Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ake ciki?"
"Komai ya kammala,yaushe zaka shigo ka gani?"
"Ba lokaci anty....amma zan duba idan na samu chance zan shigo"
"To shikenan...ka cema anni inata kiran layinta bai zuwa"
"Annin?" Ya tambaya yana dan fiddo ido kaman yana gabanta
"Bari na dubata" ya sake fadi da sauri yana katse kiran,kai tsaye annin tashi ya kira,ba jimawa kuwa ta daga ,ajiyar zuciya ya saki har sai data jiyoshi
"Ya akayi khalipha?,lafiya dai ko?"
"Anty tace tayi kiranki bata sameki ba...." Murmushi ta saki mai dan sauti,tasan ya kira ne yaji da gaske ne ko kuma wani abu ne ya faru
"Sharrin qarfen nasara ne....amma wayar a kunne take"
"To alhamdulillah....sai na dawo"
"Allah ya tsare"
"Amin" ya amsa yana jin dadi har cikin ransa sannan ya aje wayar.


"Wai me aka shirya mana ne?" Mahmoud ya sake tambayarsa lokacin da yake laluben number jibril jagoran tafiyar tasu zai tura masa texs
"Name fa?"
"Biki mana....kana nufin ba zamu gwangwanje ba?" Wayar ya aje bayan ya gama tura masa inda zasu yana murmushi
"Kasan wani abu ne mahmoud?....yarinyar ba irin sauran 'yammata bace ba....tayi universty amma saika zaci 'yar secondry ce...akwai ciwo a rayuwarta da yake hanata sukuni....,saidai ina fata haka halayyarta take bawai plan bane....saboda mahaifiyata mahmoud bana son abinda zai taba mahaifiyata" kai mahmoud yake jinjinawa cikin nazari sannan yace
"Na yadda da kai khalipha....kana da zuciya da mu'amala mai kyau,in sha Allahu ubangiji bazai bari wani ya cutar da kai ba.....yanzu yaushe za'a kaini wajen amarya?"
"Zaka iya saka kayan gwanjo?"
"Kai....kai ina....bazan iya ba magana ta gaskiya,ina laifin cikin kaya na na lalubo mai sauqi sauqi" harara khalipha ya watsa masa
"Sai kasha zamanka...don dama koni bata gama sabawa da ni ba"
"Aurenku na bani mamaki.....karon farko da na taba ganin auren da akayi babu soyayya tsakanin ango da amaryar amma duka sun amince zasu zauna da juna" ya fada yana dariya dariya,murmushi ya saki khalipha idanunshi na kallon titi
"Kawai abinda na sani shine....zan aureta ne a matsayin taimako da kallonta da nake kaman qanwata dana rasa a baya,zan aureta don in canza mata family...zan aureta don in bata farincikin da iyaye ke baiwa 'ya'yansu koda ba duka ba nasan zata samu wani bangare daga wajen anni....ina mata kallon qanwa ne bawai matar aure ba...koda na aureta zan bata 'yancin rayuwa irin na budurwa....saidai zan tsare mata mutuncinta"
"Zai yuwu?" Mahmoud ya tambaya yana kallonshi
"In sha Allah" shima ya bashi amsa bayan ya waiwayo sun hada idanu,kafada.mahmoud ya daga bayan ya danyi nazari kadan sannan yace
"Well....Allah ya bada nasara" bai amsa masa ba saboda sun iso wajen da zasuje din,babban wajen siye da siyarwa ne wanda ba nau'in suturar da basa saidawa masu kyau da tsada na qasashe daban daban,a wajen dukka motocin sukai parking,suka dunguma zasu bishi ya dakatar da su sukayi gaba shi da mahmoud da jibril sai nasir.


