Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

qilguwa kullum cikin busy yake yazama babban dan kasuwa.

Tun bayan haihuwar Ashraf *Ummy* kamar yadda Ashraf ke kiranta bata qara haihuwa ba sai 6arin datakeyi akai akai wanda sunyi maganin amma a banza.

Da farko Alhaji Auwal (Abbu) yaso ajuya mahaifarta saboda wahalar dayaga tanasha amma saita qiya acewarta abarta ahaka haka allah ta tsara mata.

Ashraf nada shekara biyar Abbu tabiyama inna, inna Raliya, ummy, inna jamila da zainab matar Nura hajji suka dunguma sukaje suka sauke faralli.


Bayan dawowarsu da yan wattanni akasama Alhaji shamsu biki dawata shuwa Arab ta garin borno.

Acikin wannan lokacin ciwon zuciyar Inna yatashi sosai babu wata wata Auwal ya daukota takawota asibitin kano aka cigaba da bata kulawa saidai dayake lokacinta na kusa kwana biyar tayi tana jinya ta rasu.

Sosai mutuwar ta girgizasu don sunyi kuka marar iyaka.

Haka suka dauki gawar suka juya wudil don Inna tabar wassiya idan tamutu koma inane a maidota wudil arufe don tafison arufeta a mahaifarta.

Bayan sati biyu suka dawo kano rayuwa tacigaba da tafiya.

Izuwa yanzu ansaka Ashraf makarantar primary ta private kuma allah yayimashi qwalwa da basirar daukar abu don shike ciwo nadaya a ajin duk qarshen term

Ba'a dadeba bikin Alhaji shamsu ya matso nanfa sukaita shirye shirye babu kama hannun yaro.

Duk tare suke komai da Alhaji Auwal don bawani dangi ke gareshiba sosai sai tarin abokan arziqi da abokan kasuwanci.

Gaggarumin biki akayi nagani na fada inda babu laifi ansha shagulgula sosai sannan aka kawo amarya khadija dakin mijinta.


Haka rayuwa tacigaba da tafiya Ashraf sai qara girma yake da wayau, arziqin Abbu sai qara hauhawa yake allah nasa mashi albarka hakan yasa yakeda maqiya da mahassada masu hassada dashi a6oye batareda yasaniba.

Bayan shekara daya da aurensu Alhaji Shamsu sai Allah ya azurtasu da samun diya mace kyakyawa sak uwarta.

Alhaji shamsu baki yaqi rufuwa don murna, ranar suna na zagayowa aka radamata sunan *SAUDATU*


bayan haihuwar da 'yan wattani su Alhaji shamsu da matarshi khadija suka fara samun matsala atsakaninsu sanaddiyar sata dayayi acire mata mahaifarta wai diya daya ta ishesu acewarshi 'ya'ya talauci suke jawowa.

Firr khadija taqi yarda acewarta bazai sata ta kashe kanta da rai ba, tun suna abin a tsakaninsu har yakai kunnen Abbu kasancewar Khadija tagayamashi ko zata samu yanunama Alhaji shamsu daidai.

Abin yaba Abbu haushi sosai saiyaje yasamu Alhaji shamsu har company dinshi yayimashi magana shikuma sai abin ta hassalashi sosai ganin wai khadija takai qararshi wajenshi kamar wani ubanshi.

Nanfa Alhaji shamsu yafara zazzaga bala'i ta inda yake shiga batanan yake fitaba, aranar dakyar Abbu yafito company din rai 6ace abinda beta6a faruwaba a tsakaninsu.


Shikuma Alhaji shamsu yana komawa gida yarufe khadija da fada ta inda yake shiga batanan yake fitaba yace kuma cire mahaifa dole ayi muddin tanason cigaba da zama dashi.

In taqaice muku dai saidai auren yamutu da abu yaqi dadi wanda hakan ba qaramin 6ata ran Abbu ba yayi.

Wannan karon har gida Alhaji Auwal ya tadda Alhaji shamsu sukayi tatass inda daganan abotarsu ta shekara da shekaru ta watse.

Ummy sam bataji dadin hakanba amma ya suka iya?

Kan kace me? Har labarin 6atawarsu ya zagaye koina da aka sansu, mutane sai jimamin abun suke yayinda wasu suke farinciki akan haka.

