Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

zamu tafi tare,sai dai kazo ka d'auke ni anjima"


Kamar karfe nawa?


"Kana da agogone"?


Oho,nikam ki fad'amin.


"Yanzun 8:12 zuwa 10:00 sai kazo ka d'auke ni"


Toh shikenan yace Yana zama,d'aukar abincin yayi ya cigaba da ci


Sumayya Kam fita tayi da yaron,sai da sukazo kusa da titin first bank taga shagunan a bude kamar Rana ga wuta ako ina,"tsaya Kai mu Shiga shagon nan" tace ma yaron tana Kama hannunsa suka tsallaka titi,shagon ta shiga"excuse me"tace ganin Mai shagon inyamurine


Yes ma barka da zuwa shigo ciki customer ki duba Kaya


Da mamaki sumayya ke kallonsa Ashe ya iyya hausa,yauwa "sannunka,Kaya nake so"


Ok wani iri?


"Jallabiyoyi"


Ok ki shigo gasunan kizo ki zaba Wanda ya miki,yace Yana zazzaro Mata jallabiyoyi sunfi kala goma


Guda uku sumayyaa ta zaba masu masifan kyau fari da baki Mai maiko sosai da hula sai Kuma Mai aiki ruwan sararen samaniya,takalmi ta sai Masa Mai kyau na tambarin Adidas silifas ne,sai t-shirt da 3quiter sai Jean's,sosai Sumayya Tama Al'ameen sayayya harda Turare na maza ta sai Masa da abin haske Kai da gemu,sai kusan 9:26 suka je gidan Matan da zatama lalle


Lalle Sumayya ta Mata baki da ja, Al'ameen tun 10 yazo Amma Basu Gama ba,ya zauna Yana jiranta a kofar gidan


Suna Gama lallen Sumayya ta karbi kudinta laidan da ta aje a kulle a gefe na kayan da ta saima Al'ameen ta saba,waje ta nufa


Tana fita taga yayan khadija a zaune


"Yayan khadija mu tafi Koh"tace Masa


Kun gama?


"Eh mun Gama"


Ok yace Yana mikewa tafiya suke shuru,can dai Al'ameen ya kasa hakuri Jin yanda yakejin motsen laida a hannun Sumayya


Sumayya nikam laidan menene a hannunki Kato haka don nasan dai laida kananu basa Kara haka?


"Abu na saya"ta basa amsa


Kala baice ba suka cigaba da tafiya har suka Isa gida,Dayake sunyi wanka dazun yasa Kaya kawai suka chanja


Yauma kwanciya sukayi tare bayan Al'ameen ya Gama kwsan rabonsa


Washe gari da safe bayan Al'ameen ya tafi masallaci, Ghana must go nasa ta bude Daman jiya ta kirga kayan jallabiya ukune sai wando da riga D'aya sai 3quiter D'aya sai armless D'aya sai gajeren wando biyu vest D'aya, kwasosu tayi ta juye a basket na dattin kayanta,sabbin kayanda ta suyo jiya ta mayar cikin bakkon ta shirye Kamar yanda kayan suke a kirge sauran Kuma ta aje sai Randa ya wanke kayansa biyu masu dattin saita musanya Masa,


Vaseline insa da ya kusa karewa ta juye a laida daukar manda ta siyo Masa tayi ta diga a cikin gongomin kamar yanda baseline insa yake, Haka ma tamasa da sabulu


Sai 6:30 Al'ameen ya shigo gidan


Sumayya Kam ganin ya shigo d'akin da sauri ta d'auki takalmin sa ciny'ayyen ta saka Masa sabo,ta dawo d'akin,kudi ta basa 2k yasai musu dankalin turawa boket D'aya sai k'wai guda biyar,


Fita yayi a d'akin bayan ya karbi kudin yazo ya zura takalminsa,sai Kuma ya cire da sauri,ya ringa laluben bakin dakalin Amma wayam baiji takalminsa ba


Sumayya!!ya k'wala Mata Kira


"Na'am"Sumayya ta amsa tana fita a d'akin itama


Sumayya Banga takalmina ba pls ki duba mini Mana?


"Ba gashinan a gefenka ba" tace tana kallonsa


Wannan ba nawa bane


"Nawa kenan?kadaisan banda takalmi irin wannan soson"?


