Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

shine babba a sannan bazai wuce shekara goma sha shida ba,duk da haka yaso tasowa da nuna rashin amincewarsa kan abinda ke faruwa,to amma qarancin shekaru da kuma duk sanda ya doshi anni da maganar maimakon ta bashi hadin kai sai kawai ta saka kuka,tana ganin kamar ta dukiya kawai suke bayan wanda suka rasa yafi dukiyar da duk abinda ke cikinta,hakan yasa ya janye ba mataimaki babu mai qwarara masa gwiwa.


Kafin kace meye wannan sun kwashe duk wata kadara daya mallaka,suka debo kauyoyin bogi da sunan duk dukiyar alhj sa'id banki sun karbe saboda bashin daya cicci kafin barinsa duniya,abinda ya rage musu kawai shine gidan da suke ciki sai motar hawanshi guda biyu,wanda shima easa muqullin akayi,muqullan kuma khalipha ne ya kwashe ya boye sanda suka haukace da nemansu,basu da tsayyaye gakan ya sanya dole suka haqura da qaryar da suka yanka musu,ko a sannan khalipha sai daya qaryatasu ya kuma yi maganganu son ransa saboda yasan duk abinda suka fada qarya be,basu ji kunya ko nauyin idon mahaifiyarsa ba,basuji tausayin maraicinsa ba suka mishi duka suna zqginsa kan bashibda mutunci baisan darajar na gaba dashi ba,yarin dasu kansu sun shaida sanda mahaifinsa nada rai ko kallon banza basa iya masa,bawai don wani abu ba A'ah,duk sharrinka da hassadarka idan kaga iyalan sa'id kasan sun samu tarbiyya fiye da duk wani yaro dake cikin danginsu,basu fara ji a jikinsu ba saida kowa ya watse ya kama gabanshi,aka barsu saisu yasu,suka soma cin abinda tayi saura daga kudin hannunsu da kuma store din gidan,don ko daya alhj sa'id ya gatanta anni bai barinta ta saida komai(kira a garemu mata,kada gata da dadin da miji yake baki yasa ki rungume hannunki kiqi sana'a komai qanqantarta,saboda ba wanda yasan ya rayuwa zata kaya mishi,ko babu talauci akwai mutuwa akwai tsufa).


Zara bata barin dami,sannu a hankali komai nasu ya tasamma qarewa,a nan anni ta shiga tsantsar tashin hankali,yaranta basu saba da wahalar rayuwa ba cikin qaramin lokaci saiga talauci na bayya a jikinsu,makaranta aka korosu ganin anci tearm biyu ba kudin makaranta ba dalilinsa suka koma zaman gida,duk wanda tasan suna huldar arziqi da maigidanta ta nemi taimakonsa amma kowa ya janye hannunshi yaqi tabuka komai,masu ragowar imanin ciki ne zasu taimaka daya biyu suma saisu watsar(irin rayuwar da muke ciki kenan a yanzu,kaci arziqin mutum amma bayan qasa ta rufe idonshi kana kallo iyalinsa su shiga halin ni 'yasu ba damuwarka bane,bamusan cewa kukan maraya cikin al'umma musifa da bala'i bane a cikinmu,kina ko kana katanga daya da maraya zai iya kwana baici abinci ba amma ke washegari kina da sauran da zaki zubar a bola,bamusan tashin hankalin dake jiran duk mutumin da zai kwana a qoshe maqocinsa ya kwana da yunwa ba koda kuwa ba marayu bane,ta yaya zamu rabu da ganin musifu da bala'i a rayuwarmu d'aya nabin d'aya?,ga cin dukiyar maraya data zama ruwan dare,Allah S W T yana fada cikin qur'aninsa mai girma , *_wadan nan da suke cin dukiyar maraya da zalunci haqiqa suna cin wuta ne a cikinsu,da sanju zasu shiga wutar sa'ira_* ,bama dukiyar maraya ba kawai,hatta da haqqin wani idan kaci ranar gobe qiyama duk abinda kaci din haka zaka zo dashi a kafadarka gaban zatin Allah komai girmansa komai qanqantarsa saika dauko shi,gaban mutane da aljannu qwari da dabbobi,tun daga zamanin annabi adamu har zuwa zamanin annabi muhammadu a gaban idanunsu za'a maka hisabi,Allah da kanshi yace *_haqiqa ubangiji baya zalunci dai dai da qwayar zarra_*
Allah ya shiryemu yasa mu gyara dabi'unmu,ya rabamu da cin haram da cin haqqin daba namu ba Allahumma amin.)



