Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

bakin kofa yarakata yabude mata kofa tafita tana mai murmushi tai cikin gida, guda kawayenta suka shiga yi suna mata kirari Aneesa sai dadi takeji kaman zata mutu haka aka wuni sai bayan magrib baki suka fara tafiya Aneesa ta gyara gidan tass Ammi taje tai wanka da ruwan turare dana yan magungunan data hadama kanta dan Dady yabata kudi dasu tasaisai abinda take bukata na gyarani jiki.



Washe gari koda gari yawaye daidai da tsinke Aneesa bata bari Ammi ta daga ba ita ta gyara ko ina tahada ubansun abinci a big pot dan tasan anjima kadan zasuyi baki, sanan ta hura wani wutan ta daura ruwan wanka kafin tawuce ta shigo daki tai wurin Ammi, kallonta Ammi tayi tace "sako hijabi kije wajen Maman Aisha ki kiramin ita, sonake ragowan abincin nan da baban ki yakawo ayi biki dashi duk tazo ta kwasa ko" gyadamata kai Aneesa tayi tace "zataji dadi sosai kuwan Ammi dama baban su yanzu baya aiki" hijabi tasa taje takira maman su Aisha tare suka dawo ita tawuce kitchen tadaiji yanda maman su Aisha keta godema Ammi harda kukan ta, girkin takarasa taje tai wanka tadawo daki dama tariga ta ijiye kayan dazata sa tai gayu sosai yauma lacey takara sawa pitch wayaga ansami lace daban daban kyau tayi.

Wuraren bayan la'asar din kaman yanda Dady yafada motoci suka cika anguwan kaman za'azo daukan budurwa, Momma ce tazo da kawayenta guda uku suka shigo dakin kebewa tayi da Ammi dataji tana so sosai dan kallo daya kacal tama Ammi tasan zatafi sauran matan Dady hankali ta shirya Ammi tasa mata alkyabba akan hadadden lapaya dake jikinta sanan aka hadu da kawayen Ammi yan anguwa aka kai Ammi mota, Momma ta turo bodyguard ciki Aneesa na nuna musu kayansu dazasu kai mota akwatin nan su dayan abubuwan dasuka tattara duk suka tafi dashi tadauko dogon hijabin ta har kasa pitch tasa da takalmin ta mai kyau look so decent and magical tafito ta kulle gidan tajefa key cikin jaka tazo da sauri motan da akasa Ammin ta aciki Momma dataji tanason Aneesa tace "zoki zauna wajen maman ki" da sauri tazo dan dama tafiso ta zauna wajen Ammi ba dayan motan ba, motan daga Ammi sai momma sai kuma ita, kawayen momma na motan farko su kadai, sai motan karshe kuma kawayen Ammi ne aka dau hanyar City Abuja. Aneesa sai kalle kalle take oh yanzu zasu koma new gidansu ne.




Agaban wani katafaren tangamemen gida da sojoji guda uku ke waje akai horn wani soja daban daga ciki yabude musu kofa suka shiga, tundaga Gate Aneesa ke kirga manya manyan flat din dake makeken compound din, bata taba ganin hadadden gida hakaba ko gidan dataje kwanaki tai lalle albarka, babu kowa atsakar gidan saidai kofa dataga ana bubbudewa kaman an hada baki ana lellekowa, a parking space akai parking da sauri direban yafito ya zagayo yabude musu itadai Aneesa sai kallon ikon Allah take, Momma ce tafara fitowa ta kalli Aneesa dake murmushi bakinta yaki rufuwa tace "fito daughter" ahankali Aneesa tafito da kafar damanta dake cikin safa ta ijiye akan interlock din dake kasan gidan wani irin faduwa gabanta yayi tareda wani irin sanyi dataji ya shiga tundaga kasan kafan nata har zuwa brain dinta, "menene daughter?" tambayan momma yasa tadawo daidai murmushi tayi tace "kashina ne yay kara kas kas Mommy" dan dariya Momma tayi tace "gajiya ne kin aikatu saisa anjima kafin ki kwanta saikiyi wanka da ruwan zafi zakiji dadi" gyadama Momma kai tayi tafito gabaki daya wani irin iska ne taji yakada ta harsaida hijabinta ya shiga rawa ga sanyi daya ziyarci kowani gaba na jikinta, fito da Ammi Momma tayi Ammi tafito daga motan wani irin guda Momma tasaki kaman dabiyu tai gudan kawayen Ammi suka fara wake kawayen Momma na amshi suna tafi akai hanyar flat din Ammi itadai Aneesa na gefen Ammin ta, Rauda dake falo dukta kosa yafito ta kalli maman su datai kini kini da rai itada hajar suna keke ta window tace "Mama please kibarni naje na ga sabuwar matan Dady" dakuwa Mama tamata tace "inkin isa kifita kigani, mai bakin hali, mara mutunci yarinyar dabata kishin uwarta" tabe baki tayi tawuce fuuu tai dakinta cikeda fushi dajin haushin Mamansu.
_Duk wacce takaranta batare data biyaba, Allah ya isa, keda Allah, mai son book tamin magana 07012181461_

