Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kai da fahimta gami da rashin daukar komai da zafi
"Amma ace tun safe kima gidan nan me mike baki koma gidanki ba safiya?" Murmushi tayi tana dubansa sannan tace
"Magana nakeso nayi da kai ne daddy" ta qarashe maganar yana dan satar kallon mommy,bisa dukkan alamu batason yin maganar tana wajen kenan,ya fahimceta,hakan ya sanya ya dubi mummy dake kici kicin zuba masa abincin darenshi wanda aysha ce ta girka yace
"Jeki hadamin coffe sa'adatu"
"Toh" tace tana aje serving spoon din hannunta ba tare data fahimci komai ba ta miqe ta fice.


Sai data gama fita din daddy ya kalli safiyya
"Ina jinki safiya ya akayi?"
"Daddy.....kasan wanda aysha ta kawo zata aura kuwa baida wani qarfi?...daddy kaman ma dai bazai iya riqeta nake gani"
"Indai zai iya bata ci da sha da suttura da muhallin zama ya kiyaye haqqoqinta da mutuncinta da lafiyarta safiya shi ake bida a aure,amma duk da haka akwai wani abu da larabawa ke cewa khafa'a wato dacewa da juna ta wajen aure,ko musulunci ya yadda da khafaa'ah....nasan halayen yaro kuma na binciki lamarinsa naga yana da ikon da zai iya riqe mace....yana da aiki duk da qarqashin wani yake,na gamsu da bincike na shi yasa na bashi ita" lallai daddy qila akwai abinda bai fahimta ba ko ya shige masa duhu,hakan ya sanya ta sake hada nutsuwarta tace
"Daddy....yaufa aka je ganin gidan da aysha zata zauna daddy...gidan qasa fa?" Shuru yayi yana nazarin maganarta,sai yaji shima bai gamsu data zauna a gidan ba,don idan yayi hakan tamkar baiyi adalci ba
"Gidan qasa safiya?..." Ya sake tambayarta don tabbatarwa
"Eh daddy" shuru ya sake shi da ita ba wanda ya sake cewa wani abu,ajiyar zuciya ya sauke sannan yace
"Da kanta ta kawo yaron tana sonshi bata yadda za'ayi na hanata wanda take so,idan nayi mata haka kaman banyi mata adalci bane,amma shikenan babu komai...ki tashi kije Allah yayi miki albarka....zanga yaron zanyi wani abu akai in sha Allahu"
"Na gode daddy....Allah ya qara girma" ta fada tana miqewa,dai dai sanda mommy ta dawo dauke da coffen,hakan ya sanya daddy ya sake basar da zancan
"Ina abokina ne...ko kin soma barinshi gida shima?" Dariya tayi mummy ta amsa masa
"Yau abokinka ba lafiya,haqori ya sakoshi gaba...yana daki yana bacci"
"Ashsha...Allah ya sawwaqe,a gaida babanshi"
"Zaiji in sha Allahu....mummy ni zan wuce,sai da safe"
"Ki gaida gida da sauran yaran" da haka ta fito daga falon daddyn tana jin dadi har cikin ranta,tana jin kamar ta sauke wani nauyi,sam tana jin bai dace subar aysha ta rayu cikin gidan qasa ba ba adalci bane sam,batasan me yasa duk yadda yarinyar ke da hankali da nutsuwa ba basa gani
"Allah ya kyauta" ta fada tana amsa wayar abban al'amin daya kirata ta fito su tafi.


Yayi mamakin ganin kiran daddy da kanshi kan cewa yana son ganinshi,a ladabce ya amsa mishi,saidai yace ya bashi uzuri zuwa gobe,ya fadi hakanne saboda a ranar yaje abuja za' dauki hoton yatsunshi zai sauya passport dinsa.


