Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

jefa lambar tasa,can cikin black list ta ganota,cikin hanzari ta cireta daga black list din sannan ta soma kiransa.


Dai dai lokacin yana lafe a bayan motar suna tafe, mahmoud nata tambayar sa ya akayi a gefe guda kuma yana sheqa masa dariya,qarar wayar ita ta sanyashi bude manyan idanunshi da suke a rufe,waya ce da ita daya keda number,wadda dama dominta ya siya wayar da layin,hannunshi ya kai ya daga wayar ya kara a kunnensa ba tare da yace komai ba
"Ka dawo ka amshi kudinka,ni basu nake so ba,gwadaka dama nake,kuma alamu sun nuna kaci wannan jarrabawar" irin maganganun data ringa jerowa kenan duk a niyyarta nason amintar da shi da gamsar da shi,murmushi kawai ya sake mata wanda ya ratsa kunne da qwaqwalwarta
"Am sorry to say,ida na wuce aji bana maimaita shi.....sai wata rana" ya qarashe fada yana cire wayar daga kunneshi,bai tsaya a nan ba sai daya cire layin ya karyashi gida biyu,ya sauke glass din motar qasa kadan ya watsar ta window sannan ya maidashi yadda yake ya koma jikin kujerar motar ya sake lafewa ba tare daya bi ta kan dariyar mahmoud ba,hannayensa ya saka ya rufe kunnuwansa saboda yadda mahmoud din ya hanashi sakat,daga bisani da yaga baida niyyar barinshi ya huta ya shammaceshi ya kai masa naushi,Allah ya taimakeshi ya kauce yana cewa
"A'ah,karka lahantani,haka kawai bani na kar zomon ba ai,danma ka samu wai ina rakoka,tunda an kasaka ba shikenan ba sai ka sake sabon lale....amma fa ka riqr a ranka,'yammatan zamani indai zaka ci gaba da zuwa musu a haka za'a dade ana kasaka" dariya ce ta subucewa khalipha ba tare saya shirya ba,suka dan dara tare da mahmoud din,shi kansa lamarin na bashi mamaki gamibda daure masa kai,karo na uku?,karo na uku duk tafiyar ta kasance iri guda?,sai yaushe?,sai yaushe zaiga sauyi,zaya so yaga wannan rana qwarai.
*_HUGUMA_*



0⃣3⃣

Tsaye yake cikin tafkekan dakin taron a gaban wani hamshaqin teburi wanda yake dauke da aqalla ma'aikata kimanin mutuk arba'in,hannunsa guda dafe yake da gaban teburin yayin da daya hannun yaketa wulwulgashi cike da gwanancewa duk da baisan yana yi ba,da alama bayanin da yakewa ma'aikatan da suka bashi dukkan nutsuwarsu ya dauki zafi,lokaci lokaci yana daga daya hannun nasa dake dafe da teburin yana duba agogon hannunsa,wannan kadai ya isa ya nuna maka mutum ne mai kiyaye lokaci da kuma alfanunsa.


"Is there any problem?...." Ya qarashe jimlar tasa ta qarshe yana duban fuskokin ma'aikatan,saidai kowanne ya gamsu girgiza kai suka dinga yi daya bayan daya,ganin haka ya sanya shi ya soma tattare kayanshi dake saman teburin tare da bada umarnin a rufe taron da addu'a kaman yadda yake a qa'idarsa.


Shine mutum na farko da ya soma fita,shahid ya rufa masa baya suna magana qasa qasa,a bakin hall din daya daga cikin mutanen dake tsaye a wajen ya karbi kayan hannunsa sannan yabi bayansa har cikin elevetor wadda bata saukesu ko ina ba sai hawan qarshe na kamfanin inda office dinsa yake.


Mahmoud ne kawai zaune cikin office din ya tasa computer a gaba da alamu wani aiki yake ragewa mai muhimmanci Hannu mahmoud ya baiwa shahid suka gaisa cike da alamun cikakkiyar sanayya a tsakaninsu bayan security din dake riqe da kayan khaliphan ya aje ya fice,yayin da khalipha ya wuce kai tsaye bakin freezer ya dauki ruwa ya sha bayan ya rage suit din jikinsa kana ya shige toilet,alwala ya daura sannan ya dawo cikin office din ya tadda shahid da mahmoud suna hira,wadda fiye da rabinta abinda ya shafi kasuwancinsu ne,daya daga cikin wayayoyinshi wadda ke dauke da lambobin dukkan mutanen daya baiwa muhimmanci a rayuwarsa lambarsu ke ciki,kai tsaye ya nufi bakin daya daga cikin windows din dake cikin dakin office din wanda kai tsaye zaka iya kiransu da qofa saboda kadan ne ya rage basu kai girman qofar ba,saidai glass ne zalla a jiki wanda hakan zai baka damar gano ainihin farfajiyar companyn daga sama har qasa.


Bugu biyu aka daga wayar,ya sauke ajiyar zuciya sallamar matar na ratsa kunnensa,cikin sanyin murya kaman yadda halittar muryarshi take ya amsa sallamar sannan yace"Anni...barka da warhaka"
"Barka kadai khalipha,kun fito daga taron ne?"
"Mun fito ammi,saidai aci gaba da yi mana addu'a Allah yasa mu dace"
"Ubangiji ya dafa,ya shiga lamarinku,ya zama jagora a gareku,ya albarkaci rayuwarku". Cike da jin dadi yaketa amsawa da ameen,idanunsa lumshe yana shafa qirjinsa yana jin zuciyaraa wasai
"Ya jikin anni?,kinsha maganinki na rana,naga lokaci yayi"murmushi ta saki cike da qaunar yaron nata
"Khalipha kenan baka gajiya?,kaman ba awannin da suka shude muka gama waya da kai ba,jiki alhamdulillah,magani kuma ina gama sha kiranka ya shigo"cikin murmushi ya amsa
"Ya za'ayi na gaji da jinki anni....Allah ya qara miki lafiya mai dorewa"
"Allahumma amin khalipha,Allah yayi albarka"
"Ameen anni...sai na dawo"
"Allah ya tsare" ta sake ambata cikin nuna kulawa da qauna,ya amsa sannan ya kashe wayar yana murmushi,abubuwa da yawa na dawowa cikin kwanyarsa game da annin tasa,zai iya cewa baiga uwa irin tashi ba,kuma baya zaton za'a samu,anninsa da taban ce ko cikin halittun ubangiji,da wannan zancan zucin ya qaraso inda su mahmoud suke.


🧶🧶🧶


Zaune yake gaban annin tashi cikin shigar qananun kaya na t shirt da trouser,qafafunshi tanqwashe gabanshi kuma plate ne wanda ke dauke da tuwon shinkafa miyar water leaf da ogu wadda ta wadata da ganda busashshen kifi da kuma tsokar nama,a nutse yake cin abinci gefe guda suna hira da anni,hirar dake nuna tsantsar shaquwa dake tsakaninsu,kallo daya zaka yi musu ka tabbatarwa kanka lallai akwai saboda da shaquwa mai qafi tsakaninsu
"Khalipha..." Ta ambata a hankali wanda hakan yasa ya dago kanshi yana dubanta sannan ya amsa
"Wai sau yaushe zan daina jiran ganin zuwam surukata?" Murmushi ne ya subuce masa,sai ya aje cokalin hannunsa ya fasa kai lomar da yayi niya,cikin kulawa da qauna yake dubanta sannan yace
"Kwanan nan anni,karki damu....addu'arki nake buqata kawai...ina son na kawo miki surukar da zata kulamin dake,surukar da zata daukeki a matsayin uwa....surukar da zakiji dadin zama da ita fiye dani yadda zanji" murmushi ya subuce mata,sai ta kada kai tana dubanshi
"Allah ya baka mace ya gari wadda zata zame maka majingina.....amma banda abin khalipha kana tunanin akwai irin wannan surukan yanzu?" Ta qarashe managanar tana dariya qasa qasa,don har ga Allah bata dauki burinta ta cillashi har haka ba,kullum dai addu'arta Allah ya bashi wadda zata soshi tsakani da Allah,nagartacciyar matar aure,dan marairaicewa yayi kadan sannan yace
"Anni,kin sha gayamin ba'a fidda rai da rahamar Allah"
Kai ta jinjina cike da gamsuwa tace"wannan haka yake,ubangiji ya maka zabi ja gari"
"Ameen" ya amsa yana daukar cokalinsa dinci gaba da cin abincinsa sannan yace
"Cikin sati na gaba haidar zai dawo gida hutu" murmushi tayi kaman ko yaushe
"Sun kammala jarabawar kenan"
"Eh sun samu hutu na wata biyu"
"Allah ya kai mana rai"
"Ameen" ya amsa yana daukar cup din daya cika da ruwa ya soma sha.

🧶🧶🧶


Da sauri sauri take tafiya hadi da duba agogon hannunta,qarfe tara da rabi na safe dai dai,mintuna talatin zata qara ta makara wanda hakan dai dai yake da rasa lacture dinta har na tsahon awa biyu.

Turus tayi gabanta na dan dokawa ganin asma'u zaune dafa'an cikin falon sanye da kayan barci wanda hakan ke nuna ko wanka bata yi ba bare a kai ga shirin fita,hannunta daya riqe da cup na tea tana kurba a hankali,daya hannun kuma wayarta ce samfurin iphone 8 take latsawa,jikinta sanyaye ta qaraso gefanta ta tsaya
"Ashe baki shirya ba anty asma'u?" Sai data shaqi iska kafin ta amsa
"Eh....sai eleven"
"Gashi goma lacturer din yake shiga..." Ta fada adamuwance,saboda daddy yana gidan,kusan yasan lokutan fita lactures dinsu daya ne,tare suke fita su kuma dawo tare a iya saninsa kenan,idanu ta daga ta kalleta ta watsa mata wani kallo
"Naga alamun raini na son soma shiga tsakaninmu aysha duk don saboda sharing abun hawa da muke ko...to ki shiga taitayinki,ke kanki kinsan wutsiyar raqumi tayi nesa da qasa,banda game game irin ja daddy da sunan zumunci saidai ki dinga hangoni ta cikin glass,to banson zura kai in zaki wuce kije ki hau abun hawa na haya ki wuce,dama dashi kika fi dacewa kuma dashi kika saba" tana kaiwa nan ta maqala earpiece a kunnenta da alama kira ne ya shigo mata zata amsa.


A kasalance take takawa a harabar gidan,zuciyarta cike fal da tunani,tana tsammanin kyautatawa na sanyawa kaso mutum koda baka sonshi,saidai ta gefan asma'u sam ba haka bane,mommy kuwa har yau ta kasa fahimtar a wanne aji take?,banbancin rayuwar data baro da wannan baya wuce sauyin muhalli,sutura da ilimi data samu ba,amma baya ga haka zata iya kiran yanayin da SAMMAKAL a wajenta
"A'ah,ina zaki a qafa aishatu?" Ta tsinkayi muryar daddy dake fitowa daga babban falonshi da yake ganawa da baqinsa,wanda sam bata lura da shi ba saboda zurfin tunanin da tayi,cikin hikima tayi qoqarin saisaita yanayinta,ta qaraso cike da girmamawa
"Ina kwana daddy..." Ta soma da gaisheshi,don yau duka basu samu damar haduwa ba,kasancewar jiya wajen goma na dare ya dawo qasar,ya kuma buqaci mommy ta tasota saidai tanajin sa'adda da tace masa ai ayshan tayi bacci,bayan idanunta biyu a sannan litattafanta ne a gabanta take dubawa,har lokacin data shiga dakin asma'u ta tadata kan ta fito daddynsu ya dawo amma asma'un tayi qememe tace ta gaji sa gaisa gobe,haka mommyn ta fito tace masa itama din tayi bacci
"Ina zaki aysha?" Ya sake jeho mata tambayar bayan sun gama gaisawa,bata da wata qarya da zata masa don kare asma'un wannan karon,saboda haka kai tsaye tace
"Makaranta" agogon wayarsa ya duba sannan yace
"Ina asma'un.....ina kuma drivern naku?"kanta ta duqar qasa sannan tace
" yau akwai banbancin lokacin fitar namu ne"
Kai ya jinjina,tun da can shi ba mutum bane mai yawan sanya ido da takura ba,hakan ya sanya abubuwa da dama kan gudana cikin gidan ayi musu kwaskwarima a sauya musu salo a bashi a haka ya karba ba tare da ya sani ba.


