Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Shi da Sahil kaya iri daya yake musu komai iri daya,kasancewar ma basu saba rike kudi ba sai suyi ta shawarar me zasu yi da kudin.


Washe gari Sohail ya kwanta ya bawa Sahil Amt dinsa da key din mota yace kaje ka kai Maheera shopping duk abinda take so ta siya,Sahil yace ka isa ka aikeni wato kayi kudi ni zaka aika ko? Kaje ka dauke ta ka kaita ni karka dameni tunanin Islaha nake yi na kasa dainawa,ban san a halin da take ciki ba,nayi kuskure,Sohail yace bani naje na kaita marar mutunci akan nace zan huta ka kaita duk kudin ba mu dai nake nemowa ba,Sahil yace jeka dai bazan je ba Islaha ta tafi ita yarinyar nan Allah bai yita da yar karamar sanwa ba,Duwunta kadai tallaja guda ne inji larabawa suka ce Tallaja,aba ba kadan ba yanzu ta kama hanya ta tafi duk wanda ya ganta ya kenan,Sohail yace Allah ya kiyaye kar tayi aure ma,Wanda ya sameta kuwa zai sha kallo,Sahil ransa ya baci yace bani key din naje na kai Maheera din ina dan dubawa gari ko zan dace na ganta.
Ba musu ya bashi key din ya fita.


Ibrahim kuwa tracking aka dinga masa yana biyan kudi sai da aka gano inda take har gidan da take,ya cika da farin ciki washe gari a .mota ya tafi ma da kansa sabo da shiga kauyen,ya dinga sharara tafiya yana bin location har garin da Islaha take.




400 ne 1&2 gaba daya


0175487861
Asmau Garba Muhammad
Gtbank


Yan Niger
+22790795939












AsmaBaffa
08061929616
[7/17, 3:17 PM] Asmabaffa: 🪸MUMMUNAR DABI'A 🪸
31-35




Official


By
AsmaBaffa




SADAUKARWA NE GA 'YATA TASNIM




Page naki ne
Bestynbeelat










Ibrahim yana tafiya a motarsa yace chaiiii wannan kauye haka wanne iri ne,dama har yanzu da irin wannan kauyukan a kasar nan,wannan kauye kaddara ce ta kawo ni ace kamar ni Ibrahim ina son yar wannan garin zuciyata baki kyauta min ba, 'yar wannan garin kamar ni za ace ina son yar nan kauyen Allah ya kiyaye ba mayu bane ma duk tabi ta lashe mana kurwa sai dai aga muna ramewa a rasa dalili.
Amsa ya bawa kansa yace ko ma mayyar ce haka zan aura duk su Sahil ta lashe min su.


Wasu yara suna ta faman wasa da kasa Ibrahim yana dan tsayawa kusa da yaran da niyyar tambayar su suka watse gaba daya da gudu suna cewa barayi barayi ne...sabo da sunga mota, a kauyen ana musu huduba in sunga mota su gudu barayi ne,Ibrahim ya dinga mamaki yana daga cikin mota.


Abdulrazaqu ne ya dawo daga gona da ganyen zogale da yawan gaske zai kai gida,Ibrahim ya fito daga mota tare da yi masa sallama,Hannu Ibrahim ya mika masa,Abdulrazaqu yaki bayarwa yace kawai na baka hannu mu bace tare mu gaisa daga baya baya.


Ibrahim yayi murmushi shaddarsa tana sheki tana daukan ido arsh ga jiki ya ji hutu dole Abdulrazaqu su firgita,Ibrahim yace dan Allah gidan su Islaha nake nema, Abdulrazaqu yace yayanta ne ni ma da kake gani na,Amma kai na ganka baki bakwa kama,gaskiya da kamarka tayi sai dai a auri Islaha a garin nan.


Abdulrazaqu yaji haushi yace amma kai baka da ilimi sam kazo garinmu ka tare ni kana min tambaya sai ka dinga chaba min magana ko ance maka so shi a kyau yake? Duk ga ba munana nan ba sunfi auruwa sunfi samun mazaje na gari kuma kyawawan maza suke aura,sai kayi mamaki kace me ya gani a jikinta shi gashi kyakyawa,kuma kyakyawa mace kaga tana ta fadawa hannun mazaje munana,kaga mace hadaddiya mijinta ficika baza a siye shi ba,shi so da aure ai ba ruwansa da kyau malam ka gyara kalamanka,daka ganni bakin ba Allah ne yayi ni ba,a gidanku aka kirkireni? Ko kai farin ne gaka nan wankan tarwada kai a wankan tarwadar ma da alama kanti ka shiga ka dawo haka dama ai munji labari yan birni mayuka suke shafawa har mazan,mu kuwa mun tsaya yanda Allah yayi mu,ka ganni nan ko vaseline sai na shekara ban shafa ba,watarana ma mangyada nake shafawa da sanyi amma gani dakaukau dani aikin da nake baka isa kayi shi ba.


