Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

sannan akwai quruciya tattare da ni saidai manya manyan laguzzan dana haddace basu da iyaka wanda ake gayan,wasu ina girma ina ganesu ina warwaresu,wasu kuwa har kwanan gobe bani da amsarsu bani damai zaunar da ni ya warwaren.


Qiyayyar da mamana kemin tayi grman da kaf qauyenmu sunsan me ake ciki,da yawan mutane abun na basu mamaki da al'ajabi,sai wasu suka soma min qazafin anya ba shege na tayi ba koma shine sanadiyyar sakinta da akayi asirinta ya tonu,kalmar shegiya na santa tun a qananun shekaruna....saboda akwai wata 'yar qauyenmu data taba cikin shege ta haife,irin tsangwamar da naga ana nuna mata da 'yar data haifa qarsge ma tabar garin nasan cewa ba qaramin mummunar abu bace,saidai gakan ya taimaka min qwarai wajen kare kaina da kare mutuncina wanda ba wanda ya damu da shi,kusan kalmar shegantaki daga gidanmu ta fito,daga bakin kakata ta soma fitowa.


Kullum ta Allah saina je gidansu ummi na labe a soro komai jibgar da zan sha idan ta ganni bai dameni ba,wataran naci kuka na na qoshi idan na hangota a tsakar gida,abu daya ne ya sanya na rage zuwa na janye jiki sanda ta furta cewa zata tsinen idan ba rabu da ita ba,na kuma san illar tsinuwar itaye wa yaransu ta sanadiyyar makarantar dare da na saka kaina nake satar jiki naje da daddare idan aikeni,inacin duka a nan ma da dunguri duk sanda naje na jima din,inda Allah ya taimakeni ba'a taba gani na ba cikin daliban bare aje ace an ganni a hanani zuwa tunda babu wanda yake zuwa cikin yaran gidan.


Allah ne ya hada jini na da malamin makarantar darenmu malam musbahu,yanayin rayuwar da yaga ina fuskanta ya sanyashi tausaya min sosai,yana taimakamin gun karatuna,dalili kenan daya sanya na zama zaqaqura cikin daliban,sau tari yakan ban sabulun wanka dana wanki,saidai baya bani zallar kudi,sabulu dai yana taimakan da shi,hakanan yana bani shawarwari wanda hakan ya taimakan qwarai wajen saitan rayuwata,shi ya tsayamin ya nema min makarantar gwamnati dake cikin garin takai,manyan daya hada inna yelwa da su shi ya sanya ta haqura badon son ranta ba ta barni,amma fa wani lokacin ma sai an fita break nake zuwa,watarana ma idan taso tana hanani zuwa,duk da hakan na samu karatu sosai.


A sannan aka tada zancan aurara da yara matan gidanmu wadanda suke sa'anni na ne,kowacce tana da nata saurayin amma banda ni,a sannan ma na sha cari da maganganu kala kala,sam ban damu ba don ba wanda nake kulawa ko ince ba wanda ke kulani saboda rashin gata da kuma qazafin shegantaka da aka yimin,nima hakan ya yimin,saboda babban burina shine naga na kammala primary na naci gaba,haka aka soma shirye shiryen auren su su biyar.


To ashe suna qwafe da malam musbahu,ranan da naje karbar sabulu wajensa wanda ban taba haka ba amakaranta yake bani bayan an tashi,ranar ma na matsu ne zan wanke unifoarm dina da ban samu damar wankewa ba saboda gobe monday.


Ihu muka ji wanda bamusan daga inda yake ba,ashe talle ce faccalar inna kulu,tana daga cikin masu matsanta min fiye da kowa


Tana kishi da ummina ko sanda tana cikin gidan fiye da kowa,hakanan suna shiri sosai da inna kulu,duk da shirin ba don Allah da ma'aiki bane,hakanan bai kai har zuci ba.

