Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da naci ai, Mudassir yace to sai da safe,mun gode sosai cewar Sahil ya raka Mudassir har mota, Mudassir yace shiga mota mu tafi na saukeka a gidan su Adnan yanda muka tsara,Sahil yace tab ga gidanmu mun dawo kace na koma bazan koma ba, soyayya fa zaka hana su yi,Sahil yace ba abinda za ayi sai an jira ni,Mudassir ya buga ya buga yaki yarda,haka ya tafi ya kulle musu gidan ya wuce room dinsa,wanka yayi yaci kayan dadinsa yana kallon film a dakinsa har yayi bacci.


Ango kuwa Amarya na zaune ya shiga da sallama,murmushi tayi ta cikin mayafi,hannu yasa ya fyalle mayafin yace mene haka kin sanni na sanki ki zauna kina boye fuska.
Har ya juya zai shiga toilet ya fasa ya dawo ya leka fuskarta yace naga kamar kinyi kuka,Maheera tace uhm rabuwa da gida wasa ne,nan ba wani gidan kika dawo ba? murmushi tayi me kyau zata yi fari yace dakata karki fara na gaji.


Dariya tayi tana kallo ya bude kayansa ya dakko wasu kayan baccinsa ruwan zuma sababbi,ya dauki man shafawarsa da turare da komai ya shige toilet,Maheera tayi murmushi tace idan ka shirya a gabana menene to,kofa ya rufe amma bai sa key ba,sai da yayi wankansa da brush ya dade yana faman shiryawa sai da ya shafa mai yayi komai har gashinsa ya gyara yana shafa turaren kaya Maheera ta gaji ta bude toilet din,da sauri ya juyo yace Allah ya fiki na shirya to,dariya tayi tace to me kake yi haka ne? Kin takura min daga aurenki kin dameni fa.


Kayi Alwala? yace yanzu zanyi ya juya baya,da tsokana Maheera ta rungume shi,Laaaaaa ya furta kamar an masa wani abu ya tsaya a haka kanta ta kwantar a bayansa tare da furta wayyo ni duniya dadi,Ido ya zaro waje yace ke Maheera uwaki ni na hadu da yar duniya wlh dama Sahil yace zaki karya alkawari,hannu yasa ya banbareta daga jikinsa da masifa yace ki daina bana so ni.


Murmushi tayi ta ture shi tace matsa nayi alwala,Alwala tayi ta bishi suka fito,Sallah ya ja su tace ashe ka sani,kwafa ya ja yace me kika maida ni ne? Sallah ya tayar suka yi ya musu addua yanda ake yi,suna idarwa ta rike hannunsa kwacewa yayi ya harareta,dariya tayi tsokanarsa take ta faman yi.


Sai da ta shiga wanka ya sauke ajiyar zuciya yace an takura min ni wayyo Allah aure wahala yanzu na gane da maza suke ta fada halin mata ba kyau,shi yasa maza kowa kuka yake da aure wahala na rasa ganewa sai yau.


Daure da guntun towel ta fito ya saki baki yana kallonta Maheera tana murna ta tafi da Imaninsa sai ji tayi ya furta wai ke haka kike dama aka baniva dukunkune? Ashe lukuta ce ke amma a haka kamar siririya ni siririya nake so,Maheera bata kulashi taci gaba da shirinta,ya zauna kuma sai kallonta yake kamar zai cinye ta har ta shirya ta dauko wata gantalalliyar rigar bacci da Aunty Aisha ta bata kalar kayansa na bacci ta zabo sharara da ita komai a waje da siririn pant dinta gata guntuwa rigar,Sohail yana gani ta saka abarta ta zare Towel din ya juya baya da sauri tare da furta na jawa kaina sai da Daddy yace kar nayi auren nan na kafe sai nayi gashi na hadu da gamo na.
Maheera tana jinsa tana boye dariyarta,inda yake zaune a gefen bed ta koma gabansa ta tsaya inda ya juya baya,sake juyawa yayi ya kalli gefe can,saman cinyarsa ta zauna ya dinga zamewa kamar tsutsa yana zukewa,gashinsa ya sosa ya girgiza kansa kamar haukar ta motsa,kugunta ya rike ya dagata yace wai ke bakya zama kawai,dariya tayi zata sake taba shi yace ga abinci zo kici.


