Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

komai ya ji,a gigice ta fito ta fice da sauri bata iya kallon kowa ta tare taxi ta fada ciki suka tafi,Sahil yana tsaye yana mamaki


Ya furta wonder shall never end,so duk mata haka suke wannan wato mummunar dabiarta ce ashe amma a haka kamar ta kirki,tsaki ya ja yana mamaki yace ahhh amma na dorata a cinyata harda wani ita ba haka take ba,shi yasa ni fa dama can jinina bai hadu da mata ba,indai akace mata ne to ba ruwana da su,Allah yasa nidai bana jin sha'awa,mata suje da abin su gwara da Allah yayi ni haka Dagger din bata aiki thank God ya juya zai tafi kenan sai Khalisat yar uwar Islaha ta fito cikin tsaleliyar motarta fara kal"


Sahil ta kalla ta furta wow kaga wani handsome,harshenta ta zaro ta lashi labbanta tace wannan idan na mallake shi aurensa ma zanyi,zan iya cinye wannan danye wow,da gani dan me kudi ne ba karya,anya ma kuwa yasan hausa,Sahil kuwa waya yake da Sohail bai ma san me take yi ba sai ji yayi an masa horn,bai ko juyo ba sai da ya gama wayarsa ya juya zai tafi Khalisat ta sauke glass kasa tana murmushi,ba karya ta zuba kyau doguwar rigar silk material ce a jikinta kusan tsirara tsirara haka take komai ana gani,Tunaninta zata birge Sahil sai taga ko a jikinsa kamar namiji ya kalla.


Murmushin da tasan yana kara mata kyau tayi cikin yanga da salon lankwasa murya ta furta zan iya dropping naka? Sahil da sauri ya furta no,please ta sake cewa tana wani shagwaba, gashi yana ta tunanin ko aljanun nasa zasu fada masa wace ita amma shuru,haka Islaha ya kasa gane gaskiya wanda a aikin banza kawai sai dai suji an fada musu abu amma wannan karon shuru ba labari.


Motar ya bude a fusace ya shiga baya yace muje,tace gaba zaka dawo sai kace ka shiga taxi
Yace haka nake so idan baza ki iya ba sauke ni,shuru tayi ta ja motar ta hau titi tana tambaya ina zan saukeka? Kafin ta rufe baki yace kasan gada,baki ta bude tace wacce gadar? Ya furta inda mutane suke kwana, Khalisat tayi mamaki sannan


Tace wai baka da gidan zama? Ya furta ae neman kudi nazo cirani,Wani dadi taji itakam tayi tsuntuwa,tace no ai baka samu aikin ba ko? Yace yeah, Alright muje gidanmu zan baka daki ka zauna har na wani lokacin da Allah zai sa ka samu wajen zama? Ko godiya Sahil baiyi ba ya furta Okay da fatan dai ba karuwanci zanyi ba? Domin kudin karuwanci da za a biyani bazai dauke ni ba,yana wani fisfisga shi kadai yana muzurai,dariya khalisat tayi kawai itama kyakyawa ce mashaallah komai na birge maza tana da shi.


Gidansu me kyau ta nufa da Sahil ba wani shayi ko dar dar, suna zuwa tayi parking ya fito ya kalli gidan yace gidan ba laifi,Khalisat tana murmushin jin dadi,ciki suka shiga tare.


FREE PAGE


400 NE


0175487861
Asmau Garba Muhammad
Gtbank


'Yan Niger
+22790795939








AsmaBaffa
08061929616
[7/17, 3:17 PM] Asmabaffa: https://www.arewabooks.com/chapter?id=6687e323e3651b348bbd12f6


🪸MUMMUNAR DABI'A 🪸


11-15




Official


By
AsmaBaffa




SADAUKARWA NE GA 'YATA TASNIM




Page naki ne
Mrs Chief






MASU AUDIO BAN YARDA A SATAR MIN NOVEL A JUYA BA,DUK WANDA YA DORA A CHANNEL SAI AN SAUKE.












