Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yace mu hadu a kauyen zan tura muku kudin mota kar ku bata mana lokaci sannan idan kunne yaji jiki ya tsira,su Kawu Nafiu da sauri suka ce ba damuwa.
Daddy ya kira,ya sanar masa yace to fa muma kuma Allah yayi zamu daure mu ja daya ciki,Daddy yace ban gane ba ku ja daya wanne lokaci kuma? Yace aure nima zanyi,Daddy ya ja tsaki yace a gidan ubanwa zaka saka ta a wannen gidan karami na Sohail? Arna ne ku daki uku da palo kawai, Sahil yace sanda kayi auren fari naga a gidan haya ka zauna daki ashirin da uku a gida daya,kowa daki daya daya,Mama Asmau babu layin toilet da bata sha ba.


Daddy yace kaje kayi ba ruwana,Sahil ya furta dama kawai fada maka nayi ba wai wani abu ba,to kaje Allah ya taimaka,Sahil yace Ameen matar sunanta Islaha yar duma duma ce ma,ko kai ka ganta sai ka karar da dukiyarka a kanta,Daddy yace ni ina ni ina yarinya ma da har zan karar da dukiyata a kanta,idan ma kana so baza ka samu ba dai cewar Sahil,Kwafa Daddy ya ja,yace to me kake jira ka kashe wayar mana,da kudina to a ciki cewar Sahil,"Daddy"yace na'am da masifa ya amsa,Sahil yace akwai wata Hajiya Kulu me tuwo tuwo a tasha ta dace da kai wlh da zaka aure ta da ka huce takaici,Daddy wayarsa ya kashe yana masifa me tuwo tuwo lallai yaran nan sun rainani kamata da arzikina wanda a yanzu zan iya auren irin matan su hudu ma yara yan mata,amma yazo ya fada min wata Kulu me tuwo tuwo da kuwa nayi asara.


Washe gari Sohail da Sahil suka tafi Taraba a motar haya,Islaha tana gefen Sahil minti kadan ya kalleta ko motsi tayi sai yace mene ne? Me kike so? Itama Islaha duk ta haukace irin Maheera soyayya ta gigitata,ga Maheera sai ziga Islaha take akan ta auri Sahil tayi sauri.
a can suka samu su Kawu Nafiu,an gansu a motar haya ba wanda ya kula su a gindin bishiya suka zauna,suma su Twins ba a motar gida suka je ba ga Islaha anje da ita.


Gidan Lalai ta musu jagora suka tsaya a waje Islaha ta shiga da Sallama,a tsakar gida ta iske Lalai kwance saman tabarma hannayenta biyu a ruruce amma sunyi sauki ta shanya su iska na fifita su.
Tana ganin Islaha tsoron Islaha ya kama Lalai,tace Islaha...ta mike da kyar tace sannu da zuwa Islaha,Islaha tayi mamaki tace me ya same ki Lalai? tace mutanen boye ne labari sai an zauna,Islaha tace da baki nake fa.


Lalai tana daga zaune da daura kirjinta zanin ma ya warware ya dawo cikinta nono rabebe ana gani kamar takalmi yaraf a kwance,Islaha ta manta da nonon Lalai a waje ta kira baki tace ku shigo,Lalai ba hannun da zata gyara zaninta,Sahil ne ya shugo.


Kallo daya yayiwa Lalai sai ya koma bayan kawu Nafiu yana ta kyalkyala dariya,Sohail bai sani ba ya wuce gaba shima yayi arba da nonon Lalai,baya ya dawo bayan Kawu Tukur yana ta dariya,yace Allah ya so ni na Matata chakare chakare ne,Sahil handkerchief yasa a bakinsa ya cusa a ciki wai dan kar sauti ya fito.


Sohail yace mudai ba ruwanmu su Kawu Nafiu nake ji dai dai suce kar su kyasa,Kawu Nafiu sai yanzu ya gane abinda suke yi,da sauri yace Allah ya kiyaye ko ni na wuce ajin wannan me zan kalata a jikinta,bare kuma ni cewar Kawu Tukur.


