Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

rayuwarta ta yanzu,buri gareta na karatu mai zurfi,wanda zai zameta qaqqarfar garkuwa da zata tare duk wani abu mai cutarwa daka iya ci gaba da kawowa rayuwarta farmaki
"Idan har da gaske ne babun?...me zai hana ni a bani dama na shiga layi kuma mutum na farko ko?"shiru tayi tana jin zuciyarta na bugawa,kaman yaya me yake nufi?
"Uhmmm aysha?,kinyi shiru?,ko na barki kiyi nazari?"
"Eh" ta fadi da sauri,saboda shi daya ne mafitar a yanzu don bata da amsar bashi
"Ayi tunani mai kyau" ya fada yana karya kwanar da zasu shiga bayan ta masa nuni da yatsa.


Qofar gidan ya tsaida motarsa tana yunqurin fita ta masa godiya
"Ki daina saurin godiya haka,saboda zan dawo daukarki" kai ta girgiza
"Na yafe wallahi...bansan ma lokacin da zan koma gida ba karna wahal da kai"
"Na gane dai bakison na dawo....fine...samin phone number dinki" ya fada yana miqa mata wayarshi,da ka ta saka masa number sannan ta miqa masa yayi serving,sai data shige cikin gidan sannan yaja motarsa yabar wajen.


Tana shiga aliya tayi tsalle ta riqeta
"Ke...waye ya kawoki?" Murmushi ta saki mai sanyi cikin siririyar muryarta tace
"Wannan itace tarbar da za'amin dama?"
"Yi haquri sashen...wallahi dadi ne ya sakani fadin haka....yau naga abinda ban taba gani ba"
"Rakani na soma gaida mama tukunna"
"Mama bata nan,amma kafin ki tafi zata dawo" ta fadi tana jan hannunta zuwa kan kujerun falon.


Sai data cikawa aysha gabanta da kayan ciye ciye kala kala harta rasa wanne zata ci?,bata barta ba sai data ci tasha sannan suka shiga hira,yawanci aliya ke baiwa ayshan labarai kala kala,ta kuma kwaso mata hotuna ta kalla har ta gaji,daga bisani ta sake tada mata zancan,bata boye mata komai ba don aliya qawa ce ta gari
"Aysha....ki bashi dama ina ganin..bakisan me Allah zaiyi ba,ki manta da da rayuwarki ta baya...ki manta dake wacece ki ki amshi sabuwar rayuwarki" zame hannunta tayi daga na aliya qwalla na cika idanunta
"Ta yaya Aliya zan manta wace ni?,kin manta har yanzu akwai tabo cikin rayuwata,Aliya....mahaifiyata...ta yaya zanyi aure?,ta yaya zan sanarwa da wanda zan aura bahagon labarin dake wanzuwa tsakanina da mahaifiyata...ta yaya zan fahimtar da shi...da wanne ido zan kalleshi na sanar masa?koda na mance komai komai ya wuce banda wannan aliya" ta qarasa tana girgiza kai qwalla na bin kuncinta,can qasan zuciyarta tana jin suya,hannu aliya ta saka tana share mata hawayen fuskarta
"Kinzo gidanmu maimakon ki samu farinciki saiki qare da kuka?,banason haka sashin" murmushi ta saki wanda qasan sa ciwo ne da radadi
"Kinsan me?.....bari na kira ummi kiji ki sake tabbatarwa da maganata na kan hanya" ta fadi tana zaro wayarta,duk da yadda zuciyarta ke bugun uku uku tana mata gargadin kiranta amma bata fasa yunqurin kiran nata ba.


Dab da zata tsinke aka daga,sallamar ummin ta bayyana cikin muryarta,shuru ayshan tayi ta kasa cewa komai har sai data ce
"Wake magana ne?"
"Nic....ce...aysha ce"
"Wace ayshan?" Ta tambaya a dan gintse saboda hasashen da zuciyarta ta mata
"Aysha indo"
"Bakiji me na gaya miki ba ko?.....ke wacce iriyar yarinya ce mara zuciya?....koda yake ba mamaki jininsu sama'ila yake yawo a jininki,gargadina dake na qarshe karki sake nemana na gaya miki" daga haka ta yanke wayar,a matuqar sanyayar jiki aysha ta sauke wayar daga kunjeta,murmushi mai ciwo na tashi saman fuskarta
"Kin ji kuma kin gani ko aliya?" Ta fada a rarrabe muryarta na rawa,saman kafadarta aliya ta dora ayshan sai kuwa ta fashe da kukan data jima tana so tayi bai fita ba,sai qunci da takurar zuci da take fama da shi,babu wanda zata zauna gabanshi tayi kuka har haka,idan ma akwai aminiyarta ce qwaya daya da tayi mata nisa tana nata muhallin a qauyensu.