Gidan nasu yana da kyau sosai Sahil har palo Khalisat ta shigar da shi wanda palon ya gaji da kyau da tsaruwa, murmushi tayi tace sit,zama yayi ta shiga kwalawa Mum kira tana cewa Aunty dake duk ta hanasu kiranta da Mama ko Mum kawai Aunty ce kar su kara cewa ita ta haife su,Aunty ce ta fito tare da Khairat,suka zubawa Sahil ido suna kallonsa,Aunty ta hadiyi yawu dama ace saurayinta ne,itama Khairat haka,Aunty tana yiwa Sahil kallon duniyanci tace wannan fa? Khalisat tace he is my friend zai dan zauna damu for a while kafin ya samu gidan zama,ai dakin nan a gyare yake? Aunty ta saki murmushi tace a ranta da alama akwai kudi a hannunsa.


A fili ta furta ba damuwa a gyare yake ai ki kaishi sai a kawo masa abinci da ruwa, yaje yayi wanka ya huta,Khalisat tana murna ta riko hannun Sahil tace lets go,hannunsa ya fisge tare da hade rai ya mike ya bita har bedroom lafiyayye me dauke da gado da sip da mudubi tare da toilet dakin yayi kyau,ac ta kunna masa tace kayi wanka bari naje nima zanyi wanka sai na sa yar aiki ta kawo maka abinci,Sahil dai yana kallonta da mamaki abinda suke masa ba tare da sun san shi waye ba.


Bayan ta fita yace karfa ko yan mafia ne ban sani ba,no..no..kaina yafi karfinsu baza su iya dani ba,Allah bazai basu iko a kaina ba,wani tunanin ya sake ya furta kaiiii....karfa naji na bace kar a siyar da kaina,su din banza nafi karfinsu yace sannan ya shiga toilet abinsa,wanka yayi ya fito ya saka kayansa kanana riga da wando,Navy color ya sha uban kyau sosai, gefen rigarsa ma da yar laimar ruwan jiya da ya zane shi.


Knocking yaji anyi,yace come in,a hankali aka turo kofar tare da shugowa dauke da sallama a bakinta,Sai yaji kamar yasan muryar,Islaha ce ta shugo dauke da tire a hannunta na abinci da ruwa,sanye take da Hijab har kasa tana wani dari dari,a hankali ta dago kanta suka yi ido biyu,yace you.....yana nunata da yatsa,kanta ta sadda kasa fuskarta dauke da murmushi ta dago a hankali


Fuska taga ya daure kamar bai taba saninta ba a duniya,mamaki ya kamata matuka,ransa a bace yana mata wani mugun kallo yace kalle ki kamar ta kirki a haka,munafukar banza,ido ta zaro tana kallonsa,yace ban san me ke damunku ba matan wannan zamanin masu fuska biyu,a fili kuna nuna ku na Allah ne a badini ashe kuna da wata mummunar Dabia da ba san da ita ba,daga yau karki nuna kin sanni a duniya,kuma duk wani abu nawa karki sake kice zaki taba,avoid me duk inda kika ganni karki sake ki kulani kuma karki taba min abu,abincinki dauki ki kara gaba bana bukata.


Islaha tsoro da mamaki ya kamata,ita tasan bata masa komai ba ita,a tsorace ta juya! Ya ja mata wani wawan tsaki tare da furta stupid,yana uban huci ya kwanta a saman bed din,tuni Islaha ta fita ta bar masa dakin tana mamaki me ta masa sannan me ya kawo shi gidansu a ina yasan Khalisat,jajayen lips dinta ta turo gaba tace koma mene zan gani wlh Allah yasa ace dan iska ne me neman mata wallahi sai ya hadu da rashin mutunci na sai na fito da sabuwar bad character dina a gidan Nan,kowa sai yasan Islaha bata da mutunci,kowa sai yasan ni ba a gaban uwata na taso ba,kuma sai an san ni yar tuwo tuwo ce ta raini ni,badai suna bada gabansu ba maza suna ishiriniya abinsu,mace kawai ki bada jiki namiji ya dinga ishiriniya a kanki zan gani ta ja kwafa.