Dai dai sannan usama drivansa ya turo get din gidan ya shigo,saboda ga tsammaninsa a sannan zasu tafin,hakan ya sanya daddyn ya sallameta bayan ya miqa mata sabbin 'yan dubu dubu guda biyar da sukayi saura a hannunsa wanda da alama ya gama sallamar masu neman taimako ne wadan nan suka rage,tasan baya kyauta a dawo masa da ita hakan ya sanya tasa hannu biyu ta amsa tana jero masa godiya.


Ko cikin motar tunanin karamci irin na daddyn take,har abada kuma har ta mutu ba zata taba manta alkhairinsa da karamcinsa gareta ba,qarar wayar usama ta dawo da ita hayyacinta,daga jin yadda yake amsa wayar cikin daburcewa tasan akwai magana
"Kiyi haquri ranki ya dade,yanzu zan ajeta na dawo,na dauka yau bazaki fita bane...kiyi haquri" kalmar yayita maimaitawa,saidai hakan bai hana asma'u yi masa tas ba harda alakoron zagi ta kuma katse wayar
"Kaga....ajjiyeni usama kaje ka daukota saina qarasa wani abun hawan" yana bala'in ganin qimar ayshan saboda yadda take girmamashi tamkar yayanta,hakan ya sanya yace
"Barshi kawai na qarasa dake aishatu,koda na ajekin ma na koma daukota ba tsira zanyi ba" kai ta kada
"Ka ajenin babu komai...laifin ai zai ragu idan kace mata ajjiyeni kayi ba kamar ka kaini ka dawo ba" haka ya gangara gefan titi bada son ransa ba ya ajeta ya juya ya koma,ta tsaida adaidaita sahu ya qarasa da ita,idan da sabo ta jima da sabawa da halayen asma'u,ta haddacesu tsaf,shi yasa ba komai ke bata ranta ba.


*mrs muhammad ce*👑





🧣🧣 *DAURIN BOYE* 🧣🧣


*NA*

*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*


HASKE WRITERS ASSO

(home of expert and perfect writers)✍



0⃣4⃣



Qarfe daya ta fito daga library dake cikin makarantar don ta qarasa masallaci tayi sallah,tattaunawa suka sakeyi da sauran dalibai 'yan uwanta kan lacuture din da suka gama yi,qoqarinta da yadda kanta keja yasa yawa yawan dalibai ke maqale mata saboda ta sake ganar da su abinda basu fahimta ba,ta kammala alwalar tana gab da shiga masallacin wayarta tayi tsuwwa,dakatawa tayi ta ciro tana duba mai kiran,gwaggwo asabe ce take kiranta qanwa ga mahaifiyarta,mace daya tak da ko a baya tayi qoqari wajen ganin ta taimaki rayuwarta,tana daya daga cikin jerin jama'ar da bazata mance da su ba cikin rayuwarta,gefe ta samu ta jingina da wata bishiya dake wajen bayan ta katse kiran ta kirata da kanta don kada ta cinye mata kudi,gaisawa sukayi bayan 'yan tambaye tambayen lafiyar juna da suka biyo baya tace da ita
"Indo hala bakisan malam baida lafiya ba ko?"
"Kai haba?,tun yaushe gwaggwo?"
"Sati kusan biyu kenan,har a asibitin cikin gari ya kwanta,amma alhamdulillahi yanzu jikin nasa da sauqi an sallamoshi yau kwana uku yana gida ma"
"Ayyah,Allah ya sawwaqe ya bashi lafiya,in sha Allah zan shigo garim cikin qarshen satin nan,kiyi masa sannu kafin na iso"
"Zaiji,saikinzo Allah ya kawoki lafiya"
"Ameen gwaggo na gode,ki gaishemin da su lami"
"Zasuji" daga haka ta kashe wayar ta maidata cikin jakarta tana sauke ajiyar zuciya,ta tabbata ba don gwaggwo asaben ba babu lallai tasan da rashin lafiyar malam din,ta rasa wanne irin baqin abu ta aika har baqin jini yake bibiyarta wajen danginta na uwa da uba?,me tayi musu haka da kowa ma bai damu da rayuwarta ba?,a hakan ma takan iya cewa alhamdulillah da yadda ta tsinci kanta a yanzu akan shekaru kusan bakwai zuwa goma baya da suka shude,wanda abun yayi tsananin da har bata marmarin tunawa?,saidai har yau akwai wawakeken tabo da gibi cikin rayuwarta wanda batasan ranar da wannan gibin zai cike ba,batasan randa wannan babban jigon zai rabeta ba,batasan yaushe zai waiwayo ya dubi rayuwarta duba irin na idon rahama ba kaman yadda sauran 'ya'ya ke samu daga wajen uwayensu,da wannan tunanin ta qarasa cikin masallacin ta tada sallarta.