Zama tayi tace kai fa? Yace na koshi,tace gwara ma kazo kaci tun kafin nazo na kwanta a jikinka kuma a haka zan baka da hannuna,da sauri ya dawo ya zauna,amma lokacin da ka gasa min kafa me yasa ka tabani muka yi kokawa? Sannan watarana da muka yi party Islaha har abinci ta baka a baki kuma kaci,Sohail yace ni din? Yaushe? Shi sam ya rantse ba shine ba,duk sun manta ma anyi wani party har Sahil din babu me iya tunawa.


Maheera haka suka ci abincin tare suka koshi ta tattara komai zata fita yace kin manta saka hijab karki ga Sahil a palo yana kallo,tace kace kai a dukunkune aka baka baka damu ba ina ruwanka da wani kuma,fuska ya bata yace kin rainani ko? Ni na isa ta dawo ta saka ta fita,tana dawowa ta samu ya jera pillows a tsakiya kar ma ta taba shi wai,yace kowa ya kwanta a barinsa,tace to ta kashe light tayi kwanciyarta a bangare daya shima haka,yace to baza kiyi addua ba? Ai yi nake,yace okay ki hada dani ai nayi aure ba sai nayi ba tunda cewa aka yi ki kula dani, ya juya yayi kwanciyarsa wai tayi da shi kawai.


Maheera a ranta tace na shiga uku ni Maheera wannan kaddara wacce iri ce,da haka tayi bacci itama dama su sarakan bacci ne har ya lula,duk ya har gitsa pillon da ya jera su babu ko daya duk sun fado kasa.


Farkawa Maheera tayi taga duk pillows din sun watse kasa,murmushi tayi ta koma jikinsa tana dariya a boye hannunsa ta jawo ta dora a kugunta ta matsa jikinsa ta manne ta rungume shi bai sani ba sai da asuba tayi ya farka a hankali ya bude idonsa,tunawa yayi ai Maheera ce yayi aure murmushi yayi yanzu kuma"
yana kare mata kallo,kwanciyarta ta gyara sosai,hannunsa daya ya mika yana daga kwance ya kunna light haske ya bayyana.


Wuyan rigar Maheera ya zazzage ana hango Boobs a waje chakare chakare,Sohail baki ya rufe da tafin hannu daya,yaci gaba da kallonsu da baki ya nuna su yace uhm shi yasa take wani kin saka hijab yau na gansu Allah ya toni asirinta bata da katabus,idonsa ya lumshe yace kuci gaba da kallona ina jin dadina ya koma baccinsa,yana komawa baccin aka kwalla kiran sallah ya sake farkawa yace yau makara zanyi Maheera tana nan.
Yanzu kuma yace na gode Mama zan dawo gaisuwar surukai ko dan wannan runguma da kika tarbiyyantar da yarki a kai ga nacin jikina ta makale min,tarbiyyarki tayi Mama,ban kashe kudina a banza ba.


Maheera ce ta farka a hankali ta yunkura zata tashi taji ya riketa gam yace makara zamu yi yau,tana murza ido tace da hankalin mu da sanin mu ai ba a wasa da sallah tashi muyi sallah,Sohail yace bazanyi ba ni yanzu makara zanyi yau,ta matsa masa yace naji zanyi amma bazan je masallaci ba ni wlh,tace ae tashi muje,harararta yayi ya mika mata hannu yace dagani jawo shi tayi ya tashi, yace karfa kice kece kika tashe ni ganin dama nayi baki isa kin iya dagani ba.


Toilet din ya shige ya kulle,ta zauna ta jirashi sai da yayi wanka da brush ya fito,Maheera tace munfa makara ka zauna wanka,yace wankan tsarki nayi ance duk wanda yayi aure sai yayi wankan tsarki kullum,Dariya zata karasa Maheera ta shige toilet kawai tace yau nidai na shiga uku a haka zan rayu.


Kafin ta fito yayi sallah yana Azkhar dinsa dake yaga dama,tace to matsa zanyi Sallah ya tashi ya bata waje ta saka kaya ta gabatar da Sallah tayiwa Twins addua sosai sannan ta cire kayanta sai na bacci ta kwanta,kwanciya yayi a samanta ihu ta saki ya dagata da sauri yana dariya yace ba haka kike so ba.


A gefenta ya kwanta yana kallonta yace tsaya na miki wani abu karki fadawa Sahil zai ce na karya Alkawari,Maheera tayi murmushi tace kace kar a taba ka kai baka so nice yar iska shi yasa na kyaleka,uhm uhm karki kyaleni please yace.


