Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Ba qaramar siyayya suka yo ba,har jikokinta sai data yi musu tasu tsarabar,kayan fitar biki nata dana asma'u,hakanan ta jido kayan business dinta,saidai babu ko tsinke da Allah yasa aysha taga gilmawarsa da sunan nata ne,kaya masu yawa haka aka jibgewa asma'u a store din gidan,a haka ma da wasu suna nan qarasowa.


Kwana biyu da dawowarsu taji mummyn na waya da wani mutum dake amsar kayanta a kantin kwari kan tana son kaya,da daddare sai gashi ya kawo din kuwa,a sannan yasha tana daki tana gyaran kumbarta lantana ta shigo ta kirata,kaman ko yaushe ta saka hijabinta ta fita
"Aisha ga kaya nan saiki zabi kalar wanda kikeso,daddynku ne yace a siya muku na fitar biki" kai ta tada ta dubi kayan
"Duk wanda kika dauka min yayi"
"A'ah A'ah ni babu ruwana kinsan halin daddynku,tare da asma'u muka je ta zabi wanda takeso to saboda kayan kar suyi yawa suja kilo shi yasa ba'a sai naki ba,dalili kenan daya sa nace nuraini ya kawo miki daga shagonsu kema ki zaba da kanki,tunda suma kayan su masu kyau ne"
"Mtsweew....mummy sai dana ce miki ba sai kin kirata ba,ina laifi ba ma da za'a siya mata,kawai ki zaba ki aika dasu wajen dinki ta bada size dinta,amma ai bama girma bane ki tsaya kuna wani maida magana ke da ita"
"Shikenan zabar mata,'yar uwarki zata zabar miki"
"Na gode" ta fada kawai tana miqewa tabar wajen,asma'un ita ta zaba mata atamfa da laces,kusan kayan ma mummyn ce ta sarosu kudin ya sake dawowa inda ya fita kenan,dinki ne kawai mummyn ta kai inda ake mata bayan ta dauki hotunan kayan ta turawa daddy da sunan kayan da aka siyowa asma'u ne da aysha.


Satin da suka dawo kwana hudu tsakani aka soma shirin amsar lefen asma'un,ko ba'a fada ba mai karatu yasan waye a gaba idan ba hanci ba,tun ana sauran kwana biyu a kawo lefen aka hana ayshan tsugunnawa,tamkar wasu jinin hurul ini ne zasu zo haka ake tsara komai,a randa zasu zo din kuwa kayan masu kawo lefe kawai da aka hada abun a tsaya a kalla ne,komai cikin girma harma da nuna fariya a lamarin haka aka jibge musu kaya ana jiran isowarsu.


Tabbas hamid yayi lefe irin wanda ya dace da tsarin asma'u,akwati talatin ne cif,goma pink,goma purple,goma brown,kowanne danqare yake da sutura ta alfarma,sai kayan sakun lalle,kama ga buhunhunan shinkafa,suger gero da sauran kaya,'yan uwan asma'u kaman su taka rawa banda anty safiyya data kama kanta tun sanda taga yadda 'yan uwan hamid ke bubbuda hanci suna kallon ko ina da kowa d'ai d'ai,don ko zama ma basuyi ba atsaye akayi komai,tukuicin kuwa da aka basu cewa sukayi sun gode basu amsa ba,wanda kana ganin yadda sukayi din sun raina ne,saidai da anty safiyyan ta fada asma'un rigima ta saka tace dama can bata qaunarta ita da hamid shine yanzu zata yiwa 'yan uwanshi sharri,ita ta rasa me yasa tana 'yar uwarta bata qaunarta,ta lura da da hali canzata zatayi da ayshan don ta lura tafi sonta da ita,sai abun yaso ya koma kaman ashan ce tayi da yake tafi rainata akan kowa,shuru kawai tayi musu daga qarshe saboda yadda taga sun dauki zancan tsakanin asma'un dasu anty halima,babu ma wanda ya kula da abinda ita tace ta hango din,duk idanunsu ba wannan yake kalla ba,abinda kawai suka dubawa dukiyar da aka jibgowa asma'un.