"Khalipha....khalipha" yaji ana ambaton sunansa da sauri sanda yake gab da shiga wajen sautin kuma na sake matsowa inda yake,cak ya tsaya sannan ya waiwayo a nutse yana duban inda kiran ke fitowa,zulaihat ce ke takowa cikin sauri idanunta a kanshi tana qare masa kallo
"Ashe haka khaliphan yake?" Abinda take ayyanawa kenan a ranta,wani irin kyau da kwarjini na musamman taga yayi mata
"Lallai talauci masifa ne...ko siffarsa ka ara saiya sauya maka kamanni bare ya kamaka da gaske" ta sake fada sanda take qarasowa inda yake tsayen,tana qarewa motocinsa da suka faka a wajen kallo a dabarance,saidai ta makara,gwani ne wajen saurin karantar mutum wannan baiwa ce da Allah yayi masa,duk kuma wanda ya dan jima tare da shi yasan da hakan,da idanu ya yiwa su jibril alamar su shige,yayin da ya zuba mata narkakkun idanunshi hannayensa zube a aljihun wandonsa,idanunta ta dan kautar saboda kaifi da sukayi mata,kyau da kwarjininsa suka cikata,zuciyarta ta karye har cikin ruhinta tana jin haushin wautar data tafka,da tuni yanzu wannan nata ne,da tuni mallakinya ne inda ta iya mallakar kanta ta boye zalamarta
"Yanzu muhammad haka rayuwa take don Allah?" Ta fada bayan tayi namijin qoqarin tattara dukkan qarfin halin da take da shi,bai amsa ba yadai ci gaba da kafeta da ido,ganin baida alamun amsawa ta sake hada wasu kalaman duk da ta soma karaya saidai tana fatar haqanta ta cimma ruwa
"Ba wanda baya kuskure fa....kuma ni banyi da wata manufa ba...kawai dai kuskure aka samu" ta qarashe maganar cikin lanqwashe murya tana duban cikin idanunsa da wani salon kallo da take fatan ta tafi da hankalinsa,saidai ko gezau,mahmoud ya soma tabashi kadan yana son samun qarin haske ko kuma shi khaliphan yace wani abu,sai a sannan ya dauke idanunsa daga kanta,yana murmushi can qasan ranshi mamaki na sake rufeshi....yana kuma sake baiwa kansa yaqinin babu soyayyar gaskiya a doron duniya...idan ma akwai tayi da nisan da ba kowanne dan adam ke iya kamota ba,hannu ya dagawa mansur daya daga cikin yarashi,ya gane me yake nufi,saboda haka ya tako ya iso gabanshi da jakarshi ya budeta sannan ya miqa masa,hannu ya saka ya bude,kudi ne sabbi a miqe suka bayyana,bandir biyu ya ciro ya sannan yace masa ya rufe jakar,rufewar yayi sannan ya juya da ita ya bar wajen
"Sau daya dama take zuwar ma wani mutumin a rayuwa...kuma hakan ce ta faru da ke" hannunsa ya miqa a nutse ya soka mata kudin jikin jakar hannunta dake maqale a gwiwar hannu yana murmushi
"Ina fata wannan ya zama karo na qarshe da zaki nuna kin taba sanin khalipha a duk inda zaki ganshi....ki huta lafiya" ya fada yana juyawa mahmoud ya bishi a baya ba tare da yace komai ba.


Qwallar da suka cika idanunta sai a sannan suka silalo,kunya ta cikata na mutanen dake wucewa jifa jifa ta inda suke tsaye,gefe guda baqinciki da tarin takaici sun cikata...ba wannan take so ba.....muhammad takeso ya dawo yaci gaba da sonta kamar yadda suke a baya,ya kuma aureta burinta ya cika.


"Ban taba sonta ba.....da fari nagartar ta da na gani a fuska ita ta soma jana....ga zatona zamu dai daita daga baya na koyawa kaina yadda zan sota.....ashe ma tafiyar ba mai nisa bace" ya fada a taqaice wanda yasan ya isa amsa wa mahmoud,saqon ya isa kuwa,don ya gane daya daga cikin yammatan daya nuna yana so ne a baya,ba shakka ya tabbatar batasan waye khalipha,idan yabar abu ya barshi kenan har abada bai waiwayarsa,yana da sauqin kai tausayi da son jama'a,saidai baison yaudara da ha'inci,indai kana son tafiyarku da shi tayi tsaho tilas ka kiyaye wadan nan,sau tari idan ka karanceshi bai bai zaka daukeshi a mara kirki..kuma mutum mai tsauri da dokar tsiya,saidai yafi komai dadin zama da sauqin kai idan ka fahimceshi.