******************


Qarfe biyar na yammaci yana zaune falon daddyn cikin shigar yadi wanda aka fi kira da mamar ruwan bula mai haske,cikin mutunta juna suka gaisa shi da daddyn,ya dan bawa khaliphan space ya kurbi lemo duk da bamai yawa ya sha ba sannan yace
"Malam muhammadu....ya gida ya hidimomi" yana dan shafar kansa yace
"Alhmdlh daddy komai lafiya" zamanshi ya gyara bayan yayi gyaran murya
"Nasan zaka yi mamakin kiran ka da nayi ko"
"Hakane" khalipha ya amsa
"Ba wani abu bane babba yasa na kira ka ba....ammm kasan cewa tun ba yau ba na daukeka kaman matsayin d'a a gareni...to haka yake har yanzu,musamman da zaka auri diya ta...inaso nayi maka kyauta ne kamar yadda mahaifi zai yiwa dansa" ya saurara da maganar yana ciro wasu kudi daga gefan inda yake zaune,rafa ce ta 'yan dubu dubu guda goma ya aje a gaban khaliphan
"Ga wannan.....ka karba kayi amfani da su....duk wani abu da kasan baka samu ka qarasa ba kayi da sh,ka gaya muhallinku da dan abinda zakuci" can qasan xuciyarsa qina da mutuncin daddyn yake sake gani,tabbas ya kai maqura wajen nuna talaucinsa,hakan kuma bai sanya daddyn kai tsaye yace bazai bashi aure ba,saidai kamar yana son taimaka masa ne a fakaice ba tare daya furta ba,yasan mai yiwuwa labarin gidan aka zo aka bashi.....ko kuma ita ayshan talaucin taga ya mata yawa ta soma kokwanto?,kaman daddy yasan tunanin da yake yace da shi
"Tunanin me kakeyi?....kar kayi shakka ko kokwanton karba...babu wanda yasan na baka wannan kudin ko munyi maganar da kai,daga ni saikai sai Allahn daya haliccemu,karka damu ni na baka ba tambaya kayi ba,kuma har abada qimarka na nan a ido na" boyayyar ajiyat zuciya ya saki sannan yace
"Na gode na gode daddy qwarai da karamcinka na batun yau ba,Allah ya saka maka da mafificin alkhairinsa...amma daddy... Am sorry to say bazan iya karbar wadan nan kudaden ba,zanyi dukkan abinda ya dace iyakacin iyawata da yardar Allah daga iya abinda Allah ya horemin....don Allah kar kace saina karba daddy..." Kai yake gyadawa cike da mamaki da alfahari da wadatar zuci irin ta khaliphan wadda ya santa ba tun yau ba,lallai akwai wadatar zuci mai yawa tattare da shi,hakanan daddyn ya sanya hannu ya janye kudin yana cewa
"Shikenan...Allah ya taimaka yayi jagora....yayi albarka a zamanku"
"Amin ya Allah...na gode daddy" ya fada yana miqewa sukai sallama,yayin da daddy ya bishi da kallo,har ga Allah yaso ace ya karbi kudin ko muhallin da ayshan zata zauna ya gyara musu,saboda yayi yaqinin mutumin da bai karbi kudi ba ko gida ya bashi bazai karba ba,yaso ace ya karbi kudin ma sai yayi dabarar da zai bashi gida kudin yayi wata sabgar da ita,ajiyar zuciya yayi cikin zuciyarsa yana jin bari qurar bikin auren ta lafa dole ya inganta rayuwarsu bazai qyalesu a haka ba.

🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶



Saura sati daya bikin a yadda aka tsara aliya tazo ta tasata a gaba zasu je gidansu za'a soma mata gyaran jiki
"Don Allah sashin ki bar wannan zancan,meye wani gyaran jiki don Allah?....ni kunya ma kike bani wallahi"
"Kya gama jin kunyarki ki miqe mu tafi...."
"Don Allah sashen ki barni...."
"Idan kika sake wata maganar Allah ni dake ne...ki shirya kawai" hakanan ta miqe ta shiga bayi wanka ba don tana so ba.

Tana shiryawa aliya na mata mitar tana maida kanta koma baya,har sai da ayshan ta juyo yana dan bata fuska a shagwabe kaman qaramar yarinya,wanda ta riga data saba kusan dabi'arta haka lokaci zuwa lokaci
"To kuma don Allah sashin ba ya riga ya wuce ba gashi ina shiryawa...."
"Oho dai...ina gaya miki ne donma gobe kar kice zakimin musu....don sati za'ayi ana yi"
"Haba kaman wata kaya"
"Whatever...." Aliya ta fada tana watsa hannu.