Ibrahim yayi dariya yace shi yasa ai gaka nan kamar an tonoka daga rami abokina maida wukar ka kira min Islaha idan tana nan,idan na sameta na maka alkawarin jari me tsoka ka fara kasuwanci zan maka gida me kyau a kauyen nan da babu kamarsa.
Abdulrazaqu yana jin haka yace da ina son Islaha nima amma na bar maka ita zan tsaya tsayin daka ko da tsiya sai ka aure ta ka kaddara ka sameta an gama.


Ibrahim yaji dadi yace na gode jeka zan bika a baya da mota,Ibrahim maimakon yace Abdulrazaqu ya shiga mota su tafi baya so ya shigar masa mota kar kamshin ta ya canja ya bata masa mota,a haka suka tafi shi yana daga cikin mota Abdulrazaqu yana tafiya a kafa har kofar gidan Lalai.
Ibrahim yana parking a gindin bishiya ya fito yace ai a nan gidan Islaha take? Abdulrazaqu yace ae a nan take,yace cab,Shigo ciki gidan tsohuwa ce ba wani abu ta riga ta tashi a aiki, shigo ko a wanne hali ka kalleta ba komai,Ibrahim yayi murmushi suka shiga kai tsaye gidan,Lalai tana jikin katangar kara tana leken mota a kofar gidanta riga daban zani daban.
Islaha tana zaune a gindin murhu tana ta faman iza wutar tuwo ta hada zufa idonta yayi ja sabo da hayaki.


Mamaki ya kamata ganin Ibrahim a tsakar gidan su yazo, Abdulrazaqu yace Islaha kinyi bako daga birni ai kin sanshi ko? Lalai tace sannu da zuwa maraba, ta fada daki ta dakko tabarma sabuwa ta shimfida masa a kasan bishiyar mangoro dake gidan,Ibrahim ya cire takalminsa me kyau ya zauna,tare da gaishe da Lalai,Islaha haushinsa taji da yazo amma bata nuna masa ba tunda gidansu yazo kuma dan ita yazo,mikewa tayi sanye cikin riga fitted gown ta atamfa green,komai ya fito chass,Ibrahim ya kare mata kallo irin na wayayyun yan birni kamar ba kallonta yake ba,karasowa tayi tace sannu da zuwa ina yini,kazo lafiya,ya hanya? Ta furta a jere.
ya amsa lfy Alhmdllh,shine kika taho ba sanarwa,murmushi tayi,yace ba sallama ba komai ko dan zaman tare ai kya yi mana sallama,Islaha tace ai wanda naje dominsa yasan na taho.


Kishi ne ya cika zuciyar Ibrahim yace ai shi bai damu dake ba,da ya damu dake ai da yazo,ko ya zo ne? Twins basa soyayya ba masu lafiya bane baza su iya inganta rayuwar kansu bama bare su inganta ta wani,gagararrun Aljanu ne da su, bakaken aljanu kuma masu gulma ma su suka hau kansu,da cutar aka haife su,kinga wanda aka haifa da cuta ai baya warkewa,tsoro ma muke ji kar nan gaba su fara duka ko su fara tsince tsince a bola.


Islaha tace Allah baya sa ba inshaallah zasu warke baza su taba zama hakan ba,kaima idan kun san farkon ku ai baku san karshen ku ba,Ibrahim yace Allah ne ya dora musu ba ni ba,mu bar wannan maganar muyi abinda ya kawo ni, Lalai ce ta fito da ruwa da abinci ta kawo har da hado fura ta kawo masa, Islaha tana kallon ikon Allah yanda Abdulrazaqu da Lalai suke wani nan nan da Ibrahim kamar zasu cinye shi.


