya 15k na escortion zamu je wani kamfani,Maheera tace kin san wata yayi nisa Juwairiyya bani da ki sisi wlh yanzu gashi jiya kudin hannuna na turawa Ammar ya siyowa Mama magungunanta su ma abincin su ya kusa karewa sai an siyi wani, Juwairiyya tace Aunty kina kokari ma an gode Allah ya buda bari mu jira mu gani me Allah zaiyi,nima zan duba idan na samu zaki ga Alert cewar Maheera,to Aunty na gode cewar Juwairiyya ta kashe wayar.

Islaha ta tambaya kudi za a bata? wai haka tace ni yanzu ma ban san ya zanyi ba,Islaha tace ga 20k cikin kudin asusuna ki tura mata tunda kinga ni ba abinda zan siya,Idan na karbe miki kudi ke kuma fa?
Islaha tace ba komai ai mun zama daya,rayuwa ce fa ni nasan wataran wa zai taimake ni? Kema kina taimako duk me taimako Allah baya hanashi sabo da haka karbi kawai.
Maheera karba tayi tana ta godiya tana jin dadi.


Washe gari Adnan ya samu Ibrahim yana masa magana akan Islaha lallai ya koreta ta bar musu gida taci mutuncinsa taci mutuncin matata.
Ibrahim yace Islaha kuma? Ae itace,
Gaskiya ba halinta bane kuma ma ai yarinya ce baka ganin bata da wayo kawai kayi hakuri zuwa wani lokaci su Sohail ne suke ziga ta,Adnan yace yarinyar nan bata da hankali fa,Ka dai dan kara hakuri tukun,fafur Ibrahim ya hana a kore ta shi baya ganin laifin Islaha sabo da sonta yake tsakani da Allah kuma burin aurenta yake.


Twins ma yau haka suka sha wanka suka fita neman aiki basu samo ba,wasa wasa sai da suka kwashe sati kullum suna garari da takardu amma ba labari,hakan yasa suka ce sun hakura baza su samu komai a duniya ba suka daina fita ma gaba daya kullum suna gida tare da su Maheera.


Zayna ce ta aiki Maheera kasuwa ta siyo abinda babu na kitchen,tana hanyar tafiya a kafa,sanye take cikin t-shirts brown da wando ta saka hijab daidai gwiwa tana tafiya a nutse,Wani mutum ne shi ba tsoho ba kuma baza a kirashi da yaro ba yayi parking da motarsa cikin sauri ya bude motar ya fito da kansa waje yana ta faman tari yana shidewa yana jan numfashi da kyar, yana ta daga hannu alamar a taimake shi,kasa ya fado daga cikin motar,Maheera ta lura da hakan da sauri ta karasa inda yake tana tambaya lafiya? Da me zan taimake shi,gaban motarsa yake nuna mata da yatsa,ta duba da sauri ta ga Inhaler wacce masu Athsma suke amfani da ita,da sauri ta sa masa a baki,a hankali ya fara dawowa hayyacinsa har ya gama dawowa dai dai.


Kallon Maheera yayi yace na gode kin taimakeni idan ba damuwa dan Allah ki bani number dinki za mu gaisa,ba musu ta bashi number dinta ta kara gaba,yana ta roko ta tsaya ya rage mata hanya amma taki yarda.


Bayan ta koma gida da kwana uku ta manta ma anyi wannan sai ga kiran mutumin,dagawa tayi ganin bakuwar number gaishe da shi tayi ya amsa sannan yace sunana Alhaji Saminu wanda kika taimaka lokacin da Asthma dina ta tashi,tace oh ya gida ya aiki,yace lafiya Alhmdllh,ina sake godiya fa Maheera,tace ba komai wlh ya wuce ai,yace ni sunana Alhaji Saminu Shehu kamar yanda na fada miki,nine me kamfanin J&S nigeria,ina da branch a lagos da Rivers sai kuma nan Abuja,Banyi niyyar sanar dake ba amma da kika ganni fitowa nayi daga gida zan je wajen abokina,Maheera tace mashaallah.
Ci gaba yayi da magana dalilin da yasa na miki magana naji dadi kin taimakeni,so ina da matata da yarana uku,ina so a matsayina da kika ji ki fada min abinda kike so ni kuma inshaallah zan miki.


