Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tambayar gwaggo asabe tun jiya tana jin nauyi da fargaba,Allah kadai shi yasan yadda take ji a zuciyarta
"Ya dai indon baffale?,ko fargabar auren ce irin ta amare?" Mairo wadda ta dafa kafadarta ta fada qasa qasa yadda su kadai zasu ji cikin murmushi,kai ta daga cikin qarfin hali ta maida mata murmushin
"Karki damu....zaki dace in sha Allahu wannan karon" murmushin kawai ta sake mata,kafin tace wani abu muryar inna laraba ta tsaidasu
"Zasu qarasa shiryawa ne saimu wuce".


Har suka gama shuryawar su wadan can 'yan rakiyar basu gama ba,har suka zauna suka huta bayan sun gama nasu aikin suka taba hira shiru kake ji,a qalla saida sukayi jiran awanni biyu sannan suka ce sun gama din su fito.


Da mamaki inna laraba take duban 'yan zuwa jeran,ko a mafarki bata taba tunanin zasu taka gidan aysha ba bate suyi mata jeran aure,dadewarta a gidan ya sanya zata iya fadin halin kowanne daya daga cikin dangin mummy,kai kawai ta gyada cikin ranta tana tabbatarwa kanta cewa akwai lauje cikin nadi,akwai dalilin wannan gangankon nasu,to koda ma saboda Allah zasun 'yammata irin wadan nan masu ji da kai da yauqi ina zasu tsaya yin wani jere,haka dai ta barwa ranta suka shiga motocin da zasu kaisu wajen wanda yawancinsu motocin 'yammatan ne suke ta shewa,duk su qi shiga motar da khalipha ya aiko da sunan wadda zata kaisu sun raina ajinta,sai inna laraba da su gwaggo asabe ne suka shiga.

Yana gaba saman babur dinshi lifan motocin dake dauke da kaya da su inna na biye da shi har suka isa unguwar
"Ya haka?,ya zai kawo mu wata unguwar daban kuma?" Cewar anty halima cikin fushi,da yake gwanar fushi ce ita din,abu kadan yake tunzurata
"Nima dai kamar ba unguwar da asma'u tace mana bace" inji farida tana wulwulga idanu,saboda ita kanta unguwar na daya daga cikin burinkanta a wajen zama.


Shiru ne yaci gaba da wanzuwa har zuwa sanda ya tsaida babur dinshi qofar wani katafaren gida,wanda idan ka tsaya ka qarewa gine ginen kallo kaf layin ba gidan da ya kai girma da tsaruwarshi,suma bakin gidan suka tsaida motocinsu
"Ku zauna...basai kun fito ba" ya fada yana zaro wayarshi daga aljihu,daddadannata yayi sannan ya kara a kunnenshi,waya yayi ta sakan biyar,ba'a cika sakanni goma ba katafariyar qofar gidan ta wangale,mai gadi cikin unifoarm na musamman ya bayyana,daga bayanshi kana iya hanho.