Bai wani jima a ciki ba,kaya ya zabarwa anni kamar yadda ya saba duk bayan wani dan lokaci,ya biya da kanshi kamar yadda bai yadda wani ya yiwa annin siyayya saishi ya dauko kayan da kanshi suna hira da mahmoud jifa jifa suja fito suka bar wajen.

*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*


*DAURIN BOYE*
_SAFIYYA HUGUMA_

*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_

*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_

*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_

*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_

*GA WANDA KEDA BUQATAR SAYENSU SAI YA TUNTUBI WANNAN NUMBER*
08030811300


22



Ta kowanne bangare daya shafi asma'u hidima ake tuquru ta bikin autar mummyn,babu wata rana da zata fito ta fadi ba'a tsara wani abu dangane da shirin bikinta ba, tamkar mummyn zata aurar da yara uku haka take ji.


Tun saura sati hudu bikin mai gyaran amare ke zuwa gidan,takanas mummy ta biyata kudin sati hudun take zuwa take gyara asma'un,cikin qanqanin lokaci kuwa ta sake wani kyau,fatarta tayi fes kyanta ya sake fitowa,duk wannan hidimar da ake dai dai da sau daya ba'a taba karar tsoma aysha a ciki ba,itama kuma duka bai cikin lissafinta,don sam tasama ranta aurenta ba irin nasu asma'u bane,irinta yaran gata su ya cancanci suyi irin wannan hidimar.


Kullum ta kwanta fatanta da burinta daya Allah yasa umminta tazo bikinta...Allah yasa a wannan karon umminta ta kulata...Allah yasa umminta zata rungumeta wannan karon a jikinta taji duminta kamar sauran yara,zuciyarta takanyi fari tayi haske a duk sanda wani sashe na zuciyarta ya bata qwarin gwiwar koya hasaso mata kanta kwance a cinyar ummin tata suna hira.


Tun biki saura sati uku aka je ganin gidan,gidan asma'u aka soma zuwa,itadai aysha ba'a gayyaceta ba saboda haka bata je ba,bata ma da sha'awar zuwa,don kullum sake jan jikinta take da gujewa duk wani abu da zai iya zama laifi,ta dai zauna gida tayi abincin baqi,sanda suka dawo nan falo suka baje suna hirar irin gidan alfarma da hamid ya ginawa asma'un,itakam tana tsakiyarsu tana hura hanci farinciki kamar ya kasheta,dama tasan duk wanda yaje yaga ginin sai ya yaba kafin ma akai gayi mata jere,don kusan lokaci lokaci yana daukarta suna zuwa ganin ginin abinda baiyi ba tayi magana a rushe a sake maida mata yadda takeso da haka aka kammala ginin,wanda kafin a gama din ba qaramin hasara aka dinga yi ba saboda an rushe gurare da dama an sauya da wasu plan din.


Kwana biyu tsakani mummy ta sameta a kitchen a sannan tana hadawa daddy abincin dare kamar yadda take lokaci lokaci akai akai musamman idan 'yar mulkin ta sakar mata mara ranar babu abinda ta sakata dafawa
"Ya kamata ki yiwa wancan yaron magana me yake da suna?....za'a je aga inda zaku zauna saboda asan yanayin kayan gadon da za'a siya,kada a siya kuma azo ayi asara,suyi yawa ko suqi shiga"
"Toh mummy" ta fada kawai,ita batasan ma ya ake cewa ba,batasan ta yadda zata gaya masa wai za'a je ganin waje ba.


Har washe gari bata yi yunqurin yin komai ba,bai kuma zoba don yakan dauki lokaci kafin yazo din,a daren kwana na uku da maganar mummy ta sake tuntubarta a sannan asma'u na wajen
"Ke idan zaki masa magana ki masa,idan baki iyawa ni ina da lambarsa sai na kirashi na shaida masa" cewar asma'u kanta tsaye,ganin bata kulata ba ta sake cewa
"Abinda dai kike gudu duk tsiya sai anje an gano"bar mata wajen tayi,don ita duka bata da lokacin ire iren wadan nan.


