Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kowa ya gane tuggun Mama ne da Balkisu .
Ɓangaren karatun Maryam tuni ta fara zuwa school,in za ta tafi gida ta ke barin Yusu.Mahomet kuwa shi ya karɓi ragamar kasuwanci Daddy sosai ya ke tafiya da lamurran kamar yadda ake so.
A can comsariat kuwa Abba ya bada umarnin a hora su sosai duk da Daddy yace ya yafe,Balkisu tuni ido ya raina fata duk tayi baƙi haɗi da rama saboda azaba saboda babu mai kai masu abinci wanda ake raba ma ƴan kaso shi ne su ke ci.






Sai da suka yi wata uku cur sannan aka sako su, Mama zubewa tayi gaban Daddy ta na neman gafara.
"Kin ji kunyar duniya wlh,duk da ban kasance mutumen kirki ba haka bawan Allah na ya kula da ni tun farkon kama mu da aka yi da ƙwaya a hanyar Jos.Babu wata hanya da bai bi ba dan a sako ni amman abu ya cuttura saboda sabon D.P.O da aka naɗa mai shegen zafin kai,sun ci kuɗin shi sosai fiye da yadda kike tunani dan kawai a sassauta min horo.A yadda tsarin ya ke duk wanda aka kama da irin manya ƙwayoyi halbe shi za'a yi ko kuma yayi kason rai da rai,duk tsawon shekarun da na ɗauka a kurkuku jiran mutuwar mu ne ni ke sai kwatsam aka ce an fidda uwanda ake fitarwa Zakka ciki kuwa har da sunana.Bayan mun fito ne d.p.o ke shaidan Issufu ne ya roƙi alfarmar a sakaya da sunana bayan maƙudan kuɗi da biya na cin hanci"Abba na kawowa nan kawai sai ya fashe da kuka kafin ya cigaba da cewa "abokina na gode sosai kuma ina mai sake neman afuwar ka kuskuren baya da na yanzu,haƙiƙa kai abokin kirki ne shiyasa ko da aka kama mu kai ne mutum na farko da nace a tura ma hotunana ko Allah yasa ka ji tausayina ka zo gare ni sai kuma Allah ya amsa roƙo na"da sauri Daddy ya riƙe masa hannuwa ganin Abba na shirin kama ƙafafun sa "babu komi aboki ai yiwa kai ne,sannan ka yafe masu nima da laifina a ciki da ban sanar da su tun farko ba amman Allah na gani na ɓoye hakan saboda kar na tashi hankalin su"
Mama tace "haƙiƙa ɗaukar mataki ba tare da ƙwaƙwaran bincike ba ya na tattare da dana sani marar amfani, lokacin da na ga hoton Mahmud ɗakin ka cikin mawuyacin hali na zata aiwatar furucin ka ne kayi wanda kace za ka ganin bayan sa shiyasa na fara bin duk wata hanya da zan toshe farin cikin ka a ƙarshe kuma na baiwa Balkisu guba"
"Laha'ilah to aniyar ki ta biki kuma daga yau ko sawun ki na gani sai na tara maki mutane,kai kuma ka sakar masu Ƴa tunda abun ba mutumci"Inna ke magana ta na kallon Daddy wanda dama tun tuni ya rubuta ma Balkisu takardar sakinta.




Balkisu na ganin Daddy ya miƙo mata farar takarda ta saki ihu ta na kiran ta shiga uku ta lalace "nayi maki saki ɗaya"shine abinda Daddy ya faɗa kafin ya miƙe Abba ma ya miƙe yace "sai ki san inda zaku nufa ke da ƴar ta ki"