Shekara daya da faruwar wannan al'amari Ummy tasake samun juna biyu lokacin shekarar Ashraf takwas kenan.

Sosai cikin yabata wahala sannan tasamu ta haifeshi bayan tasha baqar wahala tasamu diya mace sak Ashraf saidai bata ida kamoshi a haskeba.

Zokaga murna wajen Ashraf don sosai yake sha'awar qane ko qanwa dama.

Ranar suna na zagayowa akasamata sunan margayiya Inna wato AMINATU amma ana kiranta da *Baby*


Ana haka bikin zaharadini yataso inda ya auri yar kano suka tare a gidanshi da shima yagina a unguwar.

Kwanci tashi ba wuya, baby anfara girma don harta shekara biyu wanda yayi daidai da shekarun ashraf goma da wattanni.

Har a lokacin Abbu basa ga maciji da Daddy, sun watsar da zumuncinsu don ko labarin juna basaji.

Ana haka watarana Abbu na zaune cikin iyalanshi zaharadini ya bugo mashi waya kome yacemishi oho? Saiga Abbu ya zabura zaune har yana qwarewa da abinci

Cikin sauri ummy ta bashi ruwa suna jeramashi sannu ita da yaran.
Saida tarin ta lafa sannan ta tambayeshi lafiya? Yace ba lafiya bari yaje yadawo.

Haka ya fice be ida qarasa abincinba wanda itama ummy kasa ci tayi sai barosu ashraf datayi a dining tadawo falo tazauna tana addu'ar allah ya jiyardasu alhairi.


Acan kau Abbu yashiga tashin hankali marar misaltuwa don duka mottocinshi jami'an custom suka kame da abinda suka dauko.

Babu yadda beyiba wajen ganin an sakarmashi su amma abu yaci tura kai daga baya ma har gidanshi jami'an sukazo suka watsamashi komai suka 6alle store dinshi suka kwashe shinkafa ko taci basu bariba.

Wannan cin zarrafin baqaramin qonama Abbu rai yayiba don gani yake wannan cin fuskane babba.

Be ida shiga tashin hankaliba saida yaji cewa tsohon abokinshi kuma amininshine ummul aba'isan faruwan wannan lamarin.

Sosai abun ya dakeshi wanda har saida yakwanta ciwo.

Alokacin zaharadini ne yake taimakonsu dana magani don yadda kasan daukewar ruwa hakan komai na arziqin Abbu ya qare.

Magani akema Abbu amma kamar qaramashi ciwon ake.

Kullum cikin ambaton sunan Shamsu qolo yake yana hawaye.

Sosai su ummy dama kingin danginshi suka shiga tashin hankali akoda yaushe ummy da ashraf dashima yafara sanin komai cikin kuka suke saiya kasance Ashraf yakasa mance sunan da abbu ke yawan maimaitawa yana hawaye. Abinka da yaro saiya riqe sunan gamm a kwakwalwarshi yayinda yakema mammalakin sunan tsana wacce bata misaltuwa.


Saida Abbu yayi sati biyu sannan Allah ya dauki ranshi, mutuwar da ta girgiza jama'a da dama kar ummy ma taji labari.

Haka dole akamashi sutura jama'a takoina ancika unguwar danqam suka rakashi aka kaishi gidanshi na gaskiya.


Su ummy basu tashi gane kurensu ba saida duk aka watse nan fa talauci ya kunnomasu kai.

Gashi dama zaharadini yake dan taimakawa to shima yanzu babu mota hannunshi kuma kamar hadin baki kowa yaqi bashi dukda kau mutuncin da mutanen keyi da margayi Auwal dayake raye.

Hakan yasa yakoma kasuwa yana tsaron shago wanda abinda yake samu bewani taka kara ya karya ba.

Ganin haka yasa ummy ta tuntu6i zaharadini akan asiyarda gidan dasuke ciki su siya qarami kingin kudin saisu jujjuya.

Saida zaharadini ya tuntu6i yayyanshi na wudil saboda hadin kai irin tasu suka kauyi maraba da hakan don suma basujin dadin halin da iyalan dan uwan nasu yake ciki kawai don basuda halin taimakawa ne.