🧶🧶🧶🧶


Cikin nutsuwa ya kammala sanya maballan t.shirt dinsa wadda kudinta ya kama naira dubu biyu ita da wandon jeans dake jikinsa,har ya dauki turarensa zai fesa sai ya tuna,maidashi yayi wajensa,ya sake miqa hannu ya dauko wani daban wanda kallo daya zaka masa ka qiyasta kudinsa bazai wuce naira dubu guda ba idan yayi wuta ya fesa a jikinsa,duk da qarancin kudin turaren kuma bai cikin jinsin irin turarukan da yake mu'amala da su amma hakan bai hanashi jin dadin qamshinsa ba,saboda turare ne sanyi dake fita a hankali ba tare da ya daga hankalin wanda yake shaqa ba.


Gaban mudubi ya qarasa yana duban kansa,sai murmushi ya subucewa fuskaraa,duk da arhar kayan amma sun masa kyau
"Gwanjo" ya fada yana shafa gaban rigar dake jikin nasa zuwa saman cikinsa,yana tuna can wani lokaci baya daya shude,wani zamani da yayi tafiyar ruwa da dukkan farincikin rayuwarsu,wani qarni wanda basu taba tsammanin zaya wuce babinsa ya shafe kaman bai taba wanzuwa ba cikin littafin qaddararsu ba,tunanin ya saka ya zarce da sake gyara sumarshi da tayi matuqar yi masa kyau.


Kafin ya kai ga aje comb din hannunsa aka turo qofar dakin hade da sallama,mahmoud ne ya shigo idanunsa na kan khalipha,daga gani tambayoyi ne fal cikin qwaqwalwarsa wanda tun kafin ya zauna ya jefo masa daya
"Me haka ne malam?,ban fahimceka ba" juyawa yayi yana ci gaba da gyara kansa kafin ya bashi amsa
"Na zaci shigata kawai ta isa ta baka amsar abinda yake faruwa ko?"
"Wai har yau baka haqura ba?,baka kuma daina ba?" Ajjiye comb din yayi ta tako kusa da mahmoud din ya dauki qaramar vivo din dake aje kusa da shi ya bude bayanta ya soma qoqarin sanya mata layi
"Na sake haduwa da wata,kuma na fuskanci kaman wannan karon ina tare da nasara" dariya sosai mahmoud din ya bushe da ita harda kwantar da gadon bayansa saman gadon khaliphan,san dariyar mahmoud din bata dameshi ba saima yunqurin kunna wayar da yake bayan ya kashe nashi tsadaddun guda uku ya jefa cikin wata 'yar kyakkyawar briefcase dake nuna alamun da ita zai fita
"Me yasa kake wahalar da kanka ne babu gaira babu dalili my man.....ka saki kudi kawai ka auri duk kalar macen da kakeso kada ba jinsinka bace ba 'yar qasarka ba,kowa ya sani cewa mata yanzu kudi kawai suke so,mai kudi suke nema koda baida hali koda bai cancanta,koda ba saurayi bane koda ba kyakkyawa bane,koda jahili ne,to bare kai da babu abinda Allah bai baka ba,c'mon muhammad khalipha ka aje wannan game din a gefe ka fuskanci reality,ba irin matan da kaketa serching a yanzu,baka gani duk inda ka soma farauta daga qarshe sai kaga no signal?".