Khalisat ce ta shigo dakin Sahil cikin wata gown guntuwa maroon wacce da kadan ta rufe duwawunta,Sahil dai kamar yaga namiji again,tace ya an kawo maka abincin? Yana kakkafe idanuwa yana masifa kamar ubanta yace wata banzar yarinya ce ta kawo bana so ta sake kawo min abinci,Khalisat tace Islaha ce yar kauye,ai wannan yarinyar dabba ce gaba daya,Sahil nan take yace a'a fa Allah ya gani dai mutum ce,Khalisat zata sake magana yace ba ruwana da ita ni kawai kiyi shuru,sam baya so a zageta,Khalisat tace yar iskar yarinya.....kafin ta rufe baki ya fara waka dan kar ma yaji yana kida da bakinsa gijib... gijijib...tsayawa Khalisat tayi tana jinsa tana dariya wakar tasa ta hausa ce yake yin abarsa,Juyawa tayi tace bari na kawo maka abincin da kaina ta fice.


Dauke da abincinsa ta dawo a plate jullof rice ce ta sha hadi da naman kaza ga ruwa da lemo,zama yayi ya fara ci Khalisat ta zauna a gefensa tare da dafa kafadarsa,ya zame a hankali yana cewa hannunki nauyi,kasar da aka halicce ki da ita wajen nauyi aka ebo,,kyale shi tayi tare da furta sorry tana lasar labba,yace ko ci zaki yi ne? da sauri ta furta a'a,sai bayan ya koshi sannan ta mike ya gabatar da sallolin da ake binsa har ya idar,Khalisat tana zaune a gefen bed din tana jiransa,juyowa yayi ya kalleta tare da furta zanyi bacci,Khalisat ba kunya tace zan iya taya ka kwanciya? idanuwa ya zaro sai da ta tsorata tun kafin yayi magana a fusace ya mike ya jawo jakarsa yace ki tayani kwanciya a wanne dalili raping dina zaki yi? Mikewa tayi tana bashi hakuri I'm sorry kwanta akan yar wannan maganar zaka tafi? Kayi hakuri kwanta abinka,ta fice da sauri sannan ya kwanta abinsa.


Sohail....Adnan ya kwalawa kira....Sohail...ji wannan banzan yaron ina kiransa,Sohail ne ya fito daga kitchen da sauri,fada Adnan ya hau yi yace sabo da hauka kana ji ina kiranka,Sohail kansa ya nuna yace oh dama kirana kake yi? Uwarka nake yi cewar Adnan.
Sohail yace ai ta mutu Maman,
Ba wannan ba ai ba ita ta haife ku ba,uwarku arniya ita nake nufi, Sohail yana tsaye sanye da jean black da riga arsh color yace kai ka santa ma ashe?
Dama muna da uwa? Kuna da ita arniya ba Adnan ya bashi amsa.
Arniya ce? Taji dadinta ba ruwanta da kishirwar azumi,ta tsula tsiyarta kawai ba komai.
Adnan ido ya zaro yace uwar taku? Sohail yace kai mu bamu da uwa.


Yaya Adnan nayi sabuwar kawa me kirki,Adnan ransa ya baci nan take da kyar ya danne yace wace?
Wata ce sunanta Maheera kyakyawa ce sosai.
A ina take? A gaban layin nan take,Adnan yace lallai ya kamata na ganta mu gaisa
Sohail yace ba damuwa zan rakaka Sahil ma ya santa shima kawarsa ce mu kasan mace daya muke bukata,Adnan yayi dariya yace gaskiya ne mazaje yan biyu masu mace daya,Sohail yace ae mun sasanta kanmu ni da Sahil ko mace ta rungume shi nima sai tayi min nawa,Adnan yace nifa? Sohail yace direct yace a'a banda kai wlh ka kula mana mata sai gawarka.
Adnan ya jinjina kai yace matata zata zo anjima kayi girki me dadi,ba damuwa na kusa gamawa ma cewar Sohail"
Adnan yana takama ya juya ya haura sama abinsa.


Zuwa yamma Zayna ta sauka a jirgi,Adnan da kansa yaje ya dakko ta,tayi kiba ta kara kyau ga wanka yabi jiki,Sohail yana shirya dining ya gansu Adnan ya rungumo kugunta sun shigo,Sohail ya kura mata ido yaga Zayna ce,mamaki ya kamashi da alama itace matar Adnan din.


Nunawa tayi bata san ma Sohail ba,juyawa tayi ta kalli Adnan tace Baby wannan fa na tuna ashe fa kaninka ne,Sohail ko a jikinsa yayi murmushi yace yaya dama ita ka aura?
Adnan kiss ya mannawa Zayna a kumatu yace ita ce,Sohail yace sannu Aunty ya juya ya wuce part dinsa cike da mamaki,wai Adnan ya auri budurwar su shi da Sahil,baki ya tabe yace suji dadinsu ni ina ruwana da Allah zai sa ma ni kuka yazo min ai kwana zanyi ina yi naji dadin jikina,ai kuka wani Exercise ne daban,kuka duniya ne,dama shi Sohail haka kawai ma in kan ya motsa kuka yake shi kadai haka kawai.


Bayan Zayna ta huta dining suka zauna,Ibrahim,adnan da Zayna suna kwasar girkin Sohail suna hira abin su,Sohail ne ya fito ya wuce su da sauri,Zayna ta masa banzan kallo ta ja tsaki,bai ma san tana yi ba tuni yayi gaba,yana tafiya da uban sauri kamar zai tashi sama,wasu a layin sun sanshi sosai suna mutunci,sai magana suke masa amma sai dai ya daga musu hannu,ka rantse wani mummunan abu ne ya faru,bai tsaya ba sai da yaje shagon Maheera har ciki sannan yaci birki,ta dora kanta a table tana danna waya ya daki botiki da karfi ta tashi a firgice,dariya yayi yace nine,tace Oh Sohail ko sallama,kujera ya ja ya zauna yana so ya bata labari,yace bari na baki labari kinga ni gidanmu....gidanmu ..uhmmmm....katseshi tayi tace dan Allah ka kyale ni da surutun nan bana ganewa damuwa ta min yawa ka rabu dani,yace abu zan fada miki,tace no...ni kyaleni bazan ji ba kai labari ma kafin ka bawa mutum sai ya tsaya wahalar saurare.


Shuru yayi,wasu suka shugo siyayya ya mike ya fara basu amma duk ya rage kudin abin dari biyar sai yace ku bada dari biyu an muku ragi dole mu kawo canji a kasar nan mu da araha zamu siyar,Maheera ta mike da sauri ta fisge ledar kayan tace ke kudinki ba haka ba ta lissafa kudin da kanta,matar tace me shago ya mana kyauta ki hana yar bakin ciki,Maheera tace ba shagon sa bane malama ta karbi kudinta ta basu kaya suka fice suna Allah wadai da Maheera me kudi yayi kyauta ta hana.


Sohail ya kalli Maheera yana murmushi ya ja hancinta yace to bani alawa,kara maheera ta saki ta bige masa hannu tana shagwaba tace da zafi fa,Alawar ta ebo tace yau biyar zan baka ta mika masa ya zuba a aljihu tare da bare daya ya sa a bakinsa yace na gode na tafi gida.