Kalaman da mukaji yana fita daga bakinta shi ya daga mana hankali dukanmu nida malam musbahu
"Innalillahi wa inna ilaihir raji'una,malam musbahu....indo....ashe masha'arku kuke aikatawa?....dama abinda kukeyi kenan shi yasa ko yaushe kuke liqe da juna?...wannan wacce iriyar masifa ce....yauni talle naga masifa quru quru da idanu na" kafin kace meye wannan ta tara mana jama'a,fadi take
"Wallahi na gansu.....na gansu da idanuna turmi da tabarya" abinka da qaramin qauye dake mamaye da duhun jahilci cikin qwaqwalen mafi yawa daga cikinsu nan suka yarda,suka soma mana tofin ala tsine harda masu shirin dukanmu,ba shiri aka miqamu hannun mai gari a can gidan na kwana,a ranar naga tashin hankalin dama jima banga irinsa ba,duk da ban wani damu sosai ba saboda ni nasan cewa muna da gaskiya babu abinda mukayi,har wayewar gari zuwa yammaci maganarmu ake zuzutawa ana yayatawa cikin qauyenmu da kewaye,mai gari masanin ilimin addini ne,hakan ya sanya baiyi hukunci da ka ba saida yayi kyakkyawan bincike


Kowa ya shaidi malam musbahu hakan shi ya wankeshi ya wankeni a idanun wasu,yayin da wasu suka zauna daram kan zancan inna talle ciki harda ahalin gidanmu kafff,hakan ya sanya ma wasu daga cikin jahilan iyayen yara suka soma janye 'ya'yansu daga makarantar,hakan ba qaramin bata ran malam musbahu yayi ba,dalili kenan daya sanyashi tarkata ya nasa ya nasa yabar garin,wanda hakan niba qaramin sake sakani yayi cikin halin ha'ula'i ba,don dama tun kafin yabar garin aka hanani zuwa makarantar,ko nan da can ma an hanani fita,ina turke a daki kamar akuya daure cikin mari,komai saidai a wurga min haka zan dauka naci komai muninsa idan naji yunwa ta kamani qwarai,duk wannan abun da ake ummina na cikin garin tana gidansu amma tamfar ma batasan me yake faruwa ba,ba motsinta ba gilminta,wannan shine abu na biyu daya sake dagulamin lissafin rayuwata,kuka nake ba dare ba rana,ina zaune a daki a daure,ba wanka ba wanki ba sallah,haka na dinga zama a dakin tsahon kwanaki.


Nasan zakayi mamakin ummina ko?,kace ina mahaifanta?,su basu isa su gaya mata taji ba?,mahaifinta Allah yayi masa rasuwa,tunkan rasuwarsa kuma mahaifiyarta ta rasu don itama ita kadai ta haifa,ta taso a hannun matar ubanta,duk yadda dangin mamanta dake jahar kaduna sukaso daukarta tun a lokacin babanta yaqi,haka suka haqura suka bar masa ita,itama ta danci wuya hannun matar ubanta,saidai ba wata mai yawa bace kasancewarta mai baki,tana iya qwatar kanta,kuma bata barin ta kwana bata yadda a danne ta ba,hakan kusan shi ya ceceta.


Inna kulu matar babanta macace mai azabar son abun duniya,ko yaya zaka bata to kaine mai daraja da mutunci,tana iya take gaskiya saboda kudi ko abun duniya,tana ganin dai dai indai kana miqa mata sai ta gaza gaya maka ko gyara maka haka rayuwarta kenan,dalili daya sanya sanda mahaifiyata ta soma girma tana amfanarta ya sanya bata iya yi mata gyara ko gaya mata gaskiya,saboda ko bayan rasuwar baaba taci gaba da zama a gidansu ne ba gidan wanda ta koma,cikin makusantan ummi da wanda ya isa da ita dama wanda bai isa ba ba wanda baisa baki ba kan abinda take gwadamin wanda ni bansan mafari ba,saidai duk wanda ya mata maganar tamkar ya kawo qarshen alaqarsa ne da ita,tun ana yi har aka gaji aka zuba mata idanu.


