Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

nashi ya bata mamaki,yau ita hamid ya zaga kanshi tsaye ba wani damuwa kamar ya zagi banza
"Baiwar uwata?,idan ita din ba baiwar uwata bace ni baiwar uwarka ce?,ko yarjejeniyar da mukayi kenan da kai kafin aurenmu?,ka wargaza komai ka saba duk wani al....." Bata samu damar qarasawa ba ya kasheta da mari sannan ya nunata da yatsa
"Kin tabbata cikakkiyar mara tarbiyya wadda ba'a koya mata tarbiyya ba daga gidansu,uwata zaki zaga?,tun kafin ma dawo gidan nan labarin wulaqanta min 'yan uwa da kikayi ya iskeni,da mike zancan na karya duk alqawarin da nayi an gaya miki bansan don me mike sona ba?,bansan samari nawa kikayi ba kafin ni duk kika qisu saboda kina tunanin na fisu arziqi?,dama an gaya min din me kike sona yanzu gashi kuwa ya tabbata,wannan aishan da kike qi kike gayamin maganganu kullum a kanta din na tsaneta tota fiki,na tabbatar da ita na aura bani da matsalar komai kome zan ciyar da ita kowanne umarni zan bata,saboda haka ta fiki wawiyar mace wadda bata iya komai ba,kuma duk kudin dana kashe miki da asarar da siyayya masu tsada da kika dinga roqa ina miki duk sai na fanshe abuna,an gaya miki ni sakarai ne bansan ciwon nema ba?,to idan baki sani ba bari in gaya miki yau free,ba'a cin kudina haka siddan koda kai ka kawoni duniyar,bare ke da mika tsinceni da haqorana talatin da hudu cif" hannu ya zura cikin aljihunsa ya fito da envalope ya farkesu,kudi ne suka zubo daga ciki,ya qirgasu ya zari wani abu daga ciki ya watsa mata sauran
"Gashinan inji tsohonki,mun hadu a banki naje kai kudi shima tasa ta kaishi,na cire kudin wainata da kikamin asara,canjin zanje naci abincin da baki girka ba" ya fada yana maida uban kudin daya zara da sunan kudin wainar fulawa,sannan ya isa gaban dustbin din data ce ta jefa wainar ya zura hannu ya laluba ya cirota a keda ya fice ya jefawa karnukansa,ba bata lokaci suka hau ci don ya koya musu cin komai,babu abinda basa ci.

🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶


Cikin qanqanin lokaci komai da komai ya kammala na karatunta,sunanta na gaba gaba cikin jerin sunayen daliban da suka samu admission,kusan tana zaune akayi mata komai,zirga zirgar da tayi bata kai ta kawo ba abinka da wadanda keda masu gidan rana,ta riga data zabi zaman hostel,ba don komai ba donta samu yin karatu sosai yadda ya kamata,sannan tanason hankalinta ya ttara waje guda,saidai kuma zata dinga zuwa gida duk weekend.

Sam anni bataso haka ba,don zuwa yanzun ayshan kusan itace mai kula da komai na annin,hatta da kayan sawarta,kitsonta abincinta da sauransu,uwa uba sabo daya shiga tsakaninsu,tana matuqar jin dadin zama da ita,duk yadda take hasashen ayshan saita karanci ta wuce nan,wata baiwa Allah yayi mata ta daban wadda ko ita ba lallai tasan da ita,saidai annin bata nuna rashin jin dadin nata ba don kada ta rage mata qwarin gwiwa ko taji babu dadi,don ta fuskanci sosai takeson karatunta,gefe guda kuma amal na dan tabukawa kada ta fuskanci ta raina qoqarinta ne itama.


Ranar da komai ya kammala ya sameta a falon anni,ta riga data saba bacci ne kawai ke maidata nasu sashen,tana zaune saman kujera annin na qasa tana lallabe mata kanta,zanen hausa take mata guda shida duk bayan kwana goma,da yake annin akwai gashi tubarkalla kasancewarta buzuwar bafulatana har bayanta jelar ke fitowa.


