Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

sonyi saboda idan ya dawo din sai ya rasa abinda zaiyi.


Da wannan tunanin ya samu da qyar ya kurbi tea wayarsa na hannunsa yana ci gaba da gwada lambar ayshan saidai koda ta shiga ma ba'a amsawa.


Daga bangaren aysha kuwa basu jima da gama waya da ummi ba ta wayar anni taji mararta da bayanta sun soma riqewa da ciwo kadan kadan,saita zaci fitsari ne ya cika mata mara,hakan ya sanya ta shiga bandaki don tayi,saidai fitsarin duka ba wani mai yawa bane tayi ta dawo ta sake kwanciya,a hankali ciwon ya soma qara yawa,tun tana daukarshi kadan har ya soma matsa mata ta miqe ta fara safa da marwa,daidai lokacin da baba atika ta shigo dakin,donko anni bata shigo da kanta ba zata turo baba atikan,bata taba bari tayi minti talatin ba'a dubota ba
"A'ah uwar masu gida kardai abunne ya taso?"
"Wallahi ban sani ba baba atika,marata ce ke ciwo kamar zata tsage" ta fada tana yarfe hannunta
"A'ah,bari na sanar da hajiya" baba atika ta fita da hanzari don shaidawa anni,saidai kafin a gyara mota a fito da kayan haihuwa ciwo ya kankama tafiya ba zata yiwu a wajen aysha ba,tilas aka haqura anni tabar baba atika a dakin,don sam kunyar annin ta hana ayshan ta sake sosai dole ta fita ta barsu a dakin,saidai bata matsa ko nan da can ba tana tsaye qofar dakin baba atikan na yu qurin ganin ta qarfafi ayshan ta tashi su qarasa asibiti,nishin data soma shi ya tabbatarwa baba atika haihuwa tazo,ta gyara wa ayshan zamanta tana qarfafarta tayi nishin don babyn ya samu ya fito,cikin ikon Allah nishi uku kacal kukan jaririyar ya karade gidan
"Alhamdulillahi" anni ta furta murmushi mai hade da qwalla da na bayyana a fuskarta.


Dai dai sanda khaliphan ya saki nannuyan ajiyar zuciya yana sake gyara zamanshi,tsahon daren duka bacci yaqi zuwa idanunshi hakanan,so yake kota halin qaqa yau yaji muryan uwaishanshi,yasha attempting din kiran anni amma baiso ta gane laifi ya yiwa aysha taqi daga wayarshi,ayau kam yana jin an kai matakin da dole ya kira annin,idan ma fada zata yi mishi tayi masa indai zata hadashi da aysha yaji muryarta da lafiyarta,sai kawai ya danna lambar annin yasa handsfree ya ajeta a gefe yana jiran yaji an amsa.


Kukan babyn daya cika kunnenshi a sanda aka daga wayar shi ya sanyashi tashi tsaye cak kamar wanda aka yiwa allurar sojoji
"Allaaaaaahu akhbar" ya ambata,ko ba'ace masa komai ba,ko ba'a gaya masa ba yasan cewa tabbas wannan jininsa ce,diyarshi ko diyanshi ne yau ya shaqi iskar duniya
"Khalipha,yau Allah ya albarkace da samun diya mace"
"Alhamdulillah,Alhamdulillah anni hajar ta dawo"
"Ma sha Allah" ta fada tana jin dadi har cikin ranta,tana jin kewar diyarta da tuna mutuwarta
"Anni ya humaira take?"
"Tana lpy atika tana shiryata"
"Alhmdulillahi ya dinga maimaitawa sai anni ce ta kashe wayar,kasa zaune yayi ya kasa tsaye,cikin lokaci kadan ya soma turawa 'yan uwa da abokan arixiqi cewa ya samu qaruwa,nan da nan saqonni suka dinga shigo masa ta ko ina,duk yadda yaso jin muryar ayshan anni taqi hadasu tace saita huta,kamar zaiyi hauka,har kusan kuka ya yiwa annin amma ta shareshi.