Duk wani fadi tashi ba kalar wanda bata runguma saboda farincikin 'ya'yanta da walwalarsu,Duk wannan abun yasan tana yine saboda farincikinsu,tun quruciya yaro ne mai son iyaye da son faranta musu,shi yace ta daina saida komai nata,zai fita yaga yadda zaiyi ya dinga sama musu abinda zasuci din,sam ta hana shi tace bata amince ba,abata haquraba anni sai data qarar da duk wani abu nata mai daraja.


Abu na gaba daya kunno musu kai shine yawan hauro musu gida da aka shiga yi,ga zaton masu haurowar tarin dukiyar da alhj sa'id ya tafi ya bari tana narke a gidan,wannan abun shi ya tsoratasu,musamman anni da take tsoron mutuncinta dana diyarta hajar,hakan ya sanya suka tattara kayansu sukayi balaguro zuwa gidan babban wansu alhj sa'id din wato saminu,wanda dukansu tare suka rabe dukiyar a tsakaninsu.

Sanda suka je matar gidan damai gidan dukansu basa nan,sanin su waye a wajen masu gidan ya sanya mai aikin ta saukesu sauka mai kyau,saidai tana mamakin suturar dake jikinsu,anan suka zauna sukaci suka sha cimar da suka jima rabonsu da ita.


Kafin wani lokaci hajar ta lafe jikin anni bacci ya dauketa saboda sanyin acn dake busowa,wanda rabonta dashi ta jima,a haka matar gidan damai gidan suka dawo tare da alama taren suka fito,tun shigowar saratu ta soma binsu da kallon banza kamar taga kashi,matar da ada kamar zata yiwa ummi sujjada,shima mai gidan abinda ya soma ce musu shine
"Kai yaya?,ya akayi ne mu kukazo yi" da qyar ya amsa gaisuwarmu,ummi tayi masa bayanin abinda ke tafe damu
"A gaskiya gidana babu wajen zamanku,saidai kuyi haquri aisha kuje koda gidan hamza wataqila shi yana da daki spare,ni yarana ma so nake kowa nayi masa nashi dakin daban,saidai ga wannan kwa sayi abinci don wataqila harda yunwa ma ta saku shirya wannan qaryar" ya fada yana ciro dari biyar ya miqa musu,mus'ab zai karba zuciya ta ciyo khalipha ya tankwabe hannunshi kudin ya fadi qafar alhjin,saiya daga kai ya kalleshi,dama neman qofa yake,nan yahau zage zage da tsine tsine,yana kwashewa khalipha albarka,ya kuma yi musu wuta wuta kan su fice masa daga gida bazai iya zama da mara tarbiyya ba,haka suka debi kayansu 'ya'yanshi na wajen suna sake turasu da sauran kayansu haka suka bar gidan.


Daga nan gidan qaramin cikinsu suka nufa,hakanan yana dan qananun maganganu ya karbesu
"Yanzu kaji ana tuno da tsohon zance,kawai don an siya maka gida kuma sai ayita bibiyarka" daki daya can falle a bayan gidan ya basu,dole khalipha ke kwana a waje sauran su kwana a ciki.