Dukkansu suka mishi sannu da zuwa yayin data maida kai tana ci gaba da gyarawa anni kai,shi kuma suna hira da annin,jifa jifa yakan daga kai ya dubeta sannan yaci gaba da abinda yake,tunaninsa daya ya take ji cikin ranta a yanzu haka data rasa soyayyar mahaifiya?,shi kadai yasan dadin da yake ji aduk sanda ya zauna suna hira da anninsa,ita kuwa bata taba samun irin wannan damar ba tsahon rayuwarta,amma har ta iya jure hakan ta hadiyeshi cikin zuciyarta
"Sannu takwara....kije ki nemi abinci kici kuma hakanan,tun dazun banga ko ruwa kinkai bakinki ba" murmushi tayi tana goge hannunta a kunyace tace
"Azimi nake" duban khalipha anni tayi
"Ah...amma kasan tana azumi baka gayamin ba bare a tanadar mata wani abun?" Dan dawurwura yayi sannan ya sake kallon ayshan kafin ya dubi anni,ya bude baki zaiyi magana ta rigashi
"Ban sanar mishi ba anni,saboda hanani zaiyi" ajiyar zuciya ya saki donta qwaceshi,ya bude bakinsa ne kawai ba tare da yasan me zai gayawa annin ba
"Ma sha Allah....bari nasa su atika sumiki wani abun haka"
"A'ah anni duk abinda suka dafa zan iya ci" tana gama fadin haka ta tsinkayi muryar khalipha yana qwalawa laure kira daya daga cikin ma'aikatan,cikin sakan goma ta bayyana a falon
"Idan akwai garin flour kiyimin dan wake yanzun,ayi mishi hadin salad pls"
"In sha Allahu yallabai" ta fada cikin girmamawa gami da miqewa ta juya zuwa kitchen da hanzarinta,yana waiwayowa suka hada ido da ayshan,saita sadda kai tana mamakin ya akayi yasan abincin da take matuqar so?,sau tari a gida takai duk sanda akayi danwake ko za'a daketa saitaci,hakanan koyaya aka bar ragowa bata barinsa saita bi ta cinye komai sanqarewar da yayi shida dafaffen wake(qulu),sharewa shima yayi kamar baiga kallonshi data sata ba,janyo jakarshi yayi ta office daya shigo da ita ya bude ya fito da da wasu takardu ya miqawa ayshan yana mata bayani
"Komai ya kammala,on 29 zaku fara lactures in sha Allah,yau saura sati daya kenan"tuni hawaye ya cika idanunta,kuka yana son qwace mata tana yunqurin danneshi,ta rasa me zatayi me ya kamata tayi,kaman wannan ne karo na farko da zata soma karatu haka take ji,sai ta zamo daga saman kujerar ta durqushe a gabansu shida annin
"na gode,ubangiji ya saka da mafificin alkhairi,Allah yayi muku sakamako da aljannarsa madaukakiya,Allah y...."
"Ya isa haka ayshatu...wannan addu'ar duka kina iya mana ita a zuciya,tashu ki tafi abinki,ki saka a ranki kamar a gidanku aka miki hakan" da qyar ta iya miqewa saboda kuka,inama ace a gidan nasu ne,inama ace ahalinta ne ke mata haka,duk wata soyayya da zata gani daga garesu a yanzu ba shakka akwai dalilin da yasa suke mata ita,ba haka kawai bane,da wannan kukan takai kanta sashensu ta zube saman kujera tana ci gaba da rerashi.


Gab da magariba yabar wajen annin don zuwa ya daura alwala ya wuce masallaci,tura qofar yayi bakinsa dauke da sallama,saman kujera ya hangota nannade waje guda,sheshsheqar kukanta da jan majina na fidda sauti kadan kadan,tsaiwa yayi yana dubanta duk da baya iya ganin fuskarta,duk sanda wata mace mai shekarun hajar ke kuka sai ya dinga jin kamar itace take kuka awancan lokacin da har yau ya kasa bacewa daga qwaqwalwarsa,lokacin daya sakawa suna da baqin lokaci,shi yasa a yanzun kukan nata ke sokarsa sosai,takawa ya soma yi zuwa wajen da take sai kuma yaji ana knocking,hakan yasanya ya sake juyawa zuwa wajen qofar ya bude,larai ce dauke da kayan kwanukan abinci,nuni yayi mata data aje,ta aje din kuwa a ladabce ta juya tabar wajen,ya sunkuya ya dauki kwanukan dai dai sanda ake qwala kiran sallar magariba,saman tebur din dake daura da ita ya aje
"Kukan ya isa haka,idan kuma a fasa makarantar ne kuma toh" da sauri ta tashi zaune tana hadiye kuken gami da qoqarin goge kyawawan idanunta da suka dan rine saboda kuka,ganin haka ya sanyashi wucewa ciki ya barta nan.