Sanda anni ta shiga dakin an gama shirya baby da mamanta tsaf,tuni babyn ta shiga bacci,bismillah anni tayi ta dauketa idanunta kan kyakkyawar fuskar yarinyar,khalipha sak haka ta gani,kamar sanda ta haifeshi,komai nata irin nashi ne hatta da yatsun qafafunta,
"ma sha Allah,Alhamdulillahi"Qaunar yarinyar ta ratsata lokaci guda,fuskarta qunshe da murmushi ta dubi aysha dake zaune tana shan tea mai zafi
"Sannu indo aysha"a kunyace ta amsa ma annin
"Allah ya albarkaceta,ya qareku da lafiya,ubangiji yasa cikon musulunci ce"
"Amin" ta furta can qasa yadda annin ba zata ji ba,saboda kara da kunya,
"Ki huta zuwa anjima sai muje asibiti a dubaki da kyau a tabbatar komai lafiya ko?,sai......" Bata kai aya ba kiran khalipha ya shigo wayarta,wannan shine kusan kira na bakwai da ya yiwa annin
"Ungo,karbi mijin nan naki,na tabbatar idan ba bakin nayi ba bazai taba qyaleni na huta ba" ta fada ta ajje mata wayar gefanta,sannan ta dora babyn kusa da ita ta fice a dakin tana kiran baba atika.


Tana kallo sai daya kira kusan sau uku sannan ta daga,kiran sunanta ya fara yi sai tayi fakare dashi kaman bata jiba
"Nasan kina jina uwaisha,na godr,amman don Allah kowanne hukunci zakimin kimin amma banda hanani jin muryarki naji lafiyarki" har ga Allah har a sannan ranta adan bace yake dashi,baisan yadda take kishinsa bane shi yasa ya gaya mata haka
"Me kakeson nace?,kai da zaka auro amarya tunda ni na haihu na tsufa?"
"Wayyo uwaisha don Allah karki sa na kasa bacci yau.....am sorry uwaisha bana son abinda zai sa mu raba muhalli dake uwaisha....yanzun haka wallahi bazan iya zama ba dole na sake biyo jirgi nazo na ganku keda baby na" idanunta ta lumshe,har abada tana alfahari da soyayyar da yake mata
"Ya jikin naki ina baby na dawa tayi kama?" Ya furta cikin sanyin murya dake nuna zumudi zallah
"Dani tayi kama" dariya ya qyalqyale da ita cike da nishadi
"An gaya miki ni rago ne?,to na sani nita debo komai da komai,kina kishi ne ko?" Saita tura baki kamar yana ganinta
"Nida wahala kai da kwashe kamannin" dariya ya kuma yi sosai wanda hakan ya sanya nishadi a zuciyarshi
"Tukunna ma,duka sauran wadanda zasu biyo baya ki zuba ido zaki gani",tun tana sharewa har ta saki jiki sosai,kafin suyi sallama sai daya wanke kanshi fes da soso da sabulu.


Zuwan aliya shiya katse musu hirar dole ba don sun gaji ba,aliya murna kamar tayi me
"ke bamusan kin dawo ba sai labarin haihuwa muka ji"
"Hmmm,kedai bari aliya,kwana ma biyu fa da dawowa,Allah nema yayi bazan haihu ba a can" tare suka zauna da ayshan,ranar haka baqi suka dinga tittudowa,toh abinka da idan kana dashi anayi dakai kowa burinsa yazo yaga jaririya,wasu soyayya ta domin Allah wasu ta abun hannun iyayenta,a ranar ummi ma bata iya kara ba sai datazo da dukka yaranta,basma ta qanqame babyn tana cewa itakam anan zata zauna sai anyi suna,ranar anni da ummi sunsha hira sosai,yawan baqin ya sanya basu samu damar zuwa asibitin bama sai dare,alhmdlh komai lafiya ita da babyn,sai magunguna kawai da suka rubuta mata don qarin lafiyarta,suka siya suka dawo gida.


Washe gari saiga hanan da mmn hunaifa,ranar kam an sha hira sosai,sunyi missing aysha,karatu yanata gangarawa
"Ai dama na fada wallahi,irinku su aysha sumumu kasau din nan baku iya soyayya ba,sai gashi ke data tashi damqarki ma karatun kika aje gaba daya" hanan ta fada tana hararar aysha cikin wasa,dariya aka sanya gaba daya,mmn hunaifa tace
"Ni banga laifinta ba,nima don bbn hunaifa keso,da zaice nima na aje jewar zanyi".