Kowa ya watse ya barsu su biyu a nan falo, Mahomet direct makarantar su Maryam ya nufa dan lokacin tashin su yayi tun tuni har ma ya gota.
Ya na tsayawa da mota ya tsinkayo ta ƙarƙashin icce sai turo baki gaba ta ke,sarai ta gan shi amman ta juyar da kai.A hankali ya soma takawa zuwa gare ta bayan ya rufe motar,"ran ki shi daɗe kaina bisa wuya am sorry"ta juyo ta dube sa tace "sabidar Allah ka kyauta ?tun fa ɗazu mu ka tashi shine sai yanzu za ka zo?"
"Réunion mu ka yi fah,kin san tunda Abban Balkisu ya dawo ba'a yi maganar komi ba sai yau,mu je na sauke ki gida"
"Ok naji,na san bbna yayi ta kuka na haura lokacin da ya saba gani na"
Mahomet ya taɓe baki yace "au shi kawai kike tausayi kenan banda uban shi?"dariya tayi ta buɗe seat ɗin gaba ta zauna, driving ya ke su na hira har suka zo gida.
Yusu na ganin ta ya miƙe ya fara takowa cikin irin tafiyar nan ta ƴan koyo,ɗaukar sa tayi ta cilla shi kuma ya fara dariya haɗi da yi mata gwaranci ya na nuna mata Inna .








Mama da Balkisu sosai suka yi nadama babu ranar da ba za su ban haƙuri ba akan Daddy ya mayar da Balkisu ɗakinta duk da dai har yanzu ba ta ra'ayin sa Mahomet ta ke so.
Sai da aka ruwa rana sannan ya maido ta duba da ba ta taɓa ra'ayin cutar da shi ba,tun dawowarta jiki yayi sanyi yanzu ta bar duk wata ɗagawa saboda ko ta gaishe da Inna ba kasau ta ke amsawa ba kuma yanzu Inna ta kasa ta tsare addu'o'in tsari ta ke ba kowa na gidan musamman ta sa Daddy ya ɗauki malumai duk wata a na biyan su,da wannan duk sihirin da ke jikin Abbasi ya baje kuma sosai shi ma ya gane irin sakacin da yayi a baya.






Bayan wasu shekaru


Tuni Maryam ta kammala karatun ta har ta fara aiki a asibitin Abbasi,Yusuf cikin shekara ta uku ya ke da wasu watanni tuni kuma Maryam ta samu wani ciki wanda sam bai bata wahala.
Tunda ta fara zuwa aiki maganar kirki ba ta haɗa su da Farida ba kowa sabgar gaban sa ya ke,dama can ba ɓangaren su guda ba.
Maryam ce tafe ta na daddanna waya kai taji tayi karo da mutum,ta na ɗagowa ta ga Dr nan ce wacce ta taɓa amsar number ta.
Murmushi ɗauke da fuskarta tace "Dr Halima ko?"kai ta gyaɗa tace "ashe ki na nan?wlh nayi neman lambar da kika bani sam ban ganta ba ashe da rabon za mu sake gamuwa"cewar Dr Halima .
Maryam tace "ayya bari na baki ,ya ne ko nan kike aiki?"
"A'a zan dai fara ne,ina ne office ɗin Dr Abbas ?"Dr Halima ta tambaya,kwatanta mata Maryam tayi ita kuwa tayi godiya ta tafi bayan sun yi masayar lambobi.






Knowking tayi daga can ciki aka amasa,shiga tayi bakinta ɗauke da sallama da sauri Abbasi ya ɗago jin zazzaƙar muryata sai kuma ya mayar da kansa ya amsa tare da bata izinin zama.
Dossier ɗin hannunta ta miƙa masa ya shiga dubawa,cike da jin daɗin ganin CV ɗin ta célibataire ce ba ta da aure Abbasi ya ɗago karaf idonsu ya sarƙe cikin na juna a tare kuma zukatan su suka buga......
[05/03 à 13:11] Mrs SADAUKI 💫: *45-46*