Abakin kofan flat din Ammi Momma ta tsayar da kowa ta kalli daya daga cikin kawarta dake rike dawani buta irin butan da dinan na silver dake cikeda ruwa tace "kawo butan Hauwa tai alwala sai a shiga daki" Ammi suka ba butan ahankali Ammi ta tsugunna tafara alwala ana guda ana wake saida ta gama tass sanan aka sa tai bismillah aka bude kofa ta shiga da kafar dama kasa kulle baki Aneesa tayi dataga dakin da akace na Ammin sune, dakine mai benefa a tsakiya, innalillahi komi na dakin sabo fill ga kamshin furniture's nan ko ina, kawayen Ammi ma kasa shiru sukayi sai masha Allah ake, azuciyoyin su suna ashe saisa taki aure jira take saita zaba takuma dirje, wanan gidan arxiki haka dole tai zaman kusan shekara sha tara ba aure gashinan yanzu ai yabiya ta chasko Alajin Allah kice bana sai makka su Rukayya da yarta. Sama sukayi da Ammi yayinda ake shigo da kayansu ciki har dakin Ammi suka kaita dayaji kaya gawani lumtsetsen gado royal, Momma takama hannun Aneesa suka fita daga dakin Ammi su biyu kacal wani daki dake kallon na Ammi tabude dakin yaji kaya ga fenti baby pink ta kalli Aneesa dake kallon ko ina tace "ga dakin ki nan" wani irin ware manyan idanunta Aneesa tayi ta nuna kanta tace "yanzu wanan hadadden dakin ne nawa Mummy?" gyadamata kai Momma tayi tace "eh naki ne daughter" wani irin rungume Momma Aneesa tayi tana tsalle tama manta batasaba da matan da kyau ba tsabagen murna tace "thank you, nagode nagode nagode Mummy kinji" sai kuma tasaki kuka sosai Momma taji Aneesa ta burgeta dan itama kaman Dady take tanason appreciative person komin kankanin abu ka nuna kaman a maka kyautan makka ne abun namata dadi, hannu tasa ta share hawayen datake tace "mena kuka? So kike maman ki ta shiga damuwa?" da sauri ta girgixa mata kai tace "Mummy dadi nakeji am happy, Ammi na is happy, kina sonta kuma Abba nason ta, jibe gidan da kuka bamu saisa nake gode miki, thank you so Mummy kinji Allah yabiya muku bukatun ku na alkhairi" rungume ta Mummy tayi kadan sanan tasake ta tana kallonta kaman mai tunani sai tace "kinsan menene?" da sauri Aneesa ta girgiza kai Momma tace "zan miki kawa, ko dayake bari Ince namiki kawa y'ata ce sunanta Ihsan, she's your age mate zan taho da ita nan gobe, ai zaki dinga zuwa gidana hutu ko" da sauri ta gyadama Momma kai tace "eh zan dinga zuwa Momy" "gud, yanzu stop crying zomu koma wajen maman ki kinji" murmushi tayi tace "to" Momma tace "to acire hijabin mana ustaziya ai anzo gida ko" gyadama Momma kai tayi ta zare hijabin tareda linkewa ta ijiye kan gado duk Momma na kallonta sai taji Aneesa ta kara burgeta abinda Ihsan bata iyaba kenan kome tacire daga jikinta saidai ta yar, hanunta ta kama suka wuce suka koma dakin Ammin ba'a jimaba Momma tafito ta sauka kasa dan kiran Dady ta sanar dashi matan shi basu kawo musu abinci ba ga baki, ko ruwa basu kawoba, fada Dady ya dinga yi danya fadamusu suyi harda ijiye musu kudi, hakuri Momma tabashi tace ya sharesu yanzu zatasa kawayen ta sudafa, ita da kawayenta ta tattara sukai store din gidan suka shiga girki mai rai da lafiya.