Jikinsa ya dawo da ita ta lafe yace sai kace mage wai ke zan fasa ma,na daina to cewar Maheera,carbin hannunsa ya ajiye a nutse kamar wanda yasan kan lamari ya hade fuskar su waje daya hancinsu yana gugan na juna,Maheera idanuwa ta lumshe tana jiran tsammani fuskarsa ya janye har ya matsa ya kyaleta tana a haka kamar gunki ido a lumshe tana ta jira,sai data dawo hayyacinta taga baya ma jikinta,kunyar kanta taji ta shiga sosa gashi tace a ranta me yake damuna ne zai rainani ma,dan guntun tsaki ta ja tare da kwanciya itama.


Sai wurin 9am ta tashi jin ana buga kofa, Shima Sohail farkawa yayi jin karar door bell,zata mike yace kwanta bari naje irin jarumin nan,yana fitowa ya bude kofa yaga driver Aunty Aisha ta aiko shi da lafiyayyen abinci,karba yayi suka gaisa da driver yace mun gode ya rufe kofar.
Dakin Sahil ya shiga ya samu Sahil yana baccin gajiya ya ja masa kofar ya fito ya ajiye abincin a dining ya koma bedroom ya samu Maheera ta shiga wanka.


Islaha kuwa tana komawa Lagos can gidan wata hajiya Kulu uwar tuwo taje itace take yiwa 'yan mata hanyar aiki a gidan masu kudi ko a wajen yan tuwo tuwo,Hajiya Kulu tana ganinta tace Islaha yau kece a gidan nawa daga ina haka na ganki da uban kaya? Islaha tace wlh Hajiya Kulu korata Aunty tayi kin sai dai halinta da abinda suke yi,Hajiya kulu tace bata kyauta ba wlh wasu ke bata wasu shi yasa ake ganin duk wanda yayi sana'ar tuwo tuwo a banza ake kallon mutum kawai dan duniya ne.


Yanzu ya dangin naku? Islaha ta bata labarin komai tun daga korar da Aunty tayi mata har da haduwarta da Sahil da barinta a gidan su,Hajiya Kulu ta kalli Islaha yanda take sharbar kuka wai dan a tausaya mata tana cewa kowa yaki ya tausaya min, tace na sha wuya tana shesheka,Hajiya Kulu tace to ai ke kuruciya ce ta muku yawa har su Sahil din kika ce sunansa ko? su in banda shirme ai wani za a samu ya raka ki gidanku,ke kuma daga sunyi magana sai ki bar gida cikin dare suma suna da gaskiyar su bai kamata ba,Yanzu to shi Sahil din sonki yake ko kece kike son sa?


Islaha tana hawaye tace wlh ina sonsa,mutumin nan inda kisan ya min asiri ni ba kula samari nake ba amma ina ganinsa naji zuciyata ta buga,nidai sai sonsa nake yi ba ji ba gani,nayi adduar nayi adduar sai naji na kara sonsa,nifa ko sunansa kika fada dadi nake ji, idan na hadu da wanda ya sanshi sai naji ina sonsa,Ibrahim yayansa da yake zuwa sabo da son Sahil sai naji dadi idan na gashi sabo da naga dan uwan Sahil,zuciyata sai azalzalata take na koma can wajensa,amma ina dagewa ina daurewa wlh idan na gaji mutunci na zan zubar na koma wajensa.


Hajiya Kulu tayi dariya kamar ba gobe tace dan Allah karki zubar da ajinki mutum ya kore ki haba Islaha,Islaha tana goge hawaye tace wlh idan na gaji zubar da ajina zanyi bazan iya da wannan kadadarrariyar soyayya ba,Aljanunsa ne suka shige ni suka cuce ni suka sa nake sonsa,har mafarkinsa nake yi munyi aure, ina gajiya zan barar da mutunci na.


Hajiya Kulu tace to Islaha yanzu akan namiji kike wannan uban kuka haka? Mene ma bazan yi ba namiji halittar Allah nifa zan iya haukacewa akan Sahil,ina ta daurewa duk sanda na gaji zan fusata na kai kaina,Hajiya Kulu tace to kiyi hakuri mana haka a samu aiki da wajen zamanki sai a san yanda za ayi ko? Islaha tace ayi sauri to.

Hajiya Kulu ta san Aunty tun suna tuwo tuwo a tasha tun Islaha tana karama har suka yi kudi suka dawo Lagos,dama kuma sunfi shiri da Islaha sabo da wahalar da Aunty ke bata,Hajiya kulu ita ba yar iska bace shi yasa ma sam basu fiye mutunci da Aunty ba.