"Takardu sun yi kyau gaskiya kamar mai su"cewar Abbasi murmurshi tayi tace "na gode kenan za'a ɗauke ni aikin?"
"Eh har ma an ɗauke ki,ko yanzu za ki iya farawa "Abbasi ya bata amsa da murnarta ta shiga yi masa addu'a tare da fatan alkhairi wanda hakan ya sa ta sake shiga zuciyar Abbasi.
"Bari na baki system ɗin da za ki rinƙa amfani da ita,za ki ga komi da komi da ke ciki da yadda tsarin zai rinƙa tafiya.Sannan bayan sakatariya za ki rinƙa kama wani aikin in ana buƙata musamman in bani nan"Abbasi ya faɗa ya na ɗauko wata computer wacce lokacin da ya sallami sakatariyar shi ta farko ya karɓe abar sa.Kunnawa yayi kafin ya juyo ta zuwa gaban ta yace "ki kula sosai ina son mutum mai amana duk da Adamu ya shaida min ba ki da matsala kuma ko ina ana yabon ki"
Dr Halima tace "in shaa Allah DG za ka same ni mai riƙon amana da yardar Allah kuma za ka ji daɗin aikina fatana dai Allah shige mana gaba"
Abbasi ya amsa da "amen"nan Dr Halima ta fara duduba abubuwan da ke ciki daga ƙarshe dai Abbasi ya gwada mata office ɗin ta wanda sai an zo nan sannan a shigo nasa.
Zama tayi ta fara aiki kamar agogo a ƙasan zuciyarta sai godiya ta ke ma Allah da ya kuma bata wani aikin.










A kiɗime Farida ke kallon labarun ta na fiddo ido waje,tabbas in dai ba gizo idon ta ke yi mata tabbas wannan shine Jamal mijin Hawali.
Murya cike da tsantsar hassada da baƙin ciki ta ke cewa "wai dama Jamal ne yayi coup d'État😱 na shiga uku na lalace ni Fatima Bintu,ana nufin Hawali ta zama 1ère dame/first lady ? Innalillahi wa'inna iley raji'un bari dai na kira Mama na ji "ta ɗauki waya ta kira Mama babu ko gaisu tace "Mama sojan nan da ake cewa yayi juyin mulki dama Jamal ne?sai yanzu ni ke gani a journal da aka sa maimaici"Mama tace "eh mana nima jiya na gani a tv ko kin san shi ne?"kuka Farida ta fashe da shi tace "Mama mijin Hawali ne fah wannan ƙawata wacce na ce maki na goge lambar ta bayan na sakata liste noire"
Mama tace "to mine ne na kukan ?tun yaushe ni ke yi maki faɗa ki bar duk wata shiririta ki koma ga Allah amman kika ƙi?yanzu ai ga irin ta nan"kashe kiran Farida tayi ta na jin wani irin matsanancin haushi,rabon da tayi tunanin Hawali tun lokacin da tayi ma malam Jaye maganar ya zubar da cikin jikinta yanzu kusan shekaru uku kenan duk da ta na zuwa Niamey amman ko sau ɗaya ba ta taɓa neman Hawalin ba.






Abbasi kuwa lokaci ɗaya duk ya rasa sukunin shi,wani irin son Dr Halima ne ya shige sa lokaci guda sam bai san yadda zai yi da ruhinsa ba.Dossier ɗin ya duba ya ɗauki numérota da ke jikin lettre ɗin neman aiki,tunanin yadda zai ɓullo ma lamarin ya fara kafin kuma ya tashi ya na murmurshi.
Abbasi kamfanin layin Moov ya tafi ya sayo sabon Sim da kuma ƴar ƙaramar portable,zama yayi a mota ya haɗa komi kafin ya tsara text ya tura ma Dr Halima.