Kan kace me? Har an saka gidan kasuwa aka kau siyeshi da daraja, zaharadini ya samarmasu dan qaramin gida a unguwarsu suka zauna ya miqamata kingin kudin inda taqi amsa tace yaje yaita jujjuyawa kawai.

Shima qin yarda yayi har saida magana taje gasu Kawu ibrahim nan shima kawu ibrahim yayi na'am da shawarar Ummy kan zaharadini ya juyasu tunda shima kusan beda sana'a yanzu tsayyaya albashi sai aba ummy wani kaso acikin kudin itama tafara business.


Hakan kau akayi, zaharadini yaje ya sari kayan kitchen da kudaden yayi hayar shago acikin kasuwa itakuma ummy tafara sana'ar saida kayan humra da turrarukan wuta wanda Allah ya dubi maraicinsu yasamasu albarka aciki.

Ashraf da tuni ancireshi daga makarantar kudi don yanzu tafi qarfinsu aka maidashi ta gomnati yazana common entrance dinshi yakau fito da result mai kyau yasamu admission awata makarantar gomnati ta secondary.

Ashraf yanada hazaqa sosai kasancewar yasamu good background a makarantar primary dinsu kasancewar private ce.

Ahankali yafara suna don ashraf akwai qoqari da saurin fahimta don shike topping din class dinsu duk term.

Bayan haka ga baiwar kyau da Allah yabashi don kallo daya zakamashi kasan ya hada jini da fulani.

Ganin yadda ake sonshi ake kuma lilliqemashi yaja ashraf tsirowa da halin jinkai da miskillanci.

Yaga daman kana mashi magana saiya mula yasha iska sannan ya amsa a dage.

Haka yan aji ke fama dashi musanmman masu liqemashi ya koyamasu karatu, bazaiqi koyamusu ba amma saiya wanasu son rai ya shamusu qamshi sannan ya koyamasu hakan kuma be 6atamasu rai don su shan qamshinshi ma burgesu yake don komai yake kyau yake musu.


A ss1 suka hadu da *SADEEQ UMAR* the mathematician kamar yadda aka samashi suna a school din.

Duk aji daya aka sasu kuma ga lokacin basusan junaba don sadeeq transfer akayi mashi yayi junior waec a school din, sai ya kasance dukkansu sun hadu a commercial class.


Da farko gaba da kishi suka farayi dajuna kasancewar kowa na taqama shi genius ne.

Ashraf yafishi qoqari a sauran subjects din irinsu biology, english, business studies da dai sauran subjects din da babu calculation saidai sadeeq ya dokeshi a calculation don yadda kasan aljani haka ya iya lissafi hakan baqaramin 6ata ran ashraf yakeba don yasaba shine agaba a komai.

Hakan yasashi yin kishi da sadeeq musanmman idan yaga students naxuwa wajenshi solving din lissafi.

Shima sadeeq lura dayayi da yadda ashraf kemashi wani gani gani yasashi kama kanshi yanuna besan da wanzuwarshi ba.

Haka fa akacigaba da competition tsakaninsu kowa nason gwadawa dan uwanshi iyakarshi.

Saida suka shiga ss2 suka shirya shima sadeeq ne yanemi suyi abota don harga allah ashraf na burgeshi.

Kamar yadda yasaba saida yasha qamshi yana hura hanci sannan ya amince dukda can qasan ranshi murna yake don shima sadeeq na burgeshi don sadeeq badai raha da barkwanci ba, kwata kwata beda saurin fushi saidai idan aka quleshi beda kyau sa6anin ashraf da kamar akan wuya yake abu kadan ke hasalashi.

Ahaka suka qulla abota mai qarfi duk inda kaga daya sai kaga dayan har takai babu wanda besan da abotarsuba a fadin makarantar.

Alokacin allah yasama sana'ar kawu zaharadini albarka sosai don harya canza shago ya kama babba yana cigaba da sana'arshi ta kayan kitchen ashraf na dan kama mashi da tsaron shago duk sadda beda wani aikin yi.

Ahakan suka qarashe secondary school din lokacin baby ana primary.

Baby ta taso yarinya mai rigima da iyayi ga baki zai kamar parrot, rawar kanta yasa basa shiri kwata kwata da ashraf don kwa6darta yake idan tayimashi ba daidaiba babu abinda ya dameshi saidai yana sonta sosai.