Islaha sallah tayi ta zauna Hajiya kulu ta kawo mata abinci shinkafa da miya da nama yanka uku sai salat da ruwa,Islaha tana kuka tana cin abinci wai dan Hajiya Kulu ta raimake ta.
Sai da ta koshi sannan tayi wanka ta zauna ta zuba tagumi tana tunanin Sahil.

Sai da ta kwana uku a gidan Hajiya kulu tace Islaha kawai ki zauna a wajena ki dinga tayani siyar da abinci a wajen saida abinci na mana nan gaba idan an samu aiki me kyau sai na kaiki can, Islaha tace ba damuwa,daga ranar Islaha bata sake kuka ba, idan suka shirya abinci a gida sai a zuba a manyan kuloli su jera a cikin kurar ruwa su tura zuwa layin da Hajiya kulu ke siyar da abinci,wata rumfarta ce da katon tabir da benchi sun kai hudu na zaman samari masu siyen abinci,Tebir din kuma a samansa suke jera kulolin.


Islaha kurar ta turo sanye take cikin riga da skert na atamfa tana tura kura sai ga Khalisat,Khairat,Aunty da Shema'u sai Yaseer shine ke tuka su a motar Shema'u,da sauri Aunty tace tsaya tsaya ga Islaha can tana tura kura ta koma tuwo tuwo.


Aunty duk da ita ta kori Islaha bata ji dadin ganinta a haka ba yar yayarta ce ta jini,a gaban Islaha yayi parking,Yaseer yace Aunty baki kyauta ba wlh banji dadi ba bai kamata ba,Khalisat tace shegiya gwara haka gwara da aka koreta bata da kunya,na samo saurayina kyakyawa ta rabani da shi.


Aunty ce ta bude mota ta fito tana bulbula kamshi ta sha kitson Attach,Islaha tana ganin itace ta dauke kai,Murmushi Aunty tayi tace kin iya rashin kunya baki da abinda kika taka a kasa yanzu ina amfanin wannan rayuwar? kizo mu koma gida kici gaba da zama amma sai in zaki canja hali kibi umarni na,Islaha tace Allah ya kiyaye ni ba asararriya bace.


Gwara nayi wannan sana'ar ta fimin na bawa maza kaina,Aunty tace kije jiki magayi ta shiga mota tace Yaseer muje naga alama bata ji jiki ba,Yaseer yace ke Aunty...ja mota muje ko naci uwarka wlh,motar ya ja suka bar Islaha a tsaye,kurarta ta tura tana hawaye har ta kai abincin rumfa.


Maza da yawa sunzo siya su suka dora mata abincin a saman tebir sannan ta fara zuba musu tana karbar kudinta,wani matashi yace ki sa naman kato fa ke,Islaha ta kalle shi kawai ta zuba masa a robar take away, ya karba yace kudin sai na dawo,tace hey.... don't Dear me miko min kudina bana son wasa ta bata rai,ba shiri ya mika mata kudinta ta karba ta saka a jaka ta bashi canjinsa,sai daga baya Hajiya kulu tazo.


Amarya ce taci gayu cikin sabuwar atamfa doguwar riga ta mata mugun kyau,dauri taci ture kaga tsiya baya ta gyara gashinta har baya ta sa ribbon kalar atamfar dark green,tana kamshi Sohail ya kalleta yana murmushi,Murmushin tayi masa itama,kinyi kyau yace,tace na gode kaje kayi kaima,yace nayi da asuba sai anjima,tace oh na tuna,yace ae bana karya dan a so ni,tace nima haka,yace aka sani ko na amarci kike yi,Maheera fuska ta bata ta juya,hannunta ya ruko yace hijab din fa,tace sai kace na sa kana nan kaya kullum kace sai na saka Hijab ina gidan mijina,Sahil fa yana nan,to a haka wacce shiga nayi ta rashin dacewa kowa zai iya ganina a haka haba Sohail wannan wanne irin kishi ne, Sohail yace namijin kishi ne dani.


Juyawa tayi zata fice yace dan Allah to sa mayafi please Baby,dariya tayi ita zai wa wayo har da Baby,zuwa tayi ta dauki mayafi kalar kayan ta yafa tace Allah idan kace Baby sai naji ko nayi fushi gaba daya na huce,yace Baby wuya a waje da gashin da dai Hijab dinne,harararsa tayi yace to jeki na hakura muje ya mike yabi bayanta sai kakkareta yake.


