Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kalmar harcikin zuciyarshi, bawai besan ta tsaneshin din bane, yasani amma furtawar datake ba qaramin tasiri yakeba azuciyarshi.

Yana fargabar wannan kalmar abakinta, besaniba ko wannan karon zuciyarshi zata iya daukar kalmar ba.

Da tashine dasun barshi gida, da bazai bisuba don yasan kwanan zancen, dole yauce ranar rabuwarsu kuma yasan dole ta furtamashi kalmar dake qonamashi zuciya.


Jin an dafashi a kafada yasashi dawowa duniyar tunani daya fada yabude idanunshi yajuyo ya kalli sadeeq dake kallonshi shima.

Sai alokacin yaga kamar ba tafiyaba suke, waigawa baya yayi yaga su ummy basa cikin motar wanda hakan ke nufin sun iso kenan

"Be strong" inji sadeeq yana dan jijjiga kafadarshi cikin karfafa gwiwa.

Lumshe idanu kawai yayi ya bude batareda yace komaiba.

Bude murfin kofar sadeeq yayi ya fita ya maido yarufe.

Shiru ashraf yayi na yan daqiqu sannan shima yasa hannu ahankali ya bude murfin motar.

Saida yadanyi jim sannan ya sauko kafarshi daya sannan ahankali gangar jikinshi suka biyo baya.

Wani fresh air ne ya bugeshi wanda yasashi lunshe idanu yana shaqa tareda fesarwa ahankali.


Zagayowa sadeeq yayi side dinshi shima ya tsaya yana kallonsu Kawu dake gaisawa dasu Abba da daddyn saudart.

Shima Ashraf su yake kallo koko ince Alhaji shamsu yake kallo wanda kallo daya zaka mashi kaga rashin nutsuwa atattare dashi.

Kallonshi yake cikeda tsana da kyama marar misaltuwa.

A 6angaren su kawu ibrahim kau tarba ta mutunci suka samu wajensu Abba koko ince Abban kadai don daddy bemada nutsuwar dazai tarbesu sosai.

Jiyake kamar qasa ta tsage yashige don kunya, haka dai ake gaisuwan batareda ya yarda sun hada ido da daya daga cikinsu ba.

Kamar ance yakallo wajensu Ashraf, idanunsu ne suka gauraya wanda hakan ya haddasama Alhaji shamsu faduwar gaba don shi kadai ya hango abinda ya hango a idanun ashraf.

Ganin suna tunkarosu yasashi janye idanunshi daga kansu.

Qarasowa sukayi duk suka duqa don gaidasu.

"Ina wuninku?" Inji sadeeq a sanyaye.

Saida suka amsa sannan ashraf shima yabude baki dakyar yace
"Abba barka da wuni"

Amsawa abba yayi yana murmusawa shikau daddy bece konaiba sai kauda kai dayayi.

Haka suka dunguma suka nufi masaukin baqi dake gidan gabadaya.


Zaune take bakin gado ta jingina da kan gadon hannayenta harde a qirjinta, ita kadai tasan abinda ke axuciyarta, tunda taji qaran mottoci tasan sun iso, hakan yasa bugun ziciyarta qaruwa, yaune damarta ta qarshe na qwatarma kanta yanci, yaune damarta na qarshe na za6arma kanta irin rayuwar dazata cigaba dayi, rayuwar farinciki ko akasin haka. Today is the D-day.


Bubbuga kofar da akayi yasata dagowa ahankali tana kallon kofar.

Budewa akayi daddy ya bayyana bakin kofar ya tsaya yana kallonta.

Ahankali ta hadiye wani abu dake maqoshinta tareda sadda kai

"Come daughter" yafada asanyaye.

Qara dagowa tayi ta kalleshi da dara daran idanunta sannan ta miqe ahankali ta dauki hijab dinta dake gefenta ta warware ta zurata, saigata har tana kusan sharar qasa.

Anitse ta tako har wajen daddy kanta a sunkuye, kama hannunta yayi yadan murza
"Are you ok?" Yafada ahankali

Kada mashi kai kawai tayi asanyaye

"Ok muje" daga haka yajuya yayi gaba yana jaye da hannunta.