A sannan aysha na falon ta zuba ma anty halima da anty kubra abinci ta aje musu,saboda basu tafi ba har isha'i suna falon suna hirar yawan kayan da kyansu tare da yi musu d'ai d'ai suna sake kalla,tana shirin juyawa anty kubra tace
"Ke yaushe ne kawo naki lefen?naji har yau baki ce komai ba" Kanta a qasa tana murza tafin hannunta tace
"Idan zai kawo din zai fada.....dama ya riga daya gayamin zaiyi bakin qoqarinsa ne idan sun samu,saboda ranar bikin da aka sama tayi mishi gajartar da zai iya shiryawa a tsukin" wani mugun tsaki anty halima ta saki sanda take kai lomar abincin bakinta
"Kema kubra da neman magana kike wallahi.....har wani lefe kike jira a kawo mata....saikiyita jira ai....ke tashi ki bamu waje" ta fada tana hade rai gami da kafeta da ido,asma'u dake zaune gefe ta samu nayi,dariya ta dinga harda qyaqyatawa
"Yaron oga ne fa,sai abinda oga ya gutsuro ya bashi da shi zaiyi hidiman bikin,ku bishi dai a hankali kar ya fece,dai dai ruwa dai dai qurji"
"arziqi da talauci dai duka na Allah ne,kuma zaman lpy da mutunta juna ake nema ba tarin dukiya ba"cewar anty safiyya aysha ta jiyota tana fada,a sannan tuni ta isa qofar kitchen tayi shigewarta abinta,itakam ko cikin tunaninta bata wani saqa zancan lefe,mata masu 'yanci suke bidar lefe,ita wani abu ne ya rage mata,sam bama shine damuwarta ba a yanzu.


Washegari da daddare daddy na falonshi zaune ana nuna masa kayan,asma'un na zaune gefenshi suna kallo tare,duban mummy yayi
"Banga aishatu ba yau....ina tayi ne?" Baki mummyn ta tabe
"Allah dai ya kusa raba yari da barawo" ta furta a ranta
"Tana ciki.....ka santa gwanar zama a daki sam batason zaman falo bansan me ya sa ba" asma'u ya kalla
"Jeki kira min ita" hakanan ba don taso ba ta miqe ta tafi kiran ayshan,sanda taje ayshan na kwance rub da ciki saman gadonta tana karanta wani littafin addu'o'i,ta qara yawan haddar addu'o'inta sosai saboda kariya da ingantuwar tata rayuwar
"Saiki taso kizo....kwarkwasa fidda mai giji" ta fada tana watsa mata harara sannan ta juya ta koma,a nutse ta miqe ta sanya hijabinta sannan ta zura slippers ta fito.


Cike da nutsuwa tayi sallama hannunta dauke da jug na glass wanda ke cike da lemon guava data hadashi dazun nan,fuskar daddyn ce kawai qunshe da murmushi,ta isa gabanshi ta aje cikin nutsuwa
"Daddy sannu da hutawa"
"Yauwan indon baffale....sannu kadai" ya furta yana duba jug din
"Yau kuma me na samu?" Murmushi ta saki tana sunkuyar da kanta sanda take komawa da baya tana lalubar mazauni,da kanshi ya zuba sannan ya soma kurba yana kallon kayan da asma'u ke dagawa daya bayan daya,ganin shuru daddyn baiyi magana ya sanyata fara yunqurin miqewa a zatonta ba wani abu bane sai ya dakatar da ita har sai da suka gama kallon kayan tsaf,duk da aysha jifa jifa take daga kai ta kalla ta maida kanta qasa ta saddar.


"Ma sha Allah....yanzu sai biki kenan gaba daya ran ashirin ga wata" dif sukai daga mummyn har asma'un saboda anzo wajen,anzo wajen da ba zasu yarda daddy ya hada musu biki da ayshan ba,ko komai sun daure basa jin zasu haqura da wannan din
"Daddy" aysha ta kirashi cikin sanyin nan nata
"Na'am aishatu..."
"Daddy don Allah ina neman alfarma..."
"Tame indo?" Dan jim tayi kadan sannan tace
"Ina neman alfarmar idan babu damuwa a qyale anty asma'u tayi nata bikin ashirin ga wata din...ni ranar litinin din da aka gama bikinta ina son na tafi qauye ayi nawa bikin a can,daddy......" sai kuma ta danyi jim
"Inason idan an tashi daukoni a daukoni daga tushena...inda na girma na kuma rayu a can".