Tausayin ayshan ya hana zuciyar aliya sukuni,haka ta dinga share qwalla itama,itakanta mamakin wannan lamari take wanda bama ita ba,ayshan ma baki daya batasan daga inda ya somo ba,sai data gama don kanta sannan ta goge fuskarta aliyan na lallashinta da kalamai masu dadi cike da qauna da tausayawa

A gajiye ya koma gida a ranar,hakan ya sanya hatta da abincinsa a dakinsa yaci,hakanan tsakanin amal da zeenart ba wadda ya baiwa damar ganinsa,wanka kawai yayi yayi dai dai qasan carfet yana cin abinci,qwaqwalwarsa cike take da lissafe lissafen ayyukan dake jiransa gobe da kuma cikin satin,a matuqar gajiye ya jawo briefcase dinsa don ya ciro system dinsa,sunyi da wani abokin kasuwancinsa da zasu fara harkar fita da wasu samfurin duwatsu masu daraja zuwa china zasu qarasa maganarsu a lokacin.


Har ya kammala cin abincin amma yana kan system din,sai dayaji bacci na rinjayarsa sannan ya kashe yana zuba hamma,ya bude brieafcase din ya maidata,inda ya aje kudi ya bude ya soma zarasu,don sunyi magana da haidar zai aikashi gidan kawunsu dake da buqatar kayan abinci,dubu dayan ce ta fado,cikin mamaki ya saka hannu ya dagata yana kallo,don har ga Allah ya mance da ita,a hankali ya tuno inda ya sameta,murmushi ya saki yana tuna abinda ya faru,shi kansa abun ya qayatar da shi,tamkar a majigin film,wai shine aka ci kwala ana tuhuma da cin bashin naira dari biyar
"Ya Allah" ya fada yana maida bayansa jikin kujera ya jingina,yadda komai ya faru yana dawo masa fes kamar yanzu abun ke faruwa
"Ita din wacece?" Ya tambayi kanshi,baisan ko wace ba,amma abinda tayin ya burgeshi,hakan yana nuna tana da zuciya mai kyau,ta gefe daya tsiwar asma'u da dagiyarta yana dan burgeshi,yanayin son ajinta,adonta,yana son mace mai ado bawai kwalliya ba,to ita ya fuskanci duka ta hada,a hankali bacci barawo ya saceshi a yadda yake zaunen.


Kiran sallar farko ya farka kaman yadda ya saba,sosai wuyanshi ya riqe saboda yanayin kwanciyar da yayi,da addu'a a bakinsa ya shiga bandako,wanka ya soma sannan ya daura alwala,jallabiyya ya zira bayan ya wadata jikinsa da tsadajje kuma daddadan turarensa mai sanyin kwantar da hankali,idanunsa ya lumshe yana sheqar qamshin turaren yana tuna masa da wata rayuwa can baya,rayuwar da tazo ta wuce musu tamkar a mafarki,dalili biyu yasa yake amfani da turaren lokaci lokaci,na farko yana son qamshinsa,na biyu kuma dukan daya taba ci dalilin turaren a hannun yaya ibrahim,yaya ibrahim din da a yanzu shine gatansa,rayuwa na bashi tsoro,yanayin yadda rayuwa ke garawa tana qara sashi jin tsoron Allah kadaitashi da kuma imani da shi,da ire iren wannan tunanin ya tada sallar nafila kafin zuwan lokacin asubah
.

A kullum babu wata rana da zata zo ta wuce khalipha baiyi ire iren wannan tunanin ba,wani abu ne daya shafi rayuwarsa,abu ne daya tana rayuwarsa ya kuma shiga cikin tarihinta.