Tsaf ta shirya ta saka hijabinta sannan suka fito,ta shiga dakin mummy ta sanar mata
"Saikin dawo" kawai ta fadi ba tare data damu da yaya abun zai gudana ko waye zai biya ba.


Suna harabar gidan zasu fice khalipha ya fito daga wajen daddy,zuba ido aliya tayi taga reaction na kowannensu,wucewa ayshan tayi kamar zatayi da sauri aliya ta damqi hannunta ta tsaidata,dai dai sanda khaliphan ya qaraso wajen,duk da yana dan gaggawa ya wuce saboda ya baro baqi a tahir amma saiya rage saurinsa sanda ya iso wajensu
"Ango kasha qamshi..." Aliya ta fada cikin salom tsokana,ya fahimci tana da sauqin kai da barkwanci,hakan ya sanya yayi murmushi
"Qawar amarya...ina zaku haka?"
"Gyaran jiki....da qyar na jajibo wannan amaryar taka" ta fada tana yima aysha da kanta ke qasa dariya
"Wai haka...?" Ya tambaya yana dan kallonta a fakaice
"Ina yini" ta gaisheshi a maimakon bashi amsa,ya fuskanci tana da hanyoyi da dama da take guntule zance idan bata son tsawaitarsa,shima din yana da abinyi hakan ya sanya ya kawo qarshen tsaiwar tasu
"Gashi kuma yayan naki gurgu ne babu abun hawa da.na kaiku"
"Babu komai ango....zamu qarasa a napep babu nisa daga nan" hannunsa ya sanya cikin aljihun wandonshi ya soma zaro kudi,cikin hanzari ya maidasu bayan ya duba yawansu,Allah yasa basu gani ba


Daya aljihun ya sake saka hannunsa,'yan dari biyar biyar ne hade da 'yan dari bibbiyu,baisan adadinsu ba,yana son ya qirga nawa ne amma ya kasa kasancewar bai saba hakan ba,miqa musu yayi
"Ga wannan kyayi wani abu da shi.....saidai fa haquri angon bashi da komai talaka ne" dariya aliya tayi ta sanya hannu zata amsa,ta daya bangaren aysha ta riqe hannunta,saidai bata kula da ta amsa din tana cewa
"Ba komai...Allah ya amfana wannan din"
"Amin...." Ya fada yana yabawa nagartar qawancen aliyan da aysha.


Shi ya soma yin gaba,aysha ta dubi aliya
"Me yasa zaki karba aliya....yanzun haka kudinsa fa kenan?" Murmushi ya saki sanda ya jiyo abinda ayshan ke fada,wani lokaci halayyarta na masa kamanceceniya da halayyar hajar....wata halitta mafi soyuwa a garesu da bazasu taba mantawa da ita ba,kusan yanayinsu da halayyarsu na gogayya da juna,da wannan tunani ya qarasa ficewa daga gidan ba tare daya ji qarshen muhawarar tasu ba.


"To meye don na karba din.....ya kamata ko yaya fa yasan zaiyi aure ne,za'a bashi mace kuma budurwa,bawai ya aureki kaman an bashi sadaka ba" kai aysha ta kada ta soma takawa sai aliyan tabi bayanta
"Har kullum aliya bana son ki dinga sani ina jin ni dinma kamar kowa nake bayan ba hakan yake ba"
"Ni kuma na gaji da maimaita miki wannan karatun na kema kamar kowa kike,da dama ma kin fisu a wajen Allah"kanta itama take girgizawa,tausayin aysha na rinjayar zuciyarta,ko sai yaushe zata yarda itama 'yace kamar kowa?,sai yaushe zata sake tayi rayuwa yadda kowacce mace take?,oho...Allah masani...wannan itace amsar da aliya ta baiwa kanta,haka suka dinga tafiya tamkar kurame.