Lalai ce ta kalli Islaha ta gasa mata harara tace ki zauna mana kuyi hira wajenki yazo kin wani tsaya masa kerere a ka,Islaha ta zauna tana jin haushi a ranta,Ibrahim ko ruwan su bai sha ba,bare yaci wani abu nasu ma.
Islaha ya kalla yace kina shan wahala a nan kizo mu koma gida dan Allah wannan garin bai dace da irinki ba,ke ba kalarsu bace,idan ma baza ki koma gidanmu ba muje zan kama miki hayar gida idan ma so kike zan siya miki gida naki na kanki sannan zan baki jari na bude miki wani abun na Business ki dinga yin abinki,idan ta kama har Dubai zan nuna miki yanda ake shugo da kaya ki dinga samun kudi,Islaha a ranta tace gwara a bani Sahil na kare a talauci na,a fili tace na gode ni nan yafi min idan kaga na bar nan to nayi aure.


Ai me sauki ne sai na turo manya a nemar min aurenki,Islaha tace ban shirya aure ba yanzu ni soyayya ma gaba daya bata gabana,murmushi Ibrahim yayi yace a ransa a hankali zaki shigo hannu ne yarinya,a fili kuma yace ba komai zan jiraki ni,ya dan dade yana hira tana amsawa sama sama sannan yace Alhmdllh tunda na san inda kike yanzu hankalina ya kwanta zan tafi,tace a yau zaka koma Abuja? Yace a cikin gari zan kwana a hotel gobe sai na wuce,tace yafi dai,mikewa yayi zai tafi tace ka gaida gida.


Lalai ta tsomo baki au baza ki raka shi ba? Mayafinta ta yafa tabi shi suka fita,Ibrahim sai dadi yake ji shi gani yake ma ya samu Islaha an gama,50k ya ajiyewa Lalai sabo da ya siyeta da kudi, Abdulrazaqu ma haka ya bashi 20k,sai murna suke yi,Ibrahim yace idan na dawo za a rakani gidajen yan uwan Islaha na gaishe su,Lalai ta yashe baki tace Allah ya kaimu dan nan kaji,an gode Allah ya tabbatar da alkhairi gashi kayi dace dama bata da saurayi bata kula kowa a sadaka zaka sameta,Ibrahim yace na sani ai ya wuce abinsa.


Suna zuwa jikin mota ya bude motarsa ya dakko ruwan roba ya balle ya sha abinsa,wato bazai sha na gidan ba,Islaha tace shine mu kaki shan ruwanmu ka dakko naka ai ba so bane wannan,Ya kalleta yace Typoid masifa ce sabo da ina son budurwa kawai sai na cuci kaina Typoid ta kamani ko na sha tsutsa a cikina ta hayayyafa ta cika min ciki, Typoid bata jin maga ni.


wato mu ta kashe mu kenan?cewar Islaha,Ibrahim yace ku ai kun saba ta saba da jininku ta sanku,baki ta tabe ya shiga mota sannan ya sauke glass ya miko 50k itama yace gashi kya samu ki dinga siyen wani abin,Islaha tace ina da kudi na ance maka bana ci ina koshi ne..
Nasan kina koshi mana amma garau garau gashi nan naga kin kara cikowa ma,Karki wa kanki ki karba karki koma gida kina cizon yatsa,Islaha taki karba fafur tace ina so na fada maka karka dawo wajena ni dai da Sahil nake soyayya sabo da haka bazan kula yaya na kula kani ba.


Ya kalleta cike da kishi yace Sahil baya sonki ki daina batawa kanki lokaci bai san ma kina yi ba harkarsa yake ya manta da ke ma,Islaha tace na ji duk da haka,kai fa bai ma dace ko da wasa ka kulani ba sabo da kaninka tunda tare ka ganmu,Ibrahim yace idan kika ga na hakura to kice an daura miki aure,Ba ruwana da wani Sahil kanina ne yazo muyi takara wanda ya samu shike nan ba abinda ya dameni,Islaha ta gaji tace to ka gaida gida na gode ta juya ta shige gida ko sisinsa bata karba ba.


Islaha tana komawa gida Lalai ta fara masifa tace ina lekenku kina fada masa magana,har ya baki kika karba to ubanwa kike so yaro kyakyawa da shi ga kudi dan birni,Islaha tace to ni bana sonsa kaninsa nake so karki dameni,Lalai tace to kuwa matukar baza kiso wannan ba sai dai ki bar min gida wlh,yaro dan mutunci ga kyauta,Islaha tace ae naji zan tafi bazan taba sonsa ba wlh ni bana sonsa,sabo da ya baku kudi ni zaku cuceni.


