Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da hannu daya ya zaro wayarshi ya lalubi lambar anni,bugu daya ta daga,sai yayi qoqarin saisaita temper dinsa
"Anni,wace take amfani da bedroom dina?"
"Bedroom dinka?,wace banda matarka,aysha ce"
"Aysha kuma?" Ya tambaya cikin mamaki
"Eh ita,wani abu ne?"
"A'ah,ta tsorata ne kawai ta shiga toilet tayi zaton wani ne" yayi saurin fada don karta dago wani abu
"Aifa aysha ba baya ba wajen tsoro,saika gaya mata wane ai" daga haka ta katse wayar,jifa wayar yayi gefanshi sannan ya miqe qafafunshi ya soma zare takalmin qafarsa da socka din duka gaba daya,ya rage daya daga cikin three in one suit din dake jikinsa ya sassauta tie dinsa sannan ya sake komawa dakin,tsai yayi yana qarewa dakin kallo,komai a tsaftace yake,sai towel bressier da pant dake kan gadon,sai kayan gyaran gashi dake saman madubi da cumb din data watsar waje guda saboda tsoronta,dauke kanshi yayi ya shigo ciki sosai ya doshi toilet din.


Daga can taji 'yar qara alamun an sake bude qofar bedroom din,wani tsoron ya sake kamata,sautin kukanta ya sake qaruwa sanda taji ana taba qofar bandakin,yana iya jiyo sautinta kadan kadan,haushi ya kamashi,wanne irin tsoro ne da ita haka,knocking ya fara yi saidai maimakon ta bude sake firgicewa tayi,gabanta yaci gaba da bugun uku uku,ta duba duk bandakin ba wajen tsira,kuma ta tabbata ko ihu tayi ba wanda zai jiyota cikin gidan,ganin ba alamun zata bude sai kukan banza da takeyi ba tare da yasan me takewa kukan ba ya sanyashi bude bakinsa,cikin muryarshin nan yace
"Bude mana" saboda tsoro sam bata iya tantance muryar waye ba,sai kawai zuciyarta ta bata muryar aljanu ce,cikin sautin kuka tace
"Wallahi bazan bude ba"
"Kwana zakiyi a ciki?"
"Nidai kuyi haquri don Allah"
"Mu suwa?" Ya tambayeta cikin qosawa,bata bashi amsa ba sai dif da tayi,ganin tana neman bata mishi lokaci yasa ya koma inda ya aje kayan hannunshi ranshi fal takaici,ya lalubi muqullansa daya amsa a hannun anni ya koma yana gwada na toilet din,jin ana alamun budewa ya sake sawa ta tsure,saikawai ta qarasa shigewa cikin bathtube din ta takure waje daya tana dana sanin zama abangaren ita kadai,dama tun dazun take jin motsi,dazu kuma musa'ab ya gama bata labarin ya taba gamo tsohon gidansu,tana ta dariya da tsokanarshi duk labarin ya dan bata tsoro kadan ashe da gaske yake


Sai daya gwada muqullai kusan uku abinda ya sake gajiyar dashi sannan ya dace dana bandakin,a hankali ya tura qofar ya shiga,can ya hangota ta takure gu daya,gashin kanta da bata samu damar daurewa ba ya bazu ko ina har fuskarta,daga kai tayi cikin tsoro ta dubeshi,sai a sannan ainihin siffarshi ta bayyanar mata,khalipha ne sosai tsaye cikin bandakin,sanye cikin baqaqen suit,saidai a yanzu ya cire sun glasses din dake fuskarshi,ya sake haske da kyau,sumar kanshi data fuskarshi luf da ita tana fidda wani sheqin baqi,ya sake murjewa hakanan idanunshi sun sake kyau,daga tsoro sai yanayin ta ya sauya zuwa kunya da fargaba,ta tafka babban abun kunya,bugu da qari tuna abinda ke daure a jikinta kawai ya sake sawa hankalinta ya tashi,kamar ta bace ya daina gannta haka taji,sai kawai ta maida kanta taci gaba da dunqulewa waje guda gana pretending din firgitar dazu ce bata saketa ba
"Saiki tashi ki koma ciki ki bani waje zanyi wanka" ya fada yana dubanta,duk da qoqarin kauda idanunshi da yakeyi amma hakan ya gagara,jin idanunsa take yake ko ina akanta,batajin zata iya motsawa ta wuce haka ya gabanshi
"Ki tashi matsoraciya kawai ko har yanzu baki gane wane ba?" Ya tambayeta yana harde hannunsa a qirji,shuru tayi don bata da amsar bashi
"Ko ba zaki tashi ba sai nazo na daukeki da kaina?" Jin haka ya sanyata zumbur ta miqe,saidai da qyar take iya daga qafafunta ta fito daga cikin bathtube din ta raba ta gabanshi zata fice daga bandakin,caraf yayi ya riqo hannunta yana sani,a firgice ta dago kai suka hada idanu,saita soma neman wajen buya,wanda abin dariyar jikinsa takeson shigewa ko zai daina kallonta,ba shiri ya saketa yana dariya cikin ranshi,bai fasa kallonta ba har sai data fita din sannan ya koma ya rufe bandakin da muqulli ya dawo ciki ya tara ruwan wanka.