Ina cikin wannan halin labarin yin auren ummina ya sameni,na tsinceshi ne ina daga kurkukun da aka sakani,zaman da matan gidanmu keyi qasan bishiya na kisan dabe daga safiya zuwa yammaci,an baje kolin maganar kowa na tofa albarkacin bakinsa,a nan naji cewa a legos zata zauna,ta samu mijin ne cikin dangin mamarta dake birni,kusan duk wanda zai bude baki yayi magana a kai ba alkhairi zai fada ba,sai mugun abu yarfe da sharri,duk da cewa na danji kishin wani da zata aura bayan ga baba na amma na mata murna jin zata samu ci gaba ne,duk da bata damu da rayuwata ba,haka aka sha biki cikin garin na kece raini da tsone idon 'yan adawa,yako tsone din,don zama na musamman akayi cikin gidan har na kwanaki biyu ana tattauna abinda aka gani wajen bikin da abinda ya faru,don faccalolinta banda inna talle da tata adawar ta bilhaqqi ce ba wadda bata je ba bata kuma riqo tsarabar gidan bikin ba,ina daga daki ina jiyo qarar motocin da suka zo suka dauki ummina tabar garin takai zuwa legos,a sannan kamar nayi tsuntsuwa naje na taresu na ganta koda ba zata min magana ba,koda zata dakeni,koda zata tsinemin din kamar yadda tace,don ban sani ba shin zan sake ganinta ko mun rabu kenan?,a haka ina hawaye har na daina jiyo sautin motocin.


Tun daga ranar ban sake ganin ummi na ba sai idan tazo garin ganin gida,duk sanda ko zata zo din zan saki jiki na jima a soron gidan baba ina kallonta,koda kuwa waye ya aikeni,ko aiken waye a hannuna,a sannan duka sa'anni na suna gidan aurensu,a masu shekaruna ni kadai na rage cikin gidan.


Wani zubin kuma hanyar da take bi nake zuwa na zauna,ina sane nake fitowa wai yadda zata ganni ko ta manta da ni ne,sau tari idan muka hada ido harara take cilla min ko taja min qwafa,ta rage duka na,don wani bin har tazo ta tafi ba zaka ga ta dakeni ba,hakan kuma ina zaton baya rasa nasaba da girma da taga na fara,saidai ban isheta kallo ba,ko muhalli kuma bata yarda mu hadanikam kallonta kawai nake yadda ta canza lokaci daya tayi kyau,a yadda naji mutanen gidanmu na gulmar mijinta yana da shi,tana kuma jin dadi fiye da gidanmu data bari nesa ba kusa ba.


A haka rayuwa taci gaba da garamin,ga girma na fara yi,a lokacinne na samu mutum daya yake kulani saboda qazanta ta da rashin gyara wato dan ladi,babu mutumin dana tsana a rayuwata sama da shi,saboda tantirin dan iska ne,haka nan cikakken dan shaye shaye,babu nau'in abun mayen da baya sha kaf cikar fadin garinmu an sanshi,a hakan kuma 'yan gidanmu tayani murna suke an samu mai sona,idan dan ladi zai shekara bina da yimin magana bazan kulashi ba saboda haushinsa nake ji,a haka dai bai haqura ba yake bibiyata,duk da shima wani lokaci idan ya gaji yaba min maganganu yake
"Dalla can donma na rufa miki asiri nace zan aureki?,waye ma ya taba cewa yana sonki?,aibu fal tattare dake,uwarki ma data kawoki duniya gudunki take amma ni na bugi qirji nace ina sonki,banza mara rabo,kuma wallahi saina aureki inga ta tsiya" iren iren wadan nan kalaman yake jifa na da shi koda a hanya muka hadu gaban mutane,bama irin ranar da yake a cakensa.