hango makekiyar harabar gidan,wadda ta qawatu da grass carfet da fitilu gami da furanni na alfarma da fitilu dake kunne,da hannu ya musu alamun su shigo,hakan nan suka dinga cusa motocinsu ciki wanda suka tashi laqwam a wajen,ba wanda ya iya magana cikinsu har suka gama dai daita motocin nasu kusa da wadansu kyawawan sabbi fil din motoci guda biyu
"Wai ina ne nan ne?,ina ya kawomu?,karfa yace yana nufin ya kawomu gidan uban gidan sa ne mu soma gaisheshi,an gaya masa mu mabarata ne?....ko qarqashin wani muke ci?" Cewar anty halima sanda suke fiffitowa daga motocin kowa yana qarewa harabar gidan kallo,daga yadda ta tsaru tun daga waje ya isa ya gayawa mutum cewa akwai kallo a ciki ba qarami ba
"Kaga malam mufa ba wasa ne ya kawomu ba muna da abinyi....ba gaida uban gidansa muka zo yi ba wannan matsalarsu,ka kaimu gidan qasa muje mu juye mata kayanta mu wuce"
"Kwantar da hankalinki hajiya....nan ne gidan amaryar" tofa!....sai aka soma kallon kallo tsakaninsu,yayin da murmushin farinciki ya subuce a fuskar mero inna laraba dama gwaggo asabe,duk da mamaki daya cika zuciyarsu fal suma
"Kaman yaya?...mu ba wannan fa gidan ya soma kaimu ba,bashi muka sani ba,sannan yanzu ace nan ne?,hasalima fa wancan gidan gidan qasa ne"
"Gidan qasa?" Mutumin ya fada cike da mamaki yana musu wani kallo
"Boss ne zai zauna cikin gidan qasa?....ai ko masinjansa ke ko mai masa wankin mota yafi qarfin zama cikin gidan qasa ko talauci irin haka,ina tsammanin dai a mafarki hakan ta faru kikai zaton a gaske ne"
"Uwar mafarki nayi....nace maka uwar mafarki nayi ba mafarki ba" ta fada cikin hasalar abu biyu,na farko yana son nuna mata raini raini gaban qannenta,na biyu ta yadda khalipha ya raina musu wayo ya rufesu,tashin hankali ta dinga ji yana rufto mata,ta tabbatar ko asma'u gidanta bai qarasa wannan ba,duk kyan gidanta tasan da zata ga wannan din shi zata fi so,ta yaya hakan ta kasance a kan aysha?
"Allah ya baki haquri hajiya....abun duk baikai ya haka ba...ni dan aike ne....kuma boss yace na girmamaku saboda akwai iyayenta a ciki....ga wadan can" ya fada yana nuna saitin sababbin motocin dake qasan rumfa
"Na amarya ne....ga muqullan idan kuna buqata a baku kukai mata" ya fadi yana ciro muqullan daga aljihunsa,dukkansu mutuwar tsaye sukai ba wanda ta iya magana a cikinsu,baki dayansu ba wadda batasan nawa ne kudin mota duk guda daya ba a ciki
"A'ah ka maida masa ya aje mata....duk randa aka kawo masa ita ya bata da hannunsa" cewar inna laraba da saurinta saboda tsoron karsu amshi key din wani abu yaje ya dawo,sam bata damu da kallon da suka soma jeho mata ba
"To shikenan" ya furta yana maida muqullan aljihun nasa
"Mu qarasa ciki ko?" Ya fada yana yin gaba gami da ciro wasu muqullan daban,inna laraba,mero,gwaggo asabe sune kan gaba,ba abinda bakunansu ke furtawa sai
"Ma sha Allah...alhamdulillah...kai Allah abun godiya" musamman inna laraba da tasan zaman aysha a cikin gidan,muryarta tafi ta kowa dagawa,kuma da biyu take da gayya take,ba qaramin farinciki bane a zuciyarta,ta tabbatar da cewa Allah baya zaluntar bawa saidai bawa ya zalunci kansa,hakanan ubangiji baya mantuwa,karamcinsa baiwarsa da kuma kyautarsa yawa gareta.


Qofar falon kawai tun daga nan suka sallama,inda suka gama miqa wuya sanda suka shiga falon zuwa dakunan baccin dake gidan,gini ne mai kyau mai daukar hankali wanda aka yishi cikin hikima da fasaha,tun daga falon gidan zuwa dakuna zuwa kitchen babu abinda bai saka ba na alatun rayuwa harda ma qaari
"Kai Alhamdulillah...Aysha Allah ya miki baiwa....Allah ya zaba ya baki....Allah ya tabbatar dake cikin wannan gida...yasa tsohuwar gida ce" abinda inna laraba ke fada kenan cikin farinciki suna kewaye gidan,mero ba abinda take cewa ita da gwaggo asabe sai
"Amin...amin" cikin farinciki.