Kwata kwata zamane da babu dadi ko 'yanci ko ba'a gayawa masu karatu ba,raini da wulaqanci daga wajen masu gidan da 'ya'yansu kawai ya isa ya sawa zuciya baqinciki da bacin rai,sam basa qaunarsu,rashin tarbiyya qarara da izgili,har anni basu bari ba,abinda ya dinga qona zuciyar khalipha kenan,sau tari yakan yunqura zai dauki hukuncinsu anni ta dakatar dashi,abinci sai anga dama ake basu shi,ba ruwan mai gidan da sutura man shafawa da sabulun wankinsu,hakan ya qarawa khalipha himma,kullum ta Allah saiya fita,duk aikin halak da yasan zai sama mishi kudin da zasu dan kashe buqatar data taso musu komai qaqancin aikin koda kwasar kashi ce zaiyi ta,suna zaune ne kawai akan lalura,wannan shine gidansu amal,mahaifiyar amal macace mai shegen kissa da kutungwila,tun kan wannan lokacin haka take tun zamanin da duniya keyi dasu tafi kowa shishshige,amma a yanzun yadda take saika rantse da Allah Batasan ummi ba,mus'ab da hajar kuwa basu isa su sake ba dayake sune qanana a sannan,karma hajar taji labari,haka suke zaune sam babu wani dadi takowanne bangare sai haquri kawai,suna rayuwa babu makaranta bare suturar kirki,saidai duk tsiya ba zaka samesu cikin qazanta ba,zaka samesu fes dasu,hakanan annin ta tsaya tsayin daka wajen yi musu karatun addini dana boko iya wanda Allah ya hore mata,a haka suka rufa shekara a gidan da qyar.


Qarshen zamansu a gidan kuwa ya faru ne sanadiyyar dukan hajar da amal tayi,anni ta jata tana mata nasiha tare da nuna mata hajar qanwarta ce,abinka da sun samu daurin gindi sai kawai ta zunduma ihu,yarinya qarama a lokacin da ba zata wuce wasu shekaru ba ta zabgawa anni Allah ya isa,khalipha na wajen zuciya ta ciyoshi,dama dannewa kawai yake ya jima yana jin ciwon abinda sujewa annin,mari ya zabgeta dashi mai shiga jiki,gigitaccen ihu ta saki wanda ya sanya har mahaifiyarta dake sashensu sai data jiyo,a gigice ta fito tana neman amal din,sai kuwa suka ci karo a hanya,ta daga hannunta dake dafe da fuskarta saiga shatin yatsun khalipha kwance a kai rudu rudu,ashariya ta dannan ta finciki hannun amal din suka koma sashen su annin bayan ta gama tambayar amal ba'asin abinda ya faru,dai dai lokacin da annin ta balbaleshi da fada kan marin amal din da yayi kamar zata ari baki
"Wato kuna zaune a gidan ubanta kuna cin arizqinsa shine zaku taru ku kashemin diya ko?,to wallahi bazaiyuwu ba,saidai ku fita ku bar gidan nan matuqar haka zaku dinga yiwa yaraba,kowa ya kasa zama daku mu mun haqura mun zauna daku shine zaku takurawa rayuwarmu"da sauri anni ta bude baki zata bata haquri khalipha ya tsaida annin cikin bacin rai
"banga dalilin da zaki bada haquri ba anni kiyi shuru kawai da bakinki,duk abinda yaran nan sukeyi a gidan nan a idonki mama ake amma kin taba tsawarmusu?"
"Iyyee,ni xaka zaga khalipha,to zageni,zageni.....dama ana fadar halinka ashe da gaskene,to zamanku ya qare a gidan nan wlh" ana cikin haka mai gidan ya dawo,mama na ganinsa ta saki kuka qarya da gaskiya ta soma shirya masa,nan ya hau ya zauna daram,dama mai neman kuka an jefeshi da kashin awaki,nan ya dinga lailayo ashar kai kace khaliphan ba danshi bane,kai kace bai sanshi ba basu taba hada alaqa dashi ba,bai taba cin wani abu na arziqin mahaifinsa ba,hasalima ba zaka ce gadonsu na wajensu sun lamushe shi ba,a sanda yake wannan tada jijiyar wuyar tuni khalipha ya gana hada musu kayansu tsaf,haka ya dauki wasu aliyu da mus'ab suka dauki wasu suka fice daga gidan,har bakin qofa ya musu rakiya yana jifansu da muggan kalamai kala kala,wadanda suka sanya anni zubda qwalla,yayin da khalipha idanunsa suka kada sukayi jawuri saboda bacin rai,zuciyarshi ce kawai ke tafasa,ji yake kaman ya koma ya rufeshi da duka,saidai yasan koda yaso hakan anni ba zata taba barinsa ba.