Maheera taji dadi tace wlh bana bukatar komai na gode amma akwai saurayina da dan uwansa mun dade muna neman aiki kuma an kusa bikinmu Sir amma basu samu aikin ba,'yan biyu ne kuma dan Allah ka taimaka ka bawa ko mutum daya ne aikinyi,amma a takaice idan ba dama zamu iya haduwa na baka labarin su ko zaka tausaya,Jamilu yace ba damuwa bari na baki address din Office dina,ta dinga godiya tana murna.


Suna gama waya ya tura mata address yace tazo yanzu yana Office dinsa ma.
Shiryawa tayi a gurguje cikin fitted gown ta leshi blackblue ta yafa mayafi me kyau ta saka takalmi kalar mayafin da jaka ta fice da sauri,A palo ta samu Sohail,Sahil da Islaha suna kallo,tace zanje unguwa yanzu zan dawo,Sohail ya kalleta yace kuma sai da kika yi kwalliya kice kawai party zaki je,party da safe 11am fa,to baza ki fita ba,Maheera tace hmm mamata zan turawa kudi,karya kike Sohail ya bata amsa,Sahil yace yanzu suka yi waya da wani Saminu,Sohail yace Saminuuuuuu....Maheera juyawa tayi kawai zata tafi abinta Sohail yace in kika fita kin gama yawo na fada miki.


Maheera kofa ta bude tayi ficewarta,Sohail yace za ayi jaraba....yau a gidan nan,Sahil ya fara dariya yana kallonsa yace wai ko sonta kake ne? Sohail yace so? na so wannan? Maheera ce fa ita zan so kawata ce fa? Ka kyaleta taje to,yace ai yau wannan fadan da jarabar duniya sai an yita a gidan nan,Islaha tana ta dariya tace wlh da nice kai Sohail auren Maheera zanyi.
Sohail ya nuna kansa ni na aure ta inyi me da ita? tsaki ya ja ya kalli Sahil yace kai ko haushi ma baka ji ba kana kallo ta fita,Sahil yace to ina zan iya da ita.
Sohail yana ta jira ko aljanu zasu haska masa inda taje shuru ba labari,takaici ya kama shi, Islaha sai jinsa tayi yana cewa ba wani bayani? Kamar wani boka,yana cewa ba rahoto? Mene ne rahoto a kanta? a bani bayani shuru bai ji komai ba.
Sahil ya tambaya yace kai fa? An baka bayani? Sahil yace shuru ba labari.
Sohail mikewa yayi tsaye sanye cikin jallabiyya yana sintiri a palo ya kasa zama.


Maheera kuwa har katafaren building din Saminu ta nufa,har tanfatsetsen Office dinsa aka kaishi wanda ya gaji da tsaruwa,kujera ya nuna mata yace Zauna bismillah,Zama tayi a nutse sannan suka gaisa,yace I'm busy bani labari a gurguje ina da meeting,Maheera ta kalli Saminu sanye yake cikin wani yadi wanda bai da wani tsada in ka ganshi sai ka rantse da Allah ba shine me kudi haka ba,sam kudin babu kama a jikinsa.
Labarin su Sohail ta bashi a takaice,yace amma na tausaya musu wannan wanne irin azzaluman dangi ne amma laifin iyayen ne da uwarsu da uban sune masu laifi babba.
Bamu neman ma'aikata yanzu babu wajen daukan yan aiki sam amma zan iya daukan mutum daya a ciki,zan sa a koya masa aiki,idan naga kwazonsa zan bashi babban matsayi sannan sai ya koma karatu in ya gama sai ya kawo min takardunsa,kije ki tuntube su" su zabi daya a ciki sai na bashi aiki,amma nayi ne sabo da ke, jin kince shi zaki aura,Maheera tace na gode tana ta godiya suka yi sallama ta fito.
Tana zuwa gida Sohail kawai ta samu a palo ransa a bace yana ta zirga zirga tasan hali,da kuka ta shugo tare da dingishi da kafa,rudewa yayi ganin ta dawo da kuka sai ya manta da fadan da zaiyi,ya karaso da sauri ya riketa yana tambayarta menene? Lafiya?