Ta gefan su anty halima kuwa bakuna zuwa jikkuna sun mutu murus,kowacce cikin 'yammatan zuciyarta ta tafi,xasu iya cewa tsahon zamansu da burikansu basu taba shiga gida irin wannan ba....duk cikinsu babu wadda bata ji inama inama ace itace zata shigo gidan ba
"Kutumar uba....mutumin nan fa DON ne wallahi da alama"cewar mufida qanwar mijin anty halima sanda take qarewa gidan kallo karo na barkatai,batasan sau nawa ta kalli gidan ba,babu lungu ko saqo na gidan da bata kashe selfie ba....bama ita kadai ba har sauran yammatan
"amma asma cin kai ce....tace mana fuqara'u wal maskin ne shi?....inaga dai bata gano dai dai ba wallahi" inji nusaiba
"Ni gani nake anya wannan baifi hamid kudi ba?,ko a ina ta somashi?" Fatima qanwar mummy ta fada
"Da Allah ku yiwa mutane shiru kun cika mana kunne da surutan banza da wofi......." Anty halima ta fada cikin zafi da qunar rai,lallai ba shakka khaliphan DAURIN BOYE NE,yazo musu ne a duqunqune kenan?,ita a karan kanta tasan cewa babu gami tsakanin khalipha da hamid,hamid eh lallai yana da kudi....saidai duka basu kai yadda suka zata ba,sun zaci yafi haka,fariya da dagawa da son a sani ya qarawa arziqin nasa ado ake masa kallon yafi haka,yayin da khalipha ya iya takunsa,yake dora komai a muhallinsa da mizanin hankali da nutsuwa.


Hannun nusaiba ya kai kan wani daki wanda shi kadai ne basu buda ba bayan na mai gidan,dakin na manne da bedroom din ayshan,binta sukayi duka a baya "gwara mu kashe qwarqwatar idanunmu...kai....wlh ji nake kamar a mafarki....indo?,indon da tazo daga qauye wai itace da wannan gidan?,anya ba qarya mutumin nan yake mana ba raina mana wayo kawai yake don ya burge ya kawomu gidan jama'a?" Inji anty kubra
"Nima tunanin da nake kenan" anty halima ta fada cikin sanyin jiki gami da tausayawa qanwarta,tasan yanzun zata tashi hankalinta matuqar taji cewa gidan ayshan ya kerewa nata.


Daki ne guda wanda aka shiryawa sif ta jikin bango kowanne gefe da tarin hangers na maqale sutturu,sutturu ne sabbi a dinke iya ganinka babu kalar wanda babu
"Innalillahi....oh my god" nusaiba ta fada tana rufe bakinta da hannunta tana fiddo idanunta,abun yayi masifar burgeta da tafiya da ita,ba ita kadai ba kusan duk wadanda suka shigo dakin,saidai hassada data cika zuciyar wasu daga ciki hakan ua gaza tarihi
"Na shiga uku.....indo ina zata kai wadan nan sutturu?....wannan kuwa zata gama saka su harta mutu?" Cewar mero tana dafe qirji,dariya inna laraba ta saki
"Suttura ai itace mutum kuma bata yawa....kuma bai kai mata lefe ba bawan Allah ashe haka ya tsara zaiyi mata" ta fadi cikin murmushi,kayan suka dinga bi daya bayan daya suna tabawa dubawa da fadin kudin wadanda suka san kudinsa,wanda basu sani ba kuwa saidai hasashe kawai da suke,tun suna dubawa suka gaji suka koma kan jakankuna takalma da mayafai,qarshe haqura sukai da qwaqwqwafinsu suka fito daga wajen bayan sun gama daukar hotuna,a falo suka tadda anty halima zaune wanda tunda ta saka kai dakin sai ta fito da sigar amsa waya bata kuma komawa ba,gefanta kubra ce zaune itama cikin sanyin jiki,bala'i ta hausu da shi kan uban meye suka a wajen,kamar basu taba ganin kaya ba?.


"Halima ina zaton saimu koma haka harda motar kaya ko?,tunda naga gidan babu abinda yake buqata ko cokali kuwa"cewar inna laraba,wani banzan kallo ta juyo ta watsawa matar data darawa ma mahaifiyarta a shekaru
"Ke kinga inna laraba,na gama fuskantar take takenki fa...tunda muka shigo gidan nan kike rawar qafa kina neman gindin zama....shine zaki gayawa mutane magana a fakaice,butulu shekararki nawa kina cin arziqinmu daga ke har indon?,ina cewa badon muba da tuni ana qauye ana fama da kirci da faso?,to mu duk girman arziqi bai rudarmu don mun saba gani ba yau farau ba" maganar ta yiwa inna laraba ciwo qwarai,a ganinta ko babu komai haliman ta girmamata ko don furfurarta,cikin murmushi da danne bacin rai tace mata
"Ki adana fushinki don bani nayi ba Allah ne ya nuna ikonsa a kai....duk wani abu da kuka hana aysha sai gashi yau Allah ya bata ninkinsa....duk abinda kuke zaton bata cancanceshi ba sai gashi yau Allah ya bata sama da shi,kun hanata mota qarama qwaya daya sai gashi Allah ya bata manya biyu,kun bata daki mafi qanqanta a gidan sai gashi Allah ya bata masarauta guda....kun siya mata kayan daki a qasar nan maimakon qasar waje kuma saiti daya sai gashi Allah ya bata wasu fiye da daya fin biyu ma,ya qawata mata gidan aurenta da jin qansa da rahamarsa....kinga kenan ba yina bane yin Allah ne...idan kunga dama ku aje abinda ke ranku ku rungumi yarinyar da bata taba taka muku ba bare ta zubar muku,ba sawa ba futarwa sai ku da kuke amfana ma da ita,baky dubi maraicinta ba,baku dubi rauninta ba kuke gallaza mata da gasata a ruwan sanyi ba tare da duk wani mara dogon nazari da tsinkaye ya fuskanci hakan ba,kun manta cewa Allah ke daukaka bawa a duk sanda yaso,kun manta cewa talaka da mai kudi duka Allah ne ya haliccesu badon yafison wani ba sai wanda yafi biyayya a gareshi,kun manta cewa dan kauye mutum ne mai daraja shima kamar kowa....qauye muhalli ne mai daraja tun a zamanin annabawa?,tunda ko annabinmu an bada shi raino a can,ya rayu da su bai kuma taba qyamatarsu ba,halima wannan ishara ce a gareku,ruwanku ku gayara ruwanku ku dora daga inda kuka tsaya,aysha dai tayi gaba amma zaku iya biyota a baya"miqewa anty halima tayi ta soma zuba ruwan bala'i,duk wani bacin rai dake ranta take furtashi a sannan,su anty kubra ke riqeta amma bata ji bata gani,murmushi inna laraba tayi
"Iyaka a dakatar dani bakin aiki ko?....ki sama ranki to daga nan zan wuce cikin nawa ahalin,karki manta yarona da qafarsa yazo zai tafi da ni mahaifiyarku ta dakatar da shi,ta roqeshi ya barni saboda sabo,ina fata baki manta ba?,abu daya zan gaya miki kafin na wuce shine...kibi ko ince kubi duniya a sannu,a yanzu ishara daya tazo muku...idan baku sauya ba sauran isharorin na nan tafe,bikin indo kuwa har qauyen takai in sha Allahu,na barku lafiya" ta fada tana juyawa nan ta fice ta barsu,anty halima naci gaba da kumfar baki.


*mrs muhammad ce*👑*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN BAKI BIYA BA DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING_*

*_LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*

*DAURIN BOYE*
_SAFIYA HUGUMA_

*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_

*BURI DAYA*
_HAFSAT RANO_

*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_

*_,IDAN KINA BUQATAR SIYA KI TUNTUBI WANNAN NUMBER (08030811300)_*


*KO KUMA*
(07067124863)

*DB*


25


Bin kowannensu da kallo kawai asma'u take sanda suke zayyanawa mummy yadda suka samu gidan ayshan,jin abun take kamar almara,ji take kaman mafarki,tsaye kawai take ta kasa tabuka komai kamar wadda aka zarewa duk wata laka ta jikinta
"Qarya ne....qarya kuke waini zaku zolaya,ta ina yaron oga zai samu irin wannan gidan?,ni zaku tsokana bayan nafi kowa sanin wayeshi,mtseww" Ta fada tana banka musu harara,nusaiba ce tayi caraf ta ciro wayarta ta soma gwadawa asma'un selfie din da suka sha cikin gidan
"Kanbu" asma'u ta lailayo ashar din kai tsaye cike da baqinciki takaici cakude da hassada,zama tayi da sauri gefan gado kusa da nusaiba
"Who is khalipha?" Ta fada tana tambayar kanta,tabbas babu shakka akwai wani daurin boye dangane da al'amarin,tabbas wannan khaliphan ba shine wanda ta sani ba,akwai wani khaliphan boye a bayan khaliphan data sani,ta yaya zata yadda,ta yaya zata amince aysha ta auri wannan khaliphan?bayan duka yaqin da tayi a baya kan hana faruwar hakan,abinda ya dinga kai komo kenan a zuciyarta,cikin fushi da hanzari ba tare data cewa kowa komai ba ta fice daga dakin,tana jin kamar iska ke tafe da ita ba qafafunta ba.