Bayan result dinsu yafito ne suka samu daddadan albishir na scholarship da aka bada a school dinsu na mutane biyar qasar waje wanda ciki harda ashraf da sadeeq.

Farincikin ranar har rawa saida suka taka.

Cikin dan qanqanin lokaci aka gama shirin komai suka lula UK karatu.

Acanma bata sauya zaneba suna zuwa ba'a wani jimaba sukayi fice a school din saboda qoqarinsu ga hadin kai don kodayaushe tare suke dukda kamar kaji suke kodayaushe cikin fada suke donma sadeeq nada haquri.

Nanfa akaimasu caa don lokacin sun zama samari masu jida kyau da gayu dukda sadeeq ba fari bane amma baqinshi mai kyau ne ga uwa uba fara'a dake qarawa mutum kyau dayakeda ita.

Kan kace me yanmatan school din sukai musu caa dukda vasu cika tunkarar Ashraf ba don ba qaramin kwarjini yake musuba gashi fuskarshi ba wasa kullim a dinke take.

Sa6anin sadeeq da ba ruwanshi idan mace ta tinqareshi saiyace yanada aure harda 'ya'ya biyu qauye idan kuma tanason yayi nabiyu daita ya kaita qauye to.

Haka yake samu su rabu lfy dasu batareda ran kowa ta 6aci ba.

Ana haka kwatsam yaga ashraf na soyayya da suzy wata yar nigeria wanda itama karatu yakawota qasar saidai batada kamun kai ko kadan ga shiga ta fidda tsiraici.

Da farko yaso nisarda ashraf aibunta anma saiyaga kamar yana sonta sosai saiya qyaleshi saigashi basu wani yi nisaba suka rabu inda sukayi wani gaggarumin fada a filin makaranta sadda yaganta suna kissing da wani bayahude mai suna chris james

Daya nuna 6acin ransa akan haka saita fara bala'i wai bawani matsiyacin da zai hanata sakewa a school donma sun samu an biyamusu scholarship da a ina zasu ganta bare har raini yashiga tsakani?

Sosai abun ya6atawa ashraf rai don dakyar sadeeq ta janyeshi daga filin wanda yacika danqam da yan ganin qwam.

Tun daga lokacin kowa yakama gabanshi babu mai kula dan uwanshi har suka kammala abinda yakaisu suka dawo nigeria.

To anan ne zaharadini ya maidomasu dukiyarsu duka ganin ashraf ya mallaki hankalin kanshi.

Nan ummy taqi yarda suka amshi kudin kawai suka barmashi ribar dayaita juyawa hakan kuma ba qaramin dadi yayimasuba kuma hakan yaqaramata qima a idanun dangin mijinta.

Ahankali ahankali shima ashraf ya shiga harkar kasuwanci kasancewar shi dama ya karanta.

Nan sukayi hadin gwiwa da abokinshi kuma dan uwanshi sadeeq suka fara da kadan kadan har allah yasaka masu albarka suka bude tanqamemen company dinsu wanda suka samashi suna A.A ENTERPRISES LTD
wanda ahankali ahankali sukayi rassa a qasashe daban daban, talauci ya qaura a wannan ahalin suka koma kamar koma ince fiyeda yadda suke da.

Ashraf shima babanshi yabiyo a kyauta shiyasa kaf family dinshi babu mai kukan babu don babu babu din.


*CIGABAN LABARI*


sainaga ruwan comments tukun, naga alamun kwana biyu kun danyi sanyi๐Ÿ™


Ummin fasihu ce๐Ÿงš๐Ÿปโ€โ™€๏ธ

๐Ÿ‘ฐ๐Ÿป๐Ÿคต๐ŸปAUREN KWANGILA๐Ÿคต๐Ÿป๐Ÿ‘ฐ๐Ÿป
(Contract marriage)




Allah ka bamu zaman lfy a qasarmu nigeria๐Ÿคฒ

Allah ka ji6anci lamuranmu, karka barmu da kanmu๐Ÿคฒ



Story written by Ashaanty love๐Ÿ’–
(Ummin fasihu)




067



*CIGABAN LABARIN*




Wani matsanancin ciwon kai ya saukoma Ashraf nan take yayinda jikinshi har tsuma yake saboda tashin hankali.