Tana tsaka da goge kayan sawarta data wanke dazun wayarta ta dauki tsuwwa,a sannan yana zaune cikin valcony dinsa sanye da farar t.shirt qal mai qaramin hannu da farin trouser,aiki yake cikin system dinsa idonshi ya kai kan wayarta data bashi,sai a sannan ya tuna ma da abinda ya faru,rabonshi kuma da ita tun ranar,ko ya kira yayi pretending kan vivonsa daya baro a hannunta baiyi ba,hakan yasa shi yanke shawarar kiranta,wannan karon da layinsa da yake amfani da shi ya kira ba layin daya ware ba,cikin sanyin nan nata tayi sallama,idanunsa ya dan lumshe kadan sannan ya budesu,karon faro daya soma kiranta a waya tunda suke tare,amsa sallamar tata yayi sannan shuru ya biyo baya dukkansu
"Baki gane dawa kike magana ba kenan?" Ya tambaya a sake,murmushi ta saki kadan,sai daya kuma magana ta gane waye
"Na gane mana" ta fada cikin sanyi
"To waye?" Dan shuru tayi kadan sannan tace
"Yaya ne"
"Kin yarda kin bani matsayin yayan kenan?" Murmushi kawai ta saki,don harga Allah kallon yayanta take masa,bai damu da amsarta ba ya dora da
"Kira nayi na baki haquri kan rashin kawo lefe....kayanne har yau basu gama haduwa ba...kiyi haquri inaga sai bayan an daura aure za'a kawo ko a aje miki can gidan da zaki zauna"
"Babu komai...babu wata damuwa....ni dama ban saka hada lefe ba" ta amsa masa a nutse
"Au...haka ake auren budurwa...ko da yake ni yaya nake...amma duk da haka ai miji nake a idon duniya ko?,xan qoqarta nayi miki dai dai qarfina in sha Allahu bazai gagara ba"
"Ba damuwa...yanzun ma mummy ce...." Sai kuma ta kasa qarasawa,hakanan take jin nauyin fadi,biron hannunsa ya aje ya miqe qafafunsa yana shafa kansa da hannu guda


Haka nan yake jin dadin sautin ta
"Uhmmm....mummy ce meye?,Allah yasa ba wani matsalar bace ta faru" kai ta girgiza kaman yana wajen
"A'ah....wai zasuga gida ne"
"Ya salam...toh" ya furta kaman da gaske ya dan rude din,duk sai taji babu dadi....tana kallon kaman zai taimaki rayuwarta ne shi kuma gashi ana son qureshi da sanyashi cikin takura da matsala duk don saboda ita
"Babu damuwa.....kamar ranar yaushe suka ce zasu je?"
"Ban sani ba nima....kawai dai yau kwananta uku da gaya min"
"Is ok....shikenan....zuwa anjima ko gobe zan kiraki na gaya miki ranar da zasu zo din"
"Tohm..." Ta fada cikin sanyinta da ya sakashi lumshe ido,haka kawai yakeson yanayin muryarta kamar ta yara saboda zaqinta.


Yana katse layin ya soma lalubar wata number da ya tanadeta saboda irin wannan ranar,yana kira babu jinkiri aka daga,bayan sun gaisa ya bashi umarnin sama masa gida tare da gaya masa irin yanayin gidan da yakeso,unguwannin ya lissafa masa ya zabi daya daga ciki,daga bisani sukai sallama ya aje wayar yaci gaba da aikinsa yana murmushi,shi kansa idan ya tuna yadda plan dinsa ke tafiya dariya yake baiwa kansa...bai zaci abun zaiyi tsaho har haka ba,haka kawai yaji sha'awar ci gaba da yi,har zuwa yau kuma baiga komai tattare da ayshan na raini ko qyama ba,duk da cewa bashi da yaqini ko tabbas itama a kanta,bai sani ba ko yanayin rayuwarta ne yasa ta zame masa hakan,amma koma meye saura qiris komai yazo qarshe...kuma lokaci zai nuna.


Sai daya kammala komai yazo kwanciya sannan ya tura mata texs din cewa gobe ko jibi idan sun shirya suyi masa magana yazo ya rakasu,ya kashe wayar tasa ya soma addu'ar bacci,yana cikin shafawa wayarshi wadda ita kadai ta rage bai kashe ba ta soma haske,ramla ce ke kiransa,sharewa yayi yaci gaba da abinda yake,saidai har ya gama din bata daina kiran ba,tilas ya sakashi dagawar ya kara a kunnensa.