A bakin layi anni ta sake yanke shawarar suje gidan habibu,sam bayaso yayi musu da ita,hakan ya sanya baice mata komai ba suka kama hanya a qafa,duk da nisan dake tsakanin gidajen haka suka taka har gidan,tun daga yanayin yadda matar gidan ta tarbesu farkon zuwan gidan nasu sukasan cewa akwai babbar matsala,tunda khalipha yaga yadda yaran gidan ke sangarta yasan tafiyarsu ba zata taba dai dai ba,tunda suka je aka zubesu a falo ba wanda yabinta kansu,har aka gama girkin rana a gabansu yaran suka baje suka ci abinsu ba wanda ya basu koda loma daya,a sannan hajar ta soma yatsina fuska tana radawa anni cewa yunwa takeji,haquri annanin ta bata saboda tasan cewa da zarar khalipha yaji ba zaman lafiya saiya samo ya bata,wata iriyar qauna da shaquwa ce tsakaninsa da ita fiye da sauran 'yan uwanta,tun tana yi a boye har khalipha ya fuskanci abinda ke faruwa,tunawa yayi duk cikinsu babu wanda aka yiwa iyaka da abincin gidansu a sanda suke dashi idan sunzo,daga babba har yaro idan yaje kanshi tsaye yake wucewa ya zabi kalar abinda yakeso a dafa masa,sai kawai ya nufi kitchen din gidan da kanshi,yarinyar gidan ya taras (zeenart a sannan)da mai aiki tana dafa mata indomie,ya tambayi mai aikin abinci,budar bakin yarinyar sai cewa tayi
"Ba za'a bayar ba makwadaita kwadayayyu" ta fada tana murguda baki,zuciya ta tasowa khalipha yayi yunqurin danneta sabida fadan anni daya fado masa,sai ya zari plate kawai ya bude tukunya ya zubo abincin ya fito,aikuwa ta biyoshi tana ihun barawo,umma ga barawon abinci bawai kuna don batasan khaliphan ba,kawai tsabar rashin tarbiyya ce.


Mai gidan da tunda sukazo akace musu yana barci bayan sunsan tabbas yaji zuwansu shi ya sauko daga samanshi yana tambayar zeenart din ya akayi
"Alhaji zuwa yayi har kitchen ya diba mana abinci" hannu yasa ya wafci abincin yana rufe khaliphan da fada
"Wannan wanne irin sakarcin banza ne da wofi,saboda tsabar rashin tarbiyya har takai ka dauki abinda ba naka ba ba'a baka ba?,to ni wannan iskancin ba'a gidana ba" haquri anni ta soma bashi khalipha na kallo zuciyarsa na tafasa,sai daya mula don kanshi yana hura hanci yasa aka basu daki,abinci ko yace saidai su jira na dare,saboda bacin rai khalipha wuni yayi a waje bai zauna agidan ba,ba laifi wunin da yayi a waje yayi masa rana,don neman kudi yayi sosai,bai dawo ba sai bayan sallar isha'i,ya shigo gidan a matuqar gajiye,cikin tausayawa anni ke dubanshi,qwalla ce ta cika mata idanu amma saota maida saboda tasan yanzun hankalinsa zai tashi,tuna tsantsar gata da suka samu daga mahaifinsu take,amma yau rana daya rayuwa ta juya musu baya cikin qiftawa da bismillah,dubansu yayi daua bayan daya,ya tambayi kowa lafiya ko suka amsa masa da eh,awara ya ciro mai zafi ya miqawa kowa tashi,saidai ta 'yar lelen tashi hajar daban take,ya qara mata da goba irin manyan nan da yaga tana yawanso,ba qaramin dadi suka jiba kuwa,anni ta dauko wani ragowar abinci cikin kwano ta tura gabanshi
"Ga naka abincin nan kaci mu munci namu,hala ma fushi kake damu tunda ka fita baka dawo ba sai yanzu" murmushin yaqe yayi yana amsawa da annin da a'ah,tunda ya kalli abincin yasan cewa ba qoshi sukayi ba,saboda haka ya juye tashi awarar akai yace kowa ya matso yasa hannu suci abincin yafi albarka.