Sanda ya fito zai wuce masallaci tana zaune a wajen,jiranshi take ya fito ta shiga ta wanke bakinta,don idan daya yana cikin dakin dayan bai shiga har sai ya fito,har gwarashi wani lokaci zuwa lokaci yakan shiga idan akwai uzurin da bazai iya zaman jira ba,kaman zai wuce office yayi mantuwa zai dauki wani abu da makamantansu,dukkansu suna jin nunansu kaman baqi,saboda ba wanda ya taba rayuwa da wani jinsi daba nashi ba amuhalli guda sai wannan lokaci.


A bakin gate suka hadu da mus'ab da haidar,tun fadan daya yiwa mus'ab din bai sake kamashi da laifin rashin zuwa salla isha'in ko asuba ba,tare suka jera abinsu gwanin sha'awa,akwai qauna da fahimtar juna mai tarin yawa tsakaninsu,duba da wahalar da suka sha a baya wadda ita ta sake haifar da danqon qaunar junansu,haidar ke bare dabino yana ci khalipha ya kalleshi,yasan ma'anar kallon,da sauri yace
"Sorry yaya,kasan yau azumi mukayi ni da anty,ban samu na tsaya nayi bude baki ba kar jam'i ya wuceni,kuma ba'ason asha ruwa baka kai komai bakinka ba" bai sake cewa da shi komai ba,saidai yana mamakin yadda duk 'yan gidan keji da ayshan,yasan lallai ita rinjayi haidar ya soma azumin,don kwata kwata basa shiri da azumi.


🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶


Tun daga cikin dakinta take jiyo muryar hamid yana qwala mata kira,sosai kiran nashi ya bata tsoro har tana tuntube garin sakkowa saboda qara dage murya da yake wajwn kiran nata,a kitchen ta sameshi a tsaye,yayin da me aikinsu itama take tsaye gefe guda kantaba qasa kamar kazar da aka jiqa a ruwa,tana shiga ya dago mata kwalin lipton dinsu yana dubanta,sam bata fahimci me yake nufi ba sai da yayi magana
"Ya akayi ganyen shayin nan ya qare tun yau?"
"Kaman yaya?" Ta tambayeshi cikin takaici tana yamutsa fuska
"Tunda baki gane ba bari nayi miki bayani dalla dalla,sanda na kawo lipton din nan na qirgashi a gabanki na kwana sittin ne,ya akayi ya qare kwana ashirin kacal" hannayenta ta saka ta riqe qugunta duka biyun tana kallon hamid,itakam yanzu abun nashi bayan haushi ma tsantsar mamaki yake bata,koda wasa wani yace zaiyi abinda yake din yanzu sai anji kansu
"Ganyen shayin banza ganyan shayin wofi da zaka dinga yimin wannan kiran mafarautan saboda shi,kai yanzu hamid bakaji kunya ba saboda ganyan shayi kake daga jijiyar wuya haka,ohkey toni ban gaji tsiya ba,bazan bi wani lissafin ganyan shayi ba wallahi"
"Eh saboda ai bakisan ciwon kudi ba bakisan ciwon nema ba,yadda nayi almubazzaranci a waje haka ma yanzu kikeson naci gaba?,toba kudin banza gareni ba,lipton kuma saidai kici gaba da siya da kanki har kwana sittin ya cika" ya qarashe fada yana wurga kwalin a shara ya juya fuu ya fita daga kitchen din da alama ma ficewa xaiyi daga gidan donya shirya fes abinshi cikin suit kai baka ce shike magana kan lipton ba,binsa tayi da sauri tana tsaidashi,bai tsaya din ba har sai daya shiga motarsa yana shirin tada ta
"Man shafawa ta ne ya qare....inason wani irin na cikin kayana shine ya karbeni" dariya ya saki yana kallonta kamar yaga mahaukaciya
"Da Allah matsamin kina batamin lokaci kar baqina su wuce kija min asara,don na fuskanci ke bakisan darajar kudi ba"
"Wai hamid lafiyarka kuwa anya na asiri akayi maka ba?" Ta fada cikin harxuqa da mamaki,dariya ya sakeyi sannan ya ziro qafarsa daya waje kaman wanda ya fasa tafiya ya kalli cikin idanunta sosai
"Asma'u,kudi kika fiso a rayuwarki su na saka na shigo dake gidana,kin zaci ni wawa ne wamda baisan ciwon kudi ba saboda.ina da su ko?,toko dana tara bana almubazzaranci bane,kuma kaina na tarawa ba wani ko wata ba,idan zaki koyi rayuwar akwai da babu ki koya,shine kawai zaisa mu samu zaman lafiya ni dake matuqar ko zakici gaba da tambayata wani abu daya shafi in kashe kudina baki gayyaci zaman lafiya a gidan nan ba" yana kaiwa nan yaja murfin motarsa ya rufe ya kunnata ya dannawa mai gadi horn yaja motarshi ya fice.


Kuka asma'u ta saki ta juya zuwa cikin gidan a guje tana addu'ar Allah ya tasheta daga wannan mummunan mafarki da take,idan kuwa har ya tabbata mafarkin take ita da hamid ko hanya sunbar hadawa,sai data tabbatar cewa ba mafarkin bane ta soma tunanin sihiri 'yan adawa suka mata suka juyar mata da hankalin hamid dinta,banda haka mutum mai kudi kamar hamid ace yana maqo irin haka ba shakka da wata a qasa,hakan ya sanya ta dauki wayarta ta lalubi mommy don kai mata qorafi kamar yadda ta saba,don ko misqala zarratin asma'un bata da juriyar riqe damuwa ko solving matsalolin da duk zasu taso mata da kanta.


*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*
35

Kusan tunda suka taho ita da shi fuskarta ke a cunkushe,ba don komai ba sai don batasan abinda zata je ta tarar ba a gidan,sam bata wani sha'awar zuwa gidansu hamid din,duk da cewa tunda sukai aure bata taba zuwa ba sai yau daya matsanta mata sai taje,saboda zaiyi tafiya ne shima,gaba daya haushin duk wata tafiya tashi take,a yanzu baya cikakken sati daya a gida,bashi wancan gari bashi wannan,bata isa tayi qorafi ba yanzu zai hauta da gorin yana yawon neman abinda ta aureshi ne saboda shi.


A harabar gidan ya tsaida motar sannan ya kasheta,fitowa yayi hakan ya sanya itama dole ta fito tabi bayanshi tana hade fuska har suka isa falon gidan.


Qannenshi ne zaune gaban t.v suna kallo,maza biyu mata biyu sune wadanda suka rage ba'a aurar ba,mahaifiyarsu na tsakiyarsu,kowanne yaci uban asma'u a girman kai da tabara,hakan ya sanya yayansun kawai suka yiwa sannu da zuwa kowa yaci gaba da sabgarsa,babu abinda uwar tace musu don ko ita bata nuna tasan tare suke da ita ba.


Tana rakabe gefe suna ta hirarsu a qalla wajen minti talatin sannan hamid yajiyo
"Au hajiga ga tare fa muke da ita" gilashin fuskarta tadan saukar kadan ta kalli asma'un sosai sannan ta jashi sama
"Na ganta....sai yau taga damar zuwa?,koda yake ai ba yau muka fara ganinta fuskarta sananniya ce" ta fadi hakan da manufa biyu,don sanda hamid din ke neman aurenta bini bini zai kwasheta suje gidansu,saidai babban abinda ya daurewa asma'un ganin yadda dukkaninsu suka sauya,kaf dinsu ba haka suke mata ba a baya kafin ta auri dan uwansu,hakanan suja sha yata sukaci hitarsu suka godewa Allah,ko ruwa ba wanda ya kalleta da shi,sai daga qarshe ne da hamid din ya cewa qanwarsa ta bashi ruwa ta hado da asma'un,saboda tsabar baqinciki da bacin rai ko kallon ruwan bata yi ba har suka tafi.


