Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

cutar da daya ba don farantama dayan. Idan saudart ta amince zata cigaba da zama dashi to fallilahil-hamd don muma bazamu so yankewar wannan alaqar tamuba, munason saudart kamar yar cikinmu, abinda mahaifinta yayi can baya bazai ta6a shafanta ba don kwata kwata babu kamanceceniyar hallaya tsakaninsu, saudart yarinyace mai nutsuwa da tarbiya wanda samun irinta ayanzu yayi wuya, ladabi da biyyayarta yasa tunfarko ta yarda da qudurin babanta wanda ita tausayamashi tayi ganin halin dazai fada idan bata aminceba, saudart macece mai amana da zuciya mai kyau don ba don itaba da yanzu company don A.A ya fuskanci mummunar asara da karaya, muna sonta amma hakan baxaisa idan taqi yarda da cigaba da zama dashi mu tilastata tayi zaman cutuwa ba"


Ummy itama ta dora da "tun farkon haduwarmu da saudart tashiga raina, nasan she's the best wife for my son, she's a girl with a pure heart, ina jinta araina fiyeda yadda nakejin baby araina, bazamu ta6a mata dole zama da Ashraf ba, haqurin datayi dashi da farko ma ya isa, i know yamata abubuwa don ni nasan waye dana idan yanaqin abu, wataqila cin zalinta dayaitayi batareda haqqintaba yasa allah ya jarabceshi da sonta lokaci guda don dama ance idan qiyyaya tayi yawa takan zama soyyaya daga baya, yana sonta fiyeda tunaninku yanzu amma hakan bazai sa a tauyema saudart haqqinta ba, cigaba da zamansu da rabuwarsu will depend on amsarta ne"

Shiru dakin yasake dauka sai can Abba ya sauke ajiyar zuciya yace

"To yanzu abinda za'ayi shine zamu zauna dukkanmu harda Alhaji shamsu da saudart dashi kanshi mijin natan a yanke koma menene, aganina hakan zaifi? Koko?" Yaqarashe zancen yana kallonsu kawu ibrahim

"Masha allah, hakanma yayi"

"Yanzu zanma shi Alhaji shamsun magana inyaso duk yadda muka yanke zanyi informing dinku insha allah"

"To allah ya yarda yakuma mana jagora" inji kawu ibrahim

Duk amsawa da amin sukayi har lokacin mamy batabar hawaye ba.

Haka dai suka tafi kowa zuciyarshi babu dadi.

Mamy tayi kuka kamar me? Sai blaming din alhaji shamsu take da lallatamata rayuwar diyarta.

Shidai abba inbanda rarrashi babu abinda yake don shima har zuciyarshi beji dadin abinda yafaruba don shima yanason saudart harcikin zuciyarshi kamar kingin yayan cikinshi.


Aranar dai haka suka wuni cikin damuwa da bacin rai.



A 6angaren Ashraf kau tunda suka dawo yakasa xaune yakasa tsaye don fargaba, jiyake zuciyarshi zata iya tarwatsewa idan yaji mummunan sakamako, dama tunda suka tafi yaketa addu'ar allah ya dorashi akansu allah yabashi nasara don rashin saudart daidai yake da rasa farincikinshi a rayuwa.

Duk up and down din dayakeyi ummy na hankalce dashi tayi banza dashi kamar batasan me yakeba.

Sai kai komo yake a falon yaji ko zata kirashi amma tayi banza dashi daga baya ma zama yayi a falon yana kallo yayinda dukkan hankalinshi ke kan duk wani motsi da ummy zatayi.

Haka yasha zamanshi daga qarshe ummy ta tashi ta hayewarta sama tabarshi nan zaune.

Babu yadda ya iya haka ya tashi shima jiki a sanyaye yakoma part dinshi zuciyarshi namashi saqe saqe.




Zaune take a garden bisa wata plastic chair ta rungume hannayenta tana kallon waje guda babu ko kyaftawa wanda hakan ke nuna cewa tayi nisa cikin tunani ne


Tun ranar dasuka rabu da ashraf bakery dinta wurin yazama wajen zamanta, bata qara marmarin fitaba tun ranar, kullum anan take zuwa ta zauna ba uhm bare uhm uhm sai tunani wanda yazame mata jiki.