Shiru daddy yayi yana auna kalamanta,yarinyar nada nutsuwa sanin da kamata,ya tabbata da wata ce cikin 'yammatan zamanin nan masu son abun duniya son qyale qyale da qyamatar tushe babu abinda zai sanyasu yin zancan asalin nasu ma bare akai ga batun zuwa can biki
"Kin tabbatar haka kikeso,baki kuma da matsala da hakan?" Daddy ya tambayeta yana dubanta
"Eh daddy.." Ta fada tana gyada kai alamun tabbatarwa
"Shikenan to,babu damuwa" kanta ta duqar qasa
"Na gode daddy...Allah ya saka da alkhairi ya qara girma"
"Amin amin aishatu" ya amsa yana jin dadin addu'o'inta,ficewa tayi ta barsu a nan.


Tana shirin tada sallar wutiri bayan ta gama shafa'i wayarta ta dauki tsuwwa,dakatawa tayi don bata riga ta tayar din ba ta duba mai kiran,Aliya ta gani...take hannunta ya fara kakkarwa tana kokawar daga kiran kamar wadda ke dambe da wani tsabar rudewa da jin dadi,lallai Aliyar tazo mata a dai dai sanda tafi buqatarta fiye da kowanne lokaci
"Aliya.."
"Aysha" suka kira sunan juna a tare,qatuwar ajiyar zuciya aysha ta sauke,sannan cikin mutuwar jiki ta koma gefan gadonta ta zauna tana cewa
"Haba Aliya...haba..ya zakimin haka don Allah fisabilillahi.....bayan kinsan duk duniya bani da abokin shawara..kin tafi a lokaci mai tsada da muhimmanci a rayuwata kinyi dif kamar baki duniya...?" Ta qarashe fada lafuzanta na bayyana tsantsar damuwar dake maqare a zuciyarta
"Kiyi haquri sashin...wallahi dake nake kwana nake tashi...saboda ke naqi zama a nijer,kin ganni shigowata gida kenan ko zama wallahi Allah banyi ba na soma da kiranki....gayamin meke faruwa?"ajiyar zuciya ta sauke,cikin karaya tace
"meye ma bai faru ba,babu abinda ma bai faru ba sashin" idanu Aliya ta zaro kamar tana wajen cikin fargaba
"Me ya faru dake 'yar uwa gayamin"
"Wai aure zanyi,aure na ya kusa"
"Kaman yaya?,how comes?...labarin daya cancanci ace ni zan bada shi ni ake baiwa....aysha ban fahimceki ba....wanne irin aure?ina fatan babu cutarwa a ciki" dan qaramin murmushi daya fidda sauti ta saki,duk da cewa tsoro fargaba da alhini ne danqare a qasan zuciyarta
"Maganar tafi qarfin waya Aliya.....idan kin samu lokaci kyazo"
"Wanne lokaci ne zan samu?...ki jirayeni gobe da sassafe in sha Allahu"
"Allah ya nuna mana....ki gaida mama"
"Zata ji" da haka sukai sallama,aysha ta jima zaune riqe da wayar tana kallonta,jifa jifa tana sauke ajiyar zuciya,haka kawai take jin nauyin da take ji a qirjinta ya dan ragu duk da bata ce komai ba,lallai ba shakka rashin abokin shawara(aboki na gari mai addini) ba qaramin nakasu bane a rayuwar mutum.

*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*


*DAURIN BOYE*
_SAFIYYA HUGUMA_

*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_

*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_

*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_

*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_

*GA WANDA KEDA BUQATAR SAYENSU SAI YA TUNTUBI WANNAN NUMBER*
08030811300

*KO KUMA*

07067124863


*DB*



21



Goma na safiya ta kammala duk abinda take,saboda ta sani tsaf zata iya ganin Aliya a lokacin,cikin dakinta ta zauna tana 'yan gyare gyaren da suke maganin zaman banza da kuma hana kai tunani,don babu wani abu qwaya daya dake buqatar gyara cikin dakinta,tana da bala'in tsari komai nata a jere yake daki daki,tana da tsafta komai nata kal yake kaman ba'a zama cikin dakin,tun da can tana da son tsafta,koda bata da sabulun wanki ko wanka,haka zata dibi toka tayi wanka,ta sake saka tokar ta sabe kayan sawarta duk da cewa ba wai fita suke ba amma tana rage dauda,kuma tana jin dadin sanyasu a jikinta a hakan.