Maheera tace faduwa nayi mota ce ta taho kamar zata kade ni garin gudu na fadi,Sohail yace sannu to muje asibiti? tace no ina jin sauki,yace okay to tana dingishi sai ya dauketa cak,taso tayi dariya,sai ta fuske ya kaita har dakinsu,Islaha tana kwance a gefen bed yace matsa ke,Islaha ta matsa can baya ya kwantar da Maheera sannan ya cire mata takalman kafarta ya adana su har jakar a inda take ajiyewa ya sa mata,mayafin ya cire mata a hankali ya ajiye gefe ya kalli Islaha yace Jinya zanyi ki sauka kwanciya zanyi,Ba shiri Maheera ta mike zaune tace naji sauki wlh dama kadan ne,Sohail yace idan kinga banyi jinyar nan ba to na mutu,Islaha tana ta dariya ganin yanda Maheera take ta zare idanu.


Sohail Saman bed din ya haura ta mike zata gudu ya jawota ta fado kansa,tace dan Allah ka bari ba kyau,yace duk masu jinya haka suke da raki, Islaha kawo min ruwan zafi a bowl,Maheera tace na shiga uku dan Allah Sohail na yafe ka kyaleni,tsaki yaja tana rike gam gam a jikinsa,sai da Islaha ta kawo ruwan a bowl da towel karami tana ta yiwa Maheera dariya,Sohail duk ya shaketa a jikinsa,kokawa suka shiga yi shi Ita,hakan sai ya masa dadi kamar wasa suke yi,ba shiri tace iya kafa ne gata ka gasata ta miko masa kafar,sai haki suke faman yi,kafarta me kyau fara ya jawo tare da dorata a cinyarsa ya matse towel din yana dannawa a kafarta,ruwan yayi zafi fa Sohail ka rage zan kone,ko kulata baiyi ba sai da ya gama gashinsa sannan ya mike ya fita.


Islaha tana dakin bayan ya fita Maheera tace to dariyar me kike kuma? Islaha tace wlh duk ya taba miki duwawu da kirji kamar ya kama namiji,Maheera tace ina ji ai,dadi kika ji kenan? dariya tayi tace uwar dadi naji,ki zauna na baki labari amma to be sincere jikinsa wlh dadi kamar kar a daina ta furta tare da rufe fuskarta da tafin hannayen ta, Islaha tayi dariya tace yau kwana zakiyi kina tunaninsa kenan? Hmm kawai tace.


Zama tayi Sannan Maheera ta bata labarin Alhaji Saminu da haduwar su da kuma yau abinda yace,Islaha sai murna tace Alhmdllh,yanzu su biyun zaki samu kiwa bayani daya sai ya barwa daya.


Zuwa dare ganin su Adnan suna palo sai Maheera ta kirasu a sirrince suka koma garden har Islaha,Zama suka yi Maheera ta basu labarin komai akan aikin,Farin ciki ya kama Sohail da Sahil suna ta murna,Sohail yace na barwa Sahil yaje yayi aikin,Sahil yace a'a kai zaka yi ni na fika zafin nema.
Suna haka Islaha tace ga takarda mun rubuta daya yes daya no wanda ya dauke yes shine zaiyi aikin wanda ya dauki no sai yayi hakuri sai nan gaba rabonsa in ya zo,Takarda ta watsa guda biyu a nanade,Sohail ya zaba Sohail ma ya dauka ko wanne ya bude,Sohail shine ya dauki Yes Sahil kuma no? Sahil yayi dariya yace Allah yayi zabinsa.
Maheera tace to sai ka tattara iya takardun da kake dasu gobe kaje ka same shi a Office,ga address zan baka,Sohail yace na gode taho Islaha na rungume ki,Islaha da wasa ta tafi kamar gaske,Sahil ya riketa yace ba kyau fa babu aure,Maheera har ta sandare a zaune sai taga Islaha tana mata dariya a sace.


Sohail a wajen suna hira amma shi ya dauki tsinke sai faman zana zero 0 yake,Maheera tace dan Allah karka je ka zana musu Zero a takardu ka kula sosai kayi aiki me kyau,Sahil yace ai mun sha wahala kafin a samu Inshaallah zaiyi kokari ko? Sohail yace Allah ne masani yaci gaba da zana Zero,Sun dade kafin su koma ciki.