Bugun zuciyarta yashiga karuwa duk taku daya dazasuyi na tunkarar falon baqi.

Jitake kamar ta ruga don sosai zuciyarta je cikeda fargaba dakuma tsoro gakuma nauyin ummy datakeji.

Haka dai suka qarasa bakin kofar falon.

Sallama Alhaji shamsu yayi yashigo still jayeda hannun saudart da kanta ke qasa.

Duk dagowa sukayi suna amsa sallamar saidai duk idanunsu nakan Saudart.

Ahankali takebin daddy tana iya bakin qoqarinta naganin bata hardeba don tafiyarma dakyar takeyinta don tanajin yadda idanuwa ke yawo akanta.

Zama Alhaji yayi kusada Abba itakuma ta zauna qasa kusada kaffafun daddy still kanta a sunkuye.


Tunda suka shigo yadago yafara kallonta harta iso ta zauna batareda yako kyaftaba.

Wani irin yanayi na shauqi yaji zuciyarshi nashiga by mere ganinta kawai, gani yake kamar yayi shekaru be gantaba, jiyake zuciyarshi na narkewa ahankali cikin begenta, kallonta yake ba qaqqautawa burinshi kawai tadago yayi arba da kyakyawar fuskarta dake antayashi cikin shauqi.


Qoqarin tattaro sauran nutsuwarta tayi sannan cikin murya mai dan rawa rawa ta gaidasu kanta qasa.

Duk amsawa sukai in chorus, kowanne da abinda kemashi yawo cikin zuciya.

Ahankali Ashraf ya lumshe idanunshi yana sauke numfashi silently jin muryarta ta doki dodon kunnenshi, sai yanzu yake qara regretting din biyosu dayayi don jiyayi duk abinda yakeji can gida gameda ita ba komaibane jiyake kamar ya rarrafa daga inda yake zaune qasa yaje gabanta ya rungumeta.


Shiru dakin ya dauka na wani lokaci kowa da abinda yake saqawa a zuciyarshi.


Ahankali saudart tashiga dago idanunta dasuke sheqi saboda taruwa da hawaye yafara a idon, bata saukesuba a koina sai cikin na Ashraf da shima ita yakafe da idanu.

Da sauri ta sadda idanun gabanta na faduwa don ba qaramin haskemata idanu idanun nashi sukayiba.

Shima sadda kai yayi ahankali yana lumshe idanu yana sauraron yadda zuciyarshi ke halbawa.

"Longest time Alhaji shamsu" inji kawu zahradini yana kallon daddy.

Sai yanzu daddy yasamu damar hada ido da daya daga cikinsu.

Tsayawa yayi yana kallon kawu zahradini sosai don he's face look familiar

Ahankali yashiga bin sauran mutanen da kallo don placing finger akan inda yasansu.

"Kaga ikon Allah ko? Bamu ta6a tunanin zamu sake haduwaba saigashi Allah ya hadamu again amatsayin in-laws" inji zahradini yana murmushi.

Kafe zahradinin yayi da idanu yanason tuno inda yasan face din.

Suma kingin mutanen falon kafeshi sukayi da idanu except Ashraf da haryanzu idanunshi ke a lumshe itakuma saudart kanta a sadde.

Ganin yakasa gano inda yasanshi ya sauke ajiyar zuciya sannan yace "I gave up, Sorry but i can't recall you"

Murmushi kawu zahradini yayi sannan yace "zahradini ne, qani ga Auwal, *Auwal direba*"


Cak komai dake motsi ajikib Alhaji shamsu yatsaya na wucin gadi, ya kafe zahradini da idanu yayinda sunan wanda ya ambata yashiga masa amsa kuwa a kunne.

"Alhaji shamsu muhd na wudil.... *tsohon amininka*"

Gabanshine ya yanke yafadi yawara idanu yana kallon zahradini cikin dimaucewa


"Sh...shamsu? Shamsu na? Shamsu na? Kaine shamsu na?" Yafada cikin rawar murya yana nuna zahradini da yatsarshi dake 6ari.

Dan dagowa itama saudart tayi tana satan kallon daddy cikin rashin fahimta ganin yadda daddy duk ya rude lokaci guda.