Hannu yasa ya dauki briefcase dinsa tamkar bada shi mahmoud ke magaba ba ya doshi qofar fita ba tare da yace masa ci kanka ba,hakan ya sanya shi miqewa da dan tsallensa ya biyo bayansa,saidai bai sake biyo ta kan wancan maganar ba ya sauya topic,yasan ko yaci gaba ma ba amsa zai samu daga gun khaliphan ba
"ka rakani mu shiga na gida anni"
"Daga nan ni sai inda na nufa,idan ka fito daga wajenta ka kwashe su jibril duka ku wuce kamfani na tadda ku a can,ni da mota daya zan fita,bana buqatar gayya" ya fada yana gaba yana ci gaba da dubo lambar sabuwar budurwar tashi don ya sanar mata da tahowarshi.


Yana fita duka suka taso inda yake,da hannu ya tsaidasu kafin ya daga kai ya dubesu
"Mota daya ta isheni da driver,zaku jira mahmoud tare zaku tafi,zan taho daga baya" kai auka jinjina suna janyewa,yayin daya bude motar da kanshi ya shige gidan baya,drivan motar ya shiga ya tasheta suka bar harabar makeken gidan.


Layuka biyu suka rage kafin ya qarasa layin gidan nasu ya bashi umarnin ya saukeshi ya kuma jirashi a nan,ba musu ya tsaya kaman yadda ya umarceshi,ya bude ya fice.

Sannu a hankali yake takawa,shi kansa yana jin dadin takawar da yake,saboda ko banza ya motsa gabbansa,ba kamar baya ba da motar ita ta zame masa qafafunsa,sauqin abun daya bai da lalaci,duk safiyar duniya sai ya shiga dakin dake bangarensa,wanda ke cike sa nau'in qarafuna da na'urori na motsa jiki da qara lafiya.

Plashing yayi bugu biyu ya katse,shi kansa sai da dariya ta subuce masa
"Shame on you khalipha,wai yau kaine da yin plashing,Allahu yahdik" ya furta a zuciyarsa yana sakin murmushi gami da ranqwashin tsakiyar kansa,fitowarta ita yasa ya maida hankalinsa ga qofar gidan,tayi kwalliya sosai cikin atamfarta
"Sannu da zuwa" ta furta tana wuwwulga ido kaman mai neman wani abu,amma sai ta basar saboda jin kanta da take a mace mai aji
"Yauwa barka da fitowa"
"Ina kuma abun hawan yau?" Ta tambaya kai tsaye tana dubanshi,wani abu mai kama da mamaki yaso mamayarsa amma sai yayi hanzari kau da shi yace
"Kinsan qarfen nasara bashi da tabbas,yau yaqi tashi kawai sai na yanke na taho a na haya"
"Kan bala'i,ana wata ga wata" ta furta qasa qasa,sarai ya jita amma sai yace
"Na'am,me kika ce?"
"Babu komai,shigo daga ciki" ta fada ranta a alamun bace,bai musa ba yabi bayanta har setting room din gidan,duk da cewa ba baqonsa bane gidan da zuwanshi kusan na uku kenan,kallon farko zuwa na biyu zaka yankewa maxauna gidan ajin rayuwar da suke ciki,ba alamun suna cikin talauci,dukkan wata alama ta rufin asiri akwaita a gidan,kaman yadda ya tsammaci akwai tarbiyya gwargwado gidansu khadijan.


Nan ta masa sauki ta gabatar masa da abun motsa baki kamar kullum,saidai abinda ya fuskanta abinda aka kawo masa jiya idan ya sake zuwa yawansu da tsadarsu kan ragu,idan cake da doghnout da lemo yaci to zuwa na gaba doughnout da lemo kawai zai samu,yasan bai taba baiwa khadijan komai ba,haka itama bata taba roqarsa ba,saidai amma ya lura duk sanda sukayi sallama zai tafi ba tare da ya miqo komai ba yakanga bacin rai qarara a fuskarta,har idan ya koma gida ya kirata da zummar gaya mata ya iso bata dagawa,saidai duk ya share wannan bai sanyashi a babin komai ba.