Wuraren 8 na dare Dady da Aliyu suka shigo gidan ganin Aliyu zaiyi hanyar part dinshi yasa Dady yace "let's go Son ka gaida new Mum dinka" yatsine fuska yayi ahankali yace "not today Dad, mutane sunyi yawa a shashin, am having headache inaso nadan kwanta".



_duk wacce takaranta batare data biyaba Allah ya sakamin, mai son book dinan should chat me up 07012181461__*A TSAKANKANIN SOYAYYA*_





_IN BETWEEN THE LOVE_
❤ _Lies another love_❤




_✍🏿M Shakur_



3️⃣2️⃣




Fuskarshi Dady ya shafa yana kallonshi kaman maison gano wani abu cikeda damuwa yace "Gadanga na are you okay?" murmushi ya kakalo yace "yes Dad am fine, bari naje nai bacci, my regards to new Mum" gyadamai kai Dady yayi yace "love you Son" murmushi Aliyun yayi yace "I love you too old man" yawuce da gudu, dariya Dady yayi cikeda sonshi yace "zakaci gidan kune nine old man din" yajuya yana tafiya yace "kagamin yaro in karo amaryata yana cemin old man" yacigaba da tafiya yana kiran number Momma bamata amsaba tafito tazo wurinshi kudade masu yawa yabata yace "gashinan kibama wayanda sukazo, motoci na jiransu su fito amaida su gida" ahankali tace "to Yaya, nima zan wuce gobe zan zo, nama Aneesa alkawarin kawa so zan kawo mata Ihsan" dariya Dady yayi yace "I see, shikenan Allah kaimu gobe, ki kadomin wanan mai kunen kashin" dariya Momma tayi tace "Abdul shi zanma saka ya tukomu" da sauri Dady yace "kafin kiwuce ki kawomin Rukayya da Aneesa bangare na zan hada su namusu magana ne" da sauri Momma tace "to Yaya" tawuce tai hanyar flat din Ammi shikuma Dady yawuce flat din sauran matan shi yana fadamusu azo shashin shi harda yara sanan yawuce part dinshi, wanka ya shiga yay da ruwan zafi sanan ya shirya cikin simple jallabiya fara mai kyau dayadan fito da tebanshi ya feffesa turare, jin hayaniya afalon shi na yara yasa yagane sun soma zuwa, karasa shiryawa yayi tsaf yadauko faran hulan kwankwasa kaji hadisi yasa sanan yafito daga bedroom dinshi ya sauko kasa yana kallonsu da sauri kananun yaranshi na wurin Amaryan shi Amna da Ashna suka rugo da gudu. "oyoyo Dady" , murmushi yayi ya tsugunna ya dauke su dukansu sai jan gemunshi suke yana murmushi yana satan kallon duka matayen nashi dasuka zauna akan manya manyan kujerun nashi ko wacce tai kini kini da rai adole an musu kishiya barin ma Amarya, dan murmushi yayi ya kalli yaranshi su Rauda dasu hajar da sauran yaran dasuka dan tasa duk suna zaune akasa akan makeken carpet din wasu na wasa wasu na hira, karasawa yayi ya zauna akan kujeran wacce take nashi ne babba yana wasa da yaran suna dariya Rauda na murmushi dan ita bataga rashin sonsu da Dady bayayi ba da Maman su ke fada, wai Aliyu kawai yakeso ayaranshi, ita bataga hakan ba yanson su, yanason duka yaranshi, dankome suke so yana musu yana wasa dasu, Aliyu maraya ne, basu sonshi, basu kula dashi basa bashi abinci, sun tsaneshi ba dole yakula dashi da kanshi ba.


Cigaba da wasada yaran Dady yayi daidai yana jira yaji any of matayen nashi wata tagaishe shi amma basu gaidashi ba, sai kumbure kumbure suke, cikin fushi Maman su Rauda tace "wai wa muke jirane haka ake batamana lokaci" cikin fushi da kunan rai Amarya tace "ganemin fa, kya tayani tambaya sai, an shanyamu saikace kayan wanke ko yar gidan sarki muke jira ai sai haka" baki Dady yabude zaiyi magana Momma tabude kofa suka shigo itada Ammi dake sanye da hijabi har kasa sai Aneesa, itama sanye da hijabin ta har kasa tana gefen Ammin ta har wajen kujera Momma takawo Ammi da Dady yabi da kallo tace "ga kujera ki zauna" zama Ammi tayi ahankali tadan dago kanta ta kalli Dady dake kallonta cikeda natsuwa da tsantsan girmamawa tace "ina yini Alhaji, barka da dare" har wani irin lumshe ido Dady yayi da Ammi ta gaidashi muryanta na ratsa kowani bangare najikinshi, kafin ma yabata amsa ta juya ta kalli sauran matan dan kallo daya ta musu tagane matayen Dady ne tace "ina yinin mu" zama Aneesa tayi gefen kafar Ammi tace "ina yini Abba" murmushi sosai Abba yayi yace "lafiya lau daughter na, ya gajiya" cikeda kunya tana kare fuskarta da hijabi dan dakin da mutane da yawa tace "Alhamdulillah" sanan ta kalli matayen da Ammin ta ta gaida basu amsa ba tace "ina yini" dan gajeren tsaki maman Rauda taja, har ranshi Dady yaji tsakin baice komiba yasan dama bazasu amsaba ya kalli Momma data tsaya kallon komi yace "sun wuce?" "eh sun wuce yaya, nima natafi saida safe" "nagode" hannu Rauda tadagama Momma tana murmushi tace "Momma saida safe ki gaidamin da Ihsan" murmushi Momma tayi tace "zataji Rauda" tabude kofa tafice.

Ajiyan zuciya Dady ya sauke kafin ya gyara zama yabude taro da addu'a sanan ya kalli yaranshi dake zaune kan carpet din yace "yarana" atare suka amsa dukan su "na'am Dady" murmushi yayi sosai yace "na kiraku nanne sabida na nuna muku new Mummy dinku, sunanta Mummy Aliyu kokuma kuce Mummy Aneesa" duk murmushi yaran sukayi suna kallon fuskar Ammi dake kasa banda Hajar datai kini kini da rai, ganin yanda suke murmushi Dady yace "ga Aneesa nan, y'atace itama sanan yar uwarku ce, Inaso kuhada kai kuso juna banda fada kunaji" da sauri duk suka gyadama Dady kai, murmushi Dady yayi shi yasan Allah has blessed him da yara nagari but iyayen su ke batamishi su, ahankali yace "kutashi kuje ku gaida new Mum dinku" da sauri suka tashi har ana rige rigen zuwa murmushi Ammi tayi ta rungume su tana shafa kansu sai gashe da ita suke. "Mummy Aliyu ina yini, Mummy Aliyu good evening" haka suketa gaidata, Rauda ma tazo tana murmushi tace "sannu da zuwa Mummy" murmushi Ammi tayi ta shafa fuskarta tace "nagode y'ata" Hajar ma tasowa tayi ba yabo ba fallasa tace "ina yini Mummy Aliyu" lafiya lau Ammi ta amsata ganin yanda ta gaidata da kyar sanan duk suka koma suka zazzauna, murmushi Dady yayi ya kalli Ammi yace "dukan su yarana ne, su goma sha tara ne Rukayya" ya kalli yaran yace "to duk kutashi kutafi ku kwanta zanyi magana da iyayen ku" tashi sukayi ahankali harda Aneesa da Rauda tamiko mata hannu dan tun dazu data shigo take kallonta tagane ta ita Aneesa bamata ganeta ba har yanzu dan ranan dataganta tai buzu buzu, murmushi Aneesa tayi Dady na dan dariya yaji yakara son Rauda suka fita daga dakin Mama nabin bayan Rauda da harara suka rufo kofan.