Kafin kyaftawar ido har daddy ya qaraso gaban zahradini ya kamo hannunshi duka
"Kana nan dama shamsu? Ina ka shiga? Na nemeka koina, ashe zamu sake haduwa?"

Duk kallo occupant din falon suke binsu dashi cikin rashin fahimta banda ashraf dabe dagoba haryanzu.

"A'a bani bane, zahradini ne qannenshi"

"To yana ina? Ina yake? Ashe zamu qara haduwa dama?" Yafada yana wurwurga idanunshi dasuka kada a falon kamar mai nemanshi, kallo daya zakamashi kasan baya cikin hayyacinshi.

Kawu ibrahim dake kallonsu shima tundazu shaye da mammakin ganin reaction din Alhaji ya bude baki dakyar yace
"Allah yamashi rasuwa, shekaru sha takwas baya"

Cak yatsaya yana kallon kawu ibrahim babu ko kyaftawa.

Jiyake kamar kunnenshi ne beji daidai ba, yayi me?

"Tun lokacinda kasa aka kame komai nashi akamashi terere zuciyarshi tabuga yamutu" inji kawu ibrahim da shima yanayinshi yafara canzawa.

Sunkuyar dakai ummy tayi tana dauke hawayen idanunta jin an fama mata tsohon mikin dake cikin zuciyarta itakau saudart she is never confused like this in her life.
Kallonsu kawai take cikin rashin fahimta, wai dama daddy yasansu ne? Tambayar datayima kanta kenan.

Ahankali Alhaji shamsu ya bude baki idanunshi sunyi jajir still yana kallon kawu ibrahim
"Ya rasu?" Yafada kusan cikin rada zuciyarshi na karyewa.

"Innalillahi waina ilaihi rajiun" yafada ahankali yana lumshe idanu ga mammakin kowa hawaye suka gani ya silalo daga idanunshi.

A mammakince saudart ke kallon daddy don tunda take bata ta6a ganin daddynta acikin wannan yanayinba.

Rarrafawa tayi gabanshi da sauri ta riqo hannunshi cikin nata itama hawaye na kawomata ganin yadda yake hawaye ba kakkautawa

"Daddy?" Saikuma ta toshe bakinta tana kuka.

Ashraf kanshi na sadde haryanzu idanunshi a lumshe yayinda zuciyarshi kemishi zafi sosai, jiyake komai na dawomashi fresh, tsanar Alhaji shamsu na qara farashi a zuciyarshi.


"Daddy menene? Why are you crying?" Tafada ahankali tana kallon daddyn

Bece komaiba sai sake damqe hannunta dayayi zuciyarshi na qara raunana

"Ashe bazamu sake saduwaba? Bazamu sake ganawa ba? He's gone shalele... Gone" yafada ahankali lokacin dasukayi ada nasake dawomashi fresh.

Saudart batace komaiba sai kallonshi datake itama tana hawaye.

"Ashe bazan samu damar neman gafararshi ba, yamutu da jin haushi na" yafada wasu hawayen na zubomashi.

Zahradini ne yayi karfin halin cewa "meye na damuwa to? Ai dama burinka ya taggayara ko yabarmaka duniyar gabadaya, why making up drama"

Kallonshi kawai alhaji yake batareda yasan inda magananshi yadosa ba.


"Ta dalilin abinda kaimashi yasashi mutuwa, meye na kuka kuma? Bayan abinda kakeso kasamu" inji kawu zahradini yana dan huci trying to control himself


Lumshe idanu Alhaji shamsu yayi zuciyarshi naqara karaya, cikin rawar murya yace
"Bansaniba, b..bansan hakan zaiyi affecting dinshi sosaiba... dana sani..." saikuma yayi shiru yana rufe fuskarshi da taffukan hannunshi.


"Dama tayaya zaka sani? Kayi hakanne don ka wulaqantashi, ya tozarta a idanun al'umma, jin cewa kaine sila yasashi kasa daukar haka, Auwal na sonka da zuciya daya, ya soka da dukkanin zuciyarshi amma ka rasa abinda zaka sakamashi dashi sai wannan don kawai kun samu sa6ani?"

Jujjuya kai kawai Alhaji yakeyi hawaye na zubomashi sosai don ba qaramin zafi zuciyarshi ke mashi ba

"Bansaniba, bansan sa6aninmu zaiyi affecting dinshi ba, nayi kuskure, nayi blunting acikin fushi ne lokacin, ya kamata yasan ba har cikin zuciyata na gayamashi magangganun ba, I was furious ne lokacin, nayi danasanin blunting agareshi tun kafinma yabar gidan" yafada cikin rawar murya sosai


"Ba blunting dinka ba yasashi collapsing, sharrin dakayi mashi ne, ka hadashi da customs su kwace komai nashi? Su biyoshi har gida su wulaqantashi duk don ya nemi kwatantamaka gaskiya? Dama gyara kayanka nazama sauke mu raba ne?" Inji kawu ibrahim da idanunshi shima suka kada

Cire taffikan hannayenshi yayi daga fuska yana kallon kawu ibrahim da jiqaqqun idanunshi cikin rashin fahimta

"Customs? Wulaqantashi? Kamar yaya?" Yafada in confusion

"Bakai bane kamashi kulla kullaba harsu customs suka kwace duka mottocinshi da abinda keciki suka biyoshi har gida suka turning gidan upside down? Ba terere dakayi mashiba yasashi kwantawa jinyar ajali sai yadda ka iya cin amanarshi ka ha'inceshi duk don ya nemi baka shawara as his amini"


Sosai kan Alhaji ya kulle don shi bema gane kan labarinnan ba bare gindinshi

"Ni? Sharri? When?" Yafada cikin mugun confusion....✍


Ummin fasihu ce🧚🏻‍♀️

🤵🏻👰🏻AUREN KWANGILA👰🏻🤵🏻
(Contract marriage)



Story written by Ashaanty love💖
(Ummin fasihu)




077



"Ni? Sharri? When?" Yafada cikin mugun confusion

Sosai kanshi ya kulle don bema gane inda zancensu ya dosaba.

"Must you pretend? Mu ba wannan bane gabanmu ba yanzu, abunda yakawomu shine samama yaranmu mafita a zamantakewar aurensu, bawai munzo yimaka titsiye ne akan abunda yafaruba shekara da shekaru, wannan tsakaninka da Allah ne da kuma margayi, sakkayar kowa na wajen allah, Allah ba azzalumin kowa bane" inji kawu ibrahim dake ganin kamar rainamasu hankali yakeson yi.


"Please karku barni cikin duhu, ku gayamin, meye kuke nufi da namashi sharri, na wulaqantashi?" Inji Alhaji shamsu cikin kasala

"Look, kamar yadda yaya ibrahim yace ba wannan yakawomu ba, munzo nan ne akan maganar auren diyarmu da danmu ne, meye na pretending? Ai what goes around comes around, gashi bayan shekaru da dama munsake hadewa da bond mai qarfi tsakaninmu wanda baxamuso ya tsinkeba akan kowane daliliba don mu munriga munbaiwa baya baya, gabanmu kawai muke duba, abinda ke tsakaninku da margayi be shafi auren 'ya'yanmu ba, ko yanzu saudart ta yarda ta xauna da danmu zamu riqeta hannu biyu bisa amana don babu abinda tayimana so stop pretending" inji kawu zahradini, kallo daya zakamashi kasan ranshi a 6ace yake.
Abba da tundazu beyi maganaba yayi saurin cewa
"Haba ku kuwa? Duk baikai hakaba, karku manta agaban yara muke and..." saikuma ya kalli daddy dake kallonsu in confusion sannan yace

"Alhaji shamsu, kace bakasan abinda suke maganaba akai?"

"I can swear to you, wlh bansan me suke nufiba"

"Ok zaka iya bamu labarin abinda yafaru bayan rabuwarku da margayi Alhaji auwal?" Inji abba yana kafeshi da idanu


Ajiyar xuciya ya sauke, shi koyaya akace margayin nan sai yaji abu ya ta6amashi zuciya, he can't believe amininshi ne yaxama babu.

Ahankali ya bude baki dakyar yafara cewa
"Auwal ba a aboki kawai na daukeshi ba ko amini, duk yawuce nan, auwal ya mayemani gurbin danuwan da bandashi, auwal komai ne agareni, masoyi, aboki, yaya.