Sahil yana palo shi karinsa yake suka fito suka iske shi yana cin abincin,Maheera tace ina kwana Sahil? Kallo daya yayi mata yace lafiya lau Amarya ta Ango,Sohail hannu ya mika masa suka gaisa yace nazo da safe kana bacci,Sahil yace zo kaji,Sohail ya duka ya mika masa kunne yace iceko ba aci amanata ba? A jira Islaha fa,Sohail shima da rada yace banyi komai ba,sai faman kus kus suke,Maheera ta wuce Dining ta zauna tayi serving kanta tayi serving Sohail ta hada masa tea da komai sannan tace Sweet yunwa nake ji.


Sohail zama yayi a dining yace har kin zuba min komai? tace ae yace Allah ya miki Albarka,bari na baki a baki,Maheera tace a ranta abu kamar hawa da sauka ayi daidai a dawo a kauce, chips din ya tsikaro da fork spoon ya sa mata a baki Maheera ta tauna jin dadi yau tafi kowa a duniya jin da takewa kanta,sai murmushin jin dadi take Sohail yana bata a baki tana ci yana ci shima, Sahil yana can daga palo yana cewa a dai tsaya iya nan.


Sohail yace karka damu yana sa tissue yana gogewa Maheera baki,Maheera dadi ya kashe ta tace haiiiiii Sweet tana wani sosa cinya kamar wacce Aljanu suka shigeta


Sahil ya kalleta dariya ta bashi ma ya dauke kansa yace sabo da anga bani da ita shine ake cusa min takaici,dariya Sohail yayi ya yace zata dawo ne kaima kaji ka daina damuwa,ni da zaka yarda ma da na aikeka,Sahil yace Ina? yace kaje ka gaida babar Maheera kafin nazo kace na gode da aka bani ita,Maheera harda rufe fuska sabo da farin ciki,Sahil yace bazan je ba gidan Aunty Aisha zanje tace naje wai za a kawo garar Maheera zan taho da su nan,Sohail yace har wata gara za a kawo ni na yafe kar a kashe min zuciya a barni nayi cefane na.


Sahil yace wlh sai mun karba in ba haka ba ta shiga uku da gorin dangin miji,na dinga gori kenan na dinga ce mata yar rashin gara,gwara ma a karba,Maheera tace sai ku kashe mutum da dariya jeka dan Allah,Sahil ya karbi key ya fita.

Yana fita Maheera ta mike tsaye Sohail yace zauna ke wai bakya zama kawai sai kin hau min jikina,Maheera tace to wai ba mijina bane ni shike nan bazan ci abincin ba ma ta juya zata tafi,da sauri ya riketa yace to zauna kadan amma karki dade ya gyara mata cinya,Maheera ta zauna ita kanta ba sabawa tayi ba kawai so take ta canja shi ya gane me akeyi.


Sahil yana fita yaga motocin Daddy sunzo kofar gidan,Sahil yayi mamaki,parking suka yi driver ya bude masa kofa ya fito,Sahil yace Daddy kaine kazo gidan nan? Daddy yace ae nine zuwa nayi naga zahiri,Sahil ya juya yace to muje suka shugo har palo,Maheera tana saman cinyar Sohail a zaune suna cin abinci sai dariya suke yi,Sallama suka ji kawai.


Daddy ya zaro ido ganin gida mashaallah,Maheera da sauri ta mike tsaye tana gyara mayafinta,Sohail yace Daddy? Alhaji Ali ya kalli gidan yace uhm ashe kuwa da gaske kuke yi shi yasa na kawo muku ziyarar bazata.


Maheera ta mike taje palon tace sannu da zuwa Daddy,zauna Daddy,Daddy yaso ganeta yace kece yar aikin su Adnan ce ai,tace ae nice,zama yayi yana mamaki yace Allah me iko kamarki kika amince lallai kowa baya rasa masoyi,ina ganin ai ko kamar su Adnan a yanda Allah ya tsaraki ko kamar su Adnan sai sun kai ruwa rana sai kuma gashi to Allah me iko.
Maheera dai durkusawa tayi har kasa ta gaida shi ya amsa yana ta faman furta Allah me iko.
Sahil yace kar dai ka kyasa Daddy ba kyau,shi yasa aka ce ka samu wata yar bazawara ka aura ka dinga mai da yawu amma kaki,an rasa me keka yi,idan baza ka iya ba mu yan mata kawo kansu suke wajen mu ka bamu zabi muyi maka hanya da dai dai kai,kunya Maheera da Daddy suka ji amma su twins ko a jikin su.