Baccin da yaso komawa bayan sallar asubar bai samu ba ya hau net yana rage ayyukan dake gabanshi,qarfe takwas ya fito daga wanka,yana tsane jikinsa da towel kira ya shigo wayarsa,ya qarasa yana duba mai kiran,ramla ce,dauke kanshi yayi kamar bai ganin kiran,yasan tatsuniyar gizo bata wuce ta qoqi,yasan bai wuce ta gaya masa cewa zata zo ba,abinda shi kuma baiso kenan,matsalar daya anni....baisan mai yasa ba....anni nada zuciyar mantuwa da yafiya,ta fishi sanin yaran su su waye suba wajensu suda iyayensu,amma tanayi kamar ta manta koma bata sani ba kwata kwata baki daya,suna zuwa su zauna mata suyu mata hidima,bayan yasan kowacce akwai manufarta cikin zuciya,shikam baijin zai manta ba kuma don bai yafe ba,a'ah..sam,amma iyaye daban suke,duk wani abu daya taba illata ko jirkita duniyar jin dadinsu baijin dan halak zai manta da hakan,dalili kenan daya sanya daga shi har haidar da salim ba wata qwaqwqwarar jituwa ko shaquwa a tsakaninsu da dukka yaran,baiga kuwa dalilin da zai saka ya zabesu a matsayin matan aure ba.


Kiran nata na katsewa kiran P.A dinshi ya shigo,a ladabce ya gaidashi shi kuma ya amsa a mutunce,nan yake sanar masa yau nefa tafiyar
"Wacce kenan haris?
" yallabai south africa din,na tura maka komai jiya ta email dinka da watsapp amma naga kaman baka gansu ba"kanshi ya dafe yana ambatar sunan Allah,shaf ya manta baki daya,don har yau yana da agender tare asma'u a capterian makarantarsu,amma dole ya aje komao saboda tafiyar nada muhimmanci
"Qarfe nawa ne tafiyar?"
"Jirgin qarfe daya ne sir"
"Is ok....ba damuwa" ya fadi yana katse wayar.


A nutse ya shirya cikin qananun kaya da sukai matuqar fidda sigarsa,sun masa kyau sosai,slippers ya saka ya fito izuwa sashin anninsa.


Ko ina agyare yake tsaf yana fidda qamshin turaren wuta na icce tamkar ba safiya ba,manyan abubuwa da yake jinjinawa anninsa da shi kenan,yake ganin da wuya ya samu mace wadda keda kaso daya cikin ukun halayenta,tsanani ko wuya,samu da talauci basu taba sanya annin nashi qazanta ba dai dai da qwayar zarra.

Tamkar ba safiya ba haka falon yake,kai baka ce ana zama cikinsa ba,dakinta ya wuce kai tsaye,a falonta dake manne da dakin gadonta ya sameta,wanda ita da iyalinta kawai ke zama a can,tsaf ya sameta kamar kullum,sanye da atamfar super riga da zani plain,dinkin jikinta yayi dai dai da shekarunta ya kuma yi mata kyau sosai,hannunta riqe da cup na tea na tangaran tana shan dafaffen shayin na'a na'a,yayin da daya hannun nata ke riqe da casbaha tana ja,qamshin falon nata daban da wanda ya baro,cikin fara'a ta aje kofin hannunta a gefe tana masa maraba da zuwa,cike da qauna ya isa gefanta ya zauna gabanta yana lanqwashe qafafunsa
"Barka da safiya anni...."
"Barka kadai muhammadu.....mun tashi lpy?"
"Lafiya lau,ya qarfin jiki?"
"Mun godewa Allah"
"To Allah ya qara lafiya da tsahon kwana mai amfani"
"Amin don isar annabi da alqur'ani....hala yau ba zaka fita bane"
"Zan fita anni....amma sai wajen azahar haka...inasu haidar ne?"
"Salim dai bai jima da ficewa motsa jiki ba,haidar kuwa kasan yana can yana bacci" sumarshi ya shafa sannan yace
"Mtswee....ya kamata na maidasu kamfani hakanan anni...zaman hutun ya isa haka"
"Ya kamata kam...nima ina shirin tuna maka....".