Duk damuwata shi nake kaimawa muhadu cikin ikon allah musamu mafita, shike kwa6ata idan nayi ba daidai ba batareda yin la'akari da yadda zanjiba, shike bani shawarwaru wanda suke matuqar yimin amfani.

Nasan bani acikin jerin mutane masu hallayen kirki, inada son kudi, ina nemansu at every narrow way, wanda hakan yasamo asaline tun kuruciyata da ban saka komai agabanaba sai neman kudi don atunani sune jindadin rayuwa, sune komai.

Auwal yasha mani fada akan hakan amma ban dauka, saidai in nuna ba gamsu kuma bazan sakeba amma hakan be hanani fasawa"

Shiru yadanyi yana sauke ajiyar zuciya sannan yacigaba dacewa

"Mun samu sa6anine dashi bayan haihuwar shalele, na buqaci muje tacire mahaifarta don aganina diya daya ta ishemu, tara 'ya'ya najawo talauci da wahala.

Nan take tanuna rashin amincewarta da hakan, na buga na raya amma taqiya acewarta baxata kashe kanta da kanta ba.

Hakan yasani fita harkarta na qaurace mata, ban yarda auwal yasan da hakanba don nasan bazai ta6a bani goyon bayaba.

Kawai ranan saigashi har shagona lokacin ban gina mall dinaba, fada sosai yaimani kamar zai cinyeni don sosai ranshi ya6aci ashe khadijah taje tasameshi ta fadamashi da abun ya isheta.

Ban tankamashiba harya gama banbaminshi yakuma ce bazata cire mahaifaba saidai ni inje a ciremin kwayakwan haihuwa idan dagaske haihuwarce banso aiba dole sai ita zata cire mahaifaba.

Raina yayi mugun 6aci a ranar kuma bawai fadan auwal yafi 6atamin raiba, A'a qarata da khadijah takai wajenshi yafi 6atamin rai.

Ina komawa gida nima najuyemata nawa kwandon masifar, ataqaice dai munfi sati ana abu guda, har allah yakawo qarshen aurenmu asanaddiyar hakan.

Bayan mutuwar aurenmu da kwana biyu Auwal ya ritsani gida, ashe labari ne yakaimashi.

Ranar naga 6acin ran auwal da ban ta6a ganiba don sosai ya wankeni tass sai akayi rashin sa'a nima lokacin awuya nake don tun bayan rabuwarmu komai yaqi yimin dadi arayuwa.

Bazanso tuna magangganun dana fasamashi ba a ranar... idona yarufe... nakasa gane kuskuren danake tafkawa.... ataqaice dai aranar abotarmu ta watse don kowa alokacin zuciyarshi awuya take ankasa samun daya daga cikinmu dazai ankare da 6arnar damuke shirin aikatawa.


Korar wulaqanci nayi mashi.... nakuma yimishi iyaka da gidana da ni kaina, shima yayimin alqawarin babu shi babu ni.

Tun fitarshi a falona kafin ma yakai gate nafara danasani saidai girman kai ya hanani aikata abinda zuciyata ke rayamin wato inbishi mu sasanta.

Haka na kwana cikin baqinciki da 6acin rai, abu ya hademin goma da ishirin, na farko na rabu da matata da shalelen diyata ga asarar babban jigo danayi.

Ganin garin ya daina yimin dadi kullum ina cikin damuwa yasani barin kasar gabadaya.

Ban tashi dawowaba sai bayan shekaru uku wanda alokacin allah ya budamin sosai naqara arziqi saidai zuciyata naga Auwal dina ina matuqar kewanshi don a daddafe nayi wannan shekarun a can qasar.


Bayan dawowata nigeria na shiga nemanshi saidai tashin farko nakasa gane gidanshi, gadaini a unguwar amma gidanshi ya 6acemin haka nagama bulayi na nakoma gida.

Ahankali ahankali nacigaba da naimanshi amma shiru, ga inda yake aikinshi babu alamun masu irin aikinshi duk ancanzama wurin fasali.

Ataqaice nakusan wata uku sannan allah ya hadani dawani abokin aikinshi Mallam yunusa wanda irin sana'arsu daya dama shima motoci gareshi don yama fi auwal jimawa a harkar.