Tun kafin aci talata da laraba a hirar tasu ta gyara zamanta tare da sake lanqwashe murya
"Ammm....dama muhammad akwai maganar da nakeso muyi"
"Ina saurarenki" ya fada yana harde qafafunshi waje guda tare da zuba mata idanunsa,haka nan taji ya mata kwarjini,abinda take yawan tunani kenan,me yasa yake yawan cika mata ido,wanda wannan dalilin yasa tun zuwansa na farko dana biyu data fuskanci ba kalar wanda take lalube bane ta kasa masa bayani,janye qwayar idanunta tayi cikin dakiya tace
"Dama.....biki zamuyi na wata qawata,so an fidda anko nakeso ka yimin" janye yatsansa dake saman lebansa yayi ya dan motsa jikinsa kadan sannan yace
"Kaman nawa ne kudin how much?" Sai da tayi rolling qwayar idanunta sannan tace
"Dubu talatinma is enought,idan son samu ne kuma 40k" murmushi ya qwace masa saidai iya shi da zuciyarsa,ba kudin data tambaya bane suka bashi mamaki don ba matsalarsa bane,don a yanzun haka akwai ninkinsu a wajensa,wanda ya fito da su ne yau dan ya mata kyauta matuqar ta sake tsallake yau din bata nemi komai daga wajensa ba,mamakinsa shine yadda yarinya budurwa da bata rasa ci sha da sutura daga gidansu ba take iya duban qwayar idon namiji ajnabinta ta roqeshi kudin da zata dinka suturawa jikinta haka kanta tsaye ba kunya,tamkar ta bashi ajiya ne,kai yake kadawa a hankai zuciyarsa na gaya masa bata gama cin jarabawa ba ba shakka
"Ya naji kayi shiru ne?" Ta tambayeshi tana dan bata rai gami da fiddo ido waje
"A'ah babu komai,kawai....gani nayi kudin basuyi yawa ba?" Tsaf ta dinke girar sama da qasa
"Just 30 to 40k dinne sukai yawa?,ko iyawa ne ba zaka yi ba?,thank god da ba'a gaban qawayena bane da nake cika musu kanka da naji kunya" murmushi ya saki yana miqewa tsaye
"Ba zakiji kunya ba in sha Allahu zan shiga na fita,amma sai kin danmin haquri kadan kinsam abinka da almajiri mai nema"
"Ba damuwa indai zasu samun,amma kar su wuce nan da one week don Allah" ta qarashe maganar a shagwabe,kai kawai ya iya jinjinawa mamaki na kasheshi,haka tayi masa rakiya har qofar gida yau cike da kulawa sannan ta juya ta koma,shi kuma yaci gaba takawa yana juya abinda ya faru tsakaninsa da khadijan har ya isa bakin motar,wanda tuni driver ya bude masa ya shige shi kuma ya maidata ya rufe sannan ya shiga mazauninsa ya tada motar suka bar unguwar.

"Ashe duk kanwar jaa ce?" Ya fada qasa qasa cikin sigar tambayar kansa da kansa bayan ya ciro sabbin kudaden dake aljihunsa ya qare musu kallo ya watsasu cikin wata ma'ajiyar dake motar ya maidata ya kulle yana sauke ajiyar zuciya,kansa ya shafa sau biyu yana kiran sunan Allah sannan ya maida idanunsa ya lumshe yana aje numfashi
*DAURIN BOYE*


*NA*

*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*

HASKE WRITERS ASSO

(home of expert and perfect writers)


0⃣5⃣



A hankali take takowa bayan fitowarta daga kitchen dauke da babban tray data shiryo abincin daddy a kai zuwa inda yake zaune yana faman rubuce rubuce cikin wasu takardu,yayin da gimbiyar tasa hajiya sa'adatu mommy ke zaune gefanshi cikin kwalliya tana aikin duba tashar da zata dace da kallonta.


Duk da yawan ma'aikatan dake gidan hakan sam bai damu ayshatu ba ko ya tsone mata idanu,takan bata lokaci aduk sadda take da dama tayi girkin da zata ciyar da mutanen gidan,musamman daddy mutumin dake da qima a idanunta,mutumin da take masa kallon mahaifi,kai tana iya cewa abinda yayi mata ko mahaifin da yayi silar kawota duniya baiyi mata shi ba,don ba zata iya cewa yau ga dadin da mahaifi yake da shi ba.


Gabansa ta aje tray din cikin nutsuwa a ladabce,ya dan daga kansa ya dubeta fuskarshi washe da fara'a
"Sannu indon baffale" murmushi ta saki saboda kiranta da wani suna daya shude can baya cikin

Please Login or Register in order to submit comment