Amma ni sai inaji Kamar ba nawa bane,nawa fa da laushi sosai ya kode


"Toh wannan in fa",ta tambaye sa tana mamakin fahimta irin nasa


Kamar sabo sabo,


"Hhhh lalle zaka tafi da kafa kenan tunda dai ga takalminka kace Wai ba naka ba"


Sumayya bafa Wasa nake ba Wannan ba takalmina bane


"Nidai naka na gani atoh"tace tana komawa d'akin


Al'ameen Kam ba yanda ya iya Haka ya saka takalmin Amma har ransa yanaji ba nasa bane.


Bayan fitar Al'ameen Sumayya aikace aikacen ta na gida ta Gama ta d'aura ruwan zafi a kittle.


Al'ameen Kam bakin kasuwa yaje ya musu sayaya ya kamo hanyar gida




Bayan Al'ameen ya dawo Sumayya ta soya dankali da k'wai sai ta hada musu tie, rufewa tayi ganin Al'ameen ya Shiga wanka


Al'ameen aban d'aki mamakine ya kamasa Jin sabulunsa na kamshi ,Amma baiyi magana ba bayan ya fitoh, d'aki ya Shiga a hankali ya bude bakkon sa jallabiya D'aya ya zare a ciki ya zaro gajeren wando da vest.


Sumayya na zaune akan kujeran tana kallonsa saka wando yayi da vest sai Kuma taga ya tsaya Yana tattaba vest in,Amma baiyi magana ba ya d'auki jallabiyar yasa,sai Kuma ya juye kayan bakkon duka a cafet Yana tattabasu.


Sumayya!ya kirata


"Na'am"tace tana kallonsa


Sumayya wa'innan ba Kayana bane?


"Akan me zakace haka"


Sumayya wa'innan Sabine kijifa kayan kamshin sabbin Kaya suke bama Turare ba kiji da karfi fa kayan ba masu laushi irin nawa bane?


"Nidai naka na gani"


Sumayya me Kika sayo jiya da naji laida na kayo kayo a hannunki?


"Ina ruwanka"ta basa Amsa


Indai baki fad'amin gaskiya ba toh bazan fad'a Miki wacece kamila, menene hadin mu da ita ba


Tabe fuska Sumayya tayi "Gaskiya n................









πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* πŸ˜‰




πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Turare suna d'ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa*


πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da* *gyara*


πŸ€πŸ€πŸ€ *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace*


πŸ€πŸ€πŸ€ *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE*


πŸ€ *Na tsunguno(habil)*
πŸ€ *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* )
πŸ€ *Turaren turara jiki after birth* ,
πŸ€ *Na d'aki(halud Al'oud)*

*UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* πŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌ


πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna bada d'aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa*


πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria*


Contact them vie
πŸͺ€08028827241 or 09033791049
IG @umsadincense


πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€
πŸ§‘β€πŸ¦― *MATAR MAKAHO* πŸ‘¨β€πŸ¦―
~ Na ~

πŸƒ *Rukayya* *Ibrahim* πŸƒ

✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwaπŸ‘Œ
free book 🀧


Page 3️⃣8️⃣&3️⃣9️⃣
"Ni Kaya na saya" ta basa amsa


Wani irin Kaya kenan?
sannan Ina Kayana?


"Nina yarda kayayyakin ka duka sabo na sai maka Naga nakan sun kode,Amma kayi hakuri bazan sake ba" tace tana Kama hannunsa dake kokarin zare jallabiyan jikinsa


Sumayya akan me Zaki sayamin Kaya bazaki fad'a mini ba saboda bani da ido saiki zo ki musanya mini,kamar wani yaro.


"Kayi hakuri kaga yanda jallabiyar nan ta karbe ka kuwa yayan khadija" tace ta ja maza zip in gaban jallabiyar,hade da d'aukar Turare ta fisa Masa,vayan ya shafa Mai


Nagode Allah ya miki albarka ya hanani Miki butulci a rayuwa Sumayya


"Ameen" tace tana jera abincin karyawan, Bismillah ta Masa suka fara ci cikin kwanciyar hankali


Bayan sun Gama cin abinci tattara Kwanukan yayi yakai waje,bayan ya ajeye, d'akin yadawo


"Toh yayan khadija wacece kamila"Sumayya ta tambaye sa


Nifa nayi Miki Alkawari ,ai basai kin Kara tambaya taba nida kaina Zan fad'a Miki kome Daya shafe kamila.


"Uhmm ba Dole na tambaya ba tunda sai jamin Rai kake yaufa da wure na Gama aiki Amma sai wani sham kamshi kake"


Nasha kamshin, kema saiki Rama.


"Wallahih ka Gama iyya jarabanka bazan biye maka ba sai naji lbrn nan ehen"


Toh zoki zauna a kusa Dani samun lbrn yafi Dadi,yace Yana zama akan kujera


Saboda tsabar sonjin lbr yasa Sumayya mikewa da sauri tazo Kan kujeran ta xauna kusa dashi


Hannu yasa ya matsota jikinsa a hankali ya rungume ta a jikinsa cikin sanyin hallintarsa murya a sanyaye yace Sumayya!


"Na'am yayan khadija"


Yau Zan baki labarin kamila Amma saikin ji labarina Nima kafun ki gane lbrn kamila dakyau.


"Yauwa Aiko Ina sonjin lbrn ka da dangan takarka da gidan ADARA duk da Ina tunanin dangin mahaifinkane Amma halayenku sun banbanta,hakan matsayinka da khadija a gidan nan na fahimci a kaskance kuke ba Kamar sauran Yan gidan ba"


Duk xakiji insha Allah Koh Nima Zan samu amsar dalilin auren mu Wanda har yau bansan dalili ba.


"Wai kana nufin ba Kaine kace kana Sona ba,aka aura maka ni "?ta tambaye sa cikin zare ido.


Nima ban sani ba Sumayya bansan dalilin auren muba Amma koma menene inaji a jikina insha Allah haduwar mu dake alkhari ce

"Insha Allah insha Allah yayan khadija" tace tana share hawaye Daya gangaro mata


Gyara zama Al'ameen Yayi a hankali ya fara magana................


*Shikaru Talatin da biyar da suka wuce baya* πŸ•’
Malam Yusuf sumul, shine cikekken sunansa da aka Sansa dashi matashine Dan shikara 35,Yusuf mutum ne Mai Hakuri addini ga kawaici baid'auki duniya da zafi ba,Yana da tsananin zurfin ciki duk yanda zaka zauna dashi bazaka taba fahimtar wani abu a tattare dashi ba shiyasa ba Wanda yasan shid'an inane Koh daga Ina yake, duk da kowa ya gansa Kuma yaji yanayin hausar sa da maganar sa Dole yasan cewa ba D'an kasa bane .


Alhaji Rabi'u ubangari. Wanda akafi sani da ubangari,maikacin gonnati ne Kuma Mai rufin asiri sosai,Yana da Mata biyu.


shine Mai gidan Yusuf, saboda tsananin hankali da nitsuwar yusuf yasa ya d'aukesa Kamar D'an gida ya basa d'aki a cikin gidansa,Yusuf na Masa aikace aikace kamar zuwa kasuwa wanki da gugan kayan yaransa da NASA na kansa Yana Kai kananun yaransa makaranta ya dawo dasu,


Yaran ubangari guda biyar ne sai yaran Yan uwansa maza biyu Mata hudu,kenan yara goma Sha D'aya ne a gidan ubangari
Zainab Fatima Auwalu lukman Nasir,sune yaran ubangari na cikinsa


Haidar Umar khairat munira safara'u murja sune yaran Yan uwansa Dayake rikewa


Yusuf da ubangari akwai kyakkyawar fahimta a tsakaninsu duk da baisan Yusuf ba Amma da zuciya d'aya yake zaune dashi ganin tsawon shikaru Bai taba nuna wani mugun halinsa Wanda mutane zasuye Allah wadai dashi ba.


Yaran gidan na basa girmansa kasancewar duk yaran gidan ya fisu a shikaru,yanajin dadin zaman gidan sosai don tun kafun Alhaji yayi aure suke tare har Allah yasa yayi aure




Yaran suna ganin girman Yusuf saboda yanda mahaifin su ke tare tashi hakan yasa suke kiransa da bappa yusufa


Zaman Yusuf a gidan ya fara gunduran sane bayan girman Yar Alhaji Rabi'u ubangari zainab,wance Allah ya diga Mata son yusuf Mai tsanani duk da a lokacin tana da shikaru 14 yayin da Yusuf keda shikara 35


Tun tana boyewa har abin ya gagara ta tinkare Yusuf da maganar.


Sosai Yusuf ya ja Mata kunne akan zancen kuma ya tabbatar Mata shi bazai aureta ba donshi a matsayin diyarsa,ya d'auketa duk yanda tayi kokarin ganin tashawo Kan Yusuf abin ya gagara,taso fad'awa mahaifyarta zancen tanason Yusuf Amma khairat Yar bappanta ta hanata saboda tasan mundin maman zainab tasan zancen daker zainab ta aure Yusuf.






ADARA FAMILY HOUSE haifafun jalingo ne tun iyaye da kakanni anan gidan Adara suka tashi don duk fad'in sintali ba gida Mai dumbin tarihi da shikarun mazauna ciki irin family ADARA tun husul sai chanje chanjen gini da ake in zamani ya shude,
Tun husul ma haka suke mutane ne masu masifan tsiya ga fad'a kamar ahlin dambe shiyasa aka musu lakabi da ADARA


Aishan ADARA d'aya ce daga cikin yaran gidan adara ,macece Mai matsifa na bugawa a jarida duk yanda kaga mala'in yaran gidan ADARA Aisha ta damasu ta shanye saboda tsananin masifarta yasa Koh saurayi Bata dashi don a lokacin abin kunyane mace takai shikara 20 batayi aure ba Amma Aisha shikarunta 20 Koh saurayi Bata dashi saboda tsananin tsoronta da maza keye
Gidan ADARA tun asali haka yake har wa yanzun.


Aishan ADARA na Saida Dan wake a bakin kasuwan main market na jalingo


Sun hadu da Yusuf ne lokacin da yaje kasuwa sayayyan kayan Miyan gidan ubangidansa,ya saye danwaken ta by mistake robanta ya fashe a hannunsa,


Ba karamin bala'i Aishan ADARA ta sauke Masa ma kwando kwando da Kuma uzzurawa saiya biyata robanta


Yusuf Kam ba karamin mamaki yasha ba ganin irin bala'in da Mai danwake ke Masa akan robanda Bai wuce sule biyar ba sai bala'i take Masa Kamar ya Mata Satan jari


Sosai Yusuf yaji haushi kala baice Mata ba ya Kama hanya Yana tafiya itakam sai binsa take sayya Biya robanta


Yusuf kam yasha Alwashin bazai biya ba ganin jarabanda take Masa haka tayita binsa harya Gama cefenen ya Kama hanyar gida bayan ya tare machine.




Duk jaraban Aishan ADARA yau taga iyyakarta don ba zagi ba duka da Mannin hauka Yusuf ya rabu da ita


Bayan dawowar Yusuf gida Sam ya rasa sukuni,tunanin Mai danwake Kam ya hanasa sukuni Sam


Ta bangaren Aishan ADARA ma hakane Sam bayan tafiyar kyakkyawar mutumin da Bata Sansa ba gabaki daya ya hanata sakat a tsawon shikarun ta Bata taba bi takan soyayya ba Amma wannan Karo tayi tuntuben so a bakin titi Wanda Bata San inda zata sake ganinsa ba




Bayan sati biyu Sam Yusuf ya kasa sukuni ya kasa hakuri sosai Y'an kwanakin nan ya gane meke d'awainiya dashi,sai a lokacin yaji tausayin zainab Ashe haka takeji yake wulakanta ta,


Farga bansa d'ayane kar yaje gareta da soyayya ta tsigalesa don Tabbas daga ganinta Yar bala'i ce sosai Abu na biyu Kuma asalinsa kar rashin sanin danginsa yasa a hanasa auren ta.


A hankali Yusuf ya fara zuwa gun Aishan ADARA cin danwake Wasa Wasa harya kasance ba ranan da baya zuwa ci haka ba ranan da basa fad'a a tsakaninsu kafun su rabu ,har shakuwa yazo ya shiga tsakaninsu Mai tsanani Wanda a zahiri kowa son junane ke d'awainiya dashi,Amma ya kasa sanar da D'an uwansa


A hankali Yusuf ya fahimci masifar Aisha a tarbiyan gidansu yake a Hankali ya Soma nutsar da ita sosai yake nuna Mata abin Bai dace ma Abu kamar Wasa Aishan ADARA ta nutsu sosai sai dai fa har lokacin in ka tabota zaka Sha bala'i sai dai in abinda ba ruwantane Bata Shiga haka zalika ta daina dambe da kowa,abin harya fara bawa jama'a mamaki sauyawan ta


Lokaci da Yusuf ya bayyana ma Aisha soyayyarsa gareta Babu wani jinkiri ta amsa sosai suke zuba love