Sunansa ta kira tace "Sohail"
Amsawa yayi ya dawo ya zauna tace ina cikin damuwa yau,na rasa wanda zan fadawa naga munfi kusa da kai, sai ya nutsu kuwa yace ae ina jinki tell me.
Tace mamana tana da lalura tana Sule ja a gida ina da kanne biyu mace da namiji nice nake kula da karatunsu,Mamana ciwon sugar ne da ita ina shan wahala ta kashe kudin magani,gashi aikin nan da na samu oga ya sani a shago baya biyana akan lokaci gashi babu abin kirki a salary din,ga kula da kaina ga yan gidanmu,ubanmu tun muna yara ya rasu,yanzu aiki nake nema wanda ya dan fi wannan ko wanke wanke da shara ne indai yafi wannan albashi zanyi,Sohail ya nutsu yanzu.


Ya dafa kafadarta yace akan wannan kike damuwa? Ki kwantar da hankalinki indai aiki ne zaki samu,zan nemo miki,kinyi karatu? Tace na fara university amma kasan bani da kudi dole na hakura yanzu ni kannena nake biyawa kudin makaranta,Sohail yace to za a samu wani karki damu kinji ke da kike da Allah,wannan ba matsala bace ki kwanta kiyi bacci in ta kama ma kina shan giya ki sha abarki aiki zaki samu Inshaallah.


Dariya Maheera tayi sosai da sosai,tace na gode to,aljihunsa ya duba ya ciro 4k yace suke nan gareni ragowar kudine da naje kasuwa siyo nama ungo ya mika mata,ta saki baki tana kallonsa yace karbi kyauta na baki kawarmu ce ke,
ta karba tana ta godiya kamar yasan bata da ko sisi sannan idan kana wajen wani a zaune dole ka dinga yiwa kanka wani abin, tace Sohail na gode,ya sake duba aljihunsa ya ciro naira ashirin yace ah sorry ungo wannan ma hada da ita.
Ta karba tana dariya tace na gode.
wajen shagon taga ya leka ya dawo da leda baka a hannunsa ya ajiye mata a table.
Mene kuma? Ta tambaya
Yace duba ki gani yana tsotsar alawa me tsinke,dubawa tayi taga naman kaza soyayye da yawa a ledar zai kai kaji biyu,ta zaro ido tace amma tun dazu baka bani ba kuma me yasa ka ajiye a waje jikin kofa?

Yace ai bana so ki gani surprise zan miki kuma na manta badan kin tuna min ba da tuni na tafi na barshi a wajen,tace kai ka soya? Yace ae,na gode sosai,yace bani daya a ciki naci karki ce na saka miki wani abu"
Maheera harararsa take tace ai nawa ne bazan baka ba,Murmushi ya fice fit ko sallama bai mata ba.
Tayi dariya kawai ta fara cin naman.


Yana komawa gida ya iske Zayna tana masifa a palo tace da Adnan ni gaskiya a kawo min mace yar aiki wacce zata dinga yi min girki da wanki da sauran hidima ta,shi Sohail ya muku naku,ni bazan iya cin girkin namiji ba,Adnan yana rawar jiki yace za a nemo yar aikin tunda haka kike bukata,Sohail yana ji yace yaya akwai wata ta iya girki sosai indai za a biyata albashi me kyau a kawo ta.


Zayna tace karka kawo mana mahaukaciya irinka fa,Sohail yaji zafin maganar amma bai ko nuna ba yace ta iya fa, ina fada muku zan kawo ta nan ta fara yi muku na gwaji,idan kuka gwadata in yayi shike nan,Adnan yace ba damuwa tunda haka kace a kawo ta gobe tayi muji,yace an gama.


Zuwa yamma likis Sohail ya koma shagon da Maheera take da sauri, Maheera tana zaune tana shan lemo da da naman da ya kawo mata, Sohail ya fado ciki yana sosa sumarsa wacce taji aski irin na kwallayen shegun gari,gashinsu kamar na mata daurewa suke da ribbon amma sun kwashe gefe da gefe an rubuta sunansu a gefe daya an saka Sohail daya barin Sahil,shima Sahil yaka yayi,Daddy yayi yayi su gyara sunki amma ba karamin kyau ya musu ba sai dai a al'adar mu ta malam bahaushe za ace ba tarbiyya.