Sha daya na safe wayarta dake aje gefanta ta dauki ringing,da sauri ta duba aliya ce
"Ina bakin gate zo ki shigo da ni..."haka ta fada mata,yawancin lokuta indai tazo din ayshan take kira tazo ta shiga da ita duk don kada wai su hadu da asma'u tayi mata kallon banza da wofi,don ba qyaleta zata yi ba.


Murmushi suka sakarwa juna sannan suka tako zuwa cikin gidan tare,gab da zasu shige sashen dakin ayshan sukayi kacibus da asma'un sanye da kayan bacci zata shiga kitchen,da alama yunwa ce ta tasheta,don tana iya kaiwa azahar a daki tana kwance kurum kamar ruwa,har ta gota sai ta dawo da baya tana duban aliya
"a'ah....anzo shirye shiryen bikin ne?" Ta furta cikin siga ta izgilanci tana dariya dariya
"Ai gwara a bada himma...mai kwarmin ido da wuri yake fara kukansa ko?,duk da yake ma a qauye za'ayi komai,ta kwana gidan sauqi" ta qarashe tana dariya,da sauri aysha ta matsa hannun Aliya tana mata nuni da kada ta kulata kenan,aliyan ta fahimci haka,saboda haka ta watsawa asma'un kallon banza sannan tace
"Kinci sa'a cikin gidanku nake.....ki tareni a waje" ta fada a zafafe tana jan hannun aysha sukayi gaba
"Ba komai....duk nasan meke damunku" ta fada tana dariya tayi kitchen,iska ta furzar daga bakinta bayan sun shiga dakin ayshan,bata iya zama ba ta dubi aysha
"Har yau wannan mara mutuncin tana nan tana iskancin nan nata....abun ma kamar gaba yake sakeyi saboda rashin taka mata burki da bakyayi ko?" Murmushi aysha ta saki tana gyara ma aliyan wajen da zata zauna bawai don akwai datti ko kaya a wajen ba
"Karki damu.....duk abinda take ba shine a gaba na ba...saboda baki taba gani an gutsuri naman jikina saboda haka ba....hasalima qimarta nake gani har kwanan gobe....saboda jinin daddy ce ita....daraja ba qarya bace...ko a lahira wani yana cin darajar wani....karkuma ki manta cewa ni din ba kowa bace....face yarinyar da hatta mahaifiyarta ta gujeta"ta qarashe cikin karayar zuciya
"wannan ba hujja bace" aliya ta fada hannunta riqe da qugunta tana kada kai
"Manta da wannan.....zauna muyi hirar yaushe gamo" ta fada tana murmushi tamkar ba abinda ke damunta a rayuwa,saidai can qasar zuciyarta tana jin tafi kowa matsala a rayuwa
"Ba hirar yaushe gamo zamuyi ba aysha....mu tattauna maganar dake gabanmu" ta fadi tana zama,yayin da ayshan ta yiwa kanta mazauni itama kusa da ita.