Lalai ta fara ruwan bala'i kizo gidana in ciyar dake amma nace kiyi abu kice a'a ai kuwa baki isa ba kici ki sha kice zaki rainani,Islaha tace iya na aikin wahala ta naci kyauta kika bani ba aiki nayi ba sannan aka bani,tuwon da rogo sai dambu ko danwake shine ake ta min gori sabo da ni bazan baki abin duniya ba,nidai na fada miki bana sonsa gwara na bar gidan kuma da bana gidan ai da baku samu kudin ba,zan iya danne ki na kwace kudin nayi tafiya ta gwara ki kyale ni kaka Lalai,ni talaka na nake so kaninsa,ba wanda yake bani ci da sha a dangi babu wanda zai fada min naji kaf garin nan,bani da mafadi sai a bari ace an dauki nauyina sannan sai a fada min naji,kullum in yini ina aiki a bani dan tuwo shike nan a dameni ace za a bani Umarni a haka zanbi umarnin? Ba a dauke ni a matsayin 'ya ba,ko Baffa Ghali dukkansu basu isa dani ba,daurin aure kuma ko a masallaci al'ummar annabi zasu daura min.


Lalai tace zaki ci ubanki da ni kike zance,duk wannan abin da kike yi kyaleki ake yi,ai dai a gabana kike to kamar kin so Ibrahima,Wallahi bazan aure shi ba cewar Islaha,shuru Lalai tayi mata suka ci gaba da aikin girki,Lalai ta kawo maggi dunkule biyu rak wai shi za a sa a miya ya isa,ga miyar da yawa,Islaha ta mike ta dakko farin maginta data siyo a boye ta faki idon Lalai ta watsa a miya sannan ta kara dunkulen biyu a ciki,haka take yiwa Lalai kullum,sai aji miya zakwai zakwai Lalai ta zaci tsabar gogewa ce da girki irin na yan birni yasa Idan Islaha tayi miya zaki kamar kar miya ta kare,sai Abdulrazaqu ma yace a dinga bawa Islaha miya tana yi gaskiya tafi dadi.


Bayan an gama girki sunyi sallar magriba,Lalai ta zubo tuwo tana ci tace kaji miyar yan bariki,miya sai bariki,amma mutane ace dunkule baya zakin miya,bayan ma farin magin nan cuta yake sawa amma wasu a dinga gabza shi a miya,Lalai tana wulla loma tace ai ni sam bana cin farin maggi duk inda naje indai an sa farin maggi a miya sai na gane,kana ci zaka ji zaki har kai,yana wani bauri kamar ruwan teku.


Islaha tana jinta tana dariya a ranta tace ace dunkule biyu rak miya kamar zan mutu idan ina ci sabo da rashin dadi,ai gwara da na siyo farin maggi na a boye na ajiye su,kullum da anzo girki zan faki ido na zuba.
Lalai tana yin sallar Isha ta mike ta dauki mayafinta tace na tafi gidan Baffanki Shamsu,Islaha tace a dawo lafiya.


Lalai tana tafiya ta dinga bin gidajen yan uwa tana basu labarin Ibrahim da irin kudinsa da kuma yanda Islaha tace ita bata sonsa talaka take so kaninsa.
Baffa Shamsu yana ji yace haba karya take wane ita, ita din banza,me akayi aka yi Islaha,Lalai tace to yace kuma zaizo ya gaishe ku zaku sha kudi ku mike tsaye so take tayi mana asara,Shamsu yace ai baza mu barta haka ba da malamai zamu hada ta dole ta so shi ta aure shi,gaba daya ki lallabata kiji sunan waccen wanda take so din ki fada min zamu bi ta wata hanyar kawai sai dai taji ta tsane shi ta fada son wannan Ibrahim kika ce ko? Lalai tace kwarai kuwa shi yasa nace bari nazo wajen ku ni tafi karfi na,baku ga yanda take min ba kamar zata dake ni har girgiza take idan tana min masifa,Shamsu yace jeki karki sake tsokanarta karki nuna komai ki nuna zabinta shine namu muma da haka zamu yaudare ta.
Lalai tace yawwa shike nan ai yanzu lallabata zanyi,bari na koma sai ka jini ina jin sunansa zan dawo na sanar maka.


Bayan Lalai ta dawo ta samu Islaha ta kunna wayarta tana game a ciki,amma ta sata a flymode, ta zauna da fara'a tace ku dai idan kuna wannan abin bakwa jin sallama,Ai na amsa cewar Islaha,Lalai tace Islaha wato dai bakya son wannan Ibrahim din? Zaki mana asarar kudi,arziki yazo mana har gida,Islaha ta turo baki tace ni bana son zancensa,Lalai tace ai muma zabinki muke so tunda kinki yarda ya zamu yi baza mu yi miki dole ba,Shi wanda kike so din iceko na kirki ne? Islaha tace ae sosai,ya sunansa ne shi wai?