Amal ce tayi sallama ta shigo falon cikin dinkin doguwar rigar atamfa,tayi kwalliya a fuskarta tamkar ba safiya ba,ta laqanci khalipha sosai,me yakeso meye baya so,kanta a qasa cikin nuna yanayin jin kunya ta qaraso,khalipha ta soma gaidawa wanda hakan sam bai masa ba sannan ta gaida anni,jima kadan tace
" me xaka ci ya khalipha"son samu yace babu komai,amma annin ta hanashi hakan,ko baya sha'awa tace ya karba,don kada ya sosa ran dan uwanshi musulmi yaga kaman ya gwasaleshi
"Bani tea mara madara"
"Kawai?" Ta tambaya cikin salo,kai ya kada mata,sai ta miqe ta fice

"Muhammadu ya maganar da mukayi abincin da za'a kai gidan kawunka?"kai ya kada idanunsa na kallon qasa yace
"Anni....anni keta daban ce....kin manta komai kenan?" Murmushi tayi mai dauke da ma'anoni da dama sannan tace
"Muhammadu...duk wanda Allah ya doraka a kanshi ka riga ka fishi kenan har abada baida yadda zaiyi....sannan rama alkhairi gamai cuta ba illa ne ba.....baida amfani a lokacin daka tserewa wani abu ka dinga qoqari da fadi tashin tunawa da shi,da kuma maida hannun agogo baya...rayuwa idan ta wuce ta wuce kenan har abada,ka kalli gaba...ka kumayi qoqarin gina gaban...ka manta baya...zuciya mai yafiya ita Allah yakeso yake maraba da ita,zuciya mai manta sharri,zuciyar dake manta alkhairi itace abar neman tsari,koda yaushe ka zama mai manta sharri,mai saka cuta da alkhairi ina fata ka fahimta"
"Na fahimta anni....madalla da samun uwa irinki...koda yaushe ina godewa Allah daya bamu ke a matsayin uwa....dai dai da rana daya baki taba umartarmu da yin wani abu ba dai dai ba komai tsanani komai wuya"ya fadi yana gyada kai
"Burin uwa ta gari muhammadu ko yaushe ta dora diyanta kan tafarkin tsira duniya da lahira"
"Haka ne....yau za'a kai in sha Allahu,zan baiwa haidar ya kai masa"
"Allah ya albarkaceka kai da 'yan uwanka duniya da lahira....ya jiqan mahaifinku"
"Amin summa amin anni",ya jima suna hira shida ita har haidar da salim suka shigo suka samesu a haka,baibar wajenta ba sai da sha daya na safiya tayi,yana matuqar jin dadin zama da mahaifiyar tasa,macace mai hikima dattako da sanin ya kamata,idan ka zauna da ita ko yaya saika amfana ko ka qaru da wani abu mai muhimmanci da baka sanshi ba.


A dan gurguje ya shirya cikin shigar suits,wanda kallo daya ya isar sanar maka da awanne aji take,yana cikin gyara tie din wuyanshi gaban madubi idanunsa suka sauka kan vivo dinshi dake aje gefan madubi,murmushi ya subuce masa sanda ya tuna agender dinsu da haduwarsu ta qarshe da asma'u,dariyar data dinga masa shida wayar tana masa kallon wani shashasha gaula,tuni ya gama gane inda ta dosa,saidai game din da suke bugawa shida ita hakanan ke burgeshi tare da bashi qawa,yakan raya a ransa tunda har take tsaiwa suyi magana koda ba mai dadi bace watan wata rana zata saurareshi,zata fuskance shi,za kuma ta zama tashi,hakanan yayi sha'awar kiranta,sai ya kunna wayar yana ci gaba da shiryawa tare da jiran ta kawo.


Yana takawa harabar gidan wayar na ringing alamun tana shiga bayan yayi sallama da anni,yaranshi suka bude qofar motocin suna jiran qarasowarshi,ganin haka ya dakata daga dan nesa kadan,ta daga wayar saidai bata amsa ba,hakan ke alamta ta gane cewa shine
"Assalamu alaikum ranki ya dade"
"Ya akayi yaron oga?" Ta fada cikin isgili tana dariya dariya,baki daya ta daukeshi kaman wani abun wasa a gareta,don tasan cewa babu hadin kifi da kaska,babu abinda ya hada kashi da fura,sam tafiyarsu ba daya bace,hanyar jirgi, mota bata isa tabi ba,murmushi ya saki,kafin yace komai tace
"Naga alama kai kam da gaske kake.....tunda har haka ne....kazo ka sameni ina son ganinka" sosai maganar ta bashi mamaki,saidai baiji komai ba,cikin salo yace da ita
"To babu damuwa,saidai yanzu haka oga ya aikeni ne,ya turani wani waje,aqalla zanyi sati biyu haka,idan na dawo zan iya zuwa?"
"Baka da case" tace da shi tana katse wayar,kashe wayar yayi baki daya yana dan nazari,murmushi yake kadan kadan,daya daga cikin yaranshi nazir ya qaraso ya amsa ya mata waje.