Da murmushi anni ke dubansu sanda suke cin abincin,ta dago wayon khalipha,zuciyarta cike da tausayinsu da kyakkyawar addu'a da kuma fata da data dinga binshi dashi,ta tabbatar cewa Allah ya bata jarumin d'a,daya tamkar da dubu.

*mrs muhammad ce*

*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*
44

Duk da cewa bai tashi a wahala ba bai kuma saba da ita ba amma data riskesu yasa hannu bibbiyu ya karbeta,ya kuma shiga bilhaqqi da gaskiya yana qoqarin ganin farinciki da walwalarsu
"Anni kema kici" khalipha ya fada yana dubanta,kai ta girgiza
"Kuci khalipha,ni cinku shine kwanciyar hankalina" sai shima ya tsame nashi hannun yaqici,sai data lallabashi da qyar sannan ya maida hannun nasa,a hakanma kusan sai suyi loma uku baiyi daya ba.


Zamanta a gidansu zeenart shima dai zama ne maras dadi,zaman qunci da takura,wulaqanci kyara da tsangwama,rashin kunya fitsara da sangarta babu wanda anni bata gani ba daga wajen yaran gidan,tsana da kyara qarara,yayin da khalipha ya dage ta wani fannin,duk hanyar da yasan zai samu kudi indai ta halas ce zaiyi komai kashinta,baida girman kai lalaci ko son jikinsa,amma da yake qasar tamu ga yadda ta zama samun sai addu'a kawai,ana samun amma da qyar,hakanan abinda ake samun bai taka kara ya karya ba,da haka ake jalautawa rayuwar yau fai gobe tsumma.


Barinsu gidan shima sanadiyyar sharrin sata da matar gidan ta dorawa anni,dukka yaran kuma suka dorar da cewa eh sun ga sanda annin ta dauka suna daki ta zaci bacci suke,haka aka musu korar kare a sannan khalipha baya nan ya tafi neman kudinsa,a qofar gidan suka wuni da kaya a gabansu,ga yunwa baci ba sha,sai yamma lis ya dawo ya samesu zube a wajen,cikin gigita ya qaraso wajensu yana tambayarsu
"Anni....lafiya?,me kike anni a waje?,kalli kayanki yadda sukai qura?,wadan nan kayanfa anni ke zakuyi dasu?" Murmushin qarfin hali ta soma saki duk don ta kwantar masa da hankali,haidar da shima ranshi ke bace tun a sannan shi ya shaida masa komao,cikin wani matsanancin fushi ya durfafi gidan gaba daya jijiyoyin kanshi sun tashi saboda bacin rai,cikinnzafin nama anni ta damqoshi,da qyar da iya tsaidashi
"Indai na isa dakai karka taka musu gida,ka wuce mu tafi" tilas ya dakata,saidai zubewa yayi a wajen ya saki kuka,yau ya kasa daurewa,bacin ran dake cin zuciyarsa yayi yawan da bazai iya daureshi ba a yau,hajar ita ta taso tana kuka ganin khaliphan na kuka,ta iso gabanshi ta soma share masa hawayen fuskarshi,kallonta yake rausayinta na kamashi,idan duk su maza ne zasu iya daurewa rayuwa,zasu iya rayuwa koda babu kayan more rayuwa babu qyale qyale ita kuma fa?,ta soma zama budurwa amma babu duk wani kayan alatu kona qyale qyale irin wadda diya mace keda buqata tattare da ita,bayason kukanta ko kadan,sai ya sakar mata murmushi yana riqe hannayenta,miqewa yayi tsaye ba tare daya ce da kowa komai ba ya isa gaban kayansu,ya goya daya ya riqe biyu a hannayensa yayi gaba,shi kadai yasan me yake ji cikin qirji da zuciyarsa,takawa ya soma yi zuwa bakin titi wanda hakan ya sanya suka bishi da sauran kayan.


Mota ya tsare musu,yana fadin sunan unguwar da zasu anni ta dubeshi,yana nufin zasu koma gidansu su zauna ne
"Khalipha,kanaso mu koma gidanmu kenan?"
"Allah yana sane damu anni yana kuma tare damu,mutanen nan dukkaninsu babu wanda zai iya riqemu,babu wanda ya tuna da halaccin abba a garesu sanda yana raye dai dai da rana daya,komawarmu gidanmu shine gata na farko da zamu yiwa kanmu" bata sake tankawa ba,duk da qarancin shekarunsa amma yana da zurfin tunani da kaifin hankali.