Cikin mota ta dinga fushi da kumbure kumbure,saidai ko kallo bata isheshi ba bare ya nuna yasan tana yi ba,har daga qarshe data gaji ta tanka
"Amma dama kawoni gidanku kayi don a cimin fuska?" Wani juyowa yayi ya dubeta ya watsar kafin ya bata amsa
"Kamar yaya?"
"Baka ga abinda akayimin ba kenan?"
"To su kike su tashi suyita rawa suna tsalle sunga halittar da basu taba ganin irinta ba,ni da Allah banason fitina kinji ko?" Nan sa'insa ta kaure a tsakaninsu,bata yi shuru ba har sai data ga yana da niyyar kai mata mangari,koda suka je gida a fusace ta fita daga motar ta buga mishi qofar motar
"Kiyi a hankali,don wallahi idan kika sake kika yimin barna taki zan siyar na gyara" ya fada cikin daga murya yadda zata iya jiyowa.

🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶🧶


Kwanaki biyar ya rage su soma lacture ta shirya tsaf don tafiya makaranta,duk wani abu daya dace babu wanda ba'a siya mata ba,siyayya irin ta 'ya'yan gata,itadai kallon komai take kamar almara,kaya kaman wadda zata shekara a can,hatta da ruwan sha khalipha bai bari ba sai daya siya mata,wani abun ma har kunyar kanta da kanta take ji duk da yadda anni ke bata qwarin gwiwa,sai take jin kamar ta zame musu wani kaya ta hadasu da hidimarta.


Tana tsaye a falon sashen nasu sagale da jakarta wadda ta zuba qananun abubuwa irin namu na mata,sai take jin kewa ta soma shigarta,jikinta ya danyi sanyi kamar zata wani garin ta barsu,a haka khalipha ya fito ya taddata,atm card ya miqa mata yana kafeta da idanunshi,a sanyaye ta amsa tana son jin qarin bayani
"Duk sanda kike da buqatar wani abu ki cire kudi ki saya,naki ne accnt dinki ne,sati mai zuwa idan Allah ya kaimu da rai da lafiya nima zanyi tafiya,zanbar qasar na tsahon shekara biyu" saita daga kai tana kallonshi,hakanan zuciyarta ta raurawa,sosai take jin ba dadi,kaman cewa yayi idan ya tafi bazai dawo ba,ganin sun hada ido kaman yadda suka saba sai kowa ya kau da kanshi
"Zan dinga zuwa a duk sanda na samu chance Ya fadi kamar ya karanci abinda yake zuciyarta,kunya ce taji tana neman kamata,kardai ace ya fahimci abinda take saqawa a ranta,saita sunkuyar da kai
"Allah ya bada abinda za'a je nema,ubangiji yayi jagora ya kade dukkan abinqi"
"Ameen kema haka" ya fada a taqaice,kasancewar tun jiya yayi mata duk jan hankalin daya kamata,iya gajeran lafazinsa kawai yayi mata dadi a rai
"Na gode" ta furta a sanyaye.


Qwalla ce fal idanunta sanda suke sallama da anni,har mus'ab ya dinga sheqa musu dariya abinsa,khalipha kam falo ya koma yayi zamanshi abunsa,kewarsu take tun kafin tabar gidan,haka suka rakota har bakin mota,inda haidar zai kaita.


Rufe motar tayi ta daga kai a hankalin,take idanunta suka shiga cikin nashi,yana tsaye bakin window din da take zaune hannunsa harde a aqirji,shima ita yake kallo,sai qwallar da take tattalin kar ta zubo ta silalo saman fuskarta,sakin hannayen nashi yayi ya bar side dinta ya koma mazaunin driver,duqawa yayi ta window din motar dai dai saitin haidar,batasan me ya gaya mishi ba na tsahon minti daya kafin ya miqe yana cewa
"Allah ya tsare hanya,a kula da hanya"
"In sha Allahu yaya" haidar ya fada yana tasar motar,yana nan tsaye hannyensa goye a bayansa har motar tasu ta fice daga gidan.