A haka ummi na tayi haihuwar farko ta haifi mace,duk sanda tazo garin saina aika yara a zuwan qawarta ke aikowa a bani yarinyar ta dade a waje na,ina son yarinyar ina qaunarta sosai,inajin kamar ota kadai nake da ita a duniya,hakan ya sanya basma ta saba da ni ta shaqu da ni,sam ummi bata farga da hakan ba sai da basma ta soma wayo ta fara yawaita yi mata zancena,a nan naga tashin hankali,tayimin duka ta kuna koran gargadi mai qarfi babu ni babu ita,itama basman bata qyaleta ba,saidai ko gezau bamuyi ba,duka kuwa muna shanshi bama ya kamar sanda basman ta sake wayo,take debo kayan bayarwa cikin na mamanta da nata take kawo min,ranar dukanmu ta hada ta daka ta kuma jefoni waje tare da aikawa gidanmu ayimin gargadin zuwa gidansu tunda ba gidanmu bane,haka inna yelwa ta dinga bala'i da masifa,shikenan duk sanda tazo gari bani ba sake fita har sai tabar garin.

*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKO SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*


*DAURIN BOYE*
_SAFIYYA HUGUMA_

*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_

*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_

*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_

*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_


*DB*


17



Tashin hankali na gaba dana sake fuskanta shine shirin aurar da ni da ake ga dan ladi,wanda babu wanda ya tambayeni ko ya tsaya jin ra'ayina aka bada ni gareshi,tamkar auren sadaka zance aka shirya yimin,domin babu abinda dan ladin ya kawo gidanmu da sunan kudin zance kayan sa rana da sauransu,hasalima sake tunzurashi ake akan cewa ya taimaka su rabu da qaya,domin wai na tasamma tsufa a gabansu,duk da cewa duka duka a sannan ban wuce shekara goma sha uku cikin ta sha hudu ba,duk da lalacewa irin ta dan ladi wai mahaifiyarsa qyama take ya aureni,tana cewa za'a joganawa danta ni,danta yafi qarfin aurena,amma da yake dai Allah ya hukunta cewa sai na shiga gidansu na dandani tasu kalar azabar haka aka daura aurena da shi,babu wani abu dake nuna cewa bikin yarinya budurwa ake,duk wani gata da akewa budurwa yayin auren fari ni ban sameshi ba ban ganshi ba,a wannan lokaci nayita zuba idanu ko zanga ummi na amma shiru,bama ganinta ba,naso ace ko wani motsi nata da zai nuna tana sane da ni ko tana sane da aure na nasamu daga gareta amma maqatau,hakanan dangin mamata suka hado kayan da zasu iya dai dai qarfinsu suka kawo amma inna yelwa ta aje gefe tace sam ita da taba kayan zuri'ar gidansu ummina,ta hadamin buta tukunya da kwanukan cin abinci,sai katifa da labulaye da fulalluka iya abinda aka jera min kenan aka daukeni ziqau babu gyara aka kaini,hana rantsuwa dai ranar an sakani nayi wanka da kyau.


Tunda aka kaini dakina qwaya daya wanda aka jawa katangar kara da makewayi kusa da shi nake zaune ina raba idanu,santin dakin nake a raina saboda sau dubu yafi bolar da nake kwana kyawun gani,tun ina jiyo hayaniyar jama'a har gidan ya dauki shuru,ina nan zaune bansan sanda tsohuwar gajiya ta sanyani na sulale nabi lafiyar ledar da aka malalawa tsakar dakin ba.


Faduwar abu da naji yif a kaina shi ya farkar da ni a zabure nayi yunqurin miqewa,saidai nauyin da yake kaina ya fi qarfina,sai dana lura da kyau naga ashe dan ladi ne,wanda maganganun da yake furtawa kawai sun isa su gaya maka a make yake qwarai..."qasa aysha tayi da kanta,cikin jin nauyi da kunya tace
"Nayi alqawarin bazan boye maka komai ba.....idan nace komai ina nufin harda rayuwar aure na da danladi....a wannan daren dan ladi ya nemi karbar haqqinsa ta qarfi,saidai sam naqi yarda,haka muka dinga artabu da shi cikin dakin,wanda daga qarshe da yaga ina neman gajiyar da shi ya kamani ya yimin duka dan gaske wanda sai da naji a jikina,duk da na saba da duka kusan ni jakarsa ce amma wannan ya shiga jikina matuqa,saboda an yishi ne cikin fitar hayyaci,kafin kace meye fuskata ta kumbure haka jiki na,yadda naga rana haka naga dare,amma duk da hakan ban fasa tashi sallar asuba ba yadda na saba,bayan na gama na samu na rabe gefe guda ina maida numfashin wahala,idanu na kan dan ladi dake baje saman katifata,ni kuwa gani kwance kan dandanyar ledar daki.


Bashi ya farka ba sai tara na safe,zuwa lokacin har tsakar gidan gidan ya cika da hayaniya kala kala ta yara da manya,da alama kowa ya shiga sabgarsa,tashi yayi yana hardewa wanda hakan ke nuna bai gama wartsakewa ba ya dubeni ya watsan harara gami da jan qwafa,da alama yana sane da abinda ya faru jiya kuma yana qufule da ni,ficewarsa yayi,tunda ya fice din kuwa ba wanda ya nemi ni hatta da shi kanshi,sai da sha biyun rana ta kusa naga yunwa na shirin hallakani na miqe na debi ruwa na shiga makewayi nayi wanka,na cika kofi da ruwa na sha,na danji dama dama a jikina sannan na saka hijabina na fito cikin gidan,gida ne kamar namu na mutane da yawa,matan yayye da matan qanne da uwar miji,haka aka dinga bina da kallo wanda nasan baya rasa nasaba da sanin wace ni da kuma kokawarmu ta daren jiya da.nasan mafi yawa sunyi zatan wani abu ne ya faru,nidai na gaidasu na wuce wajen mamar dan ladi da suke kira da fatsi,tun daga yanayin amsa gaisuwarta nasan cewa akwai wata a qasa,ilai kuwa hakanne,domin kuwa na sake fadowa jahannama ta biyu ce,duk wata bauta ta gidan kusan a kaina take,zagi hantara da gori kuwa babu kalar wanda ba'a yimin,babu wanda ban haddace ba cikin qwaqwalwata,gefe daya kuma idan dare yayi mu hadu da dan ladi wanda kullum sai yayi yunqurin karbar haqqinsa ni kuwa naqi bada hadin kai,saboda bala'in qyanqyaminsa nake ga tsoro dake tattare da ni,uwa uba qiyayyar da nake masa,idan ya gama yunqurinsa haqarsa bai cimma ruwa ba sai ya kamani yamin duka,wansa hakan bazai hana gobe da sassafe na tashi aikin gida ba koda wanne irin ciwo naji wannan ba ruwan mama fatsi bane,sau tari takanmin habaici da gugar zanar ita bata ga me nakeyi a gidan ba bata ga amfani na ba,ashe rashin tarbiyyar dan ladi ta kai ya gaya mata cewa har yau bai karbi haqqinsa a wajena ba,randa na gane hakan takaici kunya da baqinciki sun sakani kuka mai yawan gaske.


A haka naci gaba da zama cikin wannan uquba,ko qofar gida ban taba leqawa ba bare nayi tunanin zuwa gida,duk da suma gidan ba ruwansu da ni,ba wanda ya taba takowa inda nake idan ka debe yan qananun yaran gidan da basu san me ake ba,idan yawonsu ya debosu zasu shigo gidan,a nan zanta jin dadi in riqesu ina aiki muna hira ina tambayarsu mutanen gidan suna bani labarin abubuwan da suka faru da bana nan,koyaya dan uwa yake yana da dadi,hakan na yimin dadi kuma yana deban kewa.