Da azahar saiga mummy abun mamaki harda asma'u,duban tausayi aysha take musu su duka,don duk wanda ya kallesu yasan rayuwa bata gara musu kamar da,duk sai ayshan taji ta tsargu,kaman ta zubda su duk da cewa basa sati basuyi waya da mummyn ba,ran aysha saiya koma duka a bace,har suka gama yi mata barka suka tafi,asma'u tace sai ranar suna mummy kuma tace sai gobe zata dawo.


Kafin washegarin ta sanya daya dags cikin yaran khalipha ya mata bincike kan halin da ake ciki,rashin tattali ya sanya sun sanya su mummy sun sanya gadonsu a gaba sun cinye sai d'an abinda ba'a rasa ba,sai kuma abinda su anty safiyya ke taimakawa mummyn dashi,asma'u kam nata juyawa take,dashi suke kashe buqatun kansu ita da hamid din,don a yanxu ya koma ya zauna,bashi da wata qaqqwarar sana'a,da kanta ta cira kudi cikin accnt dinta wanda ita kanta tasan ba qaramin kudade bane a ciki tayi musu siyayya,don khalipha ko riba ya samu mai yawa a wani harkan saiya fitar mata da wani abun,dukkan wani abu da tasan sun rasa saida aysha ta tabbatar sun sameshi,hakanan ta qarawa asma'un jari yadda zata riqe kanta sosai,kunya ta kama asma'un har taso taqi amsa amma ayshan ta turje
"Ni kamar 'yar uwa na daukeki anty asma'u,qin karbarki bashi ne zaimin dadi ba" hawaye ta dinga sharewa tana kada kai
"Ban cancanci naci arziqinki ba ko wanne iri aysha,bansan ma ta yaya zance ki yafemin ba"murmushi aysha tayi saboda dama tasan abinda ke cinta kenan
"Karki taba sawa a ranki kinmin komai,koma me kike tunani yanzu ina yake anty asma'u,koma meye ya zamemin silar alkhairi,ya zamemin silar haduwa da mijin da samun kamarshi sai an tona,na yafemiki kome kika yimin duniya da lahira" hakanan ta amsa tana mata godiya gami da jin kunyar kanta kan dukkan wani abu data aikata,bata taba zatan cewa a rayuwa wataran wanda kake samanshi zai iya zamowa shine a samanka kai a qasanshi,koda yaushe ka zama mai kyautata mu'amalarka saboda babu wani abu dawwamamme.


Ba zato saiga khalipha ya sauka ranar suna da yammaci,yazo ganin little hajar,wanda ake kira da farha,aysha na cikin jama'a amma sai daya sanya aka kira mishi ita,hadasu yayi duka ya rungume ita da baby farha yana ajiyar zuciya,sai daya dauki a qalla mintuna biyu a haka sannan ya saki ajiyar zuciya yana dagata daga jikinsa yana fadin
"Alhmdlh,Alhmdlh" yana kissing dinta a goshi,murmushi ta sakar masa tana masa sannu da zuwa,a qalla saida ta kusan kashe awa biyu a wajensu yana kallonta kawai baby farha na wajensa,ga jama'a daketa tururuwar zuwa suna anata nemanta,da qyar da sudin goshi ya barta ta fito bayan anni tasa baki,tare da alqawarin gobr xasu wuce gidansu.


Taro ya tashi lafiya baby hajar farha tazo da goshi da alkhairi mai tarin yawa,washegari da magariba ta shirya tsaf ita da farha suna zuba qamshi suka wuce gidansu,suka bar anni da yasmin 'yar anty ruqayya da aka kawo mata.


Baby farha nada wata biyu yace zasu koma ya kammala jarrabawarsa,da fari anni taso yabarsu a gida yaje yayi ya dawo,amma daga bisani ya gaya mata akwai yiwuwar zamanshi a can hakanan suka tarkata suka tafi kowa na kewat baby farha,sun zagaya sallama har takai,zuwa wannan lokacin inna yelwa ta sake sanyi qwarai,ta tabbatar jahilci ya taka muhimmiyar rawa wajen faruwar dukkan abinda ya faru,khalipha bai tafi ba sai daya assasa islamiyya can garin ta matan aure da yara,wanda ya dauko ingantattun malamai masana sunnar Allah da ma'aiki suka hau koyar da al'ummar garin ka'in da na'in,suka yi nasarar yaqar duk wani baqin tunani,da baqar alaqa da dangantaka dake tsakanin fulani da manoma,basu bar qasar ba sai da aka sanya ranar aliya da mahmoud,wanda ya matsa qwarai yana ganin kamar zai rasa aliyar ne ko kuma taqi bashi dama.