Kaf babu abinda ta boye mata ta zayyana mata komai,shuru ne ya ratsa dakin yayin da aliya ke hadiyar yawu idanunta fes kan fuskar ayshan
"Aysha..." Ta kirata still tana kallonta
"Na'am" ta amsa tana dubanta
"Kin gamsu har cikin ranki zaki auri wannan mutumin zaki zauna da shi?" Tayi mata shigen tambayar da khaliphan ya taba yi mata,kai ta jinjina don ta tabbatar idan tace bata so tsaf aliya zata rusa komai,to idan ta rusa dinma me zata zauna taci gaba da yi cikin gidan?,meye amfanin zamanta?,a gaba wa zata hadu da shi?,gwara wannan ya nuna alamu na tausayi a gareta
"Shikenan....addu'a zamu ci gaba da yi Allah yasa kin dace...ina fata kuma asma'u idan ma tayi da niyyar mugunta mugun abinta ya koma mata kanta,auren mai kudi ba shine dacewa ba,aurwn mai kudi ba shine samun kwanciyar hankalin gidan aure ba,auren mai kudi bai cikin manyan jigon dake sawa a auri namiji,ni'ima ce da idan Allah yaga dama zaiwa wanda yaga dama bawai don yafi sonka cikin halittarsa ba,hasalima ba kowa ke dacewa kan hakan ba,amma sashin abu daya bana son kice zaki rage na hidimar biki da akewa kowacce diya mace budurwa,don kema ita ce....saboda haka zamuyi komai kamar yadda akeyi" dariya aysha tayi ta karyar da kai tana duban aliya
"Kiyi haquri sashin karki dora min abinda bazan iya ba,wallahi Allah bana sha'awar yin komai....kin manta cewa muhalli kawai zan sauya ba wani abu ba....ni haka nake ji a jikina bawai aure zanyi ba"
"Sai kuma kiyi..." Aliya ta fada tana tura dankwali gaban goshi,hakan da tayi ya sanya aysha qyale maganar don bata fiya son jayayya ba,saidai har cikin ranta bata jin tana buqatar yin wani abun.


Hira sosai suka sha da aliya,wanda tana yi tana jefo maganar biki da wani abun da za'a gudanar,itadai murmushi aysha take,komai ma ganinsa take kamar almara sani ne aliyan batayi ba take zancan wani biki,wayar aliyan ce ta fadi tunda ta sauka anijer din,bata kuma haddace lambar aysha ba,mamanta kuma itama bata gari bare ta aiko a karba mata lambar ta tura mata.


Sai qarfe uku aliya ta shirya tafiya,tare suka fito tana tako mata har wajen gate,daga can ta hango kamar shi,yana tsaye gaban mai saida agwaluma da goba irin masu turowa a baro din nan yana siya,kanta ta dauke har zasu gota shi taji ance
"Sannunku" tare suka waiwaya,ayshan ta saki dan qaramin murmushi
"Barka da yamma" ta furta a hankali,har yau bata sakewa da shi jinsa take kamar baqonta
"Barkanki..."ya amsa mata yana miqa mata ledar agwalumar daya siya mata a baqar leda
"Na gode,bari na dan raka qawata" ta fada bayan ta saka hannu biyu ta karba a mutunce
"A dawo lafiya...amma ai ba haka ake ba...bari ni nayi karambani....qawa ni suna na muhammad khalipha....nine sabon yayan aishatu" duban ayshan aliya tayi don bata gane me yake nufi ba
"Sabon yayanta da za'a daura musu aure...." Ya sake bata haske,qasan ransa yana dariyar yadda ta kasa gane zancan da farko
"Ohk....kacemin ango ne" ta furta cikin fara'a,sannan suka gaisa,nan suka barshi su kuma sukayi gaba,sosai aliya ta damqe hannun aysha
"Sashin....wannan kyau haka?....haka yake da kyau....ke ni kaman ma na san fuskarshi wallahi,kamar na taba ganinsa amma na manta a'ina....gaskiya kyakkyawa ne" itakam murmushi kawai tayi,don bata iya qare masa kallo bare ta rarrabe da kyansa ko muninsa
"Gaskiya kin dace...da alama sashin yana da kirki....saidai abinda ban gane ba....meye na wani cewa yayanki.....yana nufin a hakan zaku tafi wa da qanwa?" Ajiyar zuciya aysha ta saki
"Koma mene ni indai zai sanyani cikin ahalinsa,su zauna da ni zuciya daya su riqeni kamar daya daga cikinsu,na samu walwala da kwanciyar hankali magana ta qare" kai aliya take kadawa sannan ta dan dakata da tafiyar da take ta dubi aysha
"Ban yarda da wannan alaqar ta tafi a haka ba aysha....kisa a ranki aure zakiyi kamar kowa" murmushi tayi tana rausayar da kai bayan ta kallo gefe guda
"Nima ai ba kamar kowa bace aliya ki duba fa ki gani....ba wanda ya nemeni don zanyi aure...ban taba tattauna maganar dake damuna da kowa ba saike...kina nufin da ni 'yar gata ce...kina nufin da ana sona dukkan abinda ya faru din nan zai faru?" Ta qarashe tambayar idanunta cikin na aliya,da alamar akwai abunda ke taba ranta qwarai,kama hannunta aliyan tayi qasan zuciyarta cike fal da tausayinta
"Karki damu da kowa....karki damu da komai aysha...koba kowa mu muna tare...ki koma ki jirayi lokacin zuwa gyaran jiki....kin bar angonki kuma a tsaye,idan wata tazo wucewa kuma ta qyasa kanshi ba ruwa na,tsaf zata qwaceshi a hannunki da wannan sanyin naki" ta qarasa fada cikin sigar zolaya,dariya ta baiwa aysha har sai da tayi ta fito,har yau ba zata iya tantance wannan kyan da aliya ke fada ba
"Amma fa karki tsorata....don bai fiki kyau ba qawata" dariya sosai wannan karon ta baiwa ayshan,wanne kyau ne da ita?,yaushe ta samo kyan,mamaki take duk sanda aliya tace mata tana da kyau
"Ki gaida mama" suka qarke sallamar sanda wani mai napep yazo wucewa aysha ta tsaida mata shi suka tsadance yaja suka tafi.