Kadan kadan taci gaba da fidda qwalla tana qoqarin sharewa,haidar baice mata komai ba har sai da sukayi tafiya ta kusan minti goma sannan ya dan saki dariya
"Nikam kukan nan bansan na meye ba?,anya kukan rabuwa da anni ne bana rabuwa da yayanmu bane?" Dan harararshi tayi tana fidda qaramin murmushi,daga bisani tayi qoqarin controlling hawayenta,saidai duk da haka zuciyarta babu dadi,wayarshi ya zaro ya kira khaliphan,da alama shi ya bashi umarnin yin hakan,miqa mata wayar kawai haidar yayi yana murmushi,hannu ta sanya ta karba gami da karawa a kunnenta ba tare da tace komai ba
"Kina kuka kaman wata baby?,kinason dagawa mutane hankali,ko baki shirya ba adawo dake?" Girgiza kai tayi kama tana gabansa sannan tace
"A'ah"
"Allah ya bada sa'a" ya fada cikin low tune
"Amin na gode"
"Bashi wayar" saita waiwaya ta miqawa haidar dake boye dariyar da batsan ta meye ba,magana sukayi da bata wuce ta minti daya ba ya katse wayar yana 'yar mita
"Sai wani jaddadawa yake nayi tuqi a hankali waishi me mata,muma dai mun kusa in sha Allahu mu fara hura hanci muma" daroya ma haidar din ya bata,ita ta sani kawai dai yana jaddadawar ne saboda dan uwanshi,amma ita yaushe takai nan,haka haidar ya dinga janta da hira har ta dan saki jiki,yana bata labarin makarantar da yake can suka fara yi shi da mus'ab kafin daga bisani khalipha ya fitar da su waje.


Ajiyar zuciya ya saki yana maida wayar aljihunsa,baisan me yasha kanshi da kukanta ba harya buqaci jin yata kasance,hakanan kawai yaji yana da buqatar jin haka,sai ya sake sauke wata ajiyar zuciyar yana duban wami littafinta data dauko ta manta dashi saman kujera.


Awa guda suka isa a haka donsu tsaya cin abinci a wani gidan cin abinci dake hanya,itakam aysha har sannan babu abinda taci saboda dama can abincin safen ba damunta yayi ba,haidar na tare da ita har aka gama shigar mata da kayanta,kulawa ta musamman ta samu daga ma'aikatan dake kula da hostel din,bata san me yasa ba,saidai tuni khalipha ya gama sallamar kowa a cikinsu,hakan yasa suke ankare da zuwan ta,saidai komai ya zama normal ya tabbatar babu wani abu da zata sake buqata kaman yadda yayanshi ya umarceshi sannan yayi mata sallama,sanda zai tafin ma dai kamar zata bishi,hakanan dai ta daure ta juya zuwa ta koma hostel din.


Su uku ne a dakin,saidai sanda taje mutum biyun sun gama shirya kayansu basa nan,da alama ma ba ranar su sukazo ba,kasancewarta ita daya a dakin ya bata dama itama ta zauna ta jera komai nata a muhallinsa yadda take da buqata,koda ta gama an kusa sallar la'asar,sai kawai ta kunna gas ta dora jallop din sphaghetti sannan ta shiga bandakin dake manne da dakin ta dauro alwala.


A cooler ta aje abincin bayan ta gama,ta bude barander dake bayan dakinsu ta wanke komai ta tsaftaceshi,bata jin yunwa sai kewar gida dake damunta,tana gefan gadonta tana qarewa dakin nasu kallo,komai neat gwanin sha'awa,fata kawai take Allah yasa musulmai ne,masu halin qwarai,sai ta kasa zaman dakin,ta zari hijabinta ta zura ta lalubi muqullin dakin tanufi qofa tana duba wayarta,aliya takeson kira,yau kwana uku basu samu sunyi waya ba,kowa yana busy.