Hawaye ne ya sake qwace mata takaici na cinta na ganinta haka da yayi,gashinan shi yanzu ya saka muqulli ya kulle kanshi zaiyi wanka amma ita asirinta abayyane,qwafa tayi ita kadai tana zumburo baki.


Haka ta shirya tana qananun hawaye a gurguje don kada ya sake fitowa ya taddata a haka,duk da haka bata fasa yin kyau ba,doguwar rigar buba ce ta atamfa shadda baqa mai matuqar kyau da tsada,an mata zanen jajayen flowers manya a jiki,bata nemi dan kwali ba saita yane kanta da madaidaicin jan mayafi bayan ta hade gashinta ya bada jela daya data sauka har bayanta.


Har taje zata fita sai kuma ta kasa,bai kamata ba,ba wani magana da sukai tsakaninsu koda ta sannu da zuwa ce,saita koma kan kujerar falon ta zauna tana murza tafin hannunta a hankali tana tuna yadda abun ya faru,dama tun dazu a tsorace take da labarin mus'ab,shi ya sake tunzurata ta sake tsorata.


Idanunsa lumshe suke ruwan na ratsa jikinsa,tabbas haka ne kowa yabar gida gida ya barshi,wani dadi yake ji gashi a gida,Allah Allah kawai yake ya koma wajen anni susha hira,a hankali ya tuna abinda ya faru dazu mintina kadan da suka wuce,murmushi ya saki abun yana son bashi dariya,bai taba sanin matsoraciya bace har haka bayan sanyin da yasan a baya tana da shi ba sai yau,kai ya kada kafin ya dauraye jikinsa ya fito.

Tunani kadan tayi sai ta miqe ta fice zuwa cikin gidan,ya kamata ace tayi masa wani abu da zaiji dadi,tunda bata jin gidan sun tanadar masa wani abun don ba alamun suna da masaniyar zuwanshi a yau,ta tabbata da anni zata sanar mata,haidar da mus'ab ne kawai a falon suna shigo da jakankuna,dariya mus'ab ya sa yana dan satar kallonta,har ta wuceshi ta share sai ta tuna abinda taji yana cewa anni dazu na suprise,sai ta dawo da baya tana dubansa
"Zan rama fa,kaci bashi ne,yaa haidar harda kai aka hada baki ko?" Ta fada tana duban haidar,murmushi yayi yana daga hannu sama
"Nikam babu ruwana bansan me akeyi ba,yace min ne kawai nazo na rakashi airphort" kai ta jinjina tana wa mus'ab sign na alwashi ta wuce kitchen.


Duka 'yan aikin ma ciki sun kacame da aiki
"A'ah duk girkin meye wannan?" Ta tambayi baba atika
"Mai gida yayi zuwan bazata kinga dole a tashi a shirya masa lafiyayyen abinci" hakanan taji cewa dutynta ne wannan,ita ya kamata tayi masa wannan karramawar,koba komai ta dan nuna dan wani yanki na godiya kan kyautatawarsa a gareta,duk da baikai ya kawo ba amma zata kwatanta
"Bari ku gani,wannan girkin naku ai lokaci zai dauka baku gama ba" cikin qanqamin lokaci ta hado duk abinda take buqata ta dora,ta koma gefe ta niqa abarba tayi mishi pineapple juice wanda kafin ta garma dan qwarya qwarayar girkinta ya dauki sanyi.