Ganin ayshan nason motso damuwarta wadda zata iya shafar wuninsu na yau,sai aliya ta qara sauri ta jera da ita tana sako mata zancan makaranta da yadda result dinsu ya kaya,hakan sai ya sanyayar da zuciyar aysha,suka ci gaba da tattaunawa,har ta zabi su taka a qafa tunda wajen ba wani nisa bane can da shi,aliya bata musa ba ta biye mata suka dinga takawa a qasa suna hirarsu
"waccan 'yar qarunar naga kaman bata wani damu da carry overn data samu ba ta aure take....naji labarin ta samu c.o ko?duk da ba'a gaya min ba don kada nayi sharhi...to sai nayi,zancan duniya kuma bai buya" Aliya ta fada tana qunshe dariyarta,don ita hakan yayi mata dadi,ko banza asma'u zatasan da cewa duk inda kakai ga zama wani a duniya dole kayi lacking wani abu a rayuwarka ko kai waye.


Harararta da aysha tayi yasa ta dauke kanta gefe guda tana dariyarta hankali kwance
"Kai.." Aliya ta fada lokaci daya dariyarta tana daukewa,saita waiwayo ta dubi aysha
"Aysha.....kaman angonki fa na gani hakimce cikin motocin can" ta fada tana nuna mata motoci ukun da suka wuce a jere iri daya,bin motocin tayi da kallo kafin ta maida idonta kan aliya tana murmushi
"Dama kina gulmar wata ba dole idonki ya dinga miki gano miki abinda ba haka ba....mutumin da muka rabu da shi yanzu yanzu a gida"
"Allah seriouse aysha shi na gani...don har mun hada idanu sai naga ya dage glass din motar" wannan karon sai da aysha tayi 'yar qaramar dariya
"Idan shi kika gani yaushe ya zama haka?...yaushe ya sayi dukkan wadan nan motocin yanzu yanzu kenan daga fitowarsa daga gidanmu ko?,may be shi da oganshi ne,don kusan ko yaushe yana gaya min suna tare" Ja aliya tayi ta tsaya,yanayinta ya koma da gaske take irin yanayin da tasan ayshan zata fahimceta
"Wallahi Allah da gaske nake miki aysha khalipha na gani a cikin motocin can,kuma alamu duka sun nuna cewa ba wani yake ja ba shi ake ja motarshi ce,kayan jikinsa fa ba irin wanda muka ganshi da su bane yanzu" shiru dukka sukayi aliya na kallon aysha cikin tantama,yayin da aysha ta soma shiga tunani gami da shakka,ajiyar zuciya aliya ta saki sannan tace
"Allah aysha tun asali sam khalipha baiyimin kama da wanda ke cikin babu ko yake samu a qarqashin wani ba....kin taba qare masa kallo da kyau kuwa tun daga kanshi har zuwa tafin qafa?" Dariya ce ta kubcewa aysha duk da yanayin fargaba data soma shiga
"Aliya ta yaya zan iya kallon wani namiji haka tun daga kansa zuwa qafa koda kuwa mijina ne?" Idanu aliya ta zaro
"Mijinki?...kina nufin ba zaki iya masa wannan kallon ba....lallai aysha akwai aiki a gabanki" qaramin murmushi ta saka tana kada kai
"Muje don Allah....shi din talaka ne kamata hakan shi ya qara min qwarin gwiwar amincewa zama da shi....ba da sunan miji ba...da sunan yaya dan uwa...'yan uwan da na rasa nake fata wannan karon nayi gam da katar da su kuma managarta,bana jin akwai wani ha'inci ko qarya tsakanina da shi"
"Idan kuma abinda idanuna suka gani gaske ne kinga shikenan...shikenan kaya sun tsinke a gindin kaba" aliya ta fada tana dariya
"U r mad aliya...ba don wannan zan zauna da shi ba...na amince ne saboda naga irina ne shi,kaman yanayin rayuwarmu daya ne...idan kuma har da gasken ne....bazan iya shiga cikinsu ba na zauna,ban masa qarya ba ban boye masa komai nawa ba,ban boye masa wacece ni" dukan kafadarta aliya tayi tace
"Shutup my friend....bana son wannan maganar taki ma...muje don Allah" daga haka suka ci gaba da takawa ba tare da sun sake bi ta kan maganar ba.


Numfashi ya sauke gami da lumshe bayan sun wucewa ganinsu aliya,yana sane ya sha mur ya dauke kai gamida dagr glass din sama don tayi tsammanin cewa bashi bane idanunsa ya bude sannan yace
"Jibril"
"Na'am sir"
"Daga yau bana son a sake saukemin glass din mota qasa idan bani na bada umarni ba"
"Yes sir,in sha Allahu" daga haka motar ta dauki shiru,addu'a yake cikin ranshi Allah yasa basu ganeshi ba,don ba yanzu ya shirya bayyanar komai ba.


🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶


Biki saura kwanaki uku gidan mommy ya soma cika da jama'a 'yan uwa da abokan arziqi,kowa zancan bikin asma'u kawai yake,da yawansu ma basusan cewa itama aysha nata auren za'ayi ba,idan sun tambaya ma takan ce a can qauyen iyayenta za'ayi,eh haka ne ayshan take cewa,don itama ta matsu ta wuce qauyen nasu,ko banza naka naka ne.


Cikin kwanakin zuwa gyaran jikin sai ya soma yi mata wahala saboda hidimar baqin dake gidan,awanninta kaso mafi yawa a kitchen take yinsu,duk da itama hakan ya mata dadi don bata ga meye na wani yin gyaran jiki ba,hakan kamar wani rawar kaine a wajenta ko wuce gona da iri,don haka sai take noqewa take fakewa da cewa gidan cike yake da baqi,hakan ya fusata aliya kan zasu maidata 'yar aikinsu,ta dage kan sai ta tattara kayanta ta dawo gidansu,da qyar ta shawo kanta ta nuna mata ranat juma'a ma zasu wuce takai baki daya tunda asabar ne daurin auren.


Tun ranar laraba aka fara gudanar da bikin,gidan kuwa ya cika ya tumbatsa da 'yan uwa da hamshaqan qawayen asma'u,tun ranar ta soma shiga ta kece raini,bridal shower suka fara yi sannan sauran events din suka biyo baya,ayshan kam mafi yawan lokaci idan bata tana kitchen ko dakinta,don data je gyaran jikin da aliya ta tilastata take dawowa,yawanci da aliyan suke zuwa,saidai ita bata shigowa gidan tunda aka fata bikin a qofar gida suke rabowa ta koma ta wuce nasu gidan.
*_WANNAN LITTAFIN NA KUDI NE,IDAN KIKA GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA KI TUNTUBI WANNAN NUMBER (08030811300)_*

*KO KUMA*
(07067124863)


*DAURIN BOYE*


*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*



24




Ranar laraba da safen mommy ta kirata dakinta,sanda ta shiga akwai qannen mummyn a ciki da wasu daga cikin 'yan uwanta zazzaune,wasu a gefan gado wasu saman tiles,binta sukayi da kallo sannan suka soma qus qus a tsakaninsu,hakanan jikinta ya bata da ita suke duk da bata iya jin me suke fada amma jikinta ya bata,tana iya jin sautin dariya dariya qasa qasa daga bakunan wasu daga cikin 'yammatan dake cikin dakin,saidai batasan meye abin dariyar ba,jikinta dai atamfa ce riga da zani sai hijabi data dora iya gwiwa kanta babu dankwali,sai tudun gashinta dake matse a cikin ribbom.


A ladabce ta tsugunna a bayan mummy wadda ke gaban wardrobe tana fidda kayan da zata sanya anjima,ba tare data waiwayo ba tace
"Gobe wasu daga 'yan uwanki zasu zo daga qauye,za'a je ayi miki jere....ya kamata ki sanar da shi zuwan nasu,ya bayar da muqullin gidan ko ya rakasu,don ba lallai su su sake gane hanyar gida ba bare gidan kanshi"
"Kawai mummy ya rakamun" inji nusaiba qawar asma'u tayi caraf ta fada,cikin muryarta kana iya jiyo sautin dariyar dakeson fitowa,nusaiban 'yace ga yayar mummyn,qawancensu yayi daidai saboda hali da yazo daya,tana son harkar girma itama,tana son fantamawa,tana son kuma mu'amala da masu hannu da shuni
"Ko yazo ko ya samo wanda xai rakaku...don ko su halima sunce ma ba zasu iya gane hanyar gidan ba" dariya nusaiba ta sake da alama tasan komai ko an bata labari,sai ta kuma waske tana wa farida cousin dinta dake zaune kusa da ita magana
"Toh mummy" ta fada tana miqewa jiki a salube,tana qirga iya kwanakin daya rage zata sake shiga wata sabuwar rayuwar,ko ya zata kaya da ita ita kuma?.