Murmushi take bayan ta kashe wayar,babbar aminiyarta husna ta dubeta tana mata wani irin kallo
"Asma me kike nufi ne wai?,mutuncinki kikeson zubarwa kome?,mace irinki maisu hamid su hisham me zaki da wanda ke qarqashin gashin wani....haba asma" dariya ta saki tana duban husna
"Husna...husna...shi yasa nake sonki...tunaninmu daya,ra'ayunmu daya,saidai a wannan karon abinda na hasaso daban da naki,kinsan meke faruwa ne?" Ta fada tana gyara zamanta tare da fuskantar husna sosai
"Saikin fada" ta ambata tana duban asma'un sheqeqe
"Wannam guy din ya hadu tako ina....Allah ya masa baiwar kyau da qira....abu guda ya nakasheshi....bai mallaki hatimin da zai sanyashi mallakar zuciyata ba....amma kowanne mutum da ranarsa.....muhammad namiji ne da zaki shiga da shi kowanne waje da maza masu aji da jin su wasu ne ki kuma kankarowa kanki qima da mutunci....abu daya ne kawai,ki sama masa suttura ki bashi abun hawa duk sanda zai rakaki wani waje...." Kai husna take kadawa
"Maganarki haka take....amma asma'u,gani daya nayi masa naga kaman bazai biyu miki yadda kikeso,a ido kawai tsayayyen namiji ne,yana da wani irin kwarjini da cika ido,anya asma?" Dariya ta saki tana kada key din motarta dake hannunta
"Husnaaaa....kudi sune qarshen zance kin manta?" Murmushi ta saka tana gyada kai tare da gamsuwa da bayanan asma'u,ita kanta ya burgeta qwarai,saidai ba ajinsu bane shi saboda bai mallaki abinda za'a nuna shi ba.

🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶


Cikin sati biyun ya nemi duk wata hanya da zai dinga tuna mata da shi,batasan ya akai ba,batasan yadda ya samu number dinta ba,sai kiranshi da take samu babu qaqqautawa,bata iya wulaqanta mutum ba kaf rayuwarta,don itama bata saka kanta a lissafin mutane masu daraja ba,bugu da qari alfarma ya nema a wajenta,hakan ya sanya bata qin daga wayarshi koda na zata ce komai ba,ba zata iya cewa komai game da shi ba,don a yanzun zuciyarta tana jin kamar bata mutum ba,batajin zata karbi wani abu da ake kira soyayya,soyayyar da taje jin bata a duniyarmu,bata jin gaske ce,don bata taba dandanata ba bare ta adar da komai a cikinta.

🧣🧣 *DAURIN BOYE*🧣🧣


*NA*

*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*


HASKE WRITERS ASSO

(Home of expert and perfect writers)


12



Qarfe daya da rabi na rana suka fito daga babban meeting na duka ma'aikatan kamfanin nasa,kai tsaye shida motocinsa suka wuce katafaren gidan abinci na purple palace da yake cin abinci don suci abincin rana,tafiyar minti sha biyar ce tsakanin kamfanin nasu da wajen suka isa sukai parking,tuni nazir ya bude mishi qofa,yana shirin fitowa vivo dinsa dake can gefan set din da yake zaune ta hau qara,shaf ya mance da ita,ya waiwayo yana dubanta,yasan mutum daya ne zaya kira asma'u,ita dince,wayar ya daga ya kara a kunnensa
"Kana ta wajen ina?"ta fada kai tsaye ba tare data damu da yin sallama ba
"Ina wajen aiki"
"Ohk....kazo purple palace restaurant ka sameni" ta fadi kanta tsaye kaman wani yaronta sannan ta kashe wayar,wayar ya sauke daga kunnensa,daya daga cikin yaranshi ya kira da hannu,qarasowa yayi cikin girmamawa ya masa nuni daya matso,cikin kunne ya masa magana ta mintina,kai ya gyada ya wuce zuwa cikin wajen cin abinci,minti biyu ya dawo ya sanar masa da abinda ya aikashi yi,kai ya gyada,sake kiran daya daga cikin yaran nasa yayi ya sukai magana,cikin mintuna sai gashi ya dawo riqe da baqar leda ya bashi,ya amsa,sannan a nutse ya soma cire suits dinshi na saman guda biyu ya bar ta ciki,takalmin qafarshi ya sauya zuwa mai sauqin kudi bayan ya kira daya daga cikin yaran shi ya dauko masa cikin boot din daya daga cikin motocin nasu,eye glasses dinsa ya cire ya kashe wayoyinsa ya ajjiye ya dauki vivo din ya riqe a hannunsa hadi da cire agogon hannunsa shima ya aje sannan ya fito daga motar,da kallo suka bishi,suna yunqurin binsa ya tsaidasu
"Ku janye motocin nesa kadan da nan wajen,karku biyoni ina dawowa"
"Yes sir" dukkansu suka ce,a nutse suka janye motocin suka musu muhalli a wajen da zasu iya ganoshi.


Ita daya ce zaune kan teburin cin abincin tana danne dannen waya, tasha ado cikin gown ruwan bula,ta yane kanta da mayafi ruwan powder mai turuwa,fuskarta sanye da sun glasses daya kusa mamaye fuskarta,da sallama ya qarasa wajen,hannunsa guda zube a aljihunsa,dayan riqe da baqar ledar,kai ta daga tana amsa sallama,ya mata kyau a idanunta sosai,saidai har yanzu bata gaza ganin aibunsa ba
"Kin yini lafiya ranki ya dade"
"Lafiya lau....zauna magana zamuyi" ba musu yaja kujerar da hannu daya sannan ya zauna,ya hade yatsunsa waje daya ya zuba mata idanunsa bayan ya aje ledar a tsakaninsu,kafin wani a cikinsu yace komai daya daga cikin waitress din wajen ta qaraso riqe da purple din leda mai tambarin gidan cin abincin ta miqawa asma'u ta amsa
"Kana kusa kenan dama?"
"Eh....naje wani aike ne na oga nan kusa"
"Yayi yaron oga...."
"Ga wannan,naga ni a hanya ne na miki tsaraba" ya fada yana miqa mata ledar,janta tayi gabanta sannan ta bude,abinda ta gani ciki ya bata takaici fuska a yamutse ta dubeshi
"Meye wannan?"
"D'ata,yalo,guava"takaicin daya qumeta shi ya hanata magana
"dauki muje" ta fadi tana nuna masa ledar da ma'aikaciyar wajen ta kawo tana miqewa bayan ta masa nuni da ledar da aka kawo mata,dariya ce taso subuce masa,sai kawai ya dauki ledar ya bita.


Nasiru shi ya soma tahowa da sauri da niyyar amsar ledar hannusa bayan ya hango fitowarsu,cikin zafin nama ya sanya hannunshi ta baya ya dakatar da shi,hakan ya sanya suka tsaya cak suna kallonsu har suka isa motar asma'un,ta masa izinin ya shiga itama ta shiga sannan ta tada motar.


Shiru ne ya ratsa motar jin hakan ya sanyashi cewa
"Ina zamuje ne?,kar oga ya nemi ni fa"
"Karka sake kawo min irin wancan tarkacen...ko na maka kama da maicin irinsu?" Dasauri ya sauya yanayin fuskarsa ganin ta waiwayo inda yake zaune,ya ragewa fuskar tasa kwarjini da tsare gidan da yayi
"Kayan marmari ne fa"
"Irin naku na talakawa?" Ta fada kai tsaye,cik yaji kalmar ta caki zuciyarsa,an taba gaya masa makamanciyarta cikin wani yanayi can baya daya kasa barin ransa,shiru yayi ya lula wata tsohuwar duniya,hakan ya wanzar da shiru a tsakaninsu har suka iso inda suka niyyaci zuwa.