Ajiyar zuciya ta saki kafin tace komai,don har ta fidda ran zai daga,khalipha na wahalar da rayuwarta....bata taba tsammanin zata masa irin wannan soyayyar ba da bata bari abinda ya faru ya faru a baya ba
"Ya khalipha...."
"Yaya akayi?" Ya tambayeta ba tare daya amsa ba,harga Allah taba takura masa fiye da kowa a cikinsu,baya son mace mai naci sam
"Kayi haquri don Allah,laifin wani fa baya shafar na wani a rayuwa...ina sonka ya khalipha ka sani ina tsananin sonka....please ka bani dama mu zama abu daya....mu shimfida rayuwa mai kyau da inganci"
"Kiyi haquri bacci nake ji,idan na tashi i will call you back" katse layin yayi ya kashe wayar baki daya sannan ya kwanta,saidai maimakon bacci yazo sai rayuwar da suka tabayi a gidansu ramlat din wasu shekaru can baya suka dinga dawo masa daki daki,cikin lokaci qanqanin idanunsa suka kada,yana kwance rigingine hannayensa harde a qirjinsa sai ya canza yanayin kwanciyar tasa zuwa hannun damanshi yana ta'awizi don kore shaidan daci gaba da tunzurashi da tuna masa abinda ya riga ya shige,a hankali temper din nashi ta dinga sauka,gajiyar ranar ta lullubeshi,nutsatstsen bacci ya sauka a idanunshi.


Saidai bai jima da fara baccin ba yayi mafarkin aysha na kuka....kuka take sosai ba tare da tace wani abu ba,abinda ya sake tashinsa kenan,alwala yaje ya daura ya tada sallah yana jujjuya mafarkin cikin ranshi,tabbas akwai abinda yake damunta haka zuciyarshi ta bashi,tausayinta sosai yake yana jin tamkar qanwarshi,da wannan bacci yayi awon gaba da shi.

🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶


Tunda aysha tace za'a je ganin gida asma'u ta hana kanta tsaye ta hana kanta zaune,motsi kadan sai tace zasuje suga mansion house din aysha,har sai da mummy ta gaji da ji ta kwabeta.


Ranar da za'a din itace tayi driving dinsu,su anty halima ne...anty kubra,sai anty lubabatu,sai inna laraba,anty safiyya ce kawai bata samu zuwa ba saboda al'amin data kai asibiti ranar baya jin dadi,babu wani danginta ko daya,babu wani da zata kirashi nata qwaya daya,haka tanaji tana gani asma'u ta sanyawa motar key suka fice bayan ta saki waqa cike da nishadi.


Da kashi yaso zuwa,da kansa yaso ya musu rakiyar,saidai kuma a ranar yana da baqi da zasu zauna meeting da su,tilas ya wakilta daya daga cikin manyan yaranshi ya musu jagora,qaramar camera ya bashi wadda ya jonata da system dinsa,ta yadda zai dinga ganin duk abinda yake faruwa har su dawo.


Misalin qarfe uku da mintina suka shiga unguwar,tun daga farkon layin asma'u ke tabe baki tana fadin
"Tab..." Unguwa ce data tara marasa shi qwarai,kusan babu wani gida qwaya daya da zaka nuna wanda zai alamta maka akwai maiqo ko dukiya a gidan,wasu daga cikin gidajen ma qofar buhu ce daure ko labule a jikinta.


Qofar wani gidan qasa dan rakiyar ta tsaya,hakan ya sanya asma'u itama tayi parking,sannan suja fiffito gaba dayansu suna qarewa unguwar kallo cike da qyama kafin daga bisani su maida idonsu kan gidan da dan rakiyar ke kici kicin budewa.