_how to subscribe_
_zaki turo 300 ta account number na 3107021073 aisha Muhammad first bank, saiki turo evidence of payment ta watsap number na 07012181461 sainai adding dinki a group din a tsakanin soyyayya_

_duk wacce takaranta batare data biyaba Allah ya isa_

Gyara zama Dady yayi zaiyi magana Amarya tace "ansa y'ay'an mu sun gaidata amma ba'a saka yarta tagaidamu ba tun yanzu anfara son kai" da hannu Dady yanuna ta cikin kakkausar murya yace "Zainab ki shiga taitayin ki last warning" yay maganan babu alamun wasa atattare dashi hakan yasa kowaccen su tahadiye abinda ke ranta, Dady yayi shiru yana kallonsu kafin cikin fushi yace "data shigo ta gaida ku kun amsata ne? Anyway kubi ahankali inba hakaba zanyi mummunan saba muku" dan shiru yayi trying to calm kanshi down kafin ahankali yakira Ammi. "Rukayya" ahankali Ammi tadago kanta tace "na'am Alhaji" nuna su Mama yayi yace "ga matana nan, Kareema itace uwargida, sai Amina mai binta, sai Zainab" ya nuna amaryan shi yace "itace ta uku, inaso ki basu girman su banson neman fada da hayaniya, kwana bibbiyu ne ake amsan girki, ba'a girki General girki agidana ko wacce tana girkinta daban dan banson tashin hankali da korafi, duk randa nake dakin ki saikiyi dani, ko wacce ina samata abinci a dakinta idan wani abu yakare ba'a riga an kawoba akwai General store anan tsakar gida zaki iya dubawa in akwai abinda kike bukata saiki dauka, inaso ki zama mace mara hayaniya mara fada da kowa, ki kare mutunci kanki dana mijinki kome aka miki kifada min kafin kidau hukunci kinji Rukayya" gyadamai kai Ammi tayi tace "in sha Allah zan kiyaye duk abinda kace Alhaji, Allah yatayani yakuma yimin jagora" murmushi yayi yana kallonta yace "Ameen" sanan ya kalli sauran matan shi yace "ga yar kanwar kunan sunanta Rukayya nabaku ita amana, ku hada kanku kuyi bautan aure, ku kwantar min da hankali ku hada kan yarana, banda fada da hayaniya, Allah yamuku albarka dukanku, idan damai magana zata iyayi" da sauri Amarya tana kumbure kumbure tace "yanzu kwana nawa zakayi a wurin ta kafin kadawo wurin mu?" dan murmushi Dady yayi ganin yanda kishi ke cinta yace "kwana uku in sha Allah" Maman su Rauda cikin daure fuska tace "wanan yarinyan kuma fa damuka gani?" cikin daure fuska Dady yace "y'ata ce itama, sunan ta Fateema ana kiranta da Aneesa, dawata maganan ne?" Amina matar Dady ta biyu ne tace "badai makarantan da y'ayan mu suke zaka sata badai