Kallo daya zaka mata ka hango fadawar datayi sosai, duk takoma shiru daita kamar ba active saudart ba.


Ringing din wayarta ya maidota daga duniyar tunanin data lula.

Ahankali ta kalli wayar sannan cikin rashin kuzari ta jawo wayar ta duba.

Maryam ce hakan yasata yatsuna fuska sannan ta daga.

Sudan jima suna magana akan abinda yashafi business dinta wanda yanzu rabonta da leqasu tun ranar nan, akasalance taita amsamata suka dan tattauna sannan sukayi sallama.

Tana niyyar ajiye wayar wani kiran yashigo wayarta.

Tsayawa tayi tana kallon sunan dake yawo a screen din wayar batareda ta iya dagawa ba yayinda takejin qaruwar bugun zuciyarta.

Kasa dagawa tayi har kiran ya tsinke, babu 6ata lokaci wani kiran yasake shigowa again.

Limshe idanu tayi ahankali tayi ta bude tana kiran sunan allah.

Cikin rawar hannu tayi picking din call din ganin zai qara tsinkwa ta kara a kunne atsorace....✍


Ummin fasihu ce🧚🏻‍♀️

🤵🏻👰🏻AUREN KWANGILA👰🏻🤵🏻
(Contract marriage)



Story written by Ashaanty love💖
(Ummin fasihu)






074


"Aslm alaiki" tafada ahankali zuciyarta fall fargaba

"Wslm Amaryar contract, ya kike?" Taji anfada daga dayan 6angaren

Dumm! Gabanta ya yanke ya fadi, ahankali ta sauke wayar daga kunnenta taqara kallon screen din don qara tabbatar da mai kira din.

Maidawa tayi a kunne tafara magana ad'an daburce

"M...mamy? Mamy ina wuni?" Tafada bugun zuciyarta na qaruwa

"Save your greetings don bana buqata, banida wannan matsayin awajenki so hang it" inji mamy

Hankalinta ne yatashi wanda har saida tamiqe tsaye bakinta nadan 6ari tace
"M...mamy... mmm..meya faru please" tafada yayinda wasu hawaye suka fara kawo mata.

"Mefa? Just call to hear from you dukda bawani matsayi nakedashi awajenki ba"

"Mamy..." saikuma tayi shiru tana toshe bakinta don kuka ne ke neman kufcemata.


"Bye" mamy tafada a dayan bangaren zata tsinke kiran

"No mamy please don't hang u..."

Ding... taji an katse kiran.

Sakin wayar tayi takoma kan kujerar tana dafe kanta da hannaye bibbiyu tafashe da wani irin kuka.

"No..no" tafada tana kuka sosai.

Saurin duqawa tayi tasake daukar wayar data yar qasa tana kuka tashiga re-dialling din number mamy, hannunta sai rawa suke.

Takira yafi so biyar amma ba wanda aka daga.

Wani kukan tasake fashewa dashi tana cillar da wayar.

Dama tsoronta kenan, kullum fargabar datake kenan, shikenan tafaru taqare.

"Am doomed!" Tafada tana daura hannu aka kamar wanda aka kawoma saqon rasuwar uwarta.


Wayar tasake dauka tanufi cikin gida tana kuka sosai tashiga dialing din number Daddy.

Kallo daya zaka mata kasan bata cikin hayyacinta.

Ringing biyu daddy ya daga.

Kukanta dayaji ya katsemashi sallamarshi wanda hakan yasashi zabura amiqe.

"Shalele?"

Zubewa tayi qasan falo don harta shigo falon tana kuka sosai wayar kare a kunnenta.

"Shalele menene? Talk to me" inji daddy cikin rawar baki.

"Nashiga uku daddy, daddy am doomed!" Shine abinda kawai ta iya fadamashi cikin kuka.

"Subhanallilah! Shalele what happened? Meya sameki?" Yafada yana laluban car key dinshi kan table

"Daddy kazo... zan mutu" tafada cikin kuka sosai

Kafin yasamu damar yin wata maganar harta katse wayar.

Bashiri yayo waje hankalinshi a matuqar tashe.







Zaune yake jigum, yarasa meke mashi dadi.

Tagumi yabuga da hannu bibbiyu yana bin screen din laptop dinshi da kallo wanda ke dauke da hotonta daya fito tarr wanda duk ya turasu akan laptop dinshi daga cikin wayar databar mashi


Ahankali aka bude kofar dakinshi baby ta leqo.

Ko dagowa beyiba don bemaji budewar kofarba

Qarasa shigowa tayi da sallama wanda hakan ya fargar dashi yayi saurin dagowa.

"Yaya?... yaya wai ka sauko muyi dinner" inji baby ahankali


Komawa yayi ya jingina da kujerar dayake akai yana sauke ajiyar zuciya

"Go... banajin yunwa" yafada ahankali.

Jimm tadanyi kamar bazata wuceba saikuma tajuya tafita.


Can saigashi tasake dawowa.

Dagowa yayi yakalleta kawai batareda yace komaiba

"Yaya wai kawu yace kazo"

Lumshe idanunshi yayi ya bude
"Ok" yafada ataqaice


Saida tadan jima da tafiya sannan shima ya tashi ya dora shirt saman singlet dinshi yafito.


A dining ya taddasu duka, a ladabce ya gaidasu kai a qasa.

Kawu ibrahim kawai ya amsa ummy ko ko kallo be ishetaba.

"Zoka zauna babana" inji kawu ibrahim yana nunamashi kujerar gefenshi

A natse ya qaraso ya zauna baby tayi serving dinshi

"Now eat" inji kawu ibrahim

Ba musu yadauki spoon din yafara cakula abincin don bawani cin kirki yayimashi ba sai jujjuya spoon din dayake aciki.

Haka suka gama in silent sannan suka fara tashi daya bayan daya yarage saura kawu ibrahim da Ashraf.


Goge bakinshi kawu ibrahim yayi shima yatashi

"Kasameni a garden" yafada tareda ficewa.

Haka kawai yaji gabanshi yafadi ya kasa kai kofin ruwan a baki.

Ajiyewa yayi yana sauke ajiyar zuciya.

Tunda suka dawo yake kasa kunne yaji ki zasuyimashi magana amma shiru gashi yanzu ammashi din amma jiyake beda courage din jin sakammakon daza'a gayamashi.

Ya dade zaune awajen yana saqa da warwara kafin daga baya ya miqe dakyar ya fita zuwa garden din kamar kazar da kwai yafashe mawa aciki.




"Shalele kiyi hqr please, kibar kukan hakanan" inji daddy daya gaji da rarrashi

Zaune take jan gadonta cure wuri guda ta hade kanta da gwiwa tana kuka cikin muryarta dabaya fita tsabar kukan datasha.

"Shalele, am sorry, duk nine silar komai, ki gafarceni 'yata" yafada shima kamar zaiyi kukan

Ko dagowa batayiba haka zalika batabar kukanba hakan yasashi jawota ajikinshi cikin sigar rarrashi.


"Shalele kiyi hqr, nasan yadda kikeji, please kibar kukan haka, ni da kaina zanmasu bayyani kinji? Nina jawo komai kuma ni yakamata inga consequence dinshi, please kibar kuka please"

Itadai batace komaiba sai kukan datakeyi qasa qasa, sosai zuciyarta kemata zafi gawani sara da kanta keyi agefe daya jitake dama tamutu ta huta.


Dakyar daddy yasamu ya lalla6ata tasha tea tasha magani ta kwanta.

Ya dade sosai dakin har saida yaga tayi barci sannan ya lalla6a yafita don karya tadata.


Saida taji alamun yafita sannan ta bude kumburarrun idanunta ta miqe zaune ahankali, hade kai da gwiwa tayi tacigaba da hawaye tana kukan zuci.


Daddy a 6angarenshi shima kasa rintsawa yayi, sosai yake danasani marar amfani.

Danasani yake sosai na halinshi, yasan yanzu tuni dan kingin mutuncinshi yarigada yazibe a idanunsu mamy

Sosai yakejin kunya, sai yanzu yake mammakin yadda acan baya idanunshi suka rufe yakasa hango abubuwan dazasu biyo baya.

Alokacin shidai kawai abinda zai qaru dashi yake hange, be ta6a hangen abinda zai ragu dashiba.