Lalai ko a jikinta dake mutanen kauye ne,suka zauna a sabuwar tabarma,Sohail da Sahil sun kasa boye dariyarsu sai dariya suke suna kallon juna,Lalai ce tace Islaha miko musu ruwa mana,Sahil ya kalli Kawu Nafiu ya toshe bakinsa da hannu yace kaiiii....yana dariya,a sace kawu Nafiu ya tsawatar musu ya dinga musu signa,Sohail ne ya gaji da gani yace Islaha mu bamu saba ba azo a suturta nonon Iya.
kai ubanka kawu Nafiu ya zungure shi yana zaginsa kasa kasa.
Sahil yace Iya Lalai taci daka rannan,ai nine nan....ya karasa da dariya...dama nace sai ta kwana tana daka,Lalai ido ta zaro,Sohail yace yes yin mune,shuru tayi dan bata san kan abin ba.
Kawu Nafiu ne ya katse zancen suka gaisa da Lalai Islaha tana daura mata zani Sahil yace Allah wannan kadai ya isheka comedy...Sohail yace sai ka kwana kana kallon abinka kai ta dariya wallahi, wai Nonon Lalai suke nufi,Islaha ita kanta dariya taci karfinta ga dariyar nonon Lalai ga na su Sohail.
Abdulrazaqu ne ya shigo yace wa nake gani kamar Islaha yau sai na tattaka ki a gidan nan,shine kika mana asarar kudi sabo da ke yar iska ce yanzu kin lallabo kin dawo a ciyar dake,shegiya tambadaddiya ke kam kinyi asara,yar tsiya a haka zaki kare,ace yaro me kudi kamar Ibrahim,to ki sani har yau muna kan bakanmu Ibrahim zaki aura me ruwan nairori,shi muke so shine zabin mu.
Lalai kuwa sanda take daka ita tasan me ta ji me ta gani,sai faman cewa Abdulrazaqu take kai kayi shuru dan ubanka amma sai faman masifa yake ko bakin ma bai kula da su ba,tun a waje yaji mutane na labari Islaha tazo shine ya taho da masifarsa.






Free page 1&2 400 ne


0175487861
Asmau Garba Muhammad
Gtbank










AsmaBaffa
08061929616
[7/17, 3:18 PM] Asmabaffa: 🪸MUMMUNAR DABI'A 🪸
46-50




Official


By
AsmaBaffa




SADAUKARWA NE GA 'YATA TASNIM




Page naki ne
MARYAM T BALIYA






MASU AUDIO BAN YARDA WANI KO WATA YA JUYA MIN NOVEL BA IZINI BA.








Sohail zaiyi magana Kawu Nafiu ya hanashi da sauri yace fadan yan uwa ne ba ruwanku da shi,neman aure muka zo ku bari dan Allah muyi lafiya,shuru suka yi.
Lalai ce tayi magana tace marabanku lale marhabin sannunku da zuwa,Islaha baki muka yi ne daga Amurka? ko kuwa daga ina an bar ni a duhu?
Su Kawu Nafiu ne suka gaishe ta sannan ya mata bayanin abinda ke tafe da su,yace kuma Alhmdllh yaro da yarinya munga sun daidaita kansu shine muka zo a hada mu da iyayenta maza domin shi neman aure da maza ake yinsa ba mata ba,Sohail yace kwarai kuwa yafi inganci ma,Islaha dai ta shige daki taki fitowa wai ita kunya,amma ta rabe a jikin bango tana jin me ake cewa.


Abdulrazaqu yana tsaye kerere da rigarsa ta gona dukun dukun ya furta mu baza mu bawa kowa ba sai Ibrahim mun rigada mun masa Alkawari shi zamu bawa,Islaha ta Ibrahim ce,Kawu Nafiu yace to ai mun ji labarin zuwan Ibrahim, abinda yayi Ibrahim shi yayi Sahil gasu kannensa ne uban su daya,kuma dama Islaha budurwar Sahil ce tun farko Ibrahim neman fada ne ya kawo shi.