Islaha dariya tayi a ranta tace haba Lalai da wayona da hankalina ba a banza na zauna a birni ba kuma ina aiki da ilimina,ni zaki rainawa hankali wallahi nafi karfinku nafi karfin tunaninku,a fili kuma tace Sunansa Tijjani,Lalai tace ya mori suna Allah yasa ya gaji me sunansa shehu ibrahim Tijjani Inyasi,dariya Islaha tayi tace hmm shi dai sunansa ne haka ba wani gado.
Lalai tace to Allah ya nuna mana Allah ya kawo shi na ganshi waye wannan me sa'ar.


Islaha tace Lalai amma yanzu tunda zanyi auren ai zan daina daka da sissika? Lalai tace inji uban wa ko gomna zaki aura sai kinyi sai in kin bar gidan nan, kawai sai na dafa na baki kici a huce hauka ake a ci dake sannan aikin ma baza kiyi ba sai dai kici a kwance sannu Sa'ida sunan wata bishiya,kece shafaffiya da mai da za a nemo da wahala sannan ayi aikin wahalar duk a baki kici a kwance sabo da kece Gimbiya hakima ishashiya,gwana yar hutu,Islaha tace to naji ni ki kyale ni.


Washe gari da safe da Abdulrazaqu ya shigo sakamakon dakinsa a waje yake daban na bukka, Lalai ta ja Shi gefe tana fada masa yanda suka yi da Baffa shamsu ta inda za a bullowa Islaha, Islaha tana can tana aikinta na gyara zogale yau dambu zasu yi kuma.


Lalai yau ma da dare ta koma gidan Baffa Shamsu ta fada masa sunansa Tijjani,Baffa Shamsu yace zaici ubansa ko waye wannan Tijjanin da take so,ga Ibrahim ai yafi.
Ya mike yace muje gidan Malam Ishu da shi kadai na yarda a garin nan.
Tare da Lalai suka je har can,suka zubewa Malam Ishu bayani da abinda ya kawo su ayi musu,Malam Ishu ya buga kasar dake gabansa, Malam Ishu sai da ya buga sau uku yace gaskiya babu wani me suna Tijjani da take alaka da shi,karya ta muku,amma ba sai ta fadi sunansa ba ku kyaleta aikin ba wahala ma an raba su aikin me sauki ne,amma zaku yanka zakara kuma ita za a bawa ta ci indai ta ci naman to shike nan zata fada son Ibrahim ta gigice da gaggawa zata matsu a yi bikin,Sai shi wannan za a raba su wani rubutu zan baku ku tabbatar kun zuba mata a ruwa ta sha indai ta sha ko yaya ko ba tijjani ba ko uban waye ma a ranta sai ta daina kaunarsa kawai sai Ibrahim,kullum sai tayi kuka akan Ibrahim,da kanta zata nemo shi yazo ayi biki.


Dari biyar suka bashi sadaka a haka sai murna yake ya sha kudi,yace gobe Lalai ta dawo ya karanta manta yanda zata aikata aikin, Islaha bata san me suke yi ba,washe gari Lalai ta koma ya bata wani rubutu a leda yace shi zaki juye mata a ruwan sha idan zata sha ruwa ko yaya ki zuba indai ta sha an gama,ya dakko wata laya ya bata yace wannan idan kin yanka zakara an gyarashi kisa layar a cikinsa ki samu zare da allura ki dinke cikin zakaran tsab ki dafa shi yaji hadi,idan ya dahu sai ki farke dinkin ki cire layar ki haka rami a binne ta sai ki bata taci,ko ya taci shima an gama,kuma zaku iya ci kuma iya abin ita zai shafa,Lalai tace an gama tayi godiya ta tafi direct gidan Baffa Shamsu.


A can Baffa shamsu ya bada katon zakaransa tace a nan gidan zan dafa kawai na kai can sabo da a can zata iya ganina,Yace haka za ayi,Lalai da matar Baffa Shamsu suka gyara zakara aka wanke tas suka saka laya tare da sa zare da katuwar allura ta dinkin buhu suka dinke da kyar yanda dai layar baza ta fito ba suka lallaba suka yi farfesu me kyau lafiyayye,Lalai ta binne laya amma tunda Malam yace zasu iya cin naman duk sai da suka ci aka barwa Islaha wani dan kadan a kwano iya wanda zata ci,dama yace ko yaya indai taci shike nan dama dan ita aka yi ita kadai zai shafa.