Gashi yanzu ya tsunduma 'yarshi kwaya daya, mai son farincikinshi cikin qunci da bakinciki.




**********************************

Fada sosai kawu ibrahim yayimashi kan abinda ya aikata, ta inda yake shiga batanan yake fitaba.

Sosai jikin ashraf yayi sanyi don tunda yake beta6a ganin kawunshi cikin irin wannam 6acin ran ba.

Sai daga baya yafarayi mashi nasiha mai ratsa zuciya wanda ya ida kashe jikin ashraf.

Saida yaimashi nasiha sosai sannan ya gayamashi yadda sukayi dasu Abba, ya dora dacewa

"Yanzu dai dorewar aurenku ya danganta ne da amsar da yarinyarnan tabada, bazamu so kanmu dayawa ba, bazamu bari ayi zaman cutuwa ba, idan ta amince zata cigaba da zama dakai to fallilahil hamd, amma idan ta nuna akasin haka bazamu tilasta mataba, saidai muyima dukkanku fatan allah ya hada kowa da mafi alhairi"

Bayan haka ya sallameshi.

Tashi yayi jiki amace, yabi ta hanyar baya yashiga cikin gidan ya haye sama kamar marar lakka.

Ahankali ya zauna gefen gadonshi ya jingina kanshi da jikin gadon ya lumshe idanunshi da suke a rine.

Yasan shikenan, shikenan sun rabu da saudart sun gama.

Tun yanzu yasan matsayar aurannan, dama mai neman kuka ne aka jefa da kashi.

She hate him so much, ta tsaneshi ta tsani ganinshi burinta su rabu, meye to amsarta bayan anbata za6i yanzu na cigaba da xama dashi ko rabuwa dashi?

Ofcourse rabuwa ce, yasan bazata tsaya dogon tunaniba zata za6i rabuwa dashi.


Ahankali hawaye suka gangaro daga ruffafun idanunshi yanajin tausayin kanshi.

Yasan rabuwarshi daita daidai yake da rabuwarshi da farincikinshi.

Yasan rabuwarshi daita kamar bude sabon shafin kunci ne arayuwarshi.

His last hope was gone, yanzu baida sauran wani hope, kawai yariga yarasata yagama ne.


Adaren babu wanda ya rintsa acikinsu daga Ashraf da saudart har Alhaji Shamsu daya tsangwami kanshi yake ganin shine umul abaisan faruwar komai.



💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖



Washegari da zazzafan zazza6i saudart ta tashi.

Sosai Alhaji shamsu ya rude don jin jiki take sosai kuma taqi yarda akaita hospital saidai aka kira family doctor dinsu yazo hargidan.


Ranar wuni yayi tareda ita bekosan motsawa daga gefenta, duk motsin dazatayi saiyayi mata sannu, he's feeling guilty, yanajin duk shine silar komai, hqr kau har saudart tagaji dajinshi abakinshi. Haka ranar tazo tawuce masu dukkansu cikin qunci.


A 6angaren ashraf kau sai abinda yayi gaba.

Haka shima yawuni sukuku, saidai kaganshi zaune ya kafe waje daya da idanu yana tunani.

Baya fita gidan sai yaga lokacin sallah yayi sannan yafita masjid, daga nan kuma sai dakinshi.

Idan kuma ya sauko qasa to ankirashi ne ya sauko yaci abinci wanda ko kwata beci zai tashi wai ya qoshi daganan kuma yakoma daki ya dasa daga inda ya tsaya.


Ganin tunane tunanen bazasu amfaneshi dakomai ba yasashi tashi ya daura alwala misalin shabiyu na dare yahaye sallaya yaita nafilfili yana addu'ar allah yabashi haquri da juriyar rabuwa daita yakuma yayemashi sonta kamar yadda ya doramashi don shi yarigada ya fidda rai da kasancewa tareda ita.





Saida tayi kwana biyu kwance sannan tadanji sauqi.

Damun daddy tayi da kuka akan ita gidan mamy zata don tasan tana fushi daita.

Ganin bata ida warwarewaba yaso hanata dafarko amma ganin ta burkucemashi yasashi yarda akan tayi hqr zaikaita dakanshi washegari.

Haka ta haqura badon yasoba.


Washegari sukuku ta tashi, fargabar haduwarsu kawai take da mamy don tasan haduwarsu won't be funny at all.