Abdulrazaqu ya dora hannaye a kai yace yanzu na tabbatar 'yan uba masifa ne shi yasa na godewa Allah da Lalai kadai Mahaifi na ya aura har ya koma ga Allah kuma ni kadai ta haifa,Sohail ne yace kai lallai living thing ne babba yanzu kai kadai ta haifa dama duk kaine ka dawo mata da nono haka sai kace inji ne a bakin ka sai kace ta haifi yara ashirin,Kawu ne ya bigi Sohail,Sahil yace dama tun tana budurwa bata yi farin jini ba babanka ne kadai yaje zance shima sai da kyar abokai suna ziga shi lokacin tana tallan Alkaki.


Lalai tace wlh tunda nake ba kowa yasan zamanin da nayi tallan alkaki ba amma kai aljani ne wlh wannan ba mutane bane ku tashi ku tafi wajen Iyayenta maza,bazan iya ba dama tunda naga kyawunku haka naji a jikina ba mutane bane,Kawu Nafiu ne ya wayance yace tsokana suka yi abin ne yazo a daidai ba haka suke nufi ba, Lalai ta dan saurara a tsorace tace ina jinku,Kawu Nafiu yace kawai a raka mu wajen mazan.
Abdulrazaqu yace bazan je ba ita da take son auren ta taje ta kaiku ya juya tare da ficewa.

Islaha ce ta fito daga daki Sahil yace a nan kika zauna kenan? Ina turmin dakan? Islaha ta nuna masa,yace kinyi kokari gaskiya tafiya suka yi ta raka su gidan Baffa Gali,ganin su Sohail yayi Imani akwai kudi da sauri ya kira maza uku a dangi yace suzo anzo musu da maganar aure,har ya manta da Ibrahim,Kawu Tukur yace Sohail da Sahil su basu waje su jira a waje,sabo da baza su bari ayi abin kirki ba,suna mikewa Matar Baffa Gali ta fito dauke da danta a hannu ta zaro nono ta gaban riga yaron yana dauke a hannunta bakinsa yana a nonon yana shan abinsa.

Sohail ya kalleta ta wuce bagazan bagazan ba wani tafiya ta nuna macece,tace sannunku ta wuce, Sohail yace kai jama'a zanje na gwada akan Maheera, kun ganta da Danta bata daina haihuwa ba ai na zaci tsohuwa ce,Kawu ne ya harare shi,Sahil yace wato dai na fahimci a garin nan nono bashi da daraja da kima abin banza ne,Baffa Gali yace kuma dai kwa fada nayi nayi ta gyara taki matan kauye sai hakuri.
Iska ce ta taso filfil Sohail yana boye dariyarsa yace iska tana ta fifita shi,wai matarka ce? Baffa Gali yace ae me dakina ce,Sohail yace tab sannu,kuma idan ta wuce kana jin ta birge ka a haka? Kawu ne ya kore su nace kuje waje zan neme ku.


Fita suka yi kofar gida Islaha tana ciki wajen matan Baffa Gali,wasu yan matan kauye ne suka fito su uku suna tafiya,sai kallon su Sahil suke yi,Sohail ya kalle su suka hada ido da sauri suka dauke idon su tare da karawa tafiyarsu sauri,Sohail yace kai kuzo nan,a tsorace suka karaso 'yan matan,pic din Maheera dake kan wayar sa ya nuna musu yace kunga wannan? Suka daga kai ae suna dariya suna jin kunya,yace Sunanta Maheera duk duniya ba irinta a yanzu,kun san record din data kafa? ta kafa tarihi babba,domin itace wacce ta aure ni,Dariya matan suka yi,sun zaci wani babban abu zai fada da ta kafa tarihi a kai,Sahil yace ba kwaila bace irinku kuma,matan suka ji kunya suka fece da gudu,suna cewa kinji kamshin su kuwa,rabewa suka yi suna lekensu ta bayan bishiya, baki Sohail ya tabe suka ci gaba da hirar su da Sahil.