Ranar data zamemin ranar yayewar wani bangare na hijabin rayuwata shine ranar da dan ladi ya yimin wani irin duka wanda da qyar na qwaci numfashina,naji ciwo matuqa na sha wahala,hakan ya sanya da asuba na gudu zuwa gudanmu karon farko,abinda ban taba yi ba,kusan da qyar na kai kaina gida ina nishi ina numfarfashi,sanda na shiga ana sallar asuba,dakina na shiga nada na lafe a can,har baccin wahala ya daukeni ba tare da na sani ba,salatin da naji a kaina shi ya farkar da ni na bude idanuna,mutanen gidanmu na gani a kaina inna yelwa na akan gaba,ita ta saka hannu ta finciko ni sai gani a filin tsakar gidan,idanuna basu sauka akan kowa ba sai kan dan ladi da mama fatsi,yana wani cika yana batsewa,ashe abinda ban sani ba shine zuwa sukai nemana,wai na yiwa dan ladi sata na gudu,ba wanda yayi duba da ciwukan jikina sanoda tsabar sonkai kowa ya hau tofin ala tsine
"Gata nan munafukar Allah,inda zaka san cewa babu gaskiya ba wanda yasan da shigowarta cikin gidan....kayi haquri don Allah don annabi dan ladi ka dauketa ku koma" inji inna yelwa kenan
"A'ah...ku riqe yarku,don ni banga abinda aurenta ya qarawa dana ba sai jaraba da masifa" cewar mama fatsi tana tafa hannu da yada baki gefe,nan suka hau roqonsu har suka amince zan koma,ni kuwa a sannan na tubure kan babu abinda zai sanyani komawa,abinda ban taba aikata makamancin irinsa ba tsahon zamana da su su duka
"Dauketa dan ladi koda tsiya,uwar me zaki tsinana mana,dauketa ku tafi" inna yelwa ta fada cikin nuna qyama tamkar ba jininta ba,haka dan ladi ya dinga figata cikin bainar jama'a har zuwa qofar gida,inda ya cilloni ya biyo bayana da niyyar sungumata mu tafi.


Bansan ya akai na fada jikinsa ba,bansan ya akai na rarumeshi ba da hancina dake digar jini saboda jana da dan ladi ya dinga yi yana wujijjigani,dattijo ne mai kimanin shekara hamsin da biyar,tsam ya tsaya yana duban dan ladi dake takowa inda muke cikin isa da qafafa tamkar shi ya haifeni,dakatar da shi daddy yayi da hanashi tabani yana son jin ba'asi,matata ce daya fada ya sanya daddy bashi ni,har ya juya zai tafi sai yaji zuciyarsa bata aminta ba,hakan ya sanya ya dawo ya nemi jin ba'asi,yanayin shigar da suka gani tattare da shi ya sanya jama'a yi masa bayani na gaskiya game da rayuwata....magana ta gaskiya....tsaiwar da daddy yayi yasa alqali ya tilastawa dan ladi ya sakeni kawai ko iya ita kadai daddy ya yimin bani da abin ce masa a rayuwa,karamcinsa mai tarin yawa ne,alkhairinsa har yau bai daina bibiyata ba,ya karbi takardata ya kuma zauna da yan uwan mahaifina yace zai tafi dani,da sunso su turje,amma da yabi kowanne da hasafi cewa sukayi sai mun dawo,inna yelwa ce kawai taso taqi,yaranta suka tanqwarata ta amince

Daddy shi ya tsayan tsayin daka daya fuskanci ina son karatu,ya hadani da malamin dakewa asma'u lesson nima yake min,na zana common entrance na samu shaidar kammala primary,naci gaba da lesson na zana placement sannan aka kaini makarantar da asma'u ke zuwa,ya hadamu aji daya na fara daga ss one,har na kammala na samu shaidar kammala secondry,takarduna sunyi kyau fiye da zaton daddy,direct na samu wucewa B.U.K wadda ban jima da kammalata ba.