ko" cikin kakkausar murya Dady yace "Aneesah y'ata ce bakida ikon da zaki fadamin how da kuma tayaya zanbi da yarana, duk inda nasata wanan ba matsalan ki bace tunda dai bada kudin ki nake biyan kudin makarantan ba" zata kara magana Dady yadaga musu hannu alamun suyi shiru kafin yanuna musu hanyar kofa yace "zaku iya tafiya" tashi sukayi fuuu suka fice suka bugo kofar, ahankali Dady yatashi daga kan kujeran yakoma kan kujeran da Ammi ke zaune hannu yasa yadago fuskarta murmushi ta sakan mai mai taushi ajiyan zuciya ya sauke yace "am sorry Rukayya, kiyakuri dakome matana zasuce I know kalaman su have hurt you kiyakuri kinji" murmushi Ammi tayi ta kama hanun Dady tana shafawa ahankali tace "karka sake ban hakuri ko daya ban damuba, hasalima godiya zanma, thank you for standing as a father to Aneesa agaban kowa Abu Aneesa" murmushi Dady yayi yace "ni mahaifinta ne so don't ever thank me akan anything dazanma y'ata Ummu Aliyu" ahankali Ammi ta rungume shi tana murmushi, bayanta ya shafa murya chan kasa yace "Aneesa ta iya kwana ita kadai?" gyadamai kai Ammi tayi murya chan kasa tace "eh" murmushi Dady yayi yace "tashi to muje mumata saida safe" murmushi Ammi tayi tace "to Allah ja zamanin Maigidana" tashi Dady yayi yana murmushi yadaga ta yana rike da hannu ta suka fito daga part dinshi sukai part din Ammi Aneesa bata falo hakan yasa sukai sama atare itada Dady suka shiga dakin Aneesa harta kwanta tafara gyangyadi tarufe da bargo dan karfin AC yamata yawa yanda ta dukunkune yasa Dady yace "lafiya Aneesa ko zazzabin ne" da sauri tace "Abba sanyi nakeji" dariya Dady yayi ya rage AC to the lowest Ammi ta zauna kusada ita ta shafa kanta tace "saida safe zan tafi bangaren babanki a chan zan kwana" murmushi Aneesa tayi tace "saida safe Ammi na" ta kalli Dady daya tsaya yana kallon su sun bala'in burgeshi sosai tace "saida safe Abba na" murmushi Dady yayi yakara so wajen yaja hancin ta yace "saida safe yarinyan Abban ta" tashi Ammi tayi ta gyara mata bargon Dady ya kashe wutan dakin suka fito tareda rufe mata kofan, dakin ta Ammi ta shiga Dady ya rungume ta tabaya yace "mezaki yi anan?" dan murmushi tyi tace "kayan da zansa gobe zan dauka" hanunshi yasa tacikin hijabinta yana shafa cikinta dabaida girma ko kadan ahankali yace "karki damu akwai kayan dana ijiye awurina danake so kisamin gobe mutafi" sakinta yayi yakama hannunta suka fito daga dakin sukai sukai shashin shi.

Kulle kofa yayi yana rikeda hannunta sukai upstairs, makeken master bedroom dinshi yabude ya shiga yana rike da Ammin wani hadadden kamshi ya daki hancin ta, maida kofar yayi yarufe tareda sa hannu yazare mata hijabin dake jikinta, tana sanye dawani Jan dogon riga har kasa bin jikinta yay da kallo kafin ahankali yanuna mata bayi yace "shiga ki dauro alwala kizo"
_Asuba ta gari Ammi da Dady😎😎😎😎._
_*A TSAKANKANIN SOYAYYA*_





_IN BETWEEN THE LOVE_
❤ _Lies another love_❤




_✍🏿M Shakur_



3️⃣3️⃣



_littafin nan is not a free book, duk wacce takaran ta batare data biyaba Allah ya isa_
_sanan duk wacce tafitar min da book waje ban yafe mataba_

_gama su son this book, zaku turo 300 ta account number na 3107021073 aisha Muhammad first bank, saiku turo evidence of payment ta watsapp number na 07012181461 sainai adding dinki a group din danake posting a tsakanin soyyayya_

_masu wata magana zasu iya tuntubata ta watsapp number na 07012181461, am open for business adverts and business promotions, duk zaku iya tuntubana dan kuji yanda abin yake_



Fitowa Ammi tayi daga bathroom already Dady har yahau kan dadduma, a gefenshi tazo ta tsaya hakan yasa ya kabbarta sallan sukai raka'a biyu bayan ya idar yakama goshin ta yay addu'o'i sanan yasake ta ahankali tareda saka hanunshi ya zame hijabin jikinta ya linke ya ijiye agefe yanabin jikinta da kallo yanda doguwam rigan yamata kyau sosai, ahankali yajuya yajawo hadadden tray dake dauke da manya manyan kaji ga drinks awani separate tray yakawo gabansu, hannu yasa yadauko kaza yakai bakinta yace "lemme feed my wife, bude bakin" dan murmushi Ammi tayi tabude mai bakin, ahankali yasaka ciki ta shiga taunawa haka ya dinga feeding Ammi takoshi sosai sanan ta shiga bashi itama ci sukayi sukai nak Dady yadau tray yafita dashi zuwa kitchen din falonshi Ammi kuma ta tashi ta nannade dadduman kafin ta wuce ta shiga bayin ta wanko hannunta tareda daurayo bakinta tafito, Dady tasamu kan gado yacire jallabiyan jikinshi daga shi sai dan farin singlet da wani boxer dan dogo ya jingina da filo yana daddanna laptop din, dagokai yayi ya kalleta jin anbude kofa, ganin yanda ta tsaya agaban bakin kofa tama kasa karasowa ciki yasa ya janye hannun shi daya daga jikin laptop ya miko mata alamun tazo, karasowa tayi ahankali tahau kan katafaren gadon jawota yayi yadaura kanta kan gefen kirjinshi yana cigaba da daddanna laptop din yace "Ummu Aliyuna" dan murmushi Ammi tayi ta chusa fuskarta akirjinshi tana shakan d'adaddan kamshin dayake yi tace "barka da aiki Abu Aneesa" murmushi Dady yayi baice mata komiba ya cigaba da yan danne dannen dayake a laptop din yana murmushi duk ya kosa yagama almost minti goma yadauke shi sanna yakarasa yakashe system din ya daura akan side drawer kafin yamika hanunshi ya kashe bedside lamp din dasu kadai ne a kunne, ahankali ya gyarama Ammi datai lamo ajikinshi kwanciya yadan hayo kanta yana goga hancinshi kan fuskarta yana dan shinshina ta yace "kinyi bacci ne?" cikin wata yar murya chan kasa yar siririya yar karama irin mai kashe ran miji dinan tace "ta ina zanyi bacci mijina bai sallameni ba, bairiga yabani izinin bacci ba eh ranka shi dade" wani irin dadin kalaman ta Dady yaji baisan lokacin daya daura bakinshi kan nataba ahankali ya shiga sumbatar ta, wani irin ajiyan zuciya Ammi ta sauke tanajin wani iri sosai ahankali take shafa gemunshi har zuwa kanshi jin takasa daurewa yasa ta shiga maidamai da martani rudewa Dady yayi dan shi wani irin mutum ne dayake so yaga ana maidamai da martani yana shafawa ana shafashi abinda duka matayen shi basayi kenan su adole kunyan al'ada, rudewa yayi da sauri ya kwanta batare daya saki bakin Ammi ba yadaura ta akanshi yana tattare doguwan rigan nata sama tayashi tayi ya cire rigan ya yar akasa yakara mirginawa yahau kanta, ahankali yadaura hanunshi kan cikinta dabaida wani girma sosai dan daidai yana shafawa har zuwa sama yana kissing dinta kafin ahankali hanunshi har rawa suke yadaura hannun kan Big boobs din Ammi dan ita Aneesa tagado tanada cikan kirji bana wasaba, wani irin gauron ajiyan zuciya Dady yasauke yasaki bakin Ammi yadaga ta zaune yakai hanunshi baya ahankali ya

Please Login or Register in order to submit comment