Zata fice sukayi clashing da naana,qawa ce ga asma'u,amma ta zama kamar 'yar gida saboda yadda ake buga qawance,duban juna sukayi naana ta saki dariya,abinda tsahon sanin da aysha tayi mata bata taba yi mata ba,face kallon banza da kallon raini dake shiga tsakaninsu,saboda asma'u ta riga ta gama dorasu kan turba
"Amarya amarya" naanan ta fada,kallo daya aysha tayi mata ta dauke kanta ta wuce,karon farko da hawaye taji sun cika idanunta,karon farko data ji damuwa ta sosa zuciyarta,gefan gadonta ta zauna,tana qoqarin tsaida hawayen,saidai bata da wannan ikon,saboda zuciyarta na buqatar rage nauyin da ta jima tana dauka,cikin muryar kuka ita kadai cikin daki take cewa
"Ya Allah...kaine mafi jin qan masu jin qai...kaine mafi tausayin masu tausayi...kaine mai tallafar raunana...ya Allah...ka fini sanin wace ce ni...ka fini sanin dalilinka na sanya rayuwata a wannan bigiren,ka fini sani gobe da jibina har zuwa qarshe na,Allah kai kace mu roqeka zaka amsa mana,ya Allah....kayi ruqo da hannayena...ka yiwa rayuwa ta jagoranci...Allah karka barni dai dai da qiftawar ido ya Allah...." Ta qarashe addu'ar tana fashewa da kuka wanda ya tilastata cusa kanta cikin fulalluka don gudun fitowar sautin kukan nata.


Ta jima tana kokawa ita kadai....ta dade tana fitar da ruwan hawaye kafin ta lallashi zuciyarta.


Qarfe shida na yammaci sanda 'yammatan amarya ke shirye shiryen zuwa bridal shower aka ce mata ta fito ga 'yan uwanta nan daga takai,gabanta na dukan uku uku ta zira hijabinta ta tako zuwa falon gidan inda aka aje su don bana ce aka saukesu ba,duba da yadda yawanci mutanenmu na birni ke raina mutanen karkakara,bayan mutane ne da Allah ya musu baiwa iri daban daban masu tarin yawa fiye da mu din,fargabarta na su waye suka zo?,yaya zasu zauna da su a muhalli guda ba tare da bacin rai ko samun wata tangarda ba?.


Murmushi mai tafe da hawaye ne kan fuskarta ganin mutanen da suka zo matan,mero ce da gwaggo asabe,sai inna kulu da kuma karima matar kawunta
"Sannunku da zuwa gwaggo kunsha hanya" ta fada itama tana zama qasan carfet cikinsu kamar yadda ta samesu zaune a nan,ko banza taji dadin gani masoyan nan nata biyu meronta da kuma gwaggo asabe,akace naka naka ne hakan take,sai ta dinga jin dadi da nutsuwa har cikin ranta,bakinta yaqi rufuwa gata ga meronta,falon jama'ar dake kai kawo sunyi yawa,hakan ya sanya ta kwashesu zuwa cikin dakinta,ba wanda ya damu da su don ba wanda ya qara bi ta kansu ma,hira suka balle sosai da ita,kusan duk rabi labarin na garinsu ne,kamar aliya tasan da zuwansu saiga wayarta,ta gaya mata zuwan nasu take tace gata nan zuwa,babu jimawa sai gata kuwa da kulolin abinci,duk da gidan basu da damuwar abinci amma bata son aysha ta damun kanta wajen sai tayi girki,don dama ba'a son ranta ana mata gyaran jiki take shiga kitchen ba cewar aliya.


Sanda ta qaraso gidan an ragu sosai duk an dode zuwa wajen da za'a gudanar da bridal shower din,hakan yasa ta dan jima suna hira da su,da yake itama sam bata da qyamatar mutane,hakan tana da fira fiye da aysha da kuna saurin sabo.