Baffa Gali da wuri suka Amince suka ce su ko yaushe suka shirya ba matsala su saka ranar daurin aure,gani suke su Sohail wasu attajirai ne,sai da suka fito suka bawa su Sohail labari yace ku fada yaushe kuka shirya? Sahil yace yanzu ma a daura,Kai shashasha rana za a tsayar su sunce wata biyu,Sahil ido ya zaro yace zan iya mutuwa sauri nake wata daya kawai zan iya hakuri, a matse nake Kawu bana bacci,Kawu ya zaci irin sha'awar nan ce ta damu Sahil harda daukan abin da muhimmanci yace to Inshaallah bari a fada musu.


Ya koma ya sanar musu,suna ta jira a basu kudin aure da komai su hau kai su danne sai da aka kira Sohail aka fada masa har sadaki da komai suka ce million daya,Sohail yace komai da komai? Suka ce ae mu yaran mu tsada ne da su,ba ragi? Cewar Sohail,suka ce ba ragi,yace ku duba mana ko dubu hamsim ku kankare,ba kudi ne damu ba kyawun ne kawai,suka ba ragi daga haka, yace ba matsala ya za muyi zan tura mata a account.


wani dukul suka ji,Baffa Gali yace ai iyaye ake damkawa, Sohail yace akan na baku bacci ya gagare ku gwara ku bari a bata abinta, kuka karbi kudin nan baza ku ji da dadi ba da kanku zaku dawo da su, Baffa Gali ya zaci kara zasu kai su wajen yan sanda irin ai zasu je wajen malamai su rufe musu baki sunci banza,nan take suka ce ba matsala,Sohail yace akwai me account? Baffa Gali yace ina da shi,nan take ya bayar aka tura masa,sai washe baki suke banza ta fadi.


Sallama suka musu suka fito,Baffa Gali yace munci banza yau zanje wajen malam Idi a rufe musu baki babu wanda zai tambayi kudin,har Islaha baza ta taba bude baki tace ina kudin aurenta ba,dariya suka yi Gali yace ai ni ko aron gona na karba ta mutum to da kanka zaka zo ka siyar min da gonar, idan kuwa kudi na karba bashi to sai dai a lahira na biya suna ta dariya.


Kawu Nafiu ne bayan sun fito yace ni naga saurin yardar su babu ko bincike sam sam,basu san wa zasu bawa 'yar su ba sun yarda,wannan yarinya bata da gata wlh,ace ba bincike kawai sun karbi kudin aure har an sa rana, Sahil yace sun taimaki kansu da suka yarda badan haka ba duk sai sun kwana akan kayoyi yau.


Islaha tana fitowa Sahil yace Amarya kusa da su ta karasa tana murmushi,Sohail yace an tura musu kudin aurenki komai da komai million daya kudina yanzu saura kadan a accnt kin kara min arziki na dade ina tarawa.
Hawaye Islaha ta fara ta rike Sahil tana shagwaba Allah....Allah...ni...uhmmmm...ya za ayi ku basu kudin...baza fa su bani ba...Sahil yace wayyo Kawu dadi shagwaba,Kawu da sauri suka yi can gaba sunji abin na twins ba kunya.


Kawu Nafiu,yace ayi sauri a aurar da Sahil wlh sai yayiwa yar mutane ciki bashi da kunya, Kawu Tukur yace yanzu watakil da kake gani Matar Sohail watakil ciki ne da ita,kasan irin yan shashashun yaran nan wlh sunfi kowa shegen sha'awa da son mata,Kawu Nafiu yace baka gani ba nonon tsohuwa ma kalla suke.