Haka ta shirya jiki amace kallo daya zaka mata kasan atsorace take.

Daddy ne yaita kwantarmata da hankali ganin yadda duk ta tashi hankalinta.

Haka suka fita daga gidan suka dau hanyar gidan mamy kowanne da irin fargabar dayake....✍



Sorry for the short chappy🙏


Please sai kun dinga hqr dani yanzu, wlh bansamun zamane kamar da.

Da ace yadda nake samun lokaci ne kamarda da yanzu book dinnan yaqare.

Yanzu typing dinma kanshi wahala yakebani don am always busy.

Please bear with me, yanzu ba kullum zaku dinga jinaba, amma duk ranarda am less busy zan dinga yimuku mai yawa🙏

Nagode da qaunar dakukemani da littafin nan.

Masu cigiyata da masu kirana duk nagode, Allah yabar qauna da zumunci, Allah yabarmu tare har abada💖


Ashaanty loves you so much😘💖💖💖💖💖

🤵🏻👰🏻AUREN KWANGILA👰🏻🤵🏻
(Contract marriage)




Story written by Ashaanty love💖
(Ummin fasihu)




075



Fitowa duk sukayi daga cikin motar duk suna kallon qaton gate din gidan.

Asanyaye saudart tajuyo ta kalli daddy kallo daya zakamata kasan a tsorace take

"Kishiga sweetheart, kimin sallama da Abban nayi losing din contact dinshi"

Nodding tayi a sanyaye sannan ta nufi gate din kamar wanda kwai yafashe mawa aciki.

Saida tayi knocking sau uku sannan taji alamun za'a bude gate din

Budewa akayi fuskar maigadin ya bayyana, yana ganinta ya washe baki yana mata maraba.

"Anty kece? Yau banda mota kikazo?"

Murmushi kawai tayi tace "eh bani kadai bace, Abba fah?"

"Yana ciki bema dade da dawowa ba ma"

"Ok" daga haka tashige ciki gabanta na faduwa.


Ahankali ta danna doorbell din kofar cikin sanyin jiki.

Shirun dataji yasata qara dannawa.

Gani tayi an murda handle din daga ciki hakan yasata dan ja baya gabanta na faduwa.

Abdul ne tagani yana turo baki, yana ganinta ya waro idanu tareda kiran sunanta da karfi ya rungumeta.

Dukda bacikin nutsuwa takeba saida ta murmusa tana riqeshi itama

"Aunty kece? Kitaho" yafada yana jawo hannunta zai shigar daita ciki.

Saurin tirjewa tayi tareda jawoshi baya ta tsugunna daidai tsawonshi sannan tafara magana cikin muryar rada

"Ina Abba?" Tafada tana dan wara manyan idanunta

"He's upstairs" ya amsa shima cikin rada

"Mamy?"

"Tana falo"

"Doing what?"

"Tana tayamu homework"

Ganin tana kallonshi atsorace yasashi qara qasa da murya
"Aunty menene?"

Furza iska tayi daga bakinta sannan tace
"Nothing... mushiga"

Da sallama suka shiga, Abdul agaba jaye da hannun saudart dake taka kasa kamar mai tausayinta

Su kamal da tundazu suke kallon kofar don tabbatar da ita dince suka miqe aguje suka nufeta suna murna banda Aminu dake murmushi kawai daga inda yake zaune.

Wara masu hannu itama tayi absentmindedly tana kallon mamy da ko dagowa daga kallon littafin habeeb batayiba fuskarnan murtuk

Jiki asanyaye tayimasu habeeb murmushi ta qaraso ciki simi simi kamar marar gaskiya.

Dan nesa da mamy taxauna qasa tana kallonta a sanyaye abdul sai zubamata surutu yake.

Saida tagama amsamashi sannan ta dago takalli mamy a raunane
"Mamy ina wuni?"

Idan ku masu karatu kun amsa to itama ta amsa.

Sake gaisheta tayi wannan karon ma babu amsa saima tattara littafan gabanta data shigayi tana maidamasu cikin jakka.

"Mamy aunty na gaisheki" inji abdul don shi atunaninshi bataji bane.