Tamkar kango haka gidan ya koma,babu komai a cikinsa,basusan wanda ya shigo ya kwashe sauran furnitures din dake cikin gidan ba,amma koma wane duk yadda akayi yana da spare key din gidan,duba da yanayin ginin gidan gini ne irin na masu kudi mai cike da security,ba yadda suka.iya haka suka gyara sauran abinda ya rage a gidan,suka hadu suka share gidan tas,abinda basu taba ba bazasuma iyaba saboda girmansa masu aiki ke musu,amma yau babu ko mutum daya daya zauna dasu cikin ma'aikatansu kowa ya kama gabanshi.


Khalipha shi yaci gaba da daukar dawainiyarsu,ya hana annin yin komai,duk wani aikin qarfi kona wahala yana ciki,saidai kuma qoqarin nashi yana gazawa,sakamakon dan abinda yake samun bai taka kara ya karya ba bazai wadacesu ba,nan da nan wahala ta sake bayyana muraran ajikinsu,kana kallonsu kasan yunwa ta samu gindin zama a jikinsu,ba'a maganar sutura dama ko karatu duk wannan tuni ya jima da fin qarfinsu,dole anni ta soma sana'a itama,wanda wankau ne zuwa daka,sai ya zamana ba'a samu sosai saboda yanayin yadda unguwar tasu take,uwa uba ma duk wanda ya kalli gidan nasu daga waje zaiyi dariya ne kawai yace rainin hankali akeso a yiwa mutane,jama'ar dake da gida irin wannan me zai kaisu yin wankau ko daka?,hajar ita ke fita maqotan unguwanninsu tana amso musu wankin ko daka ba tare da sanin khalipha ba,ranar daya sani din kiwa kwanan bacin rai yayi,yayi kuka yayi kuka har yaji babu dadi,kanshi kawai yake tuhuma yana ganin kaman qoqarinsa ya gaza,bayan kuma duk wani qoqari yana yinsa,duk wani aiki daya fado hannunsa matuqar bana haram bane to zaiy ya sama musu abinda zasuci koda kuwa kwasar kwata ne,ita kuma anni tausayinsa take,tana ganin wahalar da yakeyi tayi yawa,dalili kenan daya sanya ta kama sana'ar.


Tafi tafi sai aikin qarfin ma ya zama sai kana da hanya ko.kana da wani daya sanka,zaman gida saiya auri khalipha,yanaji yana gani gidan block din aljh idris yayan mahaifinsa yaje neman aiki suka hanashi,anni ita ta bashi shawarar yaje ya sameshi a gida suyi magana wala'alla yasakasu su daukeshi,da fari yaqi saboda shikam ya sare da halayyarsu gaba dayansu ya aje ta tasu a gafe,musamman alhj idris da dukkansu ya fisu mugun hali,daga bisani ne ya amince don baisan me annin ta hango ba.


Randa yaje din yayi kusan awa biyu yana jiran idris din bai bada umarnin ya shigo ba,sai daga bisani ne yaronshi ibrahim wanda baifi shekara daya ya baiwa khalipha ba yazo ya kirashi suka shiga falon alhj idris din tare
"Cire takalmanka mana malam" ibrahim din ya fada yana katsawa khalipha tsawa,dubanshi khalipha yayi donshi nashi takalman na daure a qafarshi bai cire ba,sai a sannan ya lura,takalmi ne da abbanshi shi ya siyo musu,kudinsa yakai dubu talatin ya dauka ana khaliphan ya baiwa ibrahim daya,nashi kam ya dade dacin kasuwarshi a lokacin da hajar bata da lafiya,basu da kudin magani babu dalilinsa ya saida ya siya mata magani,dama ba wani tayi arziqi suka masa ba kwata kwata dubu goma aka sayeshi.