Qofar da aka turo saura qiris ta daki goshinta,da sauri taja baya tana duban mai shigowar,matashiyar budurwa ce wadda duka duka shekarunta basufi na ayshan ba,doguwa ce bata da jiki,kalarta choculet ce mai daukan ido da sheqi,tana da doguwar fuska da jerarrun fararen haqoranta,idanu ta zaro tana fadin
"Ah sorry sister....sannu Allah yasa ban bigeki ba" murmushi aliyan tayi,yanayin yadda take magana kawai ya isa ya gaya maka tana da surutu
"Babu komai,baki sameni ba"
"Alhmdlh....kece ragowar room partner dinmu da baki qaraso ba ko?" Ta fadi fuskarta qunshe da murmushi wanda ke nuna haka yanayinta yake,kai aysha ta gyada
"Eh"
"Thank god...amma naji dadi....ni sunana halimatu abdullahi musa,amma anfi kirana da hanan,daga hotoro nake,saidai iyayena duka na zaune a abuja,kefa?"
"Sunana aysha umar modibbo"
"Fulani girl?" Hanan ta tambayeta tana dage gira,dariya aysha tayi,yadda hanan din bata da wahalar sabo yake bata mamaki,kai ta gyada mata again
"Kice na shirya,na kusa koyon fillanci" tare suka sake sakin dariya gaba dayansu
"Well,na tsaidaki da surutu na ko,naga kamar fita zaki da alama uzuri gareki" komawa ayshan tayi da baya ta nemi wajan zama,don zuwa yanzu kuma bata da wani sauran dalilin fita
"A'ah,zaman shuru ne dama yamin yawa nace bari na dan fita naga yanayin hostel din"
"No more loniless tunda na dawo" ta fadi still tana murmushi gami da zube jakunkunan dake hannunta
"Naje na amshi saqo ne daga wajen uncle dina....ga wata azababbiyar yunwa da nikeji...nace ma ya tausayan ya sayan wani abu amma yaqi" ta fada tana kwabe fuska,dariya aysha tayi tana nuna mata cooler din data zu a abinci
"Ga abinci can saiki diba kici" ido ya fiddo
"Kai amma kin taimakeni wallahi,dama maman hunaifa nake saka ran idan ta rigani dawowa na samu daga wajenta,to itama kinga shuru" ta qarasa fada tana bude abincin,qamshin ya daki fuskarta saita lumshe ido
"Tun kafin naci ma nasan zatayi dadi wallahi,sauko muci"
"Kaman a qoshe fa nake"
"Ba wani nan,saidai idan nima bakiso naci ne" jin haka ya sanya aysha ta sauko,hanan ta zuba musu tare suka soma ci tana ci gaba da jan aysha da hira,itadai kallonta kawai aysha take,tana mamakin saurin sakewa irin na hanan,bata da baqunta sam,saidai ta lura tana da kirki matuqa,tana da hankali tsafta sannan uwa uba da ganinta yar qwalisa ce wato gayu,da haka suka gama cin abincin,suna tsaka da wanke hannunsu aka sake turo qofar dakin nasu,wata matashiya ce ta sake shigowa,shigowarta ya sanya hanan yin dif,da aysha suka gaisa sannan ta dubu hanan
"Kin dawo amma koki sanar min?"
"Babu buqatar hakan tunda gashi yanzu kin ganni" hanan ta fada tana miqewa ta bude bandakinsu ta shiga,ta dade matashiyar a tsaye hanan bata fito ba,hakan shi ya tilasta mata tafiya,sai data tafi sannan hanan ta fito tana jan tsaki gami da mita,ita dai aysha naji bata ce komai ba hakanan bata tambayi dalili ba,saboda ba dabi'arta bace.


Hanan na idar da sallah aka sake knocking,wata matar ce ta sake shigowa,fara ce itama qal da ita,ba siririya bace haka bamai qiba ba,tana sanye da doguwar rigar material da mayafinta,a qalla zata girmewa su aysha da shekara hudu haka,hannunta rungume da yarinya wadda bata wuce shekara daya ba,sai jakar mata data ratayo,bayanta security ne mata dauke da jakankuna manya guda biyu,da sauri hanan ta miqe tana fadin
"Oyoyo hunaifa" ta karbe yarinyar daga hannun mamata,murmushi matar take idanunta na kan aysha
"Sannu da zuwa" ayshan ta fada itama tana murmushi
"Yauwa

Please Login or Register in order to submit comment