Sahil yana wani Lallashin Islaha tace ya za ayi ku basu kudi kun san baza fa su bani baaaaa.....ta karasa da kukan shagwaba,Sohail yayi dariya yace ka fara shiga Masifa Sahil,ina nan ina fama da Maheera zaka gane aure ba hutu a cikinsa.


A haka suka koma gidan Lalai,Baffa Gali har da sawa a biyo su da fura da nono har gidan Lalai,ga abinci rogo dafaffe da kuli,Lalai tana jikin bishiya inda suka barta zani ya sake sutalewa ya koma kasan ciki,Sahil dariya ta kamashi yace muna ta zuwa a sa'a,Kawu kalli suka sake sakin Dariya,Sahil ya juyo ya kalli Sohail yace yayi malafa da shi.


Lalai tana kallon su aka kawo musu rogo da fura taga Ibrahim ma ko ruwan su bai sha ba bare yaci abincin su,Sahil ne ya bude kwanon ya dauki sandar rogo fari tasss da shi ya dafu sosai,Sohail yace kawu ga takwarar mu kawu rogo wlh,Kawu yace takwara kuma waye me suna rogo anan? Sohail yace kawu ta wandonka ko basa kama irin tamu ce dukkanmu maza suna kama data wando,Kawu ya dauki kwanon rogo daya yace muje Tukur muje daga waje wannan yaran sai su kunya ta mu.


Sohail sunci iya rogon kawai,suna ta satar kallon Lalai,tace amma a nan zaku bar Islaha har lokacin aure,Sahil yace ae da jakarta ta taho ma ai,tana nan sai an daura sai na tafi da abata,Lalai tace hmmm kai ko kunya babu? Sahil yace ba gwara ni ba iya a baki ne ba zani na saki ba kirji waje, shuru ta masa sai da suka yi sallar la'asar suka tafi,a cikin gari zasu kwana sun kama hotel,Sohail ya kira Maheera yana kwance a room dinsa yace sai gobe fa muna hotel,tace tsoro nake ji fa,ba kowa kuma baka fada min ba sai yanzu dare yayi bare na kira Juwairiyya tazo mu kwana tare,Ko na tafi gidan Aunty Aisha tunda dare baiyi ba yanzu nayi sallar Isha? Da kyar ya amince ta shirya ta tafi gidan Alhaji Saminu.


Aunty Aisha tace sannu amarya yau ina da babbar bakuwa,Maheera tayi murmushi,dakin da zata kwana ta kaita tace to abinci fa? Maheera tace Alhmdllh naci kafin na fito,duk da haka sai da Aunty Aisha ta kawo mata.
Har part din Alhaji Saminu ta rakata suka gaisa sannan suka dawo dakin suna ta hira,Aunty Aisha sai labarin magungunan mata take yiwa Maheera,Maheera bata ma sansu ba,tace wai ke bakya amfani da ko wanne ne? Maheera tace uhm ina Amarya Aunty Aisha,ni duk wannan shaye shayen ba yi nake ba tukun tunda ba abinda muka yi har yau.


Ban gane ba? Maheera tace ko romance bamu taba yi ba to da alama ma bai san me ake yi ba,Aunty Aisha ta rike baki tace duk uban soyayyar nan? Sannu Maheera Allah ya miki Albarka da wata ce wlh da yanzu anji kansu,kuma wai suna karatun Qur'ani da adduoi kuwa? Aljanu basa son me nacin karatun Qur'ani suna barin jikin mutum,Maheera tace kullum sai sunyi wallahi ko da dare ko da safe,Azkhar ma baya wuce su sabo da wacce ta rike su ta dora su a hanya.


Aunty Aisha tace kina addua kema? Maheera tace sosai kullum cikinta nake Aunty.
To ya kina nuna masa yanda abin yake? Nayi nayi yaki fahimta jikinsa ma bai so na gani ba sutura,Aunty Aisha ta jinjina kai tace to fa,ikon Allah mu dage da musu addua inshaallah zasu dawo dai dai cewar Maheera.
Washe gari da wuri ya kira Maheera yace ta koma gida,haka ta koma ta gyara gidan tayi girki sabo da suna hanya.