Wani kallo ta watsamashi tace
"If i slap you, kutashi kuba mutane wuri!" Ta qrashe a tsawace.

Simi simi suka tashi harda aminu dake kan kujera sukayi sama.

Sunkuyar dakai qasa saudart tayi hawaye na kawo mata.

Tashi itama mamy tayi zata wuce hakan yasata saurin dagowa

"Mamy don allah kiyi haquri" tafada cikin muryarta dake dan rawa

Wucewa xatayi tayi saurin riqe tip din gown dinta

"Please mamy.."

Fizgewa mamy tayi tajuyo tana bankamata wani mugun kallo.

"Are you alright?"

Sunkuyar dakai tayi hawayen dake maqale a idanuwanta na gangarowa

"Am very sorry mamy, don girman allah kiyi hqr" tafada voice dinta na breaking

"sorry for what? Dama wani abu kika yimin?"

Kasa amsawa tayi sai matsar qwalla datake

"Ni bakimin komai ba, koma menene kanki kikaimawa, so you should be sorry for yourself, Aure dai shine kuka mayar abun wasa ko? Zaku kwashi kashinku a hannu daga ke har baban naki"

Jiki na rawa taqara matsota tana qoqarin riqe kafarta mamy taqara yin baya

"Ni kibar matsoni, me zan miki? Dama kinsan da zamana ne? Inada wani matsayine awajenki? No, so go to your guardian dama tare kuka tone kuka binne, stop including me" tafada cikin 6acin rai.

Taffukan hannu saudart tasa ta rufe fuskarta tana kuka sosai mai ban tausayi, jikinta har rawa rawa yake.

"Kinga tashi ki tafi, na me zakizo kicikamin gida da hayaniya? Idan zan baki shawara ma cewa zanyi ki adana hawayen da iface ifacen zuwa gaba don zaifi yimaki amfani alokacin.

Saudart kin bani kunya, am really disappointed in you, wlh ko a mafarki banta6a tunani zakiyi abinda kikayi ba.

Ina tarbiyar dana baki? Ina hankalinki, ina iliminki? Ina tunaninki?

Kin biyema kwadayyayen ubanki ya kaiki yabaro don ke keda kaico ba shiba, soon zaki zama bazawara kishiga layin zawarawa babanki kau babu abinda yashafeshi, iyaka yaga wani wanda zai qara tatsa ya auramiki shi shima bayan wasu lokuta ki fito kafin ya qara hango wani.

Ko shi Allah kanshi dayace mubi iyayenmu cewa yayi idan basu kaucewa koyarwar musulunci bane

Yanzu saudart ke bamai nusar da mahaifinki bane? Ke bame ganardashi bane ki nunamashi hanya idan yaso kaucewa? Amma kika biyemashi kega mai uba ko?

And the painful thing is ina raye? Ina raye saudart kikayi wannan abin batareda shawarata ko sanina ba? Banida matsayinda zaki kawomin damuwarki? Ya huremaki kunne baki ganina da mutunci?

Ace wai 'yata ce da auren contract? Auren kwadayi?.." tafada tana nuna kanta idanunta na kadawa.


Kuka sosai saudart keyi tana jin duk ta tsani kanta, jitake dama tamutu kafin wannan lokacin, dama batayi witnessing din wannan lokacinba a rayuwarta.

"Ku kuka sani ai, kuje can ku qarata, badai zawarci ba? Kije kiyi kiji ko akwai dadi, kikuma cigaba da biyema ubanki, watarana sai an hallakaki ta dalilinshi... yaje yayi laifi anzo andauki fansa akanki, keda bakijiba baki ganiba, go ahead Allah yabada sa'a"

Tsaki taja tajuya tayi wucewarta sama zuciyarta na quna.


Ahankali saudart ta dago kaffafunta ta dora kanta bisa gwiwa ta rungume kaffafun tacigaba da rera kukanta, nan take taji kanta nadan sarawa zazza6inda bagama sakinta ba na neman sake tasomata.


Batasan iya dadewarta awannan yanayinba taji anyi tapping din kafadarta.

Saurin dago fuskarta tayi datayi ja saboda kuka.

"Saudart?" Inji abba dake sanye da jallabiya a mammakince.