Saida khalipha ya gama bayaninsa kaf sannan alhj idris yace
"To nidai bana jin akwai abinda zan iyayi gaskiya,don tuni na miqawa yakubu haqqin kula da wajen,baiga dacewar ya daukeka ba shi yasa bai daukeka ba,saboda haka sai kayi haquri" shuru khalipha yayi ba tare da yace komai ba
"Ka tashi kaje" ya fada yana nuna masa hanya,tsam ya miqe ya fice daga falon,yana gab da ficewa a gidan yarinyar gidan daya taras dasu a falo ita da mahaifiyarta ta qwalo masa kira,tsayawa yayi cak
"Abba yace kazo" kaman baxai koma din ba,amma yadda yarinyar ta tsaya tana kallonshi yasa yajuya yabi bayanta.


"Binta tace a barka,basu damai share share ya tafi jinyar babanshi,idan kanaso zaka iya karbar aikin nasa kafi ya dawo sai a san yadda za'ayi,za'a dinga baka albashi a wata dubu biyar,sai abincin rana dana dare amma fa ba kullum ba zaka yi?" Kai ya jinjina saboda kudin koda baikai hakan ba zai iyayi,matuqar zai samu abinda zai kaiwa 'yan uwa da mahaifiyarsa.


Sanda ya koma gida yake baiwa anni labarin yadda sukayi taji dadi koba komai zai samu abinda zai riqesu,saidai kuma wani bangare na zuciyarta suya yake mata sosai,ace yau idriss shi zai dauki dan sa'id boyi boyin gida?,sa'id a sanda yana raye numfashi ne kawai baiyi musu ba,shine cinsu shansu suturarsu da duk wani kasuwanci da sukeyi,uwa uba sune suka kwashe duk wata dukiya ta sa'id din da sunan bashin banki yaci,ba ita ba hatta da khalipha sun sani sa'id din tunkan yayi bunqasar da yayi mutum ne mai tsoron bashi koda na naira biyar ne kuwa,balle har yakai kanshi banki ya karbi dukiyarsu.


Aikin da akace khaliphan zaiyu sai yatadda yaci uban hakan,gida ne mai matuqar girma wanda mahaifinsa ne ya ginawa idriss din dab da zai rasu mai dauke da dakuna da sassa sassa ginin zamani,shi zai share gidan komai girmansa,idan ta kama ma har dakin ibrahim dansa namiji tilo da yake gwadawa gata khaliphan ne zai shiga ya share,wani lokaci hatta da falon gidan hajiya binta saita hada masa da shi,baya ga haka idan i rahim ya bushi iska saiya hado masa kayansa yace ya wanke masa,haka aike lokuta mafiya yawa shike musu,dukka wadan nan hidimomin cikin kudinsa ne,bawai wani albashi na daban aka qara masa ba.


A qalla khalipha sai daya shekara uku yana wannan bautar gidan yayan mahaifinsa,cikin gidan da mahaifin nasa shiya gina masa shi,a qafa yake zuwa a qafa yake dawowa,aninci kuwa sai a debi kusan kwana hudu ba'a bashi na rana ba bare dare,duk ranar da aka bashin kuwa bawai ci yake ba,yana hadewa ne idan ya tashi tafiya ya kaiwa qannensa,wani lokaci idan yaga aikinnyi akan hanya yakan tsaya ya karba yayi kafin ya qarasa gida dinsu samu abun batarwa kafin wata ya cika a bashi albashinsa,don shi kanshi albashin idan alhj idris yaso sai wani watan ya shiga yayinkwanaki goma sha bai bashi ba,ya dinga kuma qananun maganganu shi daya yana fadin dadin ya yiwa khalipha yawa,ga cinyarwa gashi ana biyanshi kudi?,shi ai ya cancanci ma ayi masa jinjina sabida yayi abinda dukka sauran 'yan uwanshi suka kasa,khalipha bai taba daga kai ya dubeshi koya tanka mishi ba,yakanyi qoqarin danne fushinsa sarai duk sanda wani abu mara dadi ya faru,suna cin albarkacin anni data roqeshi kada ya yarda ko sau daya ya biyesu ayi wani abu mara dadi,dalilin barin gidan ya fara samo asali ne daga sanda jama'ar gidan haj binta da ibrahim suka soma qorafin ana musu dauke dauke,kusan kullum Allah ne dakullum sai anyi cigiyar an nemi abu an rasa.




Please Login or Register in order to submit comment