"Aisha....kinga baiwar da Allah yayi miki kuwa?,kinga gidanki aisha?,dama mai kudi zaki aura?" Mero ke fadin haka cikin tsantsar farinciki tana riqe da hannun aishan,sosai takejin dadi kamar ita zata zauna cikin gidan.


Sam bata kawo komai ba tayi murmushi
"Mai rufin asiri dai mero,shima talaka ne kamarmu" idanu mero ta zaro tana dubanta
"Talaka?,alqur'an kada bakinki ya sake fadin cewa shima kamarmu yake,kinsan yadda sama ta yiwa qasa nisa?,to kwatankwacin haka tazarar mu da shi take,kinga gidanki kuwa indo?....bari kigaa a wayata duk da bai dauku da kyau ba" mero ta fada tana ciro 'yar qaramar torching dinta da mijinta ta saya mata wancan wata bayan ya saida amfanin gonarsa ya samu riba mai yawa.


Dariya take kawai a sanda ta karbi wayar don tana zaton zuzuta abu ne kawai irin na meron,a ido gidan ya qayatar da ita sanda take kallon hotunan,saidai sam bata kawo kanta a ciki ba
"A ina kika samo wadan nan hotunan mero?" Aysha ta tambayeta
"Hotunan gidanki ne da muka je yanzu indo...indo ki godewa Allah,Allah ya miki ni'ima da baiwa wallahi,ba shakka Allah ya fanshe miki wahalarki ta shekara da shekaru,yanzu haka kaf kayan jeranki mun dawo dasu saboda babu wajen da zamu zuba su,hasalima wadanda muka tarar jere a gidan sai namu ya tashi kaman a bola muka tsintosu" dariya sosai aysha ta saki,labarin sai ya nishadantar da ita,don har ga Allah bata yarda da gaske mero take ba,ta daukeshi kawai a shaci fadi ko nishadi takeson sanyata saboda taga alamun damuwa tattare da ita tun dazun kafin su fita,ita kuma ba wannan ne a ranta ba,ummanta take son gani,labarin ummanta takeson ji,kulawa take buqata ta gani daga wajen umminta komai qanqantarta.


Mummy ce ta turo qofar dakin dai dai sanda aysha ke wannan dariyar,dubanta mummy tayi sai ranta ya quntata,tana tunanin tasan komai da hadin bakinta yaron ya lullubesu,ta ayyana a ranta yanzu haka tana dariyar farinciki ne da samun nasara,idanun aysha ya sauka kan mummy sai ta miqawa mero wayarta tana miqewa cikin nutsuwa tace
"Me kike da buqata mummy,da kinyi magana sai nazo basai kinzo da kanki ba" kai ta girgiza ranta na baci,a zatonta tana bacin rai ne saboda aysha sun rufeta,saidai abinda bata sani ba shine tana bacin rai ne saboda ayshan ta samu daukaka da muhallin da autarta bata samu ba,hassada kecin ranta ba tare data farga ba
"Wannan ai yafi qarfin kizo saidai ni nazo da kaina....godiya na taso takanas nayi miki,wato duk zaman da mukeyi dake da yadda muka riqeki ashe ke ba haka bane cikin ranki,kallon maqiyiyarki kikemin,kallon abokiyar adawarki abokiyar gabarki wadda bata son cin gabanki kike min,har ku hada baki da yaron nan ku rufe mana komai sai munje ganin jeranki sannan mu gani,kinsan mai arziqi ne baki gaya mana ba,amma ya zowa a sma'u a wanda baida komai saboda wani baqin nufi dake ranshi,ko ba komai da munsan waye ya bayyana kanshi xamuyi duk shirin daya dace yadda ba za'a ji kunya ba,to na gode da sakayyar da kika yimin Allah ya saka da alkhairi" ta juya tana shirin fita,iya qololuwar tashin hankali aysha ta shige shi,dama ita gwanar hawaye nan da nan ruwan hawaye ya soma layi a fuskarta,bata gane kan me mummyn ke magana ba,me take nufi ne ?batasan sanda ta isa gaban mummy ba ta tareta cikin kuka tana fadin
"Wallahi mummy ba mai kudi bane...talaka ne shima kamata,idan da mai kudi ne anty asma'u ita zata soma sanin hakan,tunda ita ta hadani da shi,ta hanyarta komai ya tabbata har kawo yau...ki tambayeta kiji" ta qarasa fada muryarta na sarqewa
"Ke dalla matsa....dake da asma'un dukanku lusarai ne...kada ma asma'un taji labari.....kunsan waye muhammad abdulhakim mai goro?,kunsan wanne irin arziqi ke gareshi,dukanku baku sani ba,cikin 'yan sa'o'in aka gayan wayeshi,aisha kin nunan iyakata kuma ina godiya" ta qarasa fada tana kewayeta gami da ficewa daga dakin.