Ummy is requesting na ya datse igiyoyin dake tsakaninshi da Saudart duka kuma she mean it don ya hango dagaske take acikin qwayar idanunta.

Jiyayi an dafa kafadarshi ta dama.

Ko be dagoba yasan sadeeq ne hakan yasashi lumshe idanunshi dasuka chanza kala yana sauraron bugun ziciyarshi.

Har lokacin sadeeq na dafe da kafadarshi saidai yarasa kalmar dazaiyi amfani dashi wajen kwantar mashi da hankali don shima hankalin nashi atashe yake don shima bega alamun wasa ko sassauci atareda ummy ba.

Sun dade ahakan sannan sadeeq yayi qarfin halin jawo hannunshi sama alamun yataso sutafi.

Babu musu yatashi dakyar suka juya suka bar falon sadeeq na janye da hannunshi shikuma yana biye dashi kamar raqumi da akala.



Zama ummy tayi bakin gado tana dafe kanta da hannu daya.

This is unbelievable, takasa yarda da abinda Ashraf ya gayamata.

Saudart? Diyar shamsu? This is super shocking.

Ya akayi takasa hango kammaninta dana mahaifiyarta? Dama kullum idan ta kalleta saitaga kamar ta ta6a sanin face din awani waje.

Ya akayi takasa ganewa duk tsawon wannan lokacin? Kenan da khadija suke waya lokaci bayan lokaci?
Ya akayi takasa gane muryarta? Ya akayi su kawu ibrahim suka kasa gane shamsu lokacinda sukaje nemama Ashraf aure?

Qarar budewar kofa dataji yasata dagowa daga dafe kan datayi tana kallon mai shigowa.

Baby ce tashigo idanunta jawur alamun taci kuka.

Kallonta tacigaba dayi harta qaraso kusada ita ta zauna qasa.

Shiru dakin ya dauka kafin baby ta dago a raunane.

"Ummy?.." sai kuma tayi shiru tana hawaye.

Itama ummin shiru tayi saidai batabar kallonta ba

"Ummy don allah karki raba yaya da aunty..please karki 6ata komai ummy, ki gyarashi instead" tafada cikin muryar kuka.


Nan ma shiru, ummy batace uffan ba.

"Ummy.."

"Get out" inji ummy ahankali

"Ummy please..."

"Out!!!" Ta daka mata tsawa wanda babu shiri ta miqe tanufi hanyar fita tana toshe baki.

Komawa ummy tayi ta jingina da kan gadon, tunanika kala kala na kai kawo azuciyarta.


********************************************

Zaune saudart take a garden din gidansu ta kafe waje guda da idanu .

Tunda tasamu labarin ummy tasan komai hankalinta yaqi kwanciya.
Koda yaushe cikin fargaba take na kar mamy taji lbr don tasan idan taji to ta kade har ganyenta.

Wayarta ce tasake daukar ringing a karo na ba adadi.

Duba takai ga wayar tana kallon sunan mai kiran yayinda takejin wani iri cikin ranta.

Baby ce, tun shekaran jiya take matsamata da kira da massages kala2 tana magiyar tayi picking din call dinta.

Sosai takejin ba dadi har cikin zuciyarta don harga Allah tana qaunar baby fiyeda tunanin mai karatu don ta dauketa ne kamar qaramar qanwar da batadashi.

Haka taita kallon kiran harya tsinke sannan tasaki ajiyar zuciya ta dauki wayar ta kasheta gabadaya don Allah yasani ko zata shekara tana kira bazata iya dagawa ba, to ta daga tace me?

Komawa tayi ta jingina da resting chair din tana lumshe idanu tana tunanin hanyar daya kamata tabi don kawo qarshen wannan qaddararren auren.




Kafin su iso wani zazzafan zazza6i ya lullu6eshi, jikinshi yayi rauu.

Ganin haka yasa sadeeq juya akalar motar zuwa gidansu don bazai iya barinshi ta kwana shi kadaiba acikin wannan halin.


Dakyar ya taimakamashi yakaishi dakinshi ta kwantar dashi sannan yafito yana amsa tambayar ummy daketa tambayarshi lfy?