Sohail yace Daddy ina kwana da sassafe sai ka taho gidan Amarya,ai ba a zuwa gidan yara da sassafe,Sahil yace ina kwana Daddy ya amsa duk sai da suka rusuna sannan suka gaishe shi.
Maheera ta dinga kawo abinci tana dire masa,su farfesu ya zaci ma ita ta girka,ta shiga kitchen ta kawo lemuka da ruwa tace Daddy ga abinci dan Allah ko kadan kaci.


Daddy ya cika da mamaki sabo da saka ido sai da yaci ya tabbatar yaji ya girkin yake,yaji dadi,Sohail yace ba ita tayi bama nata yafi wannan dadi na gidan Aunty ne wannan,ai wannan ka taba cin girkinta kaji wlh ko kakar mu Iya me Koko bata kaita iya girki ba,Daddy har sinasir ta iya,Daddy yace zaka ci uwarka Sohail ni kake fadawa ko Iya me koko bata iya ba,uwar tawa mahaifiya, Sohail yace to yan zamani sai yan zamani ai,Sahil yace wannan Special ce ba irin su Zayna bace me hanci kamar tulu.

Maheera tana durkushe a kasa,Sahil yace tashi ai kin nemi Taskirar zaman ya isa haka,Daddy yayi shuru yana jinsu yayi murmushi,Sohail yace nidai ko kowa bai yaba ba tunda ni na yaba ina son abata shike nan.
To ku zauna cewar Daddy,zama suka yi yace shi aure da kuke gani Ibada ne,Sohail yace a'a mu ba sai an mana nasiha ba mun sani,da can ba a damu damu ba sai da aka ga munyi abinmu,ko gudun muwa ba a bamu ba,a barmu idan ma duka ne mu nadawa matan namu,kudin mu ne,Daddy yace ai shike nan ya mike zai tafi Maheera tace Daddy ka gaida gida.

Yace Madalla Madalla ya fita ya tafi Sahil ya bishi yana cewa da ka tsaya an kawo garar ko kwano uku ka dauki shinkafar ba komai wlh mu har abada mahaifin mu ne kai.
Daddy ya rufe motar yana dariya ya sauke glass Sohail yace gara ai ana bawa gidan iyaye nasu Daddy ka tsaya ka tafi da ta gida duk da cewar gwauro ne kai.


Daddy son gulmarsa tasa yace Sohail yanzu kai wai hankalinka ya kwanta ko kai ga ango? Sohail yace ya hankali na bazai kwanta ba da mace fa na kwana jiya,kai kuwa yaushe rabo,ni wlh na daina jin haushi ma in kayi mana wani abun Daddy na gano dalili babu mace.
Daddy ya bawa driver Umarni ya ja mota ya tafi sai dariya yake ta yaran nasa yanda suke wanke shi tas.


Washe gari Daddy ya kira Sohail da Sahil yace suzo zasu gaisa da wani Ogansa a harkar Business,yace yana bukatar yaga yaransa gaba daya.
Sohail yana kwance yayi pillow da cinyar Maheera suna kallo a hakan ma da kyar ya yarda ya kwanta a cinyarta itace ta nace sai ya kwanta.
Sahil ne ya fito a shirye yace ka manta Daddy na jira,Sohail ya mike zaune Maheera tace ai ya shirya shima,Sahil yace da jallabiyar zai fita? tace ni to bana so wata ta ganshi,Sohail yace kyaleta muje Sahil hakan wannan yarinyar bata yarda dani,ai zata zo fita ne Allah zai kaimu itama ai tana so ta yafa mayafi,muje wallahi kika bari na fita haka kullum da hijab zaki fita.
Dariya Sahil yayi,Maheera tace muhe to ka canja abinka,tashi yayi ya wuce bedroom kafin ta shiga ya kulle ya sa key kar taga tsaraicinsa shi kam.
Sai da ya shirya ya fito ya wani mika mata turare fesa min,Maheera ta karba ta fesa masa,Sahil tausayinta yaji tabbas tana da matukar hakuri sosai ba karamin son Sohail take ba.
Sai da ta rakashi har mota suka tafi.


Suna tafiya Sahil

Please Login or Register in order to submit comment