Washe gari Sohail Ya dau wanka kace shine me kamfanin yana kamshi ya fice da sauri yana gyara agogo,Adnan da Ibrahim suka bishi da kallo sun ganshi da takardu,Ko kulasu baiyi ba bai ma nuna ya gansu ba ya wuce,dariya suka yi Ibrahim yace ana asarar wanka a hanya,Adnan yace wallahi dariya suke bani.
Sohail kuwa sai da yaje aka masa iso ciki wajen Ogan,yana shiga yaga yar yarinyar Oga Saminu kyakyawa da ita tana wasa a Office din,shi ai ya samu abin so sai ya dauketa yana dariya yace taho muyi wasa,yana ta mata wasa,Saminu a duniya yana so yaga me son yaransa,ai sai yaji kaunar Sohail,Yace kaine wanda Maheera tace? Yace ae nine ya mika masa hannu suka gaisa,daya hannun kuma yana dauke da yar Saminu,yace kaine wanda zata aura kenan mashaallah kamar ba dan kasar ba,Sohail yayi dariya yace haka ma dan uwana yake baza ka gane mu ba,zama yayi ya nutsu yarinyar tana cinyarsa,Oga Saminu sai wani washe baki yake an dauki yarsa,yace sauketa muyi magana to,Sohail ya ajiyeta yace Maheera tace nayi kokari na nutsu shi yasa zan ajiye wannan yarinyar kuma yanda tace sai na dage sosai kamfaninka sai yaci gaba a duniya,Alhaji Saminu yace Alhmdllh na yaba da kwazonka wlh,ka kwanta min a rai kuma naci alwashin baka duk wata gudunmuwa,Sohail yace na gode.


Takardunsa ya duba ya kalli yanda duk A1 ne da shi,yace ga kokari kuma,Nan take ya kira wani yaronsa yace Idris ga wannan kaje da shi office dinka ka fara masa training ka koya masa komai yanda muke tafiyar da company din nan sannan ka nuna masa yanda zai dinga tsara aikin a computer da abinda zai dinga yi,yace Okay Sir a wanne fannin za a ajiye shi,ka fara nuna masa wannan matakin zan tura maka me zaka nuna masa idan ya iya nan da 3days zan dawo da shi Office dina nan ma sai naga kwazonsa to ni nasan matsayin da zan bashi,yace an gama Sir, ya ja Sohail suka tafi,inda aka ci sa'a aikin daga wanda za ayi a computer sai takardu,Sohail ga Aljanu kafin azo a koya masa waje ma ya iya,Idris mamaki ya kamashi yace wai ka taba aiki irin wannan ne? Sohail yace kai dai muci gaba kawai,Idris yaga abin mamaki yau,idan ya bashi aiki kafin wani dan lokaci ya gama aikin,Aikin Idris da sai yayi wata yana abu daya sai yaga Sohail cikin lokaci kadan wai ya gama shi,ya duba kuma babu gyara ko tangarda.


Suka dawo fannin takardu duk paper daya ko a cike take da rubutu kallo daya ya gama da ita ya jawo wata mamaki ya kama Idris,kallo daya ya karanta ya fadi komai da ake nufi,Aikin da aka ce sai 5pm za a gamawa Sohail 12pm an gama shi,Idris ya saci jiki ya tafi Office din Alhaji Saminu ya dinga bashi labarin abinda ya gani,Saminu yasan wani labarin nasu yaji dadi,a ransa yace in hakane wannan kamfani zai ci gaba aiki da me aljanu irin wannan akwai dadi,nan gaba in naga yanda abin yake babban matsayi zan bashi kai har manager zan bashi na duka kamfanunuwa na su koma hannunsa indai yana da amana.


Sohail aka dawo da shi Office din oga Saminu kawai ya bashi System ya dinga zuba aiki,Office Office aka dinga kai Sohail sai gama musu aiki yake kamar inji ko inji bazai haka ba,Oga murna kawai yake,kuma idan suna shawara yanda kamfani zaici gaba sai aji ya kawo shawara me amfani wacce tafi ta kowa,Yau Oga yinin farin ciki yayi a Office.


2pm nayi sai ga Maheera dauke da Flask na abinci lafiyayye ta shiryo shi ta kawowa Sohail,bata shiga Building din ba daga bakin gate ta tsaya ta kirashi a waya.


Fitowa yayi ya wani soke biro a bayan kunnensa shi ga ma'aikaci,Maheera tayi tayi dariya ta more,yana zuwa yace sabo da na soke biro a bayan kunne kike min dariya,me kika zo yi? Abinci na kawo maka,murmushi yayi tare da shafa gefen fuskarta yace na gode wai so na kike ne? Maheera tace a'a kawai kaunarka nake,Kauna? Ni bana son Kauna kawai so nake so ya furta yana turo jajayan lips dinsa,ni zan tafi ko ka ci abincin ka bani na koma da shi gida,Haba ki sha wahala ki kawo kuma na cinye na kuma baki ki tafi dashi ai idan nayi haka na zama Adnan marar Imani,kije zan taho da su,please karka manta,bazan manta ba Hajjaju kin kusa zama Hajiya,a makka za a daura mana aure,Dariya Maheera tayi tace hmm,yace Allah da gaske nake da ni da Sahil da Islaha dake zamu tafi a daura mana,Sahil ne waliyyi na,ki fada a gidanku,Maheera tace ba ruwana sai kace aljanu ne zasu daura,yace to shike nan,ina siyan mota zaki ganni na daukeki munje gidanku naga danginki,ranar Mamanki ta shiga uku ta lalace da kudi,kudi dai kudi dai,ke har wani kudin zan bata nace ungo wannan ki zubar da su me rabo ya tsinta,Maheera tana ta dariya.


Flask din ya ajiye ya matsa jikinta sosai kamar zasu manne da juna,rungumeta yayi yace na gode,jikinta ta kwace ta karfi ta matsa baya tace ana kallon mu fa,kuma ni ba matarka bace,Sohail yace ke da a kauye kika girma ba a san me zakiyi ba mene haka? Dariya tayi ba shiri wai Sohail ke fadar haka,juyawa tayi ta fara tafiya zuwa yayi ya dauketa cak ya tafi da ita a haka tana cewa ka sauke ni wai mene haka iskanci ne fa wannan,Sai da yayi nisa ya sauketa yace na rage miki hanya,karki ta wahala,murmushi ta saki ta juyo tare da tsura masa kyawawan idanuwanta,juyawa yayi yace bye ya koma ciki da sauri.


Abincin da ta kai masa sai da yaje Office din Oga Saminu ya bashi yace ko zaici yace na gode na fita lunch yanzu, wajen Idris yaje yace suci tare,tare suka ci abincin na Maheera,Idris sai santi yake.


Sai 4pm suka tashi,Oga Saminu yace Sohail muje na saukeka a gida naji ma unguwar mu daya ashe,ya sake furta Sohail tabbas babu tantama zan baka aiki sannan nan gaba ma zan canja maka matsayi inshaallah indai muna raye,Sohail yayi ta godiya suka fito,Driver ne ya bude musu mota suka shiga katuwar motar Saminu ta gani ta nunawa sa'a suka wuce gida.


Suna tafiya Sohail yace gaskiya Sir baka nuna kai me kudi ne,magana ta gaskiya ka dinga cin kudinka,a yanda kake da kudi ya kamata a dinga ganinka da securities da motoci na binka ko uku ne,sannan sutura ma gaskiya ka godewa Allah ka dinga saka me tsada,kalle ni fa bani da sana'a siya mana akeyi amma takalmi na kadai sai ya siyi yadin jikinka,Alhaji Saminu yayi dariya yace kullum fadan da mukeyi da matata kenan wallahi,ita dole sai na canja ni kuma haka nake ban damu ba,Gaskiya ka canja ai shine godiyar Allah din aga banbanci,Alhaji Saminu yayi dariya yace amma a haka ake ce muku baku da hankali gashi muna magana ta nutsuwa,Sohail yace to da aka daukeni aikin za a bani mota wai?


Alhaji Saminu yace za a baka mota me tsada ta gaske sannan za a baka gida a estate me kyau,Sohail sai murna yace dama mun iya mota tun muna yara kawai dan kara gogewa zamuyi, mashaallah cewar Alhaji Saminu,ya sauke Sohail a bakin gate dinsu ya wuce gida, Sohail ma ya shiga gida dauke da takardu a hannunsa da aka ce ya karanta a gida ya cike su.