Sosai nayi farinciki alokacin don aganina nasameshi nagama saidai abinda yafadamin yasa murnata komawa ciki, baqinciki ya maye gurbinta.

Cemin yayi shekararsu daya kenan da barin qasar wai ya saida gidanshi da mottocinshi sun koma turai dazama dashi da duk family dinshi

Haka nakoma gida jiki a mace, ban daddaraba na shirya naje garinsu wudil dukda zuwana daya lokacin rasuwar mahaifinshi.

A wudil ma haka naita galbaro na nagaji don garin ya canza sosai jama'a su qara yawaita, kwanana biyu nabaro wudil jiki a sanyaye nadawo gida.

Haka nakusan cinye sati ina jimami sosai sannan dakyar nacigaba da al'amurrorin gabana saidai auwal nanan maqale a zuciyata ina kuma roqon allah kowanne sallah ya hada fuskokinmu duk daran dadewa.

Ganin kadaici yamin yawa yasa na nemi a maidomin saudart jin mamarta aure zatayi.

Dakyar suka bani ita, sai alokacin nadan samu sauqi don sosai take debemin kewa.

Haka nacigaba da rayuwata daga ni sai yata, nakasa qara aure don mata tsoro suke bani, bana fatan auro wanda zata cutarmin da yata wanda nakejinta kamar tsokar jikina.

Haka naita zama dagani sai yata ina kulada ita agefe kuma nacigaba da business dina inda daga baya na bude mall dina mai suna A.S MALL INTERNATIONAL LTD.

*A.S* din na nufin *AUWAL.SHAMSU* don har alokacin nakasa mantawa dashi, haryanzu... har gobe"
Shiru yayi yana kallon mutanen falon wanda sukayi tsitt banda kallonshi babu abinda suke, ummy idanunta sunyi jajur don tayi hawayen tayi hawayen harta gaji itama umma sosai jikinta yayi sanyi don kallo daya zaka mata kagane hakan.

6angaren su kawu ibrahim ma kallonshi suke suma da alama jikinsu duk yayi sanyi.

Sadeeq dake zaune qasan rug kusada ashraf shima kallo daya zakamashi kasan shima jikinshi amace yake don sai kallon daddy yake da expression din tausayi a fuskarshi, shikau goga Ashraf baka iya gane yanayin dayake ciki don haryanzu kanshi na qasa idanunshi kuma a lumshe saidai daga nesa kana iya hango jijjiyar data fittomashi rado rado a gefen wuya.

Saudart kau kanta na kife akan cinyar daddy tana hawaye silently.

Ahankali yakai hannu ya shafa kanta yana dan murmushi
"Saudart kadai ke gareni, ita kadai ta ragemin duniya da lahira, itace farincikina nine nata, she can do anything just to make me happy amma kwadayina da son kudi yasa nayi tampering da nata happiness din... i forced her, taso nunamin kuskuren haka amma naqiji, na fake da ciwon qarya duk don ta yarda don nasan bazata ta6a jurar ganina cikin damuwaba takasa yimin maganinta muddin tanada ikon yin hakan, haka na tilastamata ba don komaiba saidon nasan zan qaru, itama haka amma dayake allah allah ne saigashi yajuyemana komai ba kaman yadda na tsaraba, ya gwadamin ban isa inyima kaina abinda beyi niyyar yiminba saigashi i end up hurting my one and only child, sanyin idaniyata"

Shasheka saudart keyi ahankali kanta kife da cinyarshi tanajin wani abu na ta6amata zuciyarta.

"Kuyi haquri, words can't express how sorry i am, just find a place in your heart and forgive this greedy man" yafada yana lumshe idanu.

Shiru falon ya dauka, bakajin komai sai sheshekar saudart shima can qasa, anrasa wanda zai magantu cikinsu.

Dakyar kawu ibrahim yabude baki vayan wani lokaci yace
"Kenan vakai kasa aka kamama auwal kayaba?"