Mintina talatin ta gama ta shirya komai kan wani faffadan tray mai azabar kyau,ba wanda yawunshi bai tsinke ba a kitchen din(harda ni mai rubutun 😜).


Tana goge hannunta da zummar idan ta gama ta fita da abincin amal ta shigo,kana ganinta kasan bata jima da yin kwalliyar ba cikin dinkin lace
"Wai baba atika me kuke dafawa baqonmu,qamshi ya cika gidan amma shuru baku gabatar masa da komai ba?"
"Ai aikin uwar masu gida ne,gashinan da kanta ba saqo ba" baba atikar ta fada cikin murmushi wanda hakan yaja hankalin amal zuwa wajen aysha wadda take sake jera kwanukan,cikin yaqe take kallonta,nutsatsiyar kwalliyarta wadda girkin da tayi bai bata ta ba,yadda ta jera kayan abincin da qamshin da suke fiddawa,wani abu mai nauyi taji ya tokare qirjinta,sai ta kasa cewa komai ta juya ta fice cikin sanyin gwiwa.


A nutse take fitowa daga kitchen din zuwa falon,shi ta soma hangowa a gefan anni wanda hakan ya haifar mata da matsananciyar faduwar gaba wadda bata taba jin irinta ba,bata sani ba ko hakan yana da nasaba da abinda ya faru dazun?,fuskarshi fes,kyansa ya sake fitowa sosai,ganin yana niyyar juyowa ya sanyata dauke kai da sauri ta maida kan anni,dubanta yake sanda take tahowa din,sai yaga kamar an canza ta gaba daya,shidai yasan ba wannan ayshan ya tafi ya bari ba wata ce daban,abinda tayi dazun ya dawo mishi,sai yace da anni sanda ta iso wajen tana aje kwanukan
"Yaushe humaira ta koma haka?" Yayi subutar bakin fada ba tare daya shirya ba,sam anni bata fahimci tambayar tashi ba,tayi tunanin kyau da gogewar data qara yake nufi,saita saki murmushi tana jin dadi har cikin ranta,miqewa tayi tana cewa
"Sannu takwara,ki kai masa saman teburi,fita zanyi nima dubiya,drivan ma har ya iso" ta qarasa maganar tana miqewa,sai ya dubeta
"Ba hira kenan anni,kamar ma baki kewata ba?"
"Ni bance haka ba saikai khalipha?,watanka nawa?" Ya gane qorafi takeson yi masa,mafi a'ala kuma yayi shuru kar allura ta tono garma
"A dawo lafiya"
"Allah yasa,ya kamata idan ka huta kaima kaje ka dubashi,don yanzun ma tare dasu haidar zamu je"shuru kawai yayi yadan sadda kanshi,da alama baison zuwa wajen amma bazai iya musa mata ba,miqewa aysha tayi ta amshi jakar hannunta ta bita da ita a baya,suna zuwa qofar falon ta amsa
"bar aikin da ba lada kije kiyi na lada,ki kula da mijinki" kunya kaman zata nutse,kalmar saita mata banbarakwai,ba wanda ya fado mata a ranta a lokacin sai maman hunaifa da baban hunaifa,saita dinga jin girma da wani alfahari na shigarta kadan kadan,wai itama fa matar wani ce akwai igiya a kanta,hakanan taji tana son ta gwada yanda matan aure keyi,juyawa tayi zuwa cikin falon,har ta isa kanshi na qasa da alama tunani ma yake,bata tankashi ba ta kwashe kwanukan zuwa saman tebur wanda motsinta yasanyashi daga kai,saiya tsinci kanshi da binta da kallo,qamshinta daya buso zuwa hancinsa yaji ya burgeshi,ci gaba yayi da kallonta ba tare data sani ba yana jin qimarta na qaruwa cikin ranshi,zaman da sukayi da anni kafin fitowarta labarinta kaf duka kan ayshanne,irin kulawar data samu daga gunta ya tabbata ko shine iyakar abinda zai mata kenan,sai yaji tausayinta ya kamashi,lallai mahaifiyarta batasan baiwar da Allah yayi ma rayuwarta ba na samun nutsatstsiyar diya.

Sai data shirya komai sannan ta daga kai da niyyar duban me yake,sai suka hada ido,murmushi ya sakar mata saboda harga Allah bazai iya boye jin dadin kulawa da anni data yi ba,tamkar an dorawa zuciyarta wani abu haka taji,bugun zuciyarta ya sake yawa,idanunta ta lumshe tana qoqarin maida masa martanin murmushin nasa,sai kuma taji kunya ta mata dabaibayi,yanayin daya ganta da abinda ta masa dazu suka fado mata,ji take kaman qasa ta tsage mata ta shige ciki,a nutse ya taso har zuwa inda take tsaye,yaja kujerar dake kusa da ita ya zauna,saita motsa kadan ta matsa daga kusa dashi.


Ganin shuru batayi niyyar zuba komai.ba bayan shi kuma yunwa yakeji sai ya sanya hannunshi da niyyar bude flask din dake gabanshi,tare hannunsu yaje kai saboda arashin tunanin budewar da akayi yazo daya a qwaqwalensu,da sauri kowanne ya janye hannunshi,khalipha ya dunqule nasa hannun yana jin wani irin abu na masa tafiyar tsutsa a jikinsa
"Uhmmm,a sanmin naci" ya fada qasa qasa ganin taqi ta sake motsawa,sai da tayi qoqarin controlling hannunta dake rawa sannan ta iya zuba masa komai ta miqa masa
"Ka dawo lafiya ya hanya?" Ta fada cikin amfani da irin salon maman hunaifa,wanda ba qaramin kyau yayi mata ba fiye da tunaninta
"Alhamdulillah" ya amsa yana sauke ajiyar zuciya,sai tayi niyyar wucewa,ba haka yakeso ba,hakanan yaji bai gaji da ganinta ba awajen,kwalliyarta ta tsaru,sosai adon yabi jikinta
"Zama zakiyi naji me kika bayan bani nan" ya fada yana kai lomar farko bakinsa,saiya kasa ci gaba da maganar da yayi niyya,dadin abincin na kai masa ko ina,hakanan ta zauna a kujerar da ya nuna mata wadda itake facing dinsa,kanta na qasa shi kuma yaci gaba da cin abincinsa
"A ina kika koyi girki haka?"
"A gida" ta amsa masa a ataqaice
"Tun yaushe?"
"Can da dewa" daga haka bai sake cewa komai ba,yayin da sautin muryarsa daya tambayeta da ita taci gaba da amsa kuwwa a kunnenta,sai take jin kamar ba muryarsa ba,komai nashi ya sauya.


Shiru ne ya ratsa wajen,baka jin komai sai qarar cokalinsa da kuma hayaniyar masu aiki dake can cikin kitchen,daga wata kusurwa ta falon kuma amal ce rakabe tana duban abinda ke faruwa ta bayan labule,agogo yayi niyyar kalla sai ya hangi gefan skert dinta da batasan ya fito ba,qaramin murmushi ya saki cikin ransa yake cewa
"Barewa ba zatayi gudu danta yayi rarrafe ba,lallai hali jini yake bi" a hankali ya sauke idanunsa kan hannunta da take wasa da farcan hannunta da yasha jan lallenta ya koma marroon,tafin hannunsa ya dora a hankali samansu ya damqesu kadan yadda ba zataji zafi ba,da hanzari ta daga kai ta dubeshi don sanin dalilin faruwar hakan,murmushin dake shimfide saman fuskarshi saiya qarasa narkar da ita,qwayar idanunta kawai ya kalla yasan tambaya takesoyi
"Amal" ya furta kamar mai rada ta yadda idan ba ita din dake wajen ba bawanda zai iya jiyo me yake cewa
"Amal kuma?" Ta tambayeshi cikin mamaki,kai ya gyada
"Banason ki dinga nuna rashin sabo ko baqunta tsakanina dake" maganarshi ta dawo mata randa take da kwana guda a gidan,kai ta gyada masa alamun ta fahimta,qoqarin dai daita kanta tayi ya dubeta
"Bani labari dame dame ya faru bayan bani nan" ya qarashe maganar yana miqewa a nutse tare da nufar inda ya hangi amal,aysha ta bishi da kallo a sace tana ganin kaman ya qaro salo da yanga,kominshi shima ya sake sauyawa.
39
Tamkar mai neman wani abu yaje wajen,yayi kaman zai juyo ya take qafarta,wata iriyar azaba ta ziyarceta,sai ta saka hannu ta rufe bakinta dashi tana tunanin zata iya jurewa,sake taketa yayi wannan karon kasa daurewa tayi sai data qwalla qara,baya yaja ya dage labulen yana dubanta
"Me kikeyi a nan?" Tsabar azaba ya hanata magana,sai daya maimaita maganarsa cikin tsawa sannan ta iya amsashi
"Babu komai,abu nake nema...." Tsai yayi ya zuba mata rikitattun idanunta dake sake tsumata cikin soyayyarshi koda yaushe,nauyi sukai mata ta gaza daukarsu,saita sadda kai gabanta na faduwa,kunyar abinda tayi na mamayarta,da kanta ta tona kanta ta hanyar cewa
"Kayi haquri don Allah,wallahi bazan sake ba"
"Daga yau duk sanda muke zaune a falon nan mu biyu kacal ko gilmawarki kar na sake gani,bacemin a gun" ba shiri ta wuce tana dingisa qafarta.


Dariya ce sosai ta zowa aysha,ta kifa kanta a saman tebur tana qunsheta,a nutse ya tako wajen,sai yaja ya tsaya yana dubanta,sam batasan ya dawo ba sai dataji yace
"You,me kike ma dariya?" Ya dage girarshi daya,kai ta girgiza tana qoqarin hade fuskarta daga dariyar da take sadai ta gagara hakan,ci gaba yayi da kallonta yadda take son tsuke fuskarta ya taimaka wajen fito da beauty point din dake kumatunta,wanda ko sau daya bai taba kula dashi ba sai yau,qarar wayarshi ita ta dawo dashi daga duniyar kallon daya tafi,saiya fara laluba aljihunsa cikin basarwa,sai daga bisani yaga a saman tebur ya ar wayar,hannunshi ya miqa ya dauko wanda sauran kadan jikinsu ya gogi juna,hanyar waje yayi yana amsa wayar da alama mai muhimmanci ce.


A hankali ya tura qofar falon ya shiga sanyin ac da qamshin nan na musamman da tun zuwanshi yaji sashen nasa nayi ya daki hancinsa,ba wadataccen haske a falon sosai sai daya sanya hannu ya kunna makunnin qwan falon sannan hasken ya gauraye ko ina,daga can bangare daya na falon ya hangota akwance,sanye da kayan bacci ruwan hoda mai turuwa riga mai dogon da wando mai kauri,sai farin hijabi da take sanye da shi wanda bai wuce qugunta ba,gabanta takardu ne a baje da litattafai,sai torch din wayarta dake kunne da alama karatu take baccin ya sureta,sannu a hankali kamar mai sanda ya isa gabanta yana dubanta fuskarta da tayi fes kamar ba bacci take ba,quruciyarta ta fito sosai,baccin ya mata kyau,murmushi ya saki sanda ya tuna abinda ya faru dazu yana zarar daya daga cikin takaddun gabanta wanda take rubutu akai ya soma karanta rubutun dake jiki daya bayan daya


Dauke idanunshi yayi ya maida kanta yana yaba tarin basirar daya gano sanda take gyara kwanciyarta cikin baccin da alama ta gaji da kwanciyar daya bangaren ne,iya yanda take bayanin aikin da aka bata kawai ya isa ya gaya maka cikin sahun daliban da take,jinjina kanshi yayi yana yaba mata kafin ya durqusa ya maida takardar cikin 'yan uwanta sannan ya tsugunna yana tattare mata takardun waje daya.