Kuka aysha ta saki har sai da gwaggo asabe sake zaune tana kallon ikon Allah ita da mero suka taso suka riqeta gami da zaunar da ita,tsoro ne fal cikin zuciyarta,ta yaya zata shiga familynsa bayan ya soma dayi mata qarya?,a hakan zai roqeta?,a hakan zai cika alqawarin daya dauka,tana tsoro,tana tsoron faruwar wani abu,don me zai yaudareta,akanme zai ninketa yazo mata da siffar daba tashi bace,yanzu gashi ya hadata da mummyn,ya hadata da mutanen da suka zauna da ita da dadi babu dadi,ba kamar danginta da suka kasa zama da ita ba saboda wani banzan dalilinsu maras tushe wanda baici ace ya shafi rayuwarta ba.

"Ohni sadiya..wai wannan wane irin lamari ne haka yake faruwa?,indo wadanne irin mutanene haka kike zaune da su?,tunda muka zo daga wannan sai wancan?" Cewar gwaggo cikin bacin rai da tashin hankali.


Miqewa tayi tsaye ta dubi su mero
"Ina zuwa" ta fada kawai kana ta fice,da hijabin data idar da sallar azahar a jikinta don haka bata da buqatar sanya wani abun.


Parlourn daddy ta nufa kai tsaye,tayi qoqarin daidaita nutsuwarta sannan tayi sallama ta kutsa kai,su biyu ne zaune a falon shi da anty safiyya,da alama wata magana suka gama tattaunawa ko suke kan tattaunawar,dukkansu shuru sukayi ganin shigowarta falon,kai tsaye ta isa gaban daddy ta duqa tana hawaye
"Daddy don Allah ka kirashi ki bashi haquri ka gaya masa ka fasa bashi aurena,daddy bazan aureshi ba,bazan iya zama cikinsu ba" anty safiyya zatayi magana ya dakatar da ita ta hanyar daga mata hannu sannan ya maida hankalinsa wajen aishan
"Saboda me?" Ya tambayeta
"Daddy....yazo min da siffar daba tasa ba,ya yaudareni daddy,wannan ha'inci ne daddy,a haka zanje na zauna da su?" Kasa daurewa safiyya tayi sai data furta
"Aisha,anso kashe rayuwarki ne Allah ya raya ta,an hadaki dashi saboda ana tsammanin bashi da komai Allah sai ya kaiki hannun mai komai din,wannan kadai bai isa ki godewa Allah ba?,wannan abun da kike fada tamkar butulcewa Allah fa kikeso kiyi"da hanzari ta daga kai tana kallon anty safiyya,akwai wani abu,akwai wani data sani kenan game da yadda auren ya qullu?
"Aisha" daddy ya kira sunanta bayan ya dakatar da safiyya
"Me yasa baki gayamin tun farko yadda abun yake ba kika ja bakinki kika yi shuru,kina zaton da an tafi a haka na hadaki aure da shi Allah bazai kamamu ba mu duka?"fada sosai daddy ya dinga yi irin wanda bai taba yi ba,alama ranshi ya baci sosai,kuka ta dinga yi tana bashi haquri,yace sam nauyin bakinta baiyi masa ba,haquri ta bashi da alqawarin ba zata sake ba,daga bisani ya kwantar mata da hankali da bata labarin farkon sanin daya soma yiwa khalipha a rayuwarsa.
"na sanshi can shekarun baya masu yawa ta sanadin faduwar jakar kudadena,kudade ne masu yawa wanda banda kudaden akwai muhimman takarduna harda na kamfani na,sosai na shiga tashin hankali a sannan,saboda matuqar kudaden suka bace a sannan tsaf zan iya shiga talauci bana wasa ba,cikin ikon Allah kwanaki uku da faruwar haka aka kira wayar kamfani na akace ni ake nema kan kudina dana yar,nayi murna sosai na buqaci inda zanje mu hadu da wanda ya tsinci kudin,ba bata lokaci ya bani adress din gidansu,yace nayi haquri,yana da wani uzuri ne da baya barinsa ya fita daga gida da da kansa zai kawomin,nikam a sannan kota kan hakan baibi ba,saboda ko a qafa yace min na tafi wata qasar na amso zuwa zanyi
Sanda na isa gidansu nayi matuqar mamaki,gashi dai gida har gida irin ginin masu kudi da wadata na sannan amma kana masa kallon farko zakasan babu da talauci ta tasamma yi masa raga raga,mamaki na bai sake qaruwa ba sai dana shiga na tadda matashin dan shekara ashirin na jiyyar mahaifiyarsa magashiyyan rai a hannun Allah da qannenshi maza guda biyu,kana kallonsu kasan kuka suka gamayi dukansu,sanda na amshi kudin na tambayeshi nawa yakeso ga mamakina sai yace min babu komai,alfarma daya yake da buqata na biya kudin aikin mahaifiyarsa ta rabu da zafi da radadin ciwon da take fama da shi,na zaci zai buqaci sama da haka,amma sai yace min buqatarsa kenan,matsanancin ciwon suger take fama da shi wanda shi har takai ga ya taba mata qoda za'a mata aiki.