A jingine ta sameshi jikin katangar qofar gidan hannayensa rungume a qirjinsa,ta saci kallonsa tana son gano kyan da aliya ke fada saidai hada idanun da sukai ya hana hakan tasiri,tana jin nauyin ya ganta tana kallonshi ba tsari hakan a wajenta,kauda kanta tayi sannan tayi gaba zata shige
"Da kin tsaya mun gaisa....wucewa zanyi daga aiken oga nake karyaga na jima ban dawo ba" bata ce komai ba ta dawo da baya,nesa dashi ta tsaya kamar yadda suka saba,a fakaice yake karantarta kamar yadda ya saba,yana mamakin halayenta sosai,sam.bata damu da wasu qyale qyale ba na rayuwa,tunda yake zuwa kulli yaumin cikin hijabi yake tadda ita,bata da yawan kazarniya ko rawar kai irin ta 'yammatan yanzu,bata da surutu bata da kallo,zai iya zuwa ya tafi baifi ta kalleshi sau biyu ba,shi dinma bawai ta kalli cikin qwayar idanunsa ba kai tsaye,dama ba wani hirar arziqi suke ba,yana zuwanne kawai saboda anni dake yawan cewa yaje din bai kamata ba,bataso tazo taqi sakewa da su,ya zamana bata saba da kowa ba
"Biki yanata qaratowa kinjini shuru ko?" Ya fada yana shafa sajen fuskarsa,ba abinda ta fada har ya gama jiran amsa ya dora
"Ina can ina fafutuka ne....duk abinda Allah ya hore zaki jini in sha Allahu...me dame zakiyi ne da bikin?,a ina zakiyi taki walimar?" Dan motsawa tayi kadan hannayenta rungume a qirjinta ta cikin hijabinta
"Karka matsa da yawa....qauye ma zan tafi a satin bikin" cikin mamaki yake dubanta
"Qauye kuma?.....me zakiyi a can?" Sai a sannan ta daga idanunta ta zubesu fes a kansa kafin ta sake janyesu ta maidasu qasa
"Can ne tushe na...kuma daga can nakeso a dauko ni....bani da inda yafi can" tayi shuru tana jiran jin me zaya fadi,gaba daya ta gama burgeshi,a wannan zamani da yawancin mutane ke bala'in gudu da qyamatar qauye....suke jin haushi da takaici idan an kirasu 'yan qauye,suke bata rai idan 'yan qauye sun rabesu,a sannan ita ta zabi ta nuna su a matsayin danginta,ta zabi kowa yaje ya ganta a cikinsu,take daga hannu tana gayawa duniya daga inda take
"Babu matsala.....duk da haka za'ayi abinda ya samu da yardar Allah....sakamin number wayarki don Allah koda buqatar kiran zai taso" ya fada yana miqa mata vivo dinsa da ya baiwa nasir dazu ya saka reza ya jijji mata ciwo,saika dauka tsabar dadewa ne ya saka ta qoqe,idanu ya zuba mata sanda ta amsa ko zaiga qyama daga gareta ko wani abu makamancin haka,saidai fuskarta na nan a yadda take ta soma jera masa lambobin,saura lamba biyu ta gama sakawa wayar ta dauke dif,yasan da faruwar hakan amma sai ya nuna kamar bai kula ba,cikin damuwa ta dago ta dubeshi
"Ta dauke wayar ko chargy ne babu?"
"Subhanallah....,dama yau tun safe take haka....miqo in gani,Allah yasa ta tashi,gashi oga zai iya kirana kowanne lokaci" ya karba yana cire batirin,ya sake maidawa ya kunna duk da yasan ba sake tashi zata yi ba,ai kuwa bata tashin ba,fuskarsa cike da damuwa yace