Ita kuwa baiwar Allah ta na can ta na faman gérer abubuwa a computer sam ba ta tsaya bin ta wayar ta ba har sai da lokacin tashi yayi ta rufe office ɗin ta wuce gida.
A gajiye ta shiga gidan,Moma na ganinta ta saki murmurshi ta ce "sannu da zuwa Sa'adiyana ga ruwan wanka can na zuba maki a bokiti dan su sha ɗan iska"zama tayi bisa tabarmar kaba tace "Washhh!na gaji wlh ,babu ƙanƙara ne ƙishi ni ke ji"
Moma tace "a'a fah ban samu yaron da zai sawo ba sai dai ki sha na tulu"
Safar ƙafarta ta cire kafin ta miƙe ta nufi tulun ruwan,moɗa ta cika da ruwa ta tsugunna ta shanye su tas ajiyar zuciya ta sauke kafin ta aje moɗar ta wuce ɗaki.
Zane ta samu tayi ɗaurin ƙirji kafin ta fito ta ɗauki ruwan da ke cikin bokiti ta shiga banɗaki,ba ta wani jima ba ta fito.
"Ga abincin ki nan ki ɗauka ki ci,ni zan tafi gidan Rahamu in yi mata barka kuɗin auren Ƴar ta da aka kawo"cewar Moma ta na gyara luluɓi.
Halima ba tace komi ba sai kujerar katako da tajo ta zauna kafin ta buɗe kwanon abinci,wake da shinkafa ne sai ƙamshin albasa ke tashi.Bismillah tayi ta fara ci tayi kamar ba ta san Moma na kallonta ba,cike da tausayin Ƴarta ta Moma ta fice bayan nazari da karantar halin ta Halimar ta shiga.
Ƙwalla ce ta fito daga idonta ta zuba cikin kwanon abincin,duk uwar yunwar da ta ke ji sai taji sam ta ɓace.Tashi tayi ta wanke hannunta ta shige ɗaki,bisa ɗan gadon ƙarfe ta haye ta kwanta tare da lumshe ido.
In ba ta saɓa lissafi ba yanzu shekarunta sun haura talatin amman shiru babu wani tsayayen saurayi balle ayi tunanin mijin aure.
Bayan hannu ta sa ta goge hawayen da suka zuba a kumatunta a fili ta furta " *WAMAN YATAWAKAL ALALLAHI FAHUWA HASBUHU* ```Duk wanda ya sanya yaƙininsa ga Allah ba zai taɓa da na sani ba,duk wanda ya yarda da Allah ba zai taɓa tozarta ba``` "
Tashi tayi ta ɗauko wayarta daga cikin bag,lambar Maryam ta danna ma kira babu jimawa kuwa ta ɗaga.
Gaisawa suka yi kafin su fara taɓa hira wacce duk akan aikin da Halimar ta samu ne,sosai Maryam ta taya ta murna tare da alƙawarin gobe za taje har office ɗin Dr Halima.
Katse kiran tayi ta na jin haka kawai Maryam ta shiga ranta, messagerie ta shiga ta fara dubawa har ta iso ga wata lamba wacce babu suna.
"Amincin Allah ya tabbata ga sarauniyar kyau,fatan ki na lafiya" shine saƙon da ta gani,Halima ta taɓe baki ta fito ba tare da tayi reply ba.














Tamkar wanda ƙwai ya fashe ma a ciki ko kuma mace mai naƙuda haka Abbasi ya kasa tsaye ya kasa zamne.Duk da Farida ta na cikin damuwa sai da ta tambaye shi lafiya amman yace mata ba komi,ganin zaryar ba za ta fishe shi ba ya shiga toilet ya yo alwala kafin ya fito ya fara yin Sallah.
Ya na gamawa ya zauna kan tafi ya na ta tasbihi da hailala daga nan barci ya kwashe sa,Farida na ganin haka ta ɗauki wayar shi ta kama ɗan yatsan shi ta cire empreinte take wayar ta buɗe.
Bincike ta shiga yi masa ta na duba duk wani sirrin sa amman ba ta ga komi ba,tsuki taja ta ajiye wayar ta na harar sa.Hasken ɗakin ta rage bayan ta haye gado,da ta rumtse ido Hawali ta ke gani cikin gizner wacce ta sha wani tsadadden ɗinki.Ta ja tsuki ta tashi zaune,sam a rayuwarta ta tsani wani ya fi ta ko gidan biki ta tafi ta fi son ace ta fi kowa haɗuwa.








****


"Lafiyar ki wai tun ɗazu kike a nan zaune?"Mahomet ya tambaya ya na kallonta,yanayin fuskarta ya ƙara canzawa zuwa kalar tausayi tace "in na kwanta ban jin daɗi duk sai na ji cikin nan ya takura ni"
"Ok taso na rungume ki,sai ki jingina da jikina"cewar Mahomet ya na mai zama bakin bed ya miƙe ƙafafunsa.
Tashi tayi daga inda ta ke ta zo ta shiga tsakanin ƙafafun sa ta jingina da ƙirjinsa,kamar wata baby haka ya ke dadaɓa bayanta yayinda hannu ɗayan ke bisa kan cikinta ya shafawa bakinsa kuma ɗauke da addu'oi a haka barci ya ɗauke Maryam shi kuma Mahomet yayi gadin ta.