Ta bangaren haidar ma tunda yaga basma ya soma kai kawo,wanda daga qarshe ya bayyana muradinsa,ayshan dai batasan ya ake ciki ba har suka bar nigeria zuwa cyprus.


Randa zasu tashin suna tsaka da shiri aka ce ana sallama dashi,hakanan ya fito bai kammala shiryawa ba don yayi mamakin wanda ke nemansa a irin wannan lokacin ya fito zuwa falon da yake ganawa da baqinsa.


Kawu hamza,kawu munzali,kawu habibu da kawu saminu,dukkansu suna zaune qasan tile din dake malale a dakin,suna zaune tsumu tsumu kamar wadanda aka tsoma kaza cikin ruwa,kallo daya zaka yi musu kasan cewa dukkaninsu suna jin jiki na rayuwa dana abinda suka aikata.


Dubansu yake yayin da kowa ya gyara zama yana miqo gaisuwa,amsa musu yayi kadaran kadaham kafin shuru ya biyo baya an rasa wanda zai soma magana a cikinsu,kawu saminu ne yayu qarfin halin soma neman musu yafiyar khalipha,don dukkansu mutuwar idris ta zame musu izinina,daga qarshe ya rufe
"Haqiqa shaidan ya taka muhimmiyar rawa wajen yi mana huduba,da banzayen zukatanmu marasa son Allah,muka bijire muka kwashe dokiyoyinku muka cinye,sannan uwa uba muka kasa kula daku muka yiwa mahaifinku butulci,mutuwar idris kawai ta isa ta nuna mana makomarku matuqar baka yafe mana ba kuma bamu nemi yafiyar Allah ba,iya halin da muke ciki ma yanzu kawai munga ishara babba,bamu da nutsuwa cikin gidajenmu da rayuwarmu,yaranmu duka kowanne da tashi matsalar Allah ya jarrabemu,ka daure badonmu ba badon halinmu ba ka yafe mana"


Iska mai zafi ya furzar da ita daga bakinsa yana qoqarin controlling kanshi,tsahon mintuna biyar shuru ya ratsa falon
"Allah ya yafe mana gaba daya" dukkansu qwalla suke sharewa suna godiya,yana tsaye yana kallonsu har suka gama ficewa daga falon sannan ya juya ya koma ciki,zuciyarshi cike fal da tunani kala kala,rayuwa ita haka take,dukkan yadda ka dauketa haka take zuwa maka,mafitarka daya kabi Allah kabi dukkan dokokinsa.

60


*_BAYAN SHEKARA GOMA SHA BIYU_*



Misalin sha d'aya na safe jirgin dake dauke da iyalan muhammad khalipha sa'id mai goro ya sauka a filin sauka da tashin jiragen sama na malam aminu kano dake kano.


Yarinya ce 'yar kimanin shekara goma sha uku ce a gaba riqe da hannun wani yaro d'an kimanin shekara biyar,bayanta wata matashiyar macace fara tas mai matsakaicin tsayi da dogon hanci,wadda kana mata kallo d'aya zaka tabbatar da cewa hutu jin dadi da gayu sun ratsata take biye da ita,fuskarta qunshe da murmushi wanda hakan ya bayyana dimple dinta dake kumatunta na hagu da dama,tana dauke da wani kyakkyawan yaron wanda baifi shekara uku ba,sak kamanninsa na muhammad khalipha ne mai goro,shine ya fito a qarshe yana ruqe da qananun akwatina masu kyau guda biyu,shima fuskarshi na dauke da murmushi da alama magana suke da uwargida sarautar mata ayshatu dake gabanshi
"Farha....oya bani jawad ki amshi trolly dinku" da gudu jawad ya zame hannunshi daga na farhan yana tawowa wajen aysha,harara khalipha ya jefawa aysha mai nuni da zallar qauna
"Hajar din zan baiwa daukan akwati?" Murmushi ta saki don dama ta sani hakan zata kasance,wata qauna yakewa yarinyar tamkar hajar dinsa,haka suka dinga takowa har zuwa inda motocin MAI GORO suke jiransu.