Muna tsaka da wannan maganar saiga 'yan sanda katsama kanmu,miqewa naga khaliohan yayi yayin da suka yo kanshi kamar kura ta samu nama syka cukuikuyeshi,yayin da yajeta rantsuwa yana fadin bashi bane,matashi dake bayansu yana cewa
"Karku saurara masa,qarya yake ku dakeshi"ni na miqe na musu magana,sannan na tambayi ba'asi,nan dan samdan yace ana tuhumarshi ne da yiwa yarinyar wan babanshi fyade,kuka yake sosai a sannan yana rantsewa da duk abinda yasan me girma ne kan bashi bane,yanayin nagartar yaron ya sakamin tantama kan zancan,naja daya daga cikin 'yan sandan waje nace ya gayamin gaskiyar magana,na masa alqawarin kudade mai tsoka,nan yace ba shakka bashi bane,amma alhj idris da yaronshi ibrahim su suka biyasu kan kada au saurara idan sunzo su kamashi,daga nan su kaishi kotu ma birsin sukeso yayi,don ya matsa kan maganar gadonsu,a take na gaya masa sunana sai yayi sororo,na kira sauran 'yan sandan na sallamesu duka da wani abu,nan ibrahim yahau min hauka,nace koya wuce kona makashi kotu kan ya yiwa khalipha qazafi,haka ya wuce don kada allura ta tono garma,kuka sosai ya dinga yi mahaifiyarsa dake kwance tana tayashi,haka qannensa maza guda biyu,a sannan naso jin labarin rayuwarsu amma sai naga bashi yafi muhimmanci ba,lafiyar mahaifiyarsa itace gaba,muka je asibitin na biya duk wani abun da za'a buqata a aikin,hatta da abincin da ita da su zasu ci,cikin nasara akayi aikin aka gama lpy ta kuma samu sauqi,ina da niyya da shirin taimakon rayuwarsu tafiyar gaggawa ta sameni russia,wanda ban dawo ba sai bayan watanni shida,dana dawo su na soma nema sai na tadda sun saida gidan sun tashi,kuma ba'asan ina suka koma ba,dole na haqura da neman nasu naci gaba da saka yarona addu'a,don gaskiya nasp na riqeshi d'ana,saboda gaskiya amana da hankali da nutsuwar da naga yana da ita,uwa uba yadda naga yanason mahaifiyarshi yana tattalinta,nasan lallai sai yaro na gari ne kawai zai hada wannan nagartar"


Dukansu shiru sukayi suna jinjina labarin,yayin da zuciyar aysha ta soma kuma rabuwa

Please Login or Register in order to submit comment