Amsamata yayi da zazza6i yakeyi sannan yayi saurin fita saboda gudun ta jegomashi wata tambayar.

Tunani umma tafarayi to idan zazza6i yake ina matarshi dazai kawoshi nan?

Hakan yasata daukar wayarta tashige daki don kiran unmy taji ko lfy?

Be dadeba sai gashi yadawo hannunshi dauke da ledar magunguna yashige dakinshi.

Cikin bargo ya tadda Ashraf yashige ya qudundune sai rawar sanyi yake.

Remote din a.c ya dauka ya kashe a.c din dakin sannan ya haura kan gadon yana dan yaye bargon.

"Ya sallam" tafada jin hucin zafin daya dakeshi, ahankali yakai hannunshi a saman goshinshi yajishi rauu.

"Sorry friend" yafada cikin tausayawa

"Bari na amsomaka abinci kaci kasha magani kaji ko?"

Shidai be bude idaninshi ba bare ya amsa.

Tashi sadeeq yayi ya bude kofar yafita don samarmasu abinci.

A falo ya tadda umma zaune da alamu ma tayi zurfi a tunani, jin takunshi yasa ta dago tana kallonshi harya qaraso.

Sosa qeya sadeeq yayi yanadan sinne kai alamun rashin gaskiya sannan yace

"Umma akwai abinci?"

Nuna mashi dining tayi batareda tayi magana ba tana tunanin to meke faruwa haka wanda Hajiya Fatima tace maganar bata waya bace saidai tazo?

Fatanta dai allah yasa lfy.

Wucewa yayi dining din ya dibarmusu abincin sannan yayi sama yana sauke ajiyan zuciyar sa'ar dayaci ummy bata tambayeshi komaiba.


Dakyar yasamu ashraf yaci abinci don har saida umma tasa baki sannan yadanci yasha magani yakoma ya kwanta yana rufe jikinshi gabadaya da bargo.

A ranar dai barci rabi da rabi yayi marar dadi saidai alhamdullilah zuwa safe jikin yadanyi sauki zafin jikin ya rage sosai saidai har lokacin kanshi nadan sarawa.

Yanzu ma bawani breakfast din kirki yayiba yatashi tashiga wanka yafito yabude closet din sadeeq ya ciro wasu qanannun wanda da alamu sabbi mane ya fara shiryawa.

Fitowa sadeeq yayi daga wanka shima ya tsaya yana kallon Ashraf dake taje sumarshi gaban mirror.

Qarasowa yayi shima wajen mirron yana daujan wani lotion ya matsa a hannu yafara murzama jikinshi.

"Ina zuwa haka?" Ya tambayi ashraf dake taje kanshi

"Ummy" yabashi amsa a taqaice

"Ok bari nima na shirya na rakaka"

"No katafi company kawai"

"Why? You need me, don't you?"

"Yes, amma company yafini buqatarka, katafi kawai nima zanzo bekamata ace daga ni harkai ba wanda yajeba" yafada yana daukan turaren dudduba turarrukan sadeeq yanason ganin wanda yakamata yafesa don babu kalar nashi anan.

"Ok but take care, uhm?"

"Sure" yafada yana ciro daya daga cikin turrarukan ya feffesa sama sama don duk basuyi mashi ba kawai manage yayi.

"Bani key" inji ashraf yana saka wayarshi a aljihu.

"Kafini sanin inda suke" inji sadeeq dake cikin closet tana za6an kayan dazaisa.

Guntun tsaki ashraf yaja yanufi bedside locker yaja ya dauki daya daga cikin keys din ya maida ya rufe.

"Natafi" yafada yana nufar qofa.

"Take care" inji sadeeq.


Koda yafito babu kowa falo sai wata mai aiki dake goge centre glass table.

Saurin russunawa tayi ta gaisheshi bako kalletaba yafice yanufi hanyar parking space yana danna dan botton din dake maqale a key din hannunshi motar tayi tsuwa.

Yaje ya bude motar yashiga ya tada yafice daga gidan.



A parking space din gidan ya tadda baby zata tafi makaranta.

Jira tayi yayi parking yafito sannan ta gaisheshi ya amsa ba yabo ba fallasa yawuce.