Bayan sati biyu Maheera,Islaha da Aunty Aisha su suke shirin biki abinsu amma Sahil yace ba abinda za ayi kawai aure za a daura su taho da Amarya,yanda aka hadawa Maheera lefe haka aka hadawa Islaha.
Alhaji Umaru ne ya kira Sahil yace ya fara zuwa Office za a nuna masa aikinsa zai fara,sai murna yake,bayan kwana biyu ya fara zuwa katafaren Office dinsa,kansa wajen da Sahil yake aiki abin kallo ne.
Alhaji Umaru ne ya bawa Sahil gida katafaren gaske part biyu sama da kasa ko wanne part,yace gudunmuwar aure ce su koma ciki shi da Sohail kowa da part dinsa,amma komai iri daya ne a ciki abinda ke wannan part din shine a can,sai ka rantse ma a daya kake ba babanci har komai na kitchen da furniture.
Kayan abinci an zuba,gidan ya sha fulawoyi da interlock ga wurin parking daban na motoci,Sohail gidan da suke ciki sai dai a bawa wasu haya.


Islaha tunda taje ba wanda ya bata sisi a kudin aurenta,Lalai tsoro take ji bata iya cewa Islaha komai bata ma iya sata aiki sai dai idan tayi girki Islaha tana ci sai ta dinga gallawa Islaha harara,ko bi ta kanta Islaha bata yi sam.
Sahil yau ya kira Islaha yace yaya sun baki kudinki kuwa? Islaha tace sisi basu bani ba,Sahil yace to kyale su karki tambaya kinji,tace to dan Allah iyaye nane karka musu komai yace ba abinda zai faru ai.


A daren cikin dare Baffa Gali yana tsaka da bacci sai yaga an daga shi sama sai ya tabo rufin kwano sai a sake shi ya fado saman tarin wata kaya,kayoyi ne cako cako kamar Allura haka ake masa kawai,ihu yake da kururuwa mutane suka cika gidan cikin dare ba a ganin kowa ba a wanda ke ganin wasu kayoyi a wajen,sannan ba a ganin Baffa yana tashi sama amma Baffa Gali Ihu kawai yake da kururuwa a kwance,jikinsa duk yayi bula bula kamar an caccake Allura,yana zan bata kudinta wallahi ban cinye ba na tuba,yanda aka yiwa Baffa Gali shima haka sauran duk wanda suka ci kudin nan ba wanda ya kwana lafiya,Amma Abdulrazaqu shi yaci banza duk zagin da yayi ba abinda aka masa.


Da sassafe sai ga matar Baffa Gali da kudi a katuwar leda ta kawo gidan Lalai ta damkawa Islaha tace gashi nan ki irga kwandala idan babu kiyi magana dan Allah inji Baffanki Gali,yanzu suna asibiti duk an tafi dasu,anya Islaha ba Aljanu zaki aura ba?
Islaha tace me ya faru da su? Lalai ta fada saman gado ta kudundune tace kudin Aljanu a dakina ku fitar min da shi,na dade ina tunanin Islaha da Aljani take soyayya,wlh ni nasan me na gani sanda na kwana ina daka,Islaha tayi dariya ta more tace Lalai duk son kudinki ga dubu ashirin ko kifi kya ci,Lalai tana lullube tace Allah ya kiyaye, Islaha ta ja kudi ta boye kasan gadon Lalai,Lalai ta fice da gudu ta bar gidan,tun daga ranar Islaha kadai ke kwana a gidan, Lalai ta koma gidan dangi sabo da akwai kudin Aljanu a dakinta.