Yana shugowa ya samu Adnan da Ibrahim a zaune a palo suna ta aiki a System sun saka Sahil Mopping yana ta mopping haka kawai akan Zayna tace su Islaha ne suka yi Mopping shine suka ce wallahi sai ya sake yin sabo.


Sohail yana shugowa ya karbe Mopper din yayi jifa da ita yace muje dan Allah,Adnan ya zaro ido yace Sohail nine na sashi da tsawa yayi maganar, Sohail tsawar yayi shima kamar wani zaki yace bazai yi ba na hanashi,ai mun fada muku mun daina aiki a gidan nan aikin kudi muke nema sabo da haka baza muyi ba muma aikin da zai amfane mu muke nema,Ibrahim yace a tunaninku zaku samu aiki a haka? Sohail yace zauna ka sa wasa sai na zana muku Zero wallahi,Sifili ba saina zana muku shi ya furta tare da jan hannun Sahil suka haura sama,Suna shiga daki Sahil yace ya aikin?


Alhmdllh suka zauna a bakin gado ya bashi labarin aikin,Sahil ya dinga murna yace har mota za a baka da gida? Sohail yace me tsada ma ina fada maka amma muyi shuru kar mu fada su, Maheera kawai zamu fadawa ko Daddy bazai ji ba sai dai a ganmu da abinmu,Sahil yace mun faso gari muma,ai kana aikin nan ina ta kallonka,Sohail yayi dariya domin yawanci ana nuna musu aljanun,shege ai na ganka har Oga sai da ya baka kujerarsa ka hau kayi masa aiki,tafawa suka yi kamar abokai,yace bari nayi wanka nazo,kaga takardun da zan cike,duba ka karanta ka cike min,Sahil ma kallo daya kamar Aljani ya dauki biro duk yayi sai kace yasan kan aikin kuma daidai yayi shima.


Islaha ce ta shiga bedroom ta samu Maheera tana bacci tace ki tashi sweetynki ya dawo daga Office,ido ta bude kadan tace bana son iskanci waye Sweetyna yayi ta dawowa mana,abinci ne ai yasan inda yake ko kije ki kai masa,baya ta juya tare da komawa baccinta.


Sahil yana fitowa yaga Amal tazo gidan itama yau ta kawowa yan uwanta ziyara,ta sha Shadda fara,Zayna ya shiga kira Yaya ta palo.....Yaya ta Palo....Zayna...ki fito kinyi bakuwa kanwar miji tazo azo a nemi shiga,kin san dangin miji masifa ne dole sai ana yin shishigi da neman taskirar zama wai bazai ce gindin zama ba.


Amal tana wani kallon up and down tana tabe baki tace wace kuma Yaya ta palo? Sahil yace Zayna ce, to mece idan ba Yaya ta palo ba matar da mate dinmu ce,sa'ar mu ce fa duk mace akace shekarun mu daya da ita ai ta zama Yaya ta palo kuma.


Amal tace lallai Ibrahim kun bari yaran nan suna shanawa shi yasa suka raina kowa,wallahi da ina nan azabar da zasu sha sai sun kwammace ba a haifo su ba yan iska mahaukata marasa kwakwalwa,ba ilimi ba komai sai jahilci da hauka.


Sahil yace hmmm ke nan tunani kike kinfi kowa ko sabo da kin auri me suffar kwadi,Aunty Amal wai ina kike saka timbin me gidanki ne? Sabo da kudinsa ke tumbin nasa ma bakya gani,Ibrahim dariya ta kusa kulle masa ciki kawai dannewa yake,Sabo da Sahil bai fiye magana ba amma duk randa yaga dama to fa za aji tone tone.


Sahil yace wallahi Aunty Amal hakuri kike yi kawai sabo da kudi,ai kuwa ba wani sonki yake ba wlh uwar gidansa itace komai dinsa ki daina hura hanci,rannan ma haka yace duk duniya ba kamarta ita yake so,sannan baki sani ba wallahi bana ya biya mata Umrah ita da yaranta kaf ke kuma yace miki kiyi

Please Login or Register in order to submit comment