Zuwa na gidan daddy na fuskanci tsangwama qarara da qyama daga wajen asma'u da mummy,saidai ita na mommy har yau bai bayyana ba,bana zarginsu bana kuma jin haushinsu...saboda a wajensu na samu rayuwa irin wadda dangina suka kasa bani....na samu 'yancin da a baya ban samu kwatankwacinsa ba,na hutu na gangar jiki koda ruhina bai samu wannan hutun da nake kwadayi ba...."idanunta suka cika fal da qwalla wadda bata iya adanata ba sai data gangaro
"Har kwanan gobe ina fatan na samu hutu na ruhi,ina son na samu salama a ruhina....amma ba zata taba samuwa ba har sai ranar dana samu soyayyar mahaifiya...har sai ranar dana san dadin dumin mahaifiya wanda tunda na tashi ban sanshi ba....tunda na tashi bansan dadin soyayyar uwa ba,saidai na hangota daga nesa,kona ganta daga wajen wasu uwayen zuwa yaransu" kanta ta kwantar saman teburin muryarta na rawa,hawayenta na qaruwa zuciyarta naci gaba da karyewa


"Wannan ita ce aisha....itace ainihin aysha,aishan da kakesom cusa taka rayuwar cikin tata qazantacciyar rayuwar,ka taba cin karo da mutum mai tarihin baqar rayuwa irin tawa?....ka taba ji?" Ta qarashe maganar tana sakin kuka mai cin rai,duk da yadda taso danne kukan.


A hankali tamkar mai sanda ya miqe daga kan kujerar kana ya zare jikinsa ya soma takawa a hankali yana barin lambun,taji a jikinta tafiya yake kuma bata da sha'awar daga kai ta kalleshi,me ya rage dama me yayi saura?,babu mutum mai hankali da zaiji gundarin rayuwarta yayi sha'awar zama da ita,shin idan an zauna da itan ma me za'a qaru da shi,me ta mallaka wanne abun sha'awa ne ko jan hankali cikin rayuwarta,har ta daina jin takunsa bata daga kai ta dubi gurbin da ya tashi ko yabi ya wuce ba.


Batasan yawan lokacin data dauka a wajen ba,har sai data ji sautin dariya bisa kanta
"Ya arce ne shima yaron ogan yaga bazai iya ba?" Ta tambaya cikin izgilanci,bata motsa ba bare ya nuna mata taji don ba itace a gabanta ba,har ta gama babatunta tayi gaba nan ta barta.


Bai nemi komai ba ha dinga takawa a hankali hannayensa zube cikin aljihunsa,duk taku daya yana tariyar labarin da ya gama saurara ne a yanzu,labarin da yake jinsa tamkar hikaya,haka ya dinga takawa har ya isa inda ya bar mutanensa,cikin hanzari suka nazir ya iso cikin girmamawa ya bude masa murfin motar ya shiga sannan ya rufe,PA dinsa nata masa magana ta window din motar bai amsa ba sai hannu da ya daga masa,hakan ya sanyashi komawa cikin daya daga cikin motocin yabi bayan sauran motocin.


"Gida zan koma" ya furta a hankali ganin sun nufi hanyar kamfani,wanda hakan ya tsara da farko,saidai baijin a yanzu zai iya,yana buqatar kebewa baya son hayaniya,hakanan drivern ya sauya akalar motar zuwa gida.


Ta qofar baya ya shiga gidan,don bai shirya haduwa da anni yanzu ba,ya tabbata da zarar ta ganshi zata karanci sauyin yanayi tattare da shi,yanzun itama zata shiga damuwa ta kuma nemi jin ba'asi,sam baisan da harshen da zai fahimtar da ita ba.


Kacibus sukayi da zeenart yaja baya da sauri suna duban juna,ita dressing din jikinsa take kallo cikin mamakin kayan jikinsa,yayin da shi kuma rashin jin dadin ganinya yayi,a irin wannan shigar idan yayi baiso kowa ya ganshi bare ya tambayeshi ba'asi,yanzun ma bai kaucewa tambayar zeenart din ba
"Bro....lafiyanka kuwa?" Dan hade rai yayi kadan ya qarawa fuskarsa kwarjini saboda baison tambayar tayi tsaho
"Me kika ga?"
"Ka duba kayan nan da kyau kuwa kafin ka saka?" Ta fada tana dudduba jikinsa da idanunta kamar mai neman wani abu,sake

Please Login or Register in order to submit comment