Motsin takardun shi ya farkar da ita,zumbur tayi ta miqe ta zauna tana dan matsawa baya,da sauri ya dora yatsanshi akan lebansa yana fadin
"Shshshsh....in kika sake kikamin ihu irin na dazu saina cinye bakin" kunya ce ta kamata daya tuno mata da kuma lafazinsa na yanzu,saita sadda kai tana gyara zamanta a fakaice saboda yadd wandon jikinta ya tattare qaurinta ya fito,maimakon daya gama hada takardun taga ya miqe sai ya koma ya zauna sosai,yana soke yatsunshi cikin na juna idanunshi a kanta
"Uhmmm,bani labarin abinda ya faru da bana nan" yatsunta ta lanqwasa suka bada sauti,cikin muryar wanda ya tashi daga barci wanda ta cakudu da yanayin sanyinta tace
"Ba abinda ya faru" lumshe idonsa yayi saboda yadda tsigar jikinsa ta zuba
"Me yasa baki nemi ni ba tunda na tafi?,haka ake yaya da qanwar?" Idanunta da suka sake haske saboda baccin da tayi ta daga ta zuba mishi su
"Ya salam" ya furta can qasan maqoshinsa ta yadda shi kadai zai iya ji
"Wai me yake damunka khalipha?" Ya tambayi kansa da kansa,baisan me yasa yake jin baqon yanayi tattare da ita ba,komai tayi sai ya bada wani reaction a jikinsa da zuciyarsa


"Kafin nayi serving number din ne ta gudu" sake gyara zama yayi sosai,haka nan yake son hirar tasu tayi tsayi,duk da cewa ya sani shine mai.laifin da bai taba nemanta ba
"Amma me yasa baki amsa ba wajen anni?"
"Hakan na nufin zata fahimci baka kirana kenan" ta sake bashi amsa a taqaice a sanyaye,murmushi yayi yana gyada kai,sai yanzu ya gane dalilin da yasa anni bata taba masa fada ba kan bai taba kiran nata ba,tafin hannayensa ya game waje daya,bashi da sauran abin cewa,gashi kuma baison zaman nasu ya qare da wuri haka,sai ya sake bude takardun daya hada matan ya soma zarosu yana mata tambayoyi kan course din da takeyi,batayi qasa a gwiwa ba ta soma bashi amsa daki daki,saidai abu daya ne da bata so shine ya daga kai ya zuba mata idanunshi,faduwar gaba da daburcewa suke sakata,har ta qare maganarta idanunshi a kanta yana gyada kai
"Ma sha Allah" ya fada sanda ya fuskanci ta gama
"Allah ya taimaka"ya fadi yana miqewa,a gajiye yake sosai don fitarsa dazu ba qaramin yawo sukayi ba
"Ameen,na gode,Allah ya saka da alkhairi ya jiqan magabata"
"Ameen" ya amsa cikin jin dadi ya wuce cikin dakin.


Koda ya fito tuni ta miqe saman doguwar kujera,da alama nufinta nan zata kwana,ita kanta tasan qarfin hali ne kawai takeson nunawa,amma tsoron da takeji Allah kadai ya sani,saboda shi kanshi falon yayi mata girma,batason ne a matsayinsa na baqo kuma muhallinsa ne ace ya kwana a nan
"Ki koma inda kika saba kwanciya ki kwana" kafada ta maqale
"Ka barshi zan kwana anan" bai sake ce mata komai ba ya juya ciki.


Duk yadda jikinsa da idanuwansa suka buqatu da barci amma hakan taqi samuwa,yayi juyi saman gadon yafi sau shurin masaki,tunda ya kwanta take masa yawo cikin idanuwanshi,komai yake dawo masa fes game da ita,yanayin daya ganta dazu zuwa yanzu daya shigo ya sameta tana bacci,tsaki yaja ya miqe ya zauna dirshan saman gadon sanda wayarshi ta soma ruri,


Tunda ya kalli number dake yawo yasan lili ce take kiranshi,hatsabibiyar matashiyar budurwar data takura rayuwarshi da sunan tana sonshi,saidai bayan soyayya da take masa tana da burin suyi soyayya irin ta watsewa wadda ita a wajensu ba wani abun aibu bane,tsaki ya kuma ja yana tuna sanda ta keta parlour dinshi a can ta taddashi har cikin dakin gadonshi,tun daga ranar bai sake yadda yabar gidan a bude ba,kashe wayar yayi baki daya bayan yayi rejecting call dinta,sake juyawa yayi ya kwanta rigingine yana addu'ar Allah yasa bacci ya daukeshi,saidai hakan bata samu ba,dole ya sauko daga gadon wani abu na kaikawo a ranshi,toilet ya shiga da niyyar daura alwala ko Allah zaisa ta sanadin haka baccin yazo.