Binshi tayi da kallo cikeda fargabar ko sun rabun da saudart din, jitake kamar takoma ciki tajiyo amma saita haqura kawai tashiga bayan motar driver ya tada suka fice.


Ya dade zaune a falon saidai babu ummy babu alamunta dukda ya aika wata yar aiki ta sanar daita zuwanshi.

Ganin zaman yafara isarshi yasashi tashi yanufi saman.

A kofar dakin ya tsaya yafara knocking ahankali.

Shiru... hakan yasa yasake knocking nanma shiru.

Saida takusan minti daya yana knocking sannan yaji muryarta a kausashe tana tambayar waye? Bayan yasan tasan ko waye don tasan kalan knocking dinshi.

Ajiyar zuciya yayi sannan yabude baki ahankali yace

"Nine ummy" yanajin wani banbarakwai don besaba ba.

"Kaine wa?" Tasake tambaya in the same husky tone.

Shafa kanshi yayi ahankali yana murmushi, lallai ummy kenan bata gane muryarshi ba take nufi.

"Ummy Danki ne Ashraf"

Tsaki yaji taja

"Ehen lfy?"

"Lfy lau ummy"

"To ya akayi?"

Shiru yadanyi yana kallon kofar da mammaki

"Bakomai ummy" yafada a sanyaye.

Shiru ya ratsa hakan yasashi cewa

"I want to see you ummy, please ki bude"

"Kazo da takadar?"

Gabanshi ne yafadi hakan yasashi yin shiru yana kallon ruffafiyar kofar.

"A'a" yafada ahankali

"Then leave my door karka sake dawowa saida takadar kaji nagayamaka"

"Ummy..."

"Leave!!" Tayi mashi tsawa daga ciki.

Babu yadda ya iya hakan ya juya jiki a sa6ule yabar kofar yasauko qasa yana jinshi wani iri.

Komawa yayi ya zauna inda ya tashi ya zubama hanyar stairs din ido yana kallo.

Ya dade ahakan amma babu alamun saukowar ummy.

Sosai yakejin ba dadi har cikin zuciyarshi.

Yasan yanada laifi amma saka sharri da sharri ai ba haramun bane.

Kuskurenshi daya shine sako wanda bata jiba bata ganiba a abun.

And now gashi abun ya rufta dashi, shi be cika burinshi na daukar fansaba, gashi allah ya jarabceshi da mugun sonta bayan mugun tsanar dayasan tayimashi ga kuma ummy na fushi dashi.

Tunawa yayi da abinda suzy tayimashi, koyaya saudart zataji idan tasan qazafin da akayi mata?

Sai jiyai be kyauta ba, na farko ya tilasta mata aurenshi ga wulaqanci da cin mutunci dayaita mata kala and to top it all ga mummunan qazafin zina da akayimata duk don ta dalilin shi.


Daga kai yayi ya kalli agogon dake manne a bangon falon yaga har shabiyun hantsi ta wuce.

Tashi yayi yagyara zaman t-shirt din jikinshi yaqara kallon hanyar stairs sannan yanufi hanyar kofar fita.


Motarshi yabude yafada ciki sannan yarufe ya tada ta fita daga gidan.


Tuqi yake in a normal speed har yazo ya parka bakin kofar gidansu.

Tsayawa yayi yana karewa kofar gidan kallo yanajin wani iri a zuciyarshi.

Ya dade ahakan sannan dakyar ya bude murfin kofar yaziro kafarshi wajen ahankali kingin gangan jikin suka fito ya maida kofar ya rufe yana qarewa gidan kallo.

Ahankali ya zagayo yana zube hannunshi cikin aljihu harya qaraso bakin gate din sannan yasa hannu yana bubbugawa ahankali.


Saida yayi bugu uku sannan yaji motsi daga ciki haka yasa yadanja baya yana kallon kofar.

Qaramar kofar gate din aka bude sannan fuskar buzun ta bayyana.

Tsayawa yayi yana qaremashi kallo shima ashraf hakan take awajenshi.

"Lfy?" Inji buzun yana dan leqen motar bayan ashraf

"Lfy lau, barka"

"Barka dai" buzun ya amsa.

Dan sa hannu ashraf yayi yana dan sosa kai

"Erm s..Saudart nanan?"