Yau Sahil yana Office wani Hakeem shima babban ma'aikaci ne yazo ya bashi key din sabuwar mota me tsadar gaske yace ta zuwa aiki ce dama suna bawa mutum mota yawanci.
Murna wajen su Sohail ba a magana.
Biki yana ta kankama kamar wasa nan ma Daddy sai Iv ya gani kawai an kuma saka masa marigayi,baiyi magana bama yasan halin su.
Ana gobe daurin aure Ibrahim da Adnan suka bar gari ma gaba daya suka wuce kasar waje sabo da kar ma suje.


Ango ma ba wata gayya da suka yi,mudassir yayi yayi suyi gayya suka ce sun gaji da biki ba a dade da yin na Sohail ba,ba a fi wata biyu da wani abu ba baza su wahalar da mutane ba,mutane yan tsirari ne suka je daurin auren,Islaha dai gyaran jiki sai ta dawo birni za ayi mata,tana can zaune gidan Lalai ita kadai kama mayya,kowa tsoronta yake ji zance ya watsu Aljani zata aura.


Ana gobe Maheera da Aunty Aisha suka tafi can ,suka samu Islaha ba abinda ya shafe ta a dangi duk an guje ta sabo da tsoron Aljanu,ita kadai ta hado cefanenta ta dora katuwar tukunya wai miyar biki zata yi,Maheera suka dinga dariya,Komai na girki ta tanadi abinta a cikin kudin auren ta iba,Aunty Aisha tace me zan gani haka? Dariya Islaha tayi tace to sunki zuwa gaba daya dangina sun gujeni,wallahi kowa naje har gida na fada musu gaba daya dangin uwa dana uba duk na fada musu har makwafta duk sunce baza su zo ba,gidan Baffa Gali har rokon su nayi mazan dai sunce za a daura aure da su a bisa laluri,Maheera suka shige dakin Lalai suna ta mamakin kalar kauyen da gidan da Islaha take,kayansu suka ajiye suka fito,Islaha har girki tayi musu suka ci abin su sannan suka fara girkinsu su uku rak,Maheera da Aunty Aisha masifar Tausayin Islaha suka ji wai ita kadai a gida,ga dangi ma ace an rasa me zuwa biki,Aunty Aisha tace Allah wadaran wannan dangi naku,baki mori yan uwa ba wlh,tace uhm.
Sai da suka yi nisa dare yayi suna ta aiki sannan matan su Baffa Gali suka zo,sai makwafta suma suka yi shahada suka shugo,ana yin sallar isha suka gudu.


Su uku suka yi miyar su ta taushe da tuwon shinkafa da safe sai farar shinkafa da miya an yanka cabbage daban,pure water aka siyo da yawa,kafin yan daurin aure su iso sun gama komai sunyi wanka,Idon Amarya duk ya tasa sabo da hayaki.
Sai 12 angwaye da su Daddy suka zo Daddy sai tsaki yake yana korafi,a rasa inda mutum zai nemi aure sai wannan kauyen.
Sohail,Ango da abokai suna motar su sai nishadin su suke yi,Ango yace yau Islaha shike nan sai abinda nace da ita kuma,Sohail yace uhmm zaka gane kurenka ne.


Sai 2pm aka daura bayan an idar da Sallah,ana daurawa Sahil ya mike yace ku tashi abinda ya kawo mu ya kare an gama,Daddy ne ya ja babbar rigarsa wai yayi shuru,Sohail yace yau ba ruwanka Ango lukwi cikin bargon ku,Baffa Nafiu ya harare su,Mutanen kauyen sai sallallami suke angwaye yan iska ne.
Amarya Islaha ta zuba kyau duk da haka sabo da a cikin na lefe Maheera ta dakko mata leshi dankarere milk and brown tayi kyau sosai,kayan lefen dama suna gida Abuja,Sai da aka daura sannan Lalai tazo,ita da gidanta amma ka rantse bakuwa ce,suka bata abinci tace o.o.o aci dadi lafiya Allah

Please Login or Register in order to submit comment