Bude idanunshi yayi ya kalleshi yace
"Wane kaya? Ni nakasa gane abinda kuke nufi"

"Bayan rabuwarku da Alhaji da shekaru biyu bakai ka hada baki da customs ba suka kama mashi mottocinshi ba da kayyayakinshi? Har suka biyoshi gida suka burkice gidan?" Inji kawu ibrahim

Girgiza kai Alhaji shamsu yayi cikin confusion
"Customs kuma? Ni alokacin ina dubai"

Abba ne ya sake cewa
"Please ko zaku gayamana abinda yafaru bayan rabuwar margayi alhaji auwal din da Alhaji shamsun?"

Shiru dakin ya dauka sannan ahankali shima kawu ibrahim yashiga bada labarin abinda yafaru bayan rabuwarsu zuwa kama mottocin margayi da akayi zuwa yadda aka gayamasu sa hannun alhaji shamsu ne zuwa jinyarshi zuwa rasuwarshi zuwa wahalhallun da iyalansa sukasha har kawo yanzu.

Sosai Alhaji shamsu tashiga tashin hankali, banda innallilahi babu abinda yake maimaitawa hawaye na zubar mashi.

Kasa cewa komai yayi don he's speechless ma.

"Amma waya fadamaku Alhaji shamsun ne keda sa hannu akan hakan?" Inji abba

"Abokan aikinshi ne"

"Can you specified?"

"Yes, tsohon ubangidanshi ne mallam tukur sai wani abokin aikinshi mallam yunusa"

"Alhaji shamsu waya cemaka margayi shamsu yabar qasarnan gabadaya?" Inji abba yana kallon daddy

Shiru yayi don he is still shock

Dakyar yabude baki bayan wani lokaci yace
"Mallam yunusa"

"Then... akwai wata qullala anan, lokacin da abun yafaru alhaji shamsu ma be qasar koko kuna ganinshi ko jin labarinshi?"

"A'a, tun bayan rabuwarsu da margayi ko labarinshi bamu sake jiba" inji zahradini

"Gaskiya to something is fishy here" inji Abba

"Yes, ni saima yanzu nafara tuna wasu abubbuwan da hankalina be karkata gareshi ba alokacin" inji kawu zahradini

"Kamar?" Inji abba cikin alamun tambaya


"Mallam tukur, farko farkon da margayi yafara hada motarshi yadan chanzamashi kullum shine yayyatashi ga mutane wai beda godiyar allah wai dan qauye yashigo qauye yanason fin ubangidanshi, alokacin banwani dauki abin serious ba don naga lafiya lau suke mu'amallarsu kamar da saidai idan benan ne zaita sukarshi, da allah ya ida budamashi kuma shi dakanshi mallam tukur din yanemi ya ajiyemashi motarshi tunda shima yazama ogan kanshi, mafari kenan dayabar tuqi, shikuma mallam yunusa dama aminin tukur kansu ahade yake.

Bayan rasuwarshi kuma sune nafarkon juyaman baya sukaqi bani mota acewarsu basuda empty mota bayan nasan akwai kawai qin badawane sukai, gaskiya nima i smell something fishy"

"Kenan sune suka hada baki aka cuceshi?" Inji kawu ibrahim cikin wani yanayi

"Bama ceba, amma definiately zasusan wani abu gameda hakan" inji abba.

Shiru falon yasake dauka, shidai daddy besake cewa komaiba don abinda ya dameshi ma ya dameshi, he's soo lost in thoughts

Ashraf kau haryanzu be dagoba saidai jikinshi yayi mugun sanyi, jinshi yake so guilty, bugawa sosai zuciyarshi take kanshi na harbawa. Tsoronshi daya shine kar ace he's taking revenge on the wrong person....✍


Please fans asani acikin addu'a, i really need your prayers, allah yacikamani da kowama burikanmu na alhairi👏

Ummin fasihu🧚🏻‍♀️

🤵🏻👰🏻AUREN KWANGILA👰🏻🤵🏻
(Contract marriage)



Story written by Ashaanty love💖
(Ummin fasihu)



078



Ba Ashraf ba su kansu kawu dasu ummy jikinsu saida yayi sanyi, they never thought Alhaji shamsu was innocent, sanin halinshi na greediness yasasu yarda cewa zai iya aikata hakan, basu ta6a kawoma ransu bashi bane.