Lalai da kwano tazo a rufe da bargajejen hakarkarin zakara a kwano,ta samu Islaha har ta gama dafa musu dankalin Hausa tayi yar miyar jajjage,Lalai tace har kin gama sannu,tace yawwa,daga gidan Baffanki nake Shamsu zakaransa ya kasa zai mutu aka yanka shi shine suka dafa naci nima a can kinga naki na taho miki da shi maza kici abinki.


Islaha karba tayi ta duba tunani yazo mata haka kawai zasu bata wani nama kuma har haka da girmansa,ga wani mutunci da Lalai take yi mata yanzu,Islaha a ranta tace nafi karfinku wlh,Lalai tace bari nayi wanka maza ki cinye a wanke kwanon zasu zo karba,Islaha ta washe dan karamin bakinta tana murmushi tace na gade bari yanzu zan cinye abina,kai amma na gode ashe dai Baffa Shamsu suna so na,Lalai ta cika baho da ruwa tana cewa ai hannunka bai rubewa ka yanke ya yar,Islaha tace bari na baje naci abina yau akwai harka,Lalai tasan dole ma sai Islaha taci gashi taga sai murna take yi,sai ta shige wankanta,Islaha tana ganin haka ta dauke naman ta jefa cikin bakar leda ta kulle ta boye a cikin jakar kayanta,dan romon kuma ta dan jagwalgwala har gefen kwano alamar anci har romon an sha,ta fito hannunta duk maiko da romon nama,Lalai ta fito a wanka sai murna take Islaha ta cinye nama,Islaha tace bani Sabulu,Lalai ta mika mata ta wanke hannunta tas,abincinta ma da zata ci ko da hannunta bata ci ba da cokali taci dankalin .


Ta fita zata kai kwano kitchen kiri kiri taga Lalai ta bude randarta ta daki da sauri ta juye wani bakin abu a randar kamar rubutu ta mayar da murfi ta rufe,bata san Islaha ta juyo zata shigo ta gani ba,fuskewa tayi kamar bata gani ba.


Tana zuwa Islaha ta sake fita tace na manta bari na dakko kofi na sha ruwa,ta dakko kofi tare da bude randa ta cika kofi da ruwa ta fice waje ta juya ta kai kofin bakinta kamar sha take tana zagawa ta watsa ruwan a jikin katangar karan ta dauraye kofin ta maida ta kife ta dawo,Lalai sai murna take an gama aiki sun samu nasara.


Islaha tsoron Lalai ta shiga yi tun daga ranar bata kara cin abin hannun Lalai ba,sannan ruwan gidan bata sha fita take ta sha a can inda suke ebowa,abinci ma indai ba ita ta dafa ba to kwana take da yunwa.


Bayan sati biyu ko nisa Ibrahim bai gani ba ganin baya samun wayarta ya sake dawowa,Islaha tana ji ance ance shine ta dauki buta tace bari nayi fitsari ta shige bayi taki fitowa,har ya shigo gidan suka gaji da jiranta taki fitowa,Lalai tun daga nan tasan aiki bai ci ba,haka ta raka Ibrahim gidan dangi gida gida ai kuwa sunga ruwan Naira duk ya siye su da kudi sun haukace sai shi.
Lalai yau ma dubu hamsim, Abdulrazaqu ma ya sha nasa kudin,yaran gari ma duk wanda yazo dubu daya dari biyar biyar haka ya dinga rabawa yaran garin,dattijai da matasan kauyen daga me 2k sai me 3k haka ya dinga rabo,duk inda ka zaga zancen Ibrahim me ruwan Nairori ake yi,har an sa masa suna me ruwan Nairori Na Islaha.


Islaha sai da ta gaji ta fito,Lalai ta fisgo hannunta ta zuba mata rankwashi dan ubanki kije yar iska marar mutunci,ta jawo Islaha har gaban motar Ibrahim inda yake tsaye yana latsa waya.
Islaha tace na fada maka gaskiya kaki ji na fada maka ka kyale ni wallahi asarar kudinka kake ji,Ibrahim yace Baffa Ghali yace ya bani,Akan Sahil kike wannan shirmen ai na fada musu komai na su Sahil din da kike hauka a

Please Login or Register in order to submit comment