Washegari
Bayan sun yi breakfast Mahomet ya sauketa *ALFARMA CLINIC* wato asibitin Abbasi wacce yanzu ƙaurin sunanta yasa mutane da dama kan zuwa daga sauran gararuwa.
Ta na tafe ta na Azkar wanda ya zame mata abokin hira kullum cikin yin sa ta ke,direct office ɗin Dr Halima ta nufa.A zaune ta tarar da ita ta na aiki a computer,ta na ganin Maryam ta rufe ta na murmurshin da ya zame mata sabo.
Cikin kujerun da ke ajiye a office ɗin Maryam ta ja ɗaya ta zauna ta na mai gaishe da Dr Halima "ina boy ya na lafiya ko?"
"Lafiyar shi lau ya na can ya na barci bai farka ba lokacin da na baro gida,ya naki yaran?"ita ma Maryam ta tambaya ta na murmurshi,yanayin fuskar Halima ya canza tace "a'a ai ban da aure ma,am ke ina ne office ɗin ki?"tayi tambayar cikin son kawar da zancen auren ,fahimtar haka yasa Maryam ma ta bar batun.
"A'a banda office ai,sai dai an keɓe mana ɓangaren mu ni da sauran abokanan aikina da sannu duk za ki saba da su"Halima na shirin magana aka banko ƙofa.
Ƙamshin turarenta ya fara yi masu iso kafin ta shigo fuskar nan a murtuƙe an sha uwar kwalliya,ba tayi sallama ba haka kuma ba ta gaishe su kwata-kwata ma ba ta kalli inda suke ba.Har ta kama handle ɗin ƙofa Dr Halima ta ɗaga murya tace "keee!"cak Farida ta tsaya kafin ta juyo a tsiyace ta zuba idonta bisa farar fuskar Halima mai ɗauke da dogon hanci irin na fulanin asali.
Dr Halima ta miƙe tace "ki jira nayi maki iso ba haka ake shiga ba babu neman izini"ƙugu Farida ta riƙe kafin ta yi mata kallon ƙasa da bisa tace "ke a suwa?wace ce ke da har za ki min katsalanda da shiga bureau mijina?"
Murmushi Halima tayi tace "sorry Madam DG dokar aikin ce ke haka,bai sanar da ni za ki zo ba shiyasa kuma nan ba'a gida ba ne ma'aikata ce"
Ganin dai kamar Halima daidai ta ke da ita yasa ta tura kofa da ƙarfi ta shiga ita ma ta take mata baya ta na dakatar da ita.
"Wace irin ƴar iskar sakatariya ce wannan da har za ta samu zarrar dakatar da ni ?"Farida ta tambayi Abbasi wanda ya tsaya ya na kallonsu ita da Halima.
"Dokar aiki ce kuma sannan ta yaya za ta gane ke matata ce tunda ba'a rubuta a goshin ki ba,Halima koma bakin aikin ki"cewar Abbasi,"ok"kawai tace kafin ta fita.
"Saboda sakatariya kake gaya min magana?"Farida ta faɗa a hasale,tasowa Abbasi yayi ya rungumeta cike da kissa irin ta su ta maza yace "haba Hubbyna miye haka saboda ƴar aiki za ki ɓata min ran ki a banza, please ban so.Yauwa faɗa min wannan kwalliyar nawa aka sayar min ita"ya ƙare maganar ya na mai kai laɓansa bisa na ta.






Sai da Dr Halima ta fito ne Maryam ke shaida mata yadda suke da Farida,ai kuwa Halima ta jinjina irin rashin mutumcin Farida da kuma rashin wayo.
Su na nan zaune Rahila ta shigo,kamar yadda tsarin ya ke dama kowa sai ya zo ya gaishe da Abbasi.
Nan ita ma ta zauna aka shiga hirar duniya kafin wani lokaci office ɗin Halima ya cika da jama'a a sannu kuma wasu suka watse jin Oga na tare da Madam ne .
[07/03 à 10:21] Mrs SADAUKI 💫: *47-48*










Kafin wani lokaci Dr Halima ta saba da sauran abokanan aikinta sai dai jinin su ya fi haɗuwa da Maryam dan ku san kullum sai sun yi waya bayan sun tashi daga aiki.Ɓangare guda ta fara kula ɓoyayyen masoyi wanda cikin lokaci guda yayi nasarar sace zuciyarta ,sosai Halima ke jin son sa.