Dukka qofofin motocin a bude suke suna jiran isowar boss din nasu,suna hangosu a hanzarce suka amshi akwatunan hannunshi suka shige mota guda shi da iyalin nashi gaba daya.


Kwabe fuska jawad yayi yana duban aysha
"Anna...ba gidan anni zamu fara zuwa ba?"
"Ban sani ba tambayi abbinku" ta fada tana gyarawa fu'ad kwanciya a jikinta,duban khalipha yake yana son magana yana tsoro,saboda last time da sukazo yace ba zasu sake zuwa su kwana wajen annin ba,saboda yadda suke qiriniya da rashin ji idan sunje,yace ba zasu hana uwarshi hutawa ba,itama farha kallon abbun nasu take,ita kanta tafison gidan annin,saboda tun suna can sunyi waya dasu amra da afaf (jikokin annin yaran basma da haidar,da 'yar mus'ab),Dukkansu suna can gidan anni suna hutu daga kai khalipha yyi ya kallesu sae ya maida kai baice musu komae ba jawad ne yakasa shiru murya a sanyaye yace pls abbu akaimu gidan ammi munyi alqawarin bazamu sake pitina ba baice mishi komai ba ganin hakan shima yaron yaja bakinshi yyi shiru.


Cikin yan mintina suka isa kataparen gidansu dake nasarawa meela road tanpatsetsen gidane da khalipha ygina da yadauki shekaru yana ginashi mention house ne nagani napada a parking space duka motocin suka tsaetsaya su jibiril sukaxo suka bude musu qopa taxuro qaparta xata pito daga motar wayarta ta soma ringing saeta dakata da pitar takira farha ta daukar mata fu'ad duba mekiran tayi inna yalwa ce sae tayi mamaki data ga number nigeria da alama ta dawo gida kenan daga jinyar qaparta da khalipha yapitar da'ita saudiyya sagas a tayi tasa akunnenta gami dayin sallama dagacen bangaren inna yalwa ta amsa
"nayi sa'a kardae kice min kindawo?" Murmushi Aisha tayi gami dacewa "nima yanzu a raina nakecewa ashe kindawo"
"Eh wolh kwanana biyar kenan da dawowa ta"
"Toh yaya jikin"
"Jiki alhmdulilahi nasamu sauqi, kitayani yiwa allaji khalipha godiya Allah yasaka da alkhairi,ya qara budi"
"Amin ai babu komai,cikin satin nan ma zamu shigo takai din in sha Allahu,su mero zasu tare sabon gidansu"
"Ma sha Allahu...an gana kenan?,ke dai indo babu abinda xamu ce dake saidai godiya da fatan alkhairi keda halipha,kaf karkarar nan babu wanda baici arxiqinki ba,babu wanda arziqinki dana mai gidanki baibi ta gidansa ba,Ashe haka rayuwa take,bakasan wanda zaka ci arxiqinsa ba....ki yafemin indo bazan daina neman yafiyarki ba har abada..." Ta qarashe maganar cikin rauni da nuna nadama
"Kai inna,ya wuce fa,sai munzo din"
"Allah ya jiqan mahaifinki indo,ki gaidamin da masu gida na da kishiyata"murmushi ta saki
"zasu ji" ta fada tana kashe wayar ta maidata jaka sannan ta qara fitowa daga cikin motar,zuwa sannan tuni khalipha da sauran yaran sun shiga ciki don haka tabi bayansu a nutse,cikin taku na cikakkiyar mace mai ilimi wadda tasan abinda take,wadda ta gogu da ilimi da zaman duniya.



Bata shiga ciki ba sai data kira mummy bayan ta kira ummi ta sanar mata dawowarsu,ta tabbatar da komai na tafiya lafiya cikin sabon gidan da khaliphan yayi musu,ya dauke shima dukkan wata lalura ta mummyn,don daddy wani mutum ne mai muhimmanci shima a rayuwarshi,bazai taba manta alkhairinsa ba a gareshi,tun daga ranar da yasan abinda ke faruwa ya amshe duk wata dawainiya da da ayshan ta akarba yaci gaba da jan ragamarta,zuciyar khaliphan mai kyau ce,ya manta dukkan wata cuta da wani mai cuta yayi masa,ya rama kowacce cuta da alkhairi,hakan yasa itama ayshan ta qara qaimi,taci gaba da kyautatawa duk wani wanda ya jibanceta na kusa dana nesa.


A nutse cikin nishadi da qaunar iyalin nata ta shiga cikin gidan,ba kowa a falon sanda ta shiga katafaren falon da xai sadaka da sassa daban daban na gidan,dakunan matar gidan,dakunan yaran gidan,ban dakuna,kitchen da kuma sashen baqi mata,sai sashen mai gidan,tunda bata gansu ba tasan ba zasu wuce dakin yaran ba,murmushi ta saki ta zare mayafin rolling dake kanta ta nufi kitchen din gidan don duba masu aikin gidan wadanda dattijan mata be guda biyu rak suke mata aiki,sai guda daya da batakai shekarunsu ba,a yanzu haka tasan suna can don sunsan da dawowarsu.


A mutunce suka gaisa,kai baka ce 'yan aikinta bane,ta dudduba abinda sukeyi sannan ta gaya musu abinda zasu dafawa yara da abinda zasu hada mata wanda zata shigo da kanta ta yiwa khalipha girkinsa.


Daga nan dakin yaran ta nufa,dakin farha na bude saidai labulen a sake yake,budewa tayi ta tura ta shiga don ta dubata,qarar ruwa taji a toilet hakan ya sanya ta saki murmushi tasan wanka take kuma da alamun da qyar idan ba gidan annin zai kaisu ba,ficewa tayi daga dakin ta shiga nasu fu'ad,yana zaune saman gadansu dukka yaran daure da towel,da alama wanka yayi musu,don ga kayansu nan saman gadon yana feshesu da turare,saita samu gefan gado ta zauna kawai tana kallonsu,tamkar yaya da qannenshi,tamkar abokanshi haka wani lokaci yake mu'amala dasu,shi yasa zata iya cewa sunfi sonshi fiye da ita,kusan dukkan wata hidimarsu bai gajiya idan har yana qasar ko yana tare dasu shi yakeyi musu,hakan ya sanya yanzun ma tayi tagumi kawai tana kallonsu tana jin hirarsu da dararrakunsu,a haka ya kammala shiryasu tsaf dai dai sanda farha ta shigo,tayi kyau cikin shadda bubar har qasa yellow mai red din stone work,shigen kayan dake jikinsu jawad yellow and red
"Good qanwata(wani lokaci yakan kira farha da haka),kinfi kowa yin kyau" murmushi ta saki cikin jin dadi,yana son yarinyar sosai saboda kama da take dashi sosai ita da jawad,jawad din ne ya tabe fuska
"Abbi.....abbi" yana langabe kai,yasan me yake nufi saboda haka ya shafa kansa
"Bakaga yadda kayi kyau ba my twinny(shima hakan yake kiransa wani lokacin saboda kamarsa da shi)" sunan yana yiwa jawad dadi sosai,saboda haka ya saki murmushi shima yana sakewa farha gwalo a boye,duka takai masa ya boye bayan khalipha
"Abbi....gwalo yakemin"kamo hannun jawad yayi ya dawo dashi kusa da ita ya kama hancinsa ya dan riqe
"Bana son tsokana,bata haquri" baki a tabe ya bata haquri,shi kuma ya juya ya kallo farha
"Ke kuma big sis ce.....saikinyi haquri" kaman xatayi kuka tace
"Hademin kai suke fa shida fu'ad abbi....."
"Qyalesu qanwata.....ki cewa anna ta samo miki 'yar uwa kinga kema kin huta"juyawa tayi bangaren da aysha take tana kallonsu,hannayenta ta hade waje guda,alamun roqo,dan hararar farha tayi kadan saita juya kaman zatayi kuka ta kalli khalipha ta daga kafadunta dukka biyu tana tabe bakinta tana nuna mishi alamun ayshan taqi,shima narkewa yayi ya mata alama yayi mata na abun tausayi ya girgiza kai yana duban ayshan
"maman yara....pls a taimaka mana a sake bamu baby girl" dubanshi tayi ta masa signa da ido na yadda yaran sukayi shuru suna jiran amsar ayshan,ta rasa yadda yaran keda shegen son yara,hatta da fu'ad da bai wuce shekara bakwai ba idan yaga yaro ko yarinya,sai kawai ta miqe ta fice a dakin tana murmushi qasa qasa.