Qara qaremashi kallo yayi wanda har hakan yafara kule ashraf.

"A'a tafita, lfy?"

"Lfy" ashraf ya amsa sannan yajuya yanufi motarshi yana jan guntun tsaki.

Binshi buzun yayi da kallo harya bude yashiga ya tada yatafi sannan ya ta6e baki ya maida kofar ya rufe.


Tuqi yake amma yarasa inda kuma zai nufa, anya ma buzun nan gaskiya ya fadamashin batanan din? To mema ya hanashi tsayawa confirming?

Tsaki yasake ja, he can't believe yau yaje kofar gidan babban maqiyinshi haryasa hannu yayi knocking din kofarshi.

Karya corner yayi ya dauki hanyar bakery dinta yana addu'ar allah yasa tanacan.


๐Ÿ’–๐Ÿ’–๐Ÿ’–๐Ÿ’–๐Ÿ’–๐Ÿ’–๐Ÿ’–๐Ÿ’–๐Ÿ’–๐Ÿ’–๐Ÿ’–๐Ÿ’–๐Ÿ’–๐Ÿ’–๐Ÿ’–๐Ÿ’–


Zaune take kan kujerar office dinta hannunta riqeda pen jujjuyashi take a paper.

Haka kawai taji yau tana sha'awar zuwa bakery din, tagaji da zaman kadaici da yawan tunani shiyasa ta yanke shawarar zuwa bakery din ko zata samu sauqi amma tunda tazo bata iya komaiba sai zaunen datayi tana jujjuya pen tana karanta wasikar jaki.

Yau ne wa'adin data dibarma sadeeq yacika, amma babu alamun nasara.

Yanzu ya zatayi? Tasan ko giyar wake tasha bazata iya kai case dinnan court ba don kamar ta kwancema kanta zane a kasuwa ne.

Bakowa takejiba sai mamy, koya ta tuna daita saitaji zuciyarta tayi rawa saboda fargaba.

Sosai take cikin damuwa dukda tana qoqarin dannewa ko don daddy daya fita shiga damuwa yake kuma blaming din kanshi a koda yaushe.


Knocking akayi a kofarta hakan yasa ta saki nannauyan ajiyar zuciya takoma ta jingina da kujerar.

"Yes? Come in"

Ahankali aka turo qofar aka shigo.

Maryam ce sanye da apron fari hannunta riqeda da littafi da pen.

"Unhun?" Inji saudart tana lumshe idanu.

"Ma'am kinyi baqo"

Tsaki tadanja, itafa bata cikin mood din ganawa da baqi

"Ok su shigo but please duk wanda tasake zuwa ace banzoba ok?" Tafada tana dan dafe kai.


"Ok ma'am" tafada tana fita daga office din.

Jimm kadan aka sake bubbugo kofar.

Tsaki tadanja

"Come in"

Maryam ce tasake shigowa da mutum biye a bayanta.

Saida mutumin yashigo sannan tajuya tafita.

Dagowa tayi daga rubutun datafara kafin su shigo tadan kalleshi ta maida idonta kan littafin tana cewa

"You are welc..." cak maganarta ta tsaya da wani abu yazo mata a brain.

Saurin dagowa tasakeyi cikin rashin gasgata da mammaki bayyananne.

Dumm.. gabanta ya yanke yafadi ganin shi dinne jingine da kofa ya harde hannunshi ya zubamata piercing eyes...โœ


Ummin fasihu ce๐Ÿงš๐Ÿปโ€โ™€๏ธ

๐Ÿ‘ฐ๐Ÿป๐Ÿคต๐ŸปAUREN KWANGILA๐Ÿ‘ฐ๐Ÿป๐Ÿคต๐Ÿป
(Contract marriage)



Allah ka qaramana zaman lfy a qasarmu๐Ÿคฒ

Allah ka ji6anci lamuranmu, karka barmu da kanmu๐Ÿคฒ




Story written by Ashaanty love๐Ÿ’–
(Ummin fasihu)



068





Mutuwar zaune tayi tana kallonshi idanunta adan ware alamun mammaki qarara a fuskarta.



Binshi tayi da kallo daga sama har

Please Login or Register in order to submit comment