Maheera ta kalle shi tace Sohail ya ka dawo?
Yana murmushi yace albishirinki
Goro ta furta tana kallonsa"
Yace kin samu aiki amma sai dai ba irin na classy girls bane irinku,girki ne zaki dinga yi,matar Yaya tace baza taci girkin namiji ba,shine nace akwai wata zata yi,kin san nawa zasu biyaki duk wata? Maheera tace nawa?
Yace dubu dari,idan kina aiki me kyau zasu iya kara miki ma.
Zumbur Maheera ta mike tana tsalle da murna kamar yarinya,tace wannan fa dubu ashirin yake bani duk wata!
Yes zanyi zanyi ba matsala,wayyo dadi Alhmdllh Allah na gode maka,tana murna tace Alhmdllh.
Gaskiya Sohail kai mutumin kirki ne na gode.


Sohail yace na fada miki ai ko kina shan giya ki sha abarki kiyi bacci aiki zaki samu,gobe zamu je zaki musu abinci da yamma zasu yi miki test in kinci shike nan an dauke ki,kuma nasan ma kin iya girki!


Na iya girki sosai Inshaallah zanyi kokari zan dage Sohail.
Sohail ya furta aha Sahil yace a gaida ki,kin san da za a haifo mu a tare muka fito duniya ba wanda ya riga wani zuwa,Maheera ta iya bi da Sohail ta kalle shi tana dariya tace Allah? Aradu ya furta yana daukan alawa


Dariya ta sake saki tace amma yau naji dadi come ba zato Sohail yaji anyi hugging nasa,ido ya zaro da sauri ya janye jikinsa tare da ja baya yace mene haka? Sahil fa baya nan,to wlh shima sai kin masa na rantse.


Ido Maheera ta zaro tana murmushi tace Sahil din? Sohail yace ke ba a wasa damu na fada miki sai kin masa shima ya hade rai,Maheera tace to never mind zan masa shima amma ai kaine abokina Sohail ka gane?
Ni bazan gane ba kawai malama zamu yi fada,Sorry to zan masa shike nan?
You promise? ya sake tambaya,tace yeah,yatsa ya mika mata yace mu kulla,ta kawo nata suka kulla ta furta shima sai an yiwa Sahil? yace kamar da kasa.


Juyawa yayi zai tafi ta ruko shi tace na sallameka ne? Ban gane ba sai ma kin sallame ni? Ke mace fa ni baza ta juya ni ba in fada miki gaskiya 'yar nan, Maheera tayi dariya tace to fa,har ya tafi ya dawo yace na fasa tafiya zo muyi game?
tace wacce iri ba kayan game a nan.
Wasan yar buya buya zamuyi,okay ka bari sai gobe idan naje test sai muzo muyi kaga ko Oga ya kama mu kawai korata zaiyi shike nan.
Sohail yace no ba a haka kuyi rabuwar mutunci basai munyi ba tunda baya so.
Okay tace kawai,kallo ya fara kare mata yace wai mene wannan a kirjin ku?
Sam Maheera bata gane ba,yace gashi nan tulu tulu ana gani.
Maheera fuskewa tayi duk da taji kunya tace shi kuka sha kuka girma,yace Allah sarki na Mama yana kabari yanzu ina tunosa ke ya akayi naki chakare chakare ita kuwa Umma Nadia nata kamar na tsohuwar saniya wacce yunwa ta kamata.
Maheer ta dinga dariya ba shiri tace Umman taku guda?


Sohail yace ke bafa ita ta haife mu ba Na Mama yana Kabari nata me kyau ne Daddy ma ya dinga ta yashe baki idan tana wajensa ya dinga ta dariyar dole hahahaha ranar girkin Mama,Allah ko ni sai na iya Auren Mamata.