Sunzo mata da gudunmawar da aka tara mata,wanda duka duka abinda suka kawo din bai kai ya kawo ba,ba kuma don basu da shi bane,a'ah...,qarfin abinma dai gwaggo asabe ce da mero,har cikin zuciyarta sai taji dadin gudunmawar duk da qanqantarta,wannan ce rana ta farko da zata bigi qirji tace ga wani abu da suka taba yi mata,dalili kenan data ji dadin abun ta kuma bashi girma.


Dukkan abinda yake gudana kusan yana sane da shi ana gaya masa,kama daga events na bikin da yadda komai na gidan ke wakana,hakan ya sanya qarfe tara na dare yayi kiranta,a sannan tana gyarawa su gwaggo wajen kwanciya suna dan taba hira ita da gwaggon da mero,don karime babu wani sabo tsakaninsu,har gwara inna kulu a kanta,don bata taba fito da muguntarta tsirara ba a kanta.

Bata samu ta dauki wayar ba har sai data gama gyara musu wajen sannan ta duba mai kiran,bin kiran tayi don tana da credit wanda daddy ne yakan sanya mata lokaci lokaci,a cewarsa bata iya tambayarsa komai koda tana da buqatar hakan,ita kuma bata saba bane,tun tasowarta bata saba ayi mata abu na,shi yasa ma bata tambaya
"Anata hidimar biki ko ke babu ke...kiyi haquri" abinda yace da ita kenan bayan sun gama gaisawa
"Yayan naki talaka ne...." Ya sake fada a karo na biyu
"Uhmmm" kawai tace tana gyata tsaiwarta,don ita gaba daya tama mance da ana wani abu a biki banda asma'u na nata taron,dan bata sha'awa ma koda zatayi ma wa zata gayyata wa take da shi?,ita duka wannan ba damuwarta bane
"Kinje wajen ne?" Ya tambayeta karo na farko,don yasan ba lallai tayi magana illa kudin wayar da zaita tafiya a haka
"A'ah" ta amsa masa a taqaice
"Saboda me?"
"Iyayena sunzo daga takai...mummy tace na shaida maka gobe zasu zo jere"
"Gashi kuma inaa..." Katsewa yayi da hazari jin ya kusa baranbarama
"Ohk....shikenan...babu damuwa,Allah ya kaimu,zan aiko wani dan uwa na sai ya rakasu"
"Tohm" ta fada kana tayi shuru tana saurare ba tare data ce komai ba,shima jin shirun daga nashi bangaren yasan hirar tasu ta qare saboda haka ya katse kiran,aje wayar tayi suka ci gaba da hirarsu dasu gwaggo.

🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶


Tun tara na safe motar kayan jeran aysha take tsaye qofar gidan wanda kayan ta siyesu ne a zooroad maimakon dubai kamar yadda daddy ya tsara a siya musu kowacce set biyu daga waccar qasa,yayin da wadanda zasu jeran suke shiryawa,wanda yawancinsu ba don Allah zasu je ba,zasu je ne kawai saboda gulma,duk da cewa yau ne dinner din asma'un.


Goma da minti biyar kira ya shiga wayarta da baquwar lamba,cikin mamaki ta daga wayar ta kara a kunneta
"Ranki ya dade nine wanda yallabai ya aiko nayi wa 'yan jere rakiya" cikin mamakin yanda yayi maganar cike da girmamawa tace
"Ohk...to zakayi haquri kadan jirasu na mintina,bari na sanar musu"
"To babu damuwa..." Katse kiran tayi sannan ta dubi inna wadda shigowarta dakin kenan tana taya su mero hada kayan da za'a tafi jeran da su
"Inna...." Ta fada a sanyaye
"Na'am indo"
"Wai wanda zai rakasun ya iso yana bakin gate"
"Toh...toh bari a sanar da su" ta fada tana sakin jakar baccon da take zugewa kana ta fice.


Shiru ayshan tayi kanta a qasa,duk da tana sauraren hirarsu gwaggo asabe jefi jefi,saidai faduwar gaba da damuwa sun mata yawa,fargabar auren take qwarai,gani take kamar zata koma 'yar gidan jiya,yayin da gefe guda na zuciyarta ke cike da damuwa,ina mahaifiyarta ta shiga?,shin ko labarin aurenta ya isa kunnenta?,tasan aure zatayi kuwa?,tana son

Please Login or Register in order to submit comment