Yau a tare suka shigo office ɗin da Maryam wacce yanzu cikinta ya tsufa sosai,cikin yanayi na tsokana Maryam tace "oh!na matsu na ga wannan Guy wanda ya sace zuciyar ki har haka,amman fah ina gudun ki hanasa komawa in ya zo"Dr Halima tayi dariya tace "Allah ki kiyaye ni,ba fah matsuwa nayi ba juste ina son ganin sa ne ido da ido yace min zai yi shigar Black ta yadda zan shaida sa amman ba zai fito yace min shi ne ba"
Maryam tace "kuma a nan CLINIC zai zo?"Halima ta bata amsa da "eh haka yace "Maryam ta ja kunera ta zauna tace "to Allah kawo sa lafiya"ta amsa da "amen "ta na mai buɗe system amman sam ta kasa yin aikin saboda ganin lokacin zuwan na sa ya gabato kamar yadda yace kafin ƙarfe takwas na safe ya buga zai zo sai ya kirata ta fito.




Su na nan zaune bini-bini sai ta duba agogon hannunta shiru har saura minti biyar kawai ya rage,Maryam ta miƙe tace "bari na tafi har zuwa heure ɗin pause sai na dawo" "ok to babu damuwa in ya zo zan kira ki ta waya"a haka dai Maryam ta fito cikin sauri ,sai kuma ta tsaya cak ganin Abbasi tsaye ya na waya yayi shigar baƙaƙen kaya tunda daga takalminsa har izuwa agogo.






Zuciyarta ce ta fara bugawa amman sai ta kawar da tunanin ta nufi ɓangaren su,gaisawa tayi da su Rahila wacce ta cika tayi fam a tunaninta Maryam ɗin ba za ta zo ba yau dan kar ta barta da aiki.
Kan hijab ta ɗora farar rigar su ta likitoci,Rahila ta taɓe baki tace "Ni kam Maryam ki na bani mamaki ke a ko ina sai kin gwadi ke Malama ce, lokacin hutu ki saurari karatu ko wa'azi wanin sa'in dan kiciyi ƙur'ani kike buɗawa a likita ki na karatu yanzu kuma hijabin ma ba za ki iya cirewa ba ki saka rigar ?"




Tunda ta fara magana Maryam ta kafeta da ido har sai da ta gama sannan ta bata amsa da "eh saboda karatun Alkur'ani cikin jinina da zuciyata ya ke,tun ina ƴar jaririyata da shi ake min tawai in ina kuka kuma a kunna min.Maganar kuma ban cire hijabi wannan ra'ayina ne saboda Musulunci yace a saka"




Duk da maganar tayi mata zafi amman sai da ta maida martani wajen cewa "Allahu Akbar to yayi musulmai shi dai imani a zuci ya ke kuma na ga dukan mu nan mata ne babu abinda za ki gwada mana sannan in forme ce da ƙugu ko ni na fi ki"
Maryam ba ta tankata ba ta fara duba wasu takardu,su kuwa sauran matan biye ma Rahila su kayi suna ƙara girmama lamarin wanda duk habaici ne ake yi ma Maryam ita kuwa da ta lura kamar dama sun daɗe su na baƙin cikinta sai ta share su.




Su na tsaka da yin hirar Barira ta shigo fuska duk a haɗe,Maryam tace "ke lafiyar ki yau?"ta tambaya bayan sun gaisa , "lafiya lau na fito daga gida waccan baƙar macen mai shegiyar izza ta zo ta ɓatan rai"
Maryam tace "wa fah?"
"Matar DG mana ni miye sunan ta ma?"da ya ke gulma ce da sauri Rahila tace "Farida ,hum ai wannan matar ta iya masifa ga shegen kishi sai kace ita ɗaya ke da miji"
Barira tace "wlh kuwa yanzu ma fah masifar ce ta ke wai ta kama sakatari na kallon shi har da ririƙeta yayi za ta kai ma Halima duka"jin an ambaci Halima ya sa Maryam cewa "da fatan dai sun kashe hutar?"
"Allah sa sun buga"cewar Rahila
Barira tace "a'a ba su buga ba saboda yadda Halima ta zabure ta nuna ita ma masifafiya ce yasa Farida ta sha jinin jikinta"ajiyar zuciya Maryam ta sauke kafin ta cigaba da aikin ta.






Rahila tace "ai naji haushi sosai wlh so nayi su ci bura ubar juna dan na san Halima sosai ta na da sanyi amman in ranta ya ɓace akwai bala'i"ai kuwa suka shiga yin zancen kowa sai zagin Farida ya ke ya na faɗin rashin mutumcin da tayi mashi.






Ganin hirar na ta hauhawa har ta koma kamar gulma ya sa Maryam ɗan tsayawa daga aikin da ta ke na ƙirgen magani tace "dan Allah ku bar maganai,nan fah zunubi ne kawai kuke rage mata sannan ba ta san ku na yi ba"ai kuwa suka yo mata caaa amman banda Barira wacce tace "kuma fah gaskiyar ki Maryam bari na tafi na duba patients"








HALIMA POV




Ta na nan zaune duk ta damu sai taji an taɓa ƙofa da sauri ta ɗaga idonta ta zuba su kan ƙafafunsa uwanda su ke sanye cikin baƙaƙen takalmi,a sannu ta fara ɗaga idonta zuwa baƙin wandonsa har ta kai ga baƙar rigar sa murmurshi tayi ta lumshe ido lokacin da zuciyarta ta raya mata shine ɓoyayyen masoyinta.
Lumsashun idon ta buɗe ta zuba su kan fuskar sa wacce ta ke ɗauke da annuri,da sauri Dr Halima ta waro ido ganin fuskar Abbasi ya na sakar mata murmurshi,ta miƙe kenan za ta takowa inda ya ke tsaye tun ɗazu Farida ta shigo ita kuwa kan fuskar Halima wacce ta ke fyau babu kwalliya face baƙin kwalli da man leɓe a nan idon Farida suka sauka da sauri ta maido dubanta ga Abbasi wanda ta lura shi Halima ke kallo.








"Uban miye kike kallo a fuskar mijina?shegiya munafuka fara mayya"cewar Farida cikin masifa da sauri Abbasi ya riƙo hannunta,cikin masifa ta ke aiko mata zagi da ta lura da Barira wacce ke tsaye bakin ƙofa ta ƙara da "duk mayyatar mace kama da jawaru ko ƴan mata sai sun bar min mijina,munafukai ai dama na daɗe da ganewa gaishe sa da kuke zowa ba na Allah da Annabi ba ne"




"Keee!ki iya bakin ki wlh in kin ɗauka ke wata tsiya ce to ni takalme na ma ya fi ki daraja banza sakarai kawai,ke har mace ce?kije gidajen daraja ki duba mata uwanda suka san darajar kan su da ta mijin su"cewar Halima jikinta har rawa ya ke wanda ya baiwa saharin jikinta damar zamewa dogon gashin kanta ya bayyana,wanda ganin sa ba ƙaramin ruɗu Farida ta shiga ba.






Cikin Halima ta sake ƙoƙarin yi Abbasi ya daka mata tsawa wacce tunda ta ke da shi ba ta taɓa sanin Abbasi mafaɗaci ba ne sai yau.
"Kan ki guda ?miye ke damun ki ?ke har kin isa ki zo ki zubar min da ƙima gaban ma'aikatana?yanzu da kike zanen ƴan mata da zawaru kawai dan kin ji mijin Barira ya mutu ne sai aka ce maki sona ta ke ko mi?"juyawa Farida tayi bakin ƙofa sai ta ga ashe tuni Barira ta bar gun.




Wani abu ta haɗiye mai

Please Login or Register in order to submit comment