Qaton botique ne wanda da alamu ke nuna na manyan yara ne,kai tsaye wajen suturun maza ta nufa tana dubawa yana biye da ita,bata masa magana ba,ita da kanta ta dinga zabar t.shirt zuwa trousers masu matsakaitan kudi tana miqa masa hadi da cewa ya duba ya gani,dariya ya dinga yi shi kadai yana biye da ita,duk abinda ta miqo cewa kawai yake yayi,yana yi yana duba price din kowanne riga da wando,a qalla ya manta yaushe rabon daya saka kaya masu wannan farashin,shi yake zabar kayan da yake so da kanshi,saidai ba cikin ire iren wadan nan qananun batique din ba.


Kaya ne kala biyar takalmi qafa biyu,kai tsaye wajen biya suka nufa aka mata total ta cire ta biya,jimillar dubu ashirin,yana biye da ita da kayan har zuwa cikin mota,dubanshi tayi kafin tace
"Ka fara amfani da wadan nan,ranar juma'a ka zabi daya daga ciki ka sanya,zaka rakani wata dinner"
"Ayyah...kinsan oga baya barina inje nan da can,sannan ni kaina bana yawon dare" wani kallo tayi masa
"Ka hadu ta halittar da Allah ya maka,saidai ka kwafsa tako ina,yaushe zan iya zaman aure da kai tabdi" ta fada cikin zuciyarta,amma a fili sai tace
"Kaman kai kace baka son yawon dare...sometimes idan kana wani abun kaman baki karatu ba" ta fadi cikin mamaki,murmushi kawai yayi yana dauke kansa,itama bata sake magana ba ta tada motar tana wani tsare gida suka tafi,saidai tana wassafa yadda zata dinga shiga da shi ne manyan gurare,cikin abokai da sauran 'yan uwa ko don ta kankarowa kanta mutunci wajen abokan takun saqa


🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶


Har qarfe shida na safe tana saman abun sallah bata koma baccinta ba,saboda breakfsat da zata shirya na asma'u.


Shida da minti goma ta nufi kitchen din,saidai yau sabanin ko yaushe tun kafin ta qarasa ta jiyo kwarafniya a kitchen din

Lauratu ta taras mai aikin mummy,a mutunce suka gaisa,akwai zaman mutunci da girmama juna tsakaninta da duka yan aikin gidan sabanin asma'u
"Yau kinyi sammako lauratu"
"Wallahi,alhaji ne yace amin magana,mu sama masa tuwon acca da safen shi zaici" murmushi aysha tayi,tasan daddy yana sane baisa an gaya mata ba,tasan yayi hakanne don kawai ta huta
"Idan kin gama hada komai ki barmin zan dafa" aysha tace da lauratu
"Kai...aikin bazai miki yawa ba....bakya gajiya da girki?"
"Girkin daddy ne fa lauratu ko kin manta"
"Af....anyi haka fa,na manta ba'a shiga tsakaninku" dariya sukai baki daya kowa ya kama nashi aikin.


Na asma'u ta fara kaiwa dining saboda taji yau zata fita makaranta da wuri,tun sanda asma'u ta soma cin abincin asma'u taqi abincin duka masu aikin gidan,sautari ayshan itake girkin ta dama na gidan wasu lokutan,bata taba gajiya ko nuna damuwarta ba


Zuwa goma ta gama na daddy shima,ta shirya komai tsaf ta diba zuwa saman dining ta shirya a can,tana niyyar barin wajen taji shigowarsa


A ladabce ta qarasa ta gaidashi ya amsa mata sannan ta gaida mummy sa'adah da suka fito tare
"Ke suka barwa girkin indo?" Cewar daddy yana murmushi,murmushin itama kawai tayi
"Sannu indo bakya gajiya,Allah yayi albarka kinji"
"Amin daddy" ta fada cikin jin dadi,don har ga Allah tana jin dadi idan ya sanya mata albarka,tana jin albarkarsa tamkar ta mahaifinta da ba zata iya tuna yaushe da yaushe ya saka mata ita ba.


Tana tsaka da shiryawa bayan tayi wanka wayarta ta dauki ringing,a nutse ta duba sai taga ahmad ne,ta danji dadi kadan tunda ko babu komai zai debe mata kewa,wata rayuwa ta taso ta kadaici tun da can zuwa yanzu,duk da cewa gidansu na can cike yake da jama'a amma ita kusan ita daya take rayuwarta,ba qawa ba aboki ba masoyi,sai daga baya qawa qwaya tak ta shigo rayuwarta.



Please Login or Register in order to submit comment