Sauke rinnanun idanunta tayi ahankali wasu hawayen na gangaromata ta gaidashi da muryarta dabata fita

"Lfy lau, what happened? Why are you crying?"

Batace komaiba sai cigaba dakukan datayi ahankali.

Miqar daita yayi tsaye yana rarrashi don yasan kwanan zancen

Dakyar yasamu tayi shiru sannan ya tambayeta daga ina take.

Jan hanci tayi sannan dakyar tace
"Gida, tare muke ma da daddy"

"Alhaji shamsu? Yana ina?"

"Waje" tafada tana sauke tagwayen ajiyar zuciya

"Ya sallam, since when? Shine baki gayama kowaba?"

Shiru tayi don ita saima yanxu ta tuna data barshi waje.

Fita yayi batareda yasake cewa komaiba.


Awaje kau daddy ne tsaye sai safa da marwa yake.

Sai imagining din abinda ke faruwa ciki yake gashi yakira number saudart yafi aqilga amma ba'a dagaba.

Jin ana bude qaramar qofar gate yasashi kafama gate din idanu sai ganin Abba yayi yafito.

Murmushi suka sakarma juna, abba ya qaraso sukayi musabaha sunama juna sallama.

"Alhaji shamsu, ashe kana waje? Wlh saiyanxu dana sauko saudart ke gayamin, kayi haquri please"

Murmushi Daddy yayi
"Bakomai Alhaji Isma'il, dama cewa nayi taimani iso, i thought baka nan ma danaji shiru"

Shiga sukayi Abba agaba daddy biyedashi suna dan ta6a fira.

Falon saukar baqi yakaishi sannan yajuya da niyyar sawa akawomashi abin ta6awa

"Alhamdullilah Alhaji, am ok" daddy ya tsaidashi da hakan

Dawowa abba yayi ya zauna yana facing din Daddy don jin abinda yakawoshi.

Dan daburcewa yayi ganin yadda ya kafamashi idanu

"Akan maganar auren yarannan ne.... it's was a mistake.... and... am regretting it" shiru yayi, shi kanshi yasan he sound stupid

"Nasan kanada labari kou?.."

Ajiyar zuciya Abba dake kallonshi tundazu yayi sannan yace
"Yes, yau kwana uku kenan dazuwansu in-law dinmu nan gidan"

Kallonshi daddy yayi yana dan wara idanu saikuma ya sauke idanunshi qasa feeling so humuilating

"I caused it all... duk laifi nane... i forced her"

Dan murmushi Abba yayi yace "yes, you made a big mistake, meyasa kayi haka Alhaji shamsu?"

Shiru yayi yakasa cewa komai, jiyake kamar qasa ta tsage ya rufta ciki, wani matsanancin kunya yakeji kamar ya 6ace ya huta.

"Yanzu dai faduwa ce tazo daidai da zama, dama nayi niyyar zuwa mall dinka mu tattauna, zamu hadu gidanka dasu in-laws din namu damu mu sassanta komai, saika fidda rana"

Shiru Daddy yayi haryanzu yakasa hada ido da abba.

Wai agaban abba kadai yakejin haka, inaga agaban in-laws din? Kokuma mai gabadaya agaban allah ranar sakamakko?

"Look everything will be alright alhaji, kawai gani nayi hakan zaifi, ahadu a samama kai mafita, aurennan yayi involving su biyu ne, dole saida yarda dukkansu, we want to hear from both of them kafin a yanke hukunci, sai inga hakan zaifi"

Hannu daddy yasa ya share gumin forehead dinshi sannan ya sauke ajiyar zuciya

"To, yanzu... yaushe zasuzo din?" Yafada ahankali

"Choose a date... duk ranarda yaimaka"

Shiru daddy yayi, tayaya zaiyi facing dinsu da wannan abun kunya, kai kwadayi beyiba, gashi da mutuncinshi da komai zaizama qaramin mutum awajen ahali mai daraja irinna A.A

"Gata... sunday kenan? Koko?"

"Hakan yayi, zan gayamasu, insha allah komai zai warware" inji abba daya lura da uncomfortableness na daddy.


Saida sukadan dade suna fira, abba na nunnunamashi abubuwan dayayi dabai kamata ba cikin hikima, dakuma illar wasa da aure.

Sosai jikin daddy yayi sanyi don magangganun abba sun shigeshi sosai.