"Hasbunallahu wani'imal wakeel! Alhaji shamsu kenan all these years damuke riqe dakai azuciya you're innocent? Ta ina zamu fara baka hqr?" Inji kawu ibrahim a sanyaye.

Shiru falon yasake dauka kowa da abinda ke ranshi, saudart kau haryanzu bata dagoba daga kifa kan datayi a lap din daddy

"Alhaji shamsu we're so sorry, mun makance mun kasa tuna shaquwa da zumuncin dake tsakaninku har muka yarda da magangganun mutanen nan, alokacin gani muke zaka iya dubada yadda abotarku ta watse kukayi baranbaran atunaninmu fansa ka dauka ta wannan hanyar don quntatawa margayi.... will you please find a place in your heart to forgive us" inji kawu zahradini shima asanyaye

"Shiyasa akace zato zunubi koda yazama gaskiya, da wane ido zamu kalleka shamsu?" Inji ummy tana share hawaye.

Ajiyar zuciya daddy ya sauke zuciyarshi na quna, shikau me yayima su mallam tukur zasu jamashi wannan sharrin? Yana iya tuna lokacin da suke aminta da margayi yadda mallam yunusa ke zuwamashi da maganar margayi cewa yaceme kaza yace kaxa duk don yaji haushi amma beta6a biyemashi ba saidai yanuna mashi bakomai ai shima yasan da zancen, bejin zai iya yafemasu, sune sanadin margayi auwal, sunsa ya mutu da baqincikinshi.

"Dan allah ku daina neman yafiya awajena, ni bakumin komaiba, ko nine a matsayinku alokacin dolene in yarda da hakan, idan ma batun yafiyane saidai in nemi naku, wataqila da banso kaina dayawaba na nuna banson haihuwa da bamu samu sa6ani da margayi ba bare har akaiga haka, kuyi haquri mu yafi juna, tabbass na koyi darasi, ko ince darussa, na gane kwadayi mabudin wahalane kuma zafin nema baya kawo samu, please forgive me too"

"Mune xamu nemi yafiyarka shamsu, ka yafemana" inji kawu ibrahim

"Allah ya yafemana bakidaya, yajiqan Auwalu na yasa ya huta yakai rahma a qabarinsa yakuma hada fuskokinmu gabadaya a aljannatul firddaus"

Da amin duk mutanen falon suka amsa cikin sanyi
"To alhamdullilah, dama komai dake wakana a rayuwarnan rubuttacene jikin lau'un mahfuz, gashi cikin ikon Allah komai ya warware mana cikin sauqi, naji dadi sosai da warwarewar wannan matsalar nakuma yi farinciki da bayyanar gaskiya adaidai wannan lokacin, Allah kenan! Kunga ikon Allah ko, bayan shekaru kusan ashirin saigashi yasake hadaku don warwaremuku gaskiya, wannan ba qaramin abun farinciki bane, fatanmu anan shine allah ya jikan margayi dama kullihin musulmai yakuma tona asirin masu sa hannu a sanadin ajalinshi, allah yacigaba da karemu daga sharrin mahassada da maqiya na zahiri da 6uya" inji Abba

Duk da amin suka amsa wanda hakan yai daidai da kwala kiran sallar azahar.

Anan duk akayi haramar tashi yin sallar zuhr din.

Daddy ya umarci saudart takaisu ummy sama su gabatar da sallar.

A kunyace ta tashi tana masu iso sukabi bayanta.

Haka duk aka fita daga falon aka bar daga Ashraf sai sadeeq.

Matsawa sadeeq yayi kusada ashraf da kanshi ke sunkuye haryanzu yakira sunanshi ahankali.

Shiru ashraf yayi kuma yakasa dagowa.

"Ka tashi mallam muje muyi sallah ko sai munrasa jam'i?"

Sai a sannan yadago ahankali ya kalleshi

"Muje" inji sadeeq yana qoqarin miqewa.

"Sadeeq how will I face this man? Tayaya zan iya fuskantarshi after all i did to him? Ya sallam" yafada yana dafe kai

"Hmm i told you ai, ba'a yanke hukunci akan abinda bakada tabbaci akai now see what happen"

"What am i suppose to do? I can't face him,

Please Login or Register in order to submit comment