Yusuf ya samu Alhaji akan maganar Aisha ba karamin murna alhajin yayi ba dayaji Yusuf ya samu wance yake so don burinsa kenan,ya tambaye Yusuf danginsa don maganar aure Dole ana bukatan dangi na jini


Hankalin Yusuf ya Tashi matuka don har kwanciya yayi a gadon asibiti Akan zancen danginsa da Alhaji ya matsa Masa akai


Karshe dai fa ubangari yaga abin fa nayine yasa sa hakura da tambayar Yusuf shi yashiga maganar auren Yusuf


Da yake ubangari ya jima tare da Yusuf kowa gani yake kamar Yan uwane hakan yasa ba dogon zance aka basa auren Aisha don Suma sun Matsu tayi aure ganin ta girma a gida


Ta bangaren zainab Yar ubangari Kam in hankalin ta yayi dubu ya Tashi tayi kuka tayi kuka Kamar zatayi hauka Amma khairat ta taka Mata birki tare da Mata alkawarin sai Yusuf ya aureta amma tabare ayi auren taga matakin da zata d'aukar Mata


Bayan auren Yusuf sumul da Aishan ADARA, Alhaji yaki yarda Yusuf ya Kama gidan haya a gidansa sukaci gaba da zama, soyayya suke shimfid'a wa Mai tsafta sosai Aisha ta nutsu suna zaune da yaran ubangari da matansa lfy Sam bata nuna musu Yar Hali sai daifa basa shiri da zainab ganin kallon banza da take mata


Sai Bayan shikara uku da auren Aishan ADARA da Yusuf kafun Allah ya baiwa Aisha ciki sosai sukayi farinciki da wannan cikin da Allah ya azurtasu,sukaci gaba da rainon cikin cikin farin ciki


Bayan Aisha ta haihuwa sun samu d'a namiji Mai matukar Kama da mahaifinsa Kamar an tsaga Kara, mahaifinsa yasa Masa suna muhammad.
Mahaifiyarsa na kiransa Al'ameen.


Da sauri Sumayya ta d'aga ido tana kallon Al'ameen dake Bata lbr"kana nufin kace mini gidan n........"


Bai bare ta karasa ba ya girgiza Mata Kai Yana Kara kwantar ta ita a jikinsa,ki aje tambayoyin ki Inna Gama saiki tambaya


Kai kawai ta gyad'a Masa


Ya cigaba.....har lokacin zainab Bata saduda da soyayyar Yusuf ba don a lokacin ta kammala secondary school nata,Amma Taki aure Dole yasa babanta nema Mata wani makarantan gaba da secondary taci gaba


Bayan haihuwa Al'ameen da shikara uku Aisha ta Kara haihuwar wani da namiji yaci sunan Salim, tun daga lokacin Aisha Bata sake samun ciki ba,sukaci gaba da kula da yaransu don a lokacin Alhaji ya budewa Yusuf shago yabar aikace aikacen gida basuda wata matsala sai na d'ansu Salim Wanda ke fama da mummunan ciwon zuciya,duk bayan wata D'aya sai sunga likita Kuma sai anci kudi.


A hakan rayuwa tayita tafiya yau Dadi gobe akasinsa Al'ameen da Salim suna matukar samun kula daga iyayen su suna Isa shiga makaranta aka sakasu yarane da suka shagu da junansu matika Kamar wasu tagwaye Dayake Salim nada gaban girma tuni ya tsara da yayansa har lokacin Aisha Bata San cewa Yusuf ba Dan uwan Alhaji bane duk da tana yawan tambayan sa labarin Yan uwansa Amma Yusuf daga tayi tambar saiya hau hada Mata fuska


Bayan wasu shikaru lokacin Al'ameen nada shikara 11 Salim nada shikara 8 a duniya. Aisha na d'auke da karamin ciki.


wata ranan juma'a da zuriyan yusuf bazasu taba mantawa da ranan b a tsawon rayuwansu ba har Abada ciwon bazaibar zukatan su ba


Da misalin karfe bakwai na dare yusuf ya dawo gida,Yana kokarin shiga shashen su sai ga khairat taresa tayi cikin kuka Wai zainab ba lfy tana dakinta Alhaji yace yaje su kaita asibiti


Da gudu yusuf ya bi bayan kairan zuwa shashen Yan matan gidan,shiya fara Shiga d'akin Yana shiga khairat taja kofar ta rufe kofar ta waje da makulli.


Yusuf na shiga d'akin ya ware ido ganin zainab ba Kaya daga ita sai d'aurin kirji a zaune akan gado


Tambayar ta yusuf ya farayi, zainab menene haka Kuma ki nemi riga ki saka yace Yana Mai kokarin bude kofar


Dariya zainab ta sake hade da furta wallahih kaji na rantse maka Yusuf tunda ka hofantar da soyayya ta kasa kafa ka shureta Nima saina jazamaka bala'i inda zaisa ka aureni Dole wannan itace kad'ai abinda zanyi na mallakeka,ka 'dauka Koh shurun da nayi na hakurane?
Ah ah wallahih ban hakura ba tanadi nake maka.


Subhanallah shine abinda yusuf ya furta cikin gigita, zainab Ashe bakida hankali wani irin shirmene haka


Hauka zakace ba shirme ba tabasa amsa tana matsowa garesa hade da fizgo kwalar rigansa ta yaga sosai tana ihu


Sosai yusuf ya razana ya Shiga kokarin k'wace kansa




Khairat Kam tana rufe d'akin ta tsaya kamar minutes biyu kafun ta fara rafka salati a tsakar gidan wayyo jama'a wani zaima zainab fyade a d'akinta yanzun nazo shiga kawai naji kofa a rufe zainab nata kuka ku kawo d'auki


Da gudu Yan gidan harda Aisha da makwanta Dayake darene ga madalisa a kofar gidan suka ruga da gudu zuwa d'akin zainab da suke Jin kukanta na tashi har lokacin


Jin kofar a rufe yasa matasan samarin unguwan suka dauko katon itace suka bugawa kofar take kofar ta balle,cikin mamaki tsoro Al'ajabi suka zubawa d'akin ido ganin abinda ke faruwa kamar a mafarki y................






πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* πŸ˜‰




πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Turare suna d'ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa*


πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€ *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da* *gyara*


πŸ€πŸ€πŸ€ *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace*


πŸ€πŸ€πŸ€ *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE*


πŸ€ *Na tsunguno(habil)*
πŸ€ *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* )
πŸ€ *Turaren turara jiki after birth* ,
πŸ€ *Na d'aki(halud Al'oud)*

*UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* πŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌ


πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna bada d'aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa*


πŸ€πŸ€πŸ€ *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria*


Contact them vie
πŸͺ€08028827241 or 09033791049
IG @umsadincense


πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€πŸ€
πŸ§‘β€πŸ¦― *MATAR MAKAHO* πŸ‘¨β€πŸ¦―
~ Na ~

πŸƒ *Rukayya* *Ibrahim* πŸƒ

✨Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwaπŸ‘Œ
free book 🀧


🏡️Wannan shafin nakune🏡️
Ummu Muhammad πŸ€
Zainab mansurπŸ€
SurayyaπŸ€


Page4️⃣0️⃣&4️⃣1️⃣
Yusuf ne kwance akan zainab suna dambe


Salati dumbin Alumman dake wajen suka sake,zainab Kam da sauri ta sake Yusuf ta matsa gefe tana kuka da rawan jiki


Yusuf Kam ya kasa magana sunkuyar da Kai kawai yayi don bazai iyya hada ido da ubangari ba


Yusuf Ashe Kai Maci Amana ne Yusuf Ashe Kai mugune Yusuf shiyasa tsawon shikarun nan kake zaune Dani da fuska biyu azzalumi maha'inci kawai wallahih nayi Dana sanin zama dakai, Allah ya isan mini tunda ka rasa Wanda zakabi sai Yar cikinka,yace hawaye na taruwan Masa a ido,matasan samarin nan basuye wata wata ba suka rufe Yusuf da duka duk yanda yaso musu bayani Basu basa dama ba


Aisha Kam ba karamin shock ta Shiga ba Daman Yusuf ba D'an uwan ubangari bane? shiyasa inta tambaye sa Ahlinsa sai yahau fushi Ashe baida gaskiya ne kwata kwata, Aisha Kam kuka take tana dana sanin Yusuf, ya zubar Mata da mutunci ya ha'ince ta


Matar ubangari waya ta d'auka ta Kira police lokacin Amma Yusuf jina jina Koh tsayuwa baya iyyayi,ga matan sa da yaransa duk suna kuka, A lokacin yaran basusan me uban yayi ba Amma tabbas sunsan ba lfy


Police na zuwa daker suka k'wace Yusuf ganin ana kokarin kisan kai, lokacin da police suka Kama Yusuf za'a fita dashi cikin tsananin azaba yake rokonsu su barshi yaga MATARSA zai Mata magana.