Kayan jikinta ta fidda ta soma daura towel,tana tsaka da daurawar taji ya rungumota ta baya,amsar daura towel din yayi tana rungume a jikinsa yana daura mata kanshi saman kafadarta yake cewa
"Kinqi kawo mana agaji nida yarana ko?" Murmushi ta fitar kawai bata ce komai ba,yana gama daura mata ya birkitota gaba daya suna fuskantar juna,yana shaqar qamshin turaren jikinta,idanunshi cikin nata yana mata wani kallo mai tafiyar da xuciya
"Da gaske muke annah....muna son yara ba zaki agazo mana ba" hannunta ta dunqule ta dora a qirjinta tana murmushi
"Allah ya kawo abbi" dan jim yayi sannan yace
"Ameen....muje in wanke matata" cak ya dagata yana takawa a hankali tana dariya tace
"Abbi baka gajiya?,ka wanke yara ka wanke mamansu?" Murmushi ya saki
"Dama ce....ai ina da cikakken time ne,idan kuma ban muku hidima ba wa zan yiwa?" Shuru tayi tana gyada kai cike da jin dadi da hamadala ga Allah.


Sai daya sakata cikin bathtube ya juya ya fice yana cewa
"Ina zuwa" minti daya sai gashi ya dawo,tare sukayi wankansu sannan suka fito,tsaf suka shirya,shi ya bata wasu kaya wanda kalarsu daya da nashi da kuma na yaran,shadda ce irinta farha,tana ta tambayarsa me ake ina zasu baice mata komai ba yace su zuba ido zata gani.


Cikin sabuwar motarshi fara qal suka shiga suka bar gidan,ita dai tanata zuba ido,basu sauka ko ina ba sai gidan anni,sam bata gane meke faruwa ba sai da suka shiga cikin gidan,tafkeken falon annin cike yake da decoration da kayan ciye ciye da qyale qyale,matar mus'ab,basma qanwarta kuma matar haidar da yaransu gaba daya a falon,suna shiga dukka qwayayen dake falon masu dauke da kaloli suka kama,wasu rubutu suka bayyana,ta daga kai tana karantawa,sai a sannan ta gane me yake nufi,murnar cikar aurensu shekara goma sha hudu cif cif dayi ya hada musu.


Sun jima a gidan annin ana sada zumunta gami da ciye ciye da shaye shaye,dukkan familyn kana ganinsu kasan cewa cikin farinciki da walwala suke,basu tashi barin gidan ba sai bayan sallar magariba,tun kafin a soma maganar tafiyar dama su jawad suka soma nacin a barsu gidan annin,dama ya shirya hakan saboda haka yace su zauna din,har sun miqe suna mata sallama ta dakatar da khalipha
"Auren amal ya taso fa,inatason gaya maka ita da zeenatu za'a hada" dan sosa kunnenshi yayi kadan sannan yace
"Yanzu ya za'ayi anni?"
"Dukkan abinda ya dace yanda ka yiwa maryam"
"To shikenan ba damuwa.....za'ayi duk abinda ya dace in sha Allahu"
"To Allah ya taimaka ya yiwa dukiya da rayuwa albarka"
"Amin ya Allah anni,amin" da haka suka juya zasu wuce,babban yaron haidar affan dake zaune waje daya yana cin abinci khalipha ya kalla
"Affan ya jikin dai?"
"Da sauqi abbi"
"Ma sha Allah Allah ya qara lpy"
"Amin" ya amsa mishi
"Anty na asha amarci lafiya" fatima matar mus'ab ta fada qasa qasa tana dariya,hararta aysha tayi,sosai jininsu ya hadi da fatiman,tana girmamata kamar yadda basma take

Please Login or Register in order to submit comment