Sai gab da magrib suka fito, abba yashiga yakira saudart dake inda yabarta suka fito yana sake rarrashinta yana assuring dinta mamy zata sakko ta kyaleta yanzu fushi take.


Sallama sukayi da abba, daddy nata mashi godiya don sosai yaqara qima a idanunshi.


Haka suka isa gida sukuku, bayan dinner daddy yashigo dakin saudart lokacin hartayi shirin barci tana zaune tabuga tagumi.

Zama yayi yafara rarrashinta yana bata hqr akan duk abinda yaimata yana nunamata tsantsan nadamarshi, sannan yafadamata yadda sukayi da abba.

Sosai hankalinta ya tashi don jitake bazata iya facing din ummy ba.

Dakyar yasamu hankalinta yadan kwanta sannan ya lalla6ata ta kwanta sannan yafita.

Kamardai kodayaushe yana fita tamiqe zaune tahada kanta da gwiwa tana tunane tunane, barci 6arawo ya sadado ya dauketa wajajen ukun safiya.



*THREE DAYS LATER*


Sorry ba yawa🙏


Ummin fasihu🧚🏻‍♀️

🤵🏻👰🏻AUREN KWANGILA👰🏻🤵🏻
(Contract marriage)



Story written by Ashaanty love💖
(Ummin fasihu)



076



*THREE DAYS LATER*


A natse yake saukowa daga stairs hannayenshi zube cikin wandon dakkakiyar shaddarshi kalar brown.

Kanshi babu hula sai sumar kanshi da tad'an taru sai shining yake don gyara

Hannunshi na haggu na sanyeda agogo rolex sai baqaqen cover shoes a kaffafunshi.


Dagowa duk sukayi suna kallon yadda yake saukowa qasa cikin sanyin jiki kanshi asunkuye.

Cikin yan kwanakin nan sun rasa gane kanshi don yayi wani laushi kamar bashi ba, haka suka bishi da kallo harya qaraso wajenda suke zazzaune suna jiranshi.

Duqawa yayi batareda ya bari sun hada ido da kowaba ya gaidasu cikin calm voice dinshi.

Duk amsawa sukayi suna kallonshi cikin tausayawa.

Kallo daya zaka mashi ka hango ramar dayayi cikin yan kwanakin nan, yaqara haske wanda hakan yaqaramashi kyau.

"To saimu yi niyya ko?" Inji kawu ibrahim

Duk tashi sukayi suka fito waje.

Motocci biyu ne a harabar.

Ummy da umma suka shiga seat din baya sai Ashraf da sadeeq dake gaba inda sadeeq ne matuqin.

Dayar motar kuma kawu ibrahim ne da kawu zahradini sai drivern dazai jasu.


Haka suka jera suka fito daga gidan suka halba titi.


Shiru motarsu ummy ta dauka kowa da abinda ke kai kawo a zuciyarshi

Sadeeq dake tuqi yad'an saci kallon ashraf daya jingina da seat dinshi ya lumshe idanu.

Janye idanunshi yayi ya maida kan titi yana qarajin tausayin abokin nashi.


*zaka ita misalta adadin qiyyayar danake maka?* maganar saudart ta ranan tadawo mashi a kwanya

*A'a*


*nima haka... baxan iya misalta qiyayyar danake makaba ada.... saidai yanzu ina iya cewa... qiyayyar danake maka ada batakai kaso daya cikin kaso goma danake maka yanzu ba*

*ka tsaneni ko? Ka tsani ka ganni cikin farinciki da walwala ko? Tell me*

*I hate you....with passion*

Haka magangganun saudart sukayita mashi amsa kuwa a kunne.

Yasan yau ne qarshen duk wani alaqa dake tsakaninsu.

Kullum saiyayi tsayuwar dare ya roqi allah akan ya yakicemashi soyyayarta acikin zuciyarshi amma yadda kasan roqo yake aqara mashi, kowanne wucewar daqiqa da qaruwar son saudart ne a zuciyarshi.

He's so weak, so broke, babu abinda ke fadar mashi da gaba sai abinda zai fito daga bakinta.

Yarasa dalili, koyaya ta furta ta tsaneshi sai yaji

Please Login or Register in order to submit comment