Gefan gadonshi ya dawo ya zauna yana tsane ruwan alwalar,bayan ya gama ya sauke hannun rigarshin,haka kawai ya kasa sake komawa gadonshi,sai ya zura slippers dinsa ya tako a hankali zuwa bakin qofa ya budeta a hankali.


Idanunshi ya shuga wuwwulgawa cikin falon,can ya hangota lokon kujera a takure waje daya kanta na saman gwiwoyinta,qofar ya saki ya taka zuwa cikin falon
"Hasbunallahu wani'imal wakil" ta fada a zabure tana miqewa sanda taji motsin tsaiwarsa,ta tsorata sosai da sauri ya riqeta yana mamakin tsoro irin nata,ganin taqi nutsuwa waje daya ya sanyashi riqe dukka hannayenta yana fadin
"Calm down nine,khalipha ne" ya qarashe fada da dan qarfi don ya dawo da hankalinta kanshi,ajiyar zuciya ta saki don ta soma bacci ne taji wannan motsin,uwa uba dama a tsorace baccin ya dauketa,bai saki hannunta ba har zuwa dakin sannan ya zame hannayensa,da hannu daya yayi mata nuni na tahau ta kwanta,saita kalleshi sannan ta dubi gadon,ta taka a hankali zuciyarta na bugawa saboda tsoron data ji dazu.


🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶


A nutse ta tura qofar dakin anni bakinta dauke sa sallama don su gaisa,saboda bata samu zama breakfast tare da su ba ta tsaya gyaran sashen nasu,tadai kammala abun karin da tasan zai ishi kowa a gidan ta gyara dining din ta bar sashen,da fara'a saman fuskar anni take sa sallamar tata
"Maraba da takwara" murmushi aysha ta saki har wushiryarta na fitowa,tana yaba yadda annin ke mata,tana jin cewa inama inama ace ita tahaifeta,inama ace itace mahaifiyarta,kanta a qasa saboda ta fuskanci suna wata magana mai muhimmanci ne ita da khalipha wanda ya nutse cikin kujerar dake falon annin yana satar kallonta can cikin zuciyarsa yana mamakin sauyarwarta,waishin dama matan cikin hijabi akwai wani sirri na musamman da suke boyo ne ko kuwa wani abu ne ya sauyata?,iyaka saninshi da ita ba haka take ba,kunnuwanshi na sauraren muryarta da suke magana da anni,ita dinma yana jin kaman ba tata ba,kodai watannin daya diba ne yasa yake ganin komai ya sauya?,har suka gama gaisawa da annin da 'yan maganganunsu baice komai ba,furucin anni na qarshe ne ya dawo dashi
"Karki zauna haka na sanki sarai ki nemi abu kici" kanta ta kada sannan taci gaba da takawa don ficewa daga dakin,sai taji tana son ta harde,ba shakka akwai wani dake kallonta,wani nauyi take ji kamar yau ta saba shigowa falon annin
"Khalipha" anni ta kira sunanshi ganin hankalinsa nai tare da ita,cikin dakewa irin ta gigaggun maza ya soma shafa kanshi kafin ya maida idanunshi a kan annin,cike da basarwa yace
"Anni yarinyar nan tana karatun nan kuwa?" Dariya ke cin anni a qasan ranta,amma a zahiri saita dake gami da bata rai
"Me ka gani?" Kai ya girgiza da sauri,don idan ta tirkeshin kan me ya gani dinma baisan me zaya ce mata ba
"Babu komai"
"Aisai ka fadi abinda ka gani" ta sake fadi tana yin kicin kicin da fuska
"Ba komai anni....na lura bakison laifinta"
"Dole kace haka khalipha saboda kaga na qyaleka kan naka laifin ban tuhumeka ba,duk yadda taso ta boyen nasan abinda ke wakana"haquri sosai ya shiga baiwa annin tare da yi mata bayanin abinda ya kawo tsaikon dawowarshi
"ita zaka je kama wannan bayanin bani ba"ta fada tana miqewa,sai ya miqe tare sa annin yana dariya qasa qasa
"Anni yanzu gwamnatina ta rushe

Please Login or Register in order to submit comment