Ginin qasa ne wanda yasha shafen sumunti da makuba,qofar katako irin ta da ta katako sosai maqale da katangar gida wanda ke nuna ta nan zaka shiga zuwa ainihin gidan,kallo daya zaka yiwa gidan kasan cewa ba sabon gini bane,kowanne idanunsa kan gidan suka isa bakin qofar,asma'u ce ta dubi dan rakiyar
"Kaga malam basai kayi wahalar saka muqulli ka bude wannan rubabbiyar qofar ba,da qafa ma budeta zamuyi" ta qarasa fada tana daga qafarta ta daki qofar,qasa da qura suka biyo qofar suka yo kanta,hakan ya sanya tayi saurin ja da baya,ita kanta mamaki take cikin zuciyarta,sam batayi tsammanin talaucin yaron oga yakai har haka bama,wani bacin rai ya sake lullubeta da haushinsa,yasan haka yake har ya zubda mata ajinta ta jera da shi?,ta hada muhallin zama da shi,lallai iya zaman da yasa tayi da shi ba qaramar cutarta ma yayi ba,batasan mutane nawa ne da suka santa suka kuma sanshi suka gansu tare ba,ta tabbata wasu sun mata dariya.


Da qyar ya iya samu qofar ta bude ya tura kai ciki suka biyo bayanshi,tsukakke kuma dogon soro suka fara taraswa mai dauke da rufin azara irin ta da,idan kaci gaba da jumurin cusa kai zuwa cikin gidan kuwa,tsakar gida ne mai fadi da yalwa wanda aka yiwa daben qasa,duqurqushin bandaki jere kusa da kitchen,sai dakuna manya falle biyu
"Ummm....indo ba'a manta gida ba" cewar anty halima,daga kai kawai inna laraba tayi ta kalleta ta dauke kanta....wato shi dan qauye ba mutum ba?...tana da yaqinin harga Allah daddy baisan duka wainar da ake toyawa ba,duk da cewa bata gidan amma tana katarin riskar wasu abubuwan,ta yaya aysha yarinyar da tayi jami'a take zaune cikin birni shekara da shekaru zatayi aure cikin wannan gidan ta kuma zauna a ciki?,ta ina zata iya taimakawa rayuwarta ta fidda ta?
"Hhhhhh,ai tazo inda ya dace da ita" cewar asma'u tana yarfa hannu tare da takawa cikin gidan tana qare masa kallo.


Ba abinda dan rakiyar yace saboda ba'a umarceshi da cewa komai ba,kuma ya tabbatar duk abinda ke wakana boss din sa yana ji kuma yana gani,bai furta komai din ba har suka gama isgilancinsu suka gama suka tako zasu fita ya rufa musu baya,yana maida muqullin zai rufe asma'u ta dubeshi
"Kana wahalar da kanka ne kawai....banda abinka wai meye abun qwaqumawa wannan kangon kwado kayita wani rufeshi,da ka barshi ma a bude don baida maraba da kango" kallo daya yayi mata ya maida kansa yana ci gaba da ruge gidan,ranshi fal da mamakin me ya hada boss da wannan gidan me zaiyi da shi?,sannan kuma meye gaminsa da wadan nan matan?,ko da ya gama rufe gidan tuni sun hau kwalta sunyi gaba abinsu.


Cikin motar ma zancan gidan sukeyi,kowa na tofa albarkacin bakinsa,anty lubabatu ce tace
"Anya ko asma'u wannan plan din baiyi worst ba....talaucin mutumin nan fa kamar yayi yawa" dan tsaki ta ja saboda sakuwarta ce
"Kinjiki kema da wani irin zance....to daga ina ita din ta fito?....ina cewa irin wannan gidan anan taci ta sha,banda ma tsaurin ido irin na talaka daga an riqeka a waje sai kace lallai sai kayi rayuwa irin tasu?,kuma wa ya hanata musanta zancan tun yana farkonshi...wai ita saliha a dole baiwar Allah.....munafuka inaga ma kyanshi ta gani ta kasa cewa bata sonshi....so ni banga wani worst ba da yayi,ungulu ce kawai zata koma gidanta na tsamiya" tabe baki anty halima tayi,sai a sannan tayi magana
"Lubabatu a yadda yarinyar nan take gani tana da kyau idan ta auri wani kan mage ne zai waye,uban kowa ma neman taka shi zatayi,irinsun nan ki gansu haka haka ba qananun 'yan iska bane idan suka samu waje...Allah ne kadai yasan manufar jaki da bai bashi qaho ba....daddy nema haka kawai ba dangin dangiro kaje ka jajubo yarinyar mutane....ta gama abinda ya kawotan ma maimakon ka maidata a'ah ka daukama ranka saika aurar da ita....bayan ko uwarta bata ta tata saikai" ta qarashe maganar da tsaki
"Shi yasa nakesonki anty halima....kinfi kowa fahimta"
"Mu ai da yake jakai ne ko?" Lubabatu ta fada tana hararta,dariya tayi tana cewa
"Bance ba".