Ba musu domin tabbas su kansu police a lokacin sunji tausayin sa sosai da sosai,wani ne a cikinsu ya taimaka Masa suka nufi wajen da Aisha ke duke tana kuka


Yusuf na Isa dukawa yayi yasa gwuwarshi a kasa cikin galabaita ya fara magana, Aisha Koh kowa zai yarda akan abinda yafaru don Allah Aisha ke kad'ai ki yarda Dani, yardan ki kawai nafiso akaf fad'in duniyan nan bayan yardan Allah,don kece abokiyar rayuwa ta in kowa zai juyamin baya ke Kika rungumeni bani da kaito Aisha Ina neman Wannan alfarman. ya karasa maganar hawaye nabin fuskar sa


Aishan ADARA Kam yau Hali ya motsa jikinta har bare yake cikin kakkauran murya ta mike ,Yusuf Yusuf wallahih nayi Dana sanin haihuwa da Kai Yusuf, nayi Dana sanin auren ka Yusuf ka cuce kanka ka cuceni Yusuf bana bukatar ka a rayuwa ta ni daga yau mijina ya mutu.


Sosai Yusuf ya fashe da kuka maicin Rai Wai waye zai fahimce sane kowa bazai yarda dashi ba kawai don an gansa a d'akin yarinya Babu bincike sai kawai ad'au mataki, me yasa tunani bazaizo musu ba duba da cewa ya rasa inda zai nemi zainab sai a cikin gidansu?


Yunkurin magana yafara ais......,da saure Aisha ta d'aga Masa hannu Yusuf Koh Babu Kai zamu rayu da yarana Koh bakai Zan iyya rayuwa Koh ba Kai rayuwar zata Mana Dadi,Amma zaman ka acikin mu shine kuncinta ka tafi bana bukatarka a yanzun,tace tana Mai kokarin baren wajen.


Da sauri yusuf ya Kama hannun Aisha,bataye wata wata ba ta tsinka Masa Mari.
Da sauri Yusuf ya sake Mata hannu


Da sauri Al'ameen Yayi wajen babansa cikin kuka ya rungume sa,abbajo menene Kaye musu suke dukanka abbajo ga fuskarka duk jini,abbajo muje asibiti a maka treatment kaji abbajon mu ka bawa police hakuri karsu tafi dakai,kuka Yusuf ya sake hade da rungumar d'ansa Dayake Jinsa Kamar bugun numfashin sa, cikin su biyun yafi kaunar Muhammad sosai.


Karka damu muhammad Zan dawo kaji laifin da ba nawa bane aka d'aura mini Wanda duniya kaf ni ake gani da laifin ,Yusuf yace ma d'ansa Yana Mai d'aukar sarkan dake wuyansa fari Mai azabebben kyau da walkiya ya d'aurawa Al'ameen a wuya, Muhammad ka kula da mamanku da kaninka kaji in mamanku ta haifi mace kace asa Mata khadija Inna mijine asa masa Shitu,Yana fad'a Masa hakan police sukazo suka Tisa keyarsa zuwa cikin mota


Bayan an tafi da Yusuf, Alhaji ubangari da danginsa Koran Kare sukama Aisha da yaranta,sosai Aisha tayita kuka tana tattara kayanta zubawa tayi a ak'watin karfe ta d'aurawa Al'ameen da salim,suka Kama hanyar sintali.


Gari gabaki d'aya ya d'auka zancen Yusuf yayi kokarin mawa Yar ubangidansa fyade,bayan isar Aisha gidan ADARA zuwa lokacin labari yazo kunnensu Dayake unguwan da suke da sintali ba nisa


Bayan isar Aisha gida ta sake haduwa da wani tashin hankali shine mahaifinta yace sai ta mayarda yaran Yusuf gun danginsa kafun ta zauna musu a gida Dayake mahaifiyar ta tarasu tun kafun auren ta,yasa ba Wanda yayi yunkurin baiwa baban ta hakuri


Aishan ADARA ta shiga tashin hankali ba kad'an ba na rashin sanin asalin Yusuf abin yayi mugun daga Mata

Please Login or Register in order to submit comment