"Idan akwai paper da biro taimaka ki rubutamin nayi maza na wuce nakai masa saqon tunda taqi tashi"
"Mu gani" tace tana miqa hannunta,wayar ya miqa mata kamar yadda ta buqata,sai yaga ta bare batirin ta ciro layin dake kai,dama babu memory a ciki,wayarta ta bude ta cire nata layukan ta dora nashi ta kunnata ta tasheta sannan ta miqa masa
"Kayi amfani da wannan,zai iya kiranka kafin ka qarasa inda yake yaji a kashe,zai kuma ji dadi....me yiwuwa ka sabawa dokar aiki ka biyo ta inda ba wajen aikinka bane a lokacin aiki" mamaki fal saman fuskarsa yake duban wayar data miqo masa,bawai mamakin tsadar wayar ba,don ya jima rabon ma daya riqe waya mai qaramin kudi kamar ta,mamakin yadda ta bashi wayar kanta tsaye yake,baya manta sanda asma'u ta soma ganin wayar hannunsa,sanda ya bata wayar yace ta saka mishi numbers dinta,sai tada ci dariya sosai kafin tace
"Wai wannan waya ce?" Ya amsa mata da eh,ta bude baki kamar zata sake magana sai kuma ta fasa,ta miqa hannu a qyamace zata amshi wayar sai kuma ta fasa
"Karta bata min hannu da Allah,bari na karanto maka digits din" da toh ya amsa mata,ta dinga karanto masa yana sakawa,sai da ya gama lodawa sannan tace
"Pls duk sanda muke tare ka dinga qoqarin boye wayarka,kar daya daga cikin friends dina su gani ka zubar min da mutunci"


"Ke dame zakiyi amfani?" Ya katse tunaninsa ta hanyar tambayarta
"Karka damu dama ba wani abu nakeyi da ita ba,ina da qaramar nokia zan saka layina a ciki" hannu ya sake miqa wa yana cewa
"Kawo waccar to ko Allah zaisa ta gyaru" kai ta kada
"Karka damu.....akwai wanda zaizo anjima ya karba za'a gyara" sai ta soma takawa tana cewa
"Ka wuce karka yi laifi.....sai anjima ka gaida hajiya".


Ya dan jima a tsaye a wajen yana juya wayar a hannunsa kafin ya soma takawa yana barin layin zuwa layin da motocinsa ke jiransa,duk a tafiyar mamakin abinda tayi ne ya masa rakiya,ya dinga jujjuya halayyarta yana hadata data asma'u,bai manta ranar data ciro dubu daya guda ta bashi da niyyar biya masa bashi duk da batasan waye shi ba
"Irin wannan sharp sharp haka yau...."cewar mahmoud dake danne danne a system din dake saman cinyarsa
"ka manta ina kan hanyar aiken oga"ya fada yana murmushi sanda motocin suka soma dagawa suna barin layin zuwa saman kwalta,dariya mahmoud ya saki sosai sannan yace
"Allah ya shiryeka khalipha....Allah ya nuna min ranar da qaryarka zata qare" bai amsa mishi ba sai wayar data bashi daya zaro ya jefata inda yake ajiye ajiyensa cikin motar,yana shirin maida locker ya rufe sai ya cireta kuma daga ciki ya hadata da wasu dacument nashi da zaije gida da su.


Wayarshi ya dauka bai ko saurari zancan da mahmoud ba ya soma duba miscal din da ya tarar,sai daya gama sannan ya lalubi wata number mai dauke da sunan anty ruqayya akai,tana shiga aka daga ba tare da jinkiri ba
"Manya.....yanzu nake shirin nemanka ai" murmushi ya saki sannan yace
"To ya akayi....ya

Please Login or Register in order to submit comment