Nannuyar ajiyar zuciya ya saki ya soma latsa system din bayan ya gama gani da jin duk abinda ya gudana tun daga qofar gidan shigarsu ciki zuwa barinsu unguwar,tunani ne cikin qwaqwalwarsa kala daban daban,mamakin baqar zuciya da mugunta irin ta wasu mutanen,buri da fatan jefaka a rana koda baka takawa kowa komai ba,aysha dai aysha ba'a son ci gabanta a rayuwa kwata kwata?,shikam wanne irin gata zaiyi mata daya dace da ita wanda zai bada mamaki ya girgiza zukatan maqiya
[1/14, 1:37 PM] Om Muhammadiyya: Mamakin abinda aysha tayi wanda ya tsarewa asma'u a rai yake,me tayi mata mai zafi da taketa yunqurin daqile duk wani ci gabanta,wacce irin macace asma'un?,bama ita kadai ba,hatta da 'yan uwanta ya fuskanci haka suke,ta ina suka gado wannan halayya?,wato da da gaske shi din haka yake zasu fi kowa farincikin dawwamarta cikin wahala kenan?.

Kusan wunin ranar baki daya abinda ke masa kai kawo kenan a zuciya,har sanda yake zaune gaban anni yake cin abinci abunda ke tsinkulinsa kenan
"Muhammadu lafiya dai?gajiya ko kuma aikin?" Dan murmushi yayi sannan a nutse ya bata labarin dukkan abinda ya faru,kai take jinjinawa cike da mamaki da.nazari
"Muhammadu yarinyar nan tana buqatar wani ginshiqi da zai tallafeta....inama ace kana mata soyayya mai qarfi wadda zata zame mata jigo?....saidai duk da haka ina jin qaunar zama da ita...sai nake jin kamar a maida daurin auren gobe ka dauketa daga cikinsu,me yasa mutane zuciyoyinmu suke ciki da kishi qyashi da hassada?...Allah ka shiryamu ka gyara mana zukatanmu"ta furta cikin sanyin jiki
"amin ya Allah....amin"



_kuyi haquri da wannan don Allah_

*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIKA GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,IDAN KINA BUQATAR SIYA KI TUNTUBI WANNAN NUMBER (08030811300)_*


*DB*




23


Tunda suka dawo babu zancan da suke sai na gidan ayshan mommy na ji bata dai tanka komai nata ciki ba,a sannan anty safiyya ta dawo daga kai al'amin asibiti,ganin ta gama da wuri sai ta zarto gida,nan ta taras da su ta kuma ji duk abinda suke fadi din,babu wanda ta cewa uffan sai tayi ma kamar batasan me yake faruwa ba,har suka gama sha'aninsu kowacce ta wuce gidanta suka bar safiyyan a gidan
"Ke yaushe zaki wuce...kowa ya tafi ya barki?"
"Mommy dukansu fa sun riga ni zuwa,kuma ma sai nayi sallar isha'i abban al'amin zaizo mu wuce tare"
"Ai shikenan..." Ta fada tana ci gaba da aikin gabanta.


A nan tayi sallar isha'i taci abinci,bata jima da kammalawa ba daddy ya shigo gidan,mintina goma ta bayar ta kwantar da al'amin sannan ta wuce zuwa falon daddyn.


Yana zaune saman kujera sanye da jallabiya,da alama daga wanka ya fito yayi shirin cin abinci,da murmushi a fuskarshi suke gaisawa,saboda duk cikin yaransa bayan asma'u itace ta biyu a wadanda yake so,itama asma'un don itace auta shi yasa ta rigashi zuwa,tana da halaye irin nashi,sauqin

Please Login or Register in order to submit comment