Dariya ta sake kama Maheera tace ashe ta hadu dai?
Yace tab ke kin isa ma kice shekarunta 47, Mamanmu ta iya sa kaya ko wanne wanka kyau yake mata ga kamshi,gata da mutunci ke Mama fa duniya ce,akwai uwar data kai tamu ma,Maheera tace Mamata fa? Sohail ya bata rai yace ko uwarki bata kai Maman mu ba.
Da sauri Maheera ta kalle shi tace zagina kayi fa Sohail,yace to ba uwarki bace? Uwarki mana nace bata kai tawa ba,nifa in kika takura min zan iya miki dukan tsiya.
Maheera tace ni din?
Kwalla ce ta cika masa ido tab da ya tuno da Mama Asmau.
Maheera tace sorry mene abin kuka? Yace baza ki gane bane... baza ki gane ba ina ta so na baki labarin damuwa ta sai kice baza kiji ba labari na akwai jira kafin a saurara,tsaki ya ja ya fice yayi tafiyarsa .


Maheera ta tsaya kamar gunki tana mamaki.
Bata yi tunanin zata ganshi ba washe gari ba
Sai gashi da yamma ya sha farar shadda tana shining ba karamin kyau yayi ba ka rantse wani me kudin gaske ne,ga kyau,ita kanta Maheera tsayawa tayi tana ta faman kallonsa,hannu daya a aljihu ya shugo yace ya garin me shago? Tace lafiya lau tana murmushi.
Hannunta ya riko yace zo mu tafi.
hararsa tayi tace bazan je ba shine jiya kayi fushi?
Yace ni din? Yana nuna kansa da yatsa yace me nayi jiyan?
Au ka manta? Yace na manta kuma har ga Allah har ya manta ma,sai da ta tuna masa yace Oh ya share zancen kamar ba shi ba.
Mikewa tayi suka fito,zata rufe shagon ya karbe key din yana cewa kawo kamar namiji mace tana wahala haka Mama bata irin haka,ai ana taba ki kice wash zan mutu.....harda gwadawa! dariya Maheera ta fara yi ba shiri har ya gama rufe shagon yace muje
Juyawa tayi tana rataya handbag dinta,yace kawo handbag din na rike miki ki daina wahala zaki yi muscles kamar na maza ki bubbude.
Jakar ya karba ya rike a hannunsa suna tafiya suna hira,yayi hauka yayi hankali a haka har suka je gidan su.


Maheera kanta ya kusa bugawa ganin irin unguwar da suke da layin da suke balle uwa uba gidan nasu tamfatsetse na gani na nunawa sa'a,tace a nan kake zaune? duk bata kawo gidan uban Sahil da Sohail bane,tunaninta ma yaran riko ne ko 'yan uwa.
Sanda suka shiga Maheera tana ta kalle kalle ya kalleta yayi dariya yace kinga gida me kamala ko? Yana dariya yace ai kamilallen gida ne wannan ba ballagazin gida ba irin naku,nasan gidanku ballagazin gida ne.
Maheera tayi dariya tace kaima ai ba naku bane,bai ce mata komai ba,yace muje na nuna miki kitchen din,In kin gama girkin ki shirya a dining sai na kira su masu gidan su dandana.
Haka ya fisgi hannunta ya jata ko ina na gidan sai da ta dinga hakkin sosai yanda yake fisgarta sai hakki take da nishi, da sauri yana nuna mata ko ina har katafaren kitchen din katon gaske komai akwai ciki,ya nuna mata komai da kayan sarrafawa,kin gane? tace ae naga komai da nake bukata akwai,yace yawwa to fara girkin ni bari naje na gyara dakin Adnan da na Ibrahim kafin nan kin gama,ta furta ba damuwa,ya juya ya tafi.


Farfesu ta fara yi na naman rago sannan ta tsara fried rice lafiyayya taji hadi da su hantar rago da naman kaza,sannan ta hada couslow da lemo ingantacce ta shirya a Dining, har da potatoe ball tayi da kwai da nama a tsakiya.
Tana gama shiryawa a dining ta

Please Login or Register in order to submit comment