Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

bata isa ta hanata ba,dadin da takeji cikin ranta kawai shine sauyi da take sake samu,ta soma yin wani irin fresh,haskenta tamkar ana qara mata shi,qiba ce har yanzun babu ita sam.

"Tunanin me akeyi?,a bawa ama labari" ama ta fadi sanda ta isa gabanta tana jan kujera guda daya dake kusa da sultana din tana zama.

Dago fuskarta tayi suka hada idanu,sai sultana din ta dan saki murmushi,alamun kunya dukka suna nunawa cikin qwayar idanunta. Zata iya cewa ba zata iya tuna zaqi ko dandanon soyayyar uwa ba,amma adan tsukin da tsautsayin ya saukar mata ta samu dukkan wata kulawa da d'a ke samu wajen uwa. Wani irin sabo me tarin yawa ya shiga tsakaninta da ama irin wanda bai taba hadasu ba,har wasu lokutan idan ta kebe take mamakin ashe dama haka take da kirki?,ashe da gaske ne abinda su aminata ke fadi a kanta a baya?.

"Ba komai" ta fada da wani irin sanyi wanda ya soma zame mata dabi'a,sanyin da abaya sam sam sultana bata sanshi ba cikin rayuwarta.

"To Allah yasa,maza ungo" aman ta fada tana miqa mata mug din hannunta me dauke da madarar shanu data tafasa mata ita da duminta.

Bata musa ba ta miqa hannu ta dauka,a nutse takai bakinta sai kuma ta sauke tana duban cup din

"Yaya dai?" Ama data dauki wayarta tana son duba calendar don ganin yau din adadin kwanaki nawa maina ya qara rabonshi dasu ta furta tana kallon fuskar sultana

"Na qoshi" ta fadi a sanyaye tana dan dora hannunta saman wuyanta. Da mamaki ta dubeta

"Amma kaman ke kika cewa bilki a kawo zaki sha ko?" Kai kawai ta dagawa ama,sai ama din ta sake maida hankalinta kanta,cikin sassauta murya tace

"Sultana banaso ki dawo da dabi'ar qin cin abinci fa,don Allah karki maido mu baya kinji?,na lura tunda muka dawo nijer kike gujewa abinci,idan nijer dinne bakiso mu koma nigeria ne gaba daya to" kai ta girgiza mata alamun a'ah,sai kuna wasu siraran qwalla suka biyo fatar idanunta. Ita batasan yadda zata yiwa ama din bayani ba,kwata kwata kamar an cire mata sha'awar abinci,tanason ci amma da ta kaishi bakinta sai taji gaba daya ta qoshi,idan kuma ta tilastawa kanta din dai amai ya fara taso mata.

Ama ta lura da hawayen,hankalinta yadan dagu ta ajiye wayar tata saman table

"Idan kina da damuwa ni mamarki ce ki gayamin sultana" ta fadi mata tana ritsata da idanu.

"Ba komai,kawai qoshi nayi" ta bata amsa tana saka yatsunta tana dauke hawayen

"Ko madararki za'a kawo miki?,yanzun sai nayi waya niamy su sakota a jirgi don tafi saurin zuwa?" Kai ta sake girgiza mata alamun dai a'ah. Duk yadda ta rayu da qaunar madarar da shauqinta da kuma jin gardinta gaba daya yanzun bata burgeta

"Zansha wannan din anjima"

"Kinyi alqawari?"

"Eh" ta amsa mata,sai ama ta gyada kai sannan ta maida dubanta ga calendar din.

Lissafinta dai dai yake,kwanakin shurawa suke tamkar cikin mafarki,duk yadda take tunanin zuwa lokacin zai nemesu zai waiwayi gida zai dawo zai kirata koda a waya ne abun ya sabawa tunaninta,babu ko daya a ciki. Tayi cigiya iyakar yinta,har a kafafen tv da radio amma shuru kakeji. Aba kuma ya nade hannunsa yana kallonta,baice komai ba bai kuma sanya baki ba. Koda yaje Nigeria ma acan din su yaaya abdulhakeem fada suka dinga zabgawa kaman su ari baki

"Kuna wasa ne,dan mutum guda kamar batan nama a miya?" Sun kira aba amma har suka gama fadansu baice komai ba,daga qarshe yace dasu

"Aiba yaro bane qarami,ya fimu sanin ciwon kansa ma yanzun,duk inda yaje zai dawo tunda dai ba qanqanin jariri bane" ran uncle abdulhakeem ya baci qwarai,saboda ya fahimci kamar m abun bai dameshi ba. Hayatudden ne ya karba da yake ya fishi sanyi da sauqin kai yayi masa magana shima

"Kuma iyayensa ne,na baku wuqa da nama yaaya,kada ku damu" jin ya fadi hakan sai ya rabu dashi kawai. Cigiyar suma suka baza sosai,amma har suka gama zamansu suka dawo da nijer din da Nigerian ba wani bayani.

Tana shiga fargaba wasu lokutan,tana shiga tunani me zurfi kan yana ina,wanne hannu zai fada?,da waye zai hadu?,sai ta furzar da iska me zafi daga bakinta daidai sanda suka hada ido da sultana. Maida wayar tayi ta ajjiye cikin zuciyarta tana maimaita addu'ar data zama sirri tsakaninta da ubangijinta na ya bawa aliyyun tarbiyyarsa dama lafiyarsa kariya,kada ubangiji ya kamashi ko ya jarabcesu silar zubar hawaye a idanunsu.

"Meye ra'ayinki kan komawa makaranta?" Tayi maganar tana monitoring mode dinta. Ambatar makarantar kadai kuwa ya canza yanayinta din,tayi qas da kanta,saidai kafin tace komai sai ga yasmine ta shigo,rungume da ledar data tabbatar siyayyyar da suka fita yine

"Sultana ga mariam inoussa ita da aicha ousmane,muna dawowa muka gansu wai basusan a nan guraren kike ba,'yan uwan gidansu alhaji saddam ne ashe". Kaf walwala da fara'ar fuskarta ta dauke,ta saki baki kawai tana duban yasmine kafin tayi magana a hankali

"Ki dakatar dasu ki gaya musu bacci nakeyi" ta fadi maganar da iyakacin gaskiyarta ne,saboda a yanzun bata qaunar hulda da duk wadanda ta sani a baya,musamman qawayenta na makaranta dama na cikin unguwa gaba daya. Gani takeyi kowa ma yasan meye ya faru da ita?,kuma kowa kallonta yakeyi da abun.

Turus yasime tayi tana duban sultana,kwata kwata ta canza,ko su dinma ba komai take shiga nasu ko ta sanya baki ba

"Yasmine,jeki ki gaya musun" ama ta yiwa yasmine magana,sai ta amsa tana juyawa tare da barin falon.

Tun a nan ta fahimci tana da buqatar canjin makaranta ne,don haka a washegari lahadi tayi mata register da wata makarantar daban. Makaranta ce me mugun tsada wadda har tafi waccan tata ta bayan tsada kuma tsari. Tasan muddin idan ba hakan tayi ba ba zata sake ba,gwara ta kaita cikin wadanda bata taba sani ba,yadda ba zatayi dari dari ko ta kasa sakewa tayi karatu cikinsu ba.

Duka a ranar lahadin ta sauya mata komai da komai,hatta da ruwa da drinks na zuwa makaranta da zata iya buqata kamar wata 'yar free nursery.

Duk dai a ranar ta fidda mota guda cikin motocinta duk da dama already sultanan akwai motar kaita makarantar,amma tace a ajjiyeta,saboda tana da burin ta sake sabuwar rayuwa,batason komai nata data taba amfani dashi a baya yanzun a dawo dashi,don hatta da sutturu duk uban tulin kayan sawarta ta sanya tanja ta fiddasu,batasan rabawa sukayi tsakanin ma'aikatan ba ko menene oho,itadai duka tayi mata juyen closet nata.



*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400
BIYU_800
UKU_900
HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875
Musaa Abdullahi safiya
Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261


*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku kudin*

09033181070


*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂*_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

Book 02 page 15


*_les jumeaux_*(the twins)???



K'arfe biyu da rabi motocin yaran gidan dake jigilar kaisu makaranta suka fara saukesu,a lokacin ama tana zaune a samanta,tana jin motsi da kai kawonsu,saidai aikin da takeyi ya dauke mata hankali,batajin zata iya saukowa a sannan,saddi ne yana yima kansa komai don ba qaramin yaro bane bare tace zai nemi wani abu daga gareta,sai sultananta da tasan ita dinma indai ba wani abu ta buqata ba ba lallai ta nemi ganinta. Waya ta dauka ta kirayi bilki me aiki tace ta duba mata sultana ta dawo?. Ba jimawa ta sake kiranta

"Ta dawo hajiya"

"Yauwa to,ki bincika ko akwai wani abu da take buqata,idan babu shikenan,sai la'asar ni zan sauko"

"To hajiya" ta amsa mata a ladabce tana aje wayar. Mintuna biyu rak bilkin ta sake kiranta

"Hajiya qofarta rufe take" dan shuru ama tayi

"Lafiya?"

"Eh kaman lafiya gaskiya don na danji motsinta"

"To yayi,ki rabu da ita wala'alla hutawa takeyi,sai na sauko din"

"To a sauko lafiya" bilki ta amsa mata.

Wayar ta aje tana dan nazari kadan tare daci gaba da aikinta da take gab da kammalawa. Lissafin shekara shekara ne,wanda bayan ta kammala din take fidda zakka haqqin Allah.

Tana gamawa din yadda taso ta zauna ta huta sai tayi sallar la'asar kuma amma sai taji hankalinta yayi kan sultana. Kashe mini laptop din tayi,ta zura tausasan slippers dinta ta miqe tana nufo stairs din.

A nutse ta sauka ta kuma nufi sashen dakunan dake qasa. Tana ratsa falon suna gaisawa da masu aikinta da yau duka basu samu ganinta ba,tana amsa musu tana dosar dakin,har ta isa qofa.

Murdata tayi har yanzu tana kulle,ta kira sunan sultana din sau biyu bata amsa ba,sai ta juya yana yiwa fainusa magana kan ta duba store ta ciro mata spare key.

Cikin qasa da minti daya fainusa me aiki ta dawo da key din ta miqa mata,ta karba ta soma gwadawa har ta samu na dakin.

Dundum yake kamar ba rana ba,cikin mamaki ta kunna fitilar dakin haske ya gauraye,idonta ya sauka kanta sanda take nade tsakiyar gado lullube da qaton duvet. Mamaki ya kama ama ta kira sunanta tana takawa ciki hadi da cewa

"Bakijin zafi zaki rufa haka?,wanne irin bacci ne wannan sai an rufe kai?" Ta furta tana janye duvet din.

Razana tayi ganin yadda sultana din ke qudundune guri guda tana rawar sanyi sosai. Farar fuskarta ta sauya launi zuwa pink color kaman yadda tasan tanayi a duk sanda take zazzabi irin wannan ko wani ciwo. Tun bata kai hannunta ba take iya jin hucin dake fita daga jikinta gaba daya,duk da hakan sai ta miqa hannunta da sauri tana taba sassan wuyanta. Saukar hannun ama a jikinta sai taji kaman an qara mata ciwon,ta maqale wuyan wasu siraran hawayen suna fita daga idanunta

"Ya salam ya Allah" ama ta furta,zafin dake jikinta yayi yawa qwarai,sai ta dauki remote na ac din dake gefan gadon ta soma da kasheta,sannan ta juyo ga sultana din tana zama sosai a gabanta

"Dama dashi kika dawo daga makaranta?,tun yaushe ne?" Ta tambayeta cikin tsananin damuwa

"Tunda na shiga classe(class)" kai amma ta girgiza tana jin hankalinta yana daguwa

"Bari na kira Dr chafa'atou,zafin zazzabin yayi yawa" ta fadi tana sauka daga saman gadon sannan ta koma zuwa sassanta da gagggawa.

Qasa tayi da kanta tana lumshe idanuwanta bayan fitar ama. Wasu hawayen masu zafi kwatankwacin zafin zazzabin jikinta suka biyo kuncinta. Ita daya tasan me takeji cikin jikinta,tanajin kamar ana kama qasusuwanta ana ballasu daya bayan daya,kowacce gaba ta jikinta ciwo take mata sosai. Wasu sabbin hawayen suka kuma biyo idanunta,tun daga wancan ranar...... tun daga randa yayi mata fyade......tun ranar da ya zalunceta ya cuceta bata sake samun lafiya ba......bata sake jin qarfi cikin jikinta ba,ya tafi da dukka kuzarinta,ya tafi da walwalarta da kuma farincikinta,tana jinta a cikin jikinta ita karan kanta kamar ba sultanan bibi ba,kamar ba itace ke rayuwa a wannan gangar jikin ba.

Dukka wayoyinta ta debo ta dawo dakin tana gwada layukan wayar Dr chafa'atou. Bude qofar dakin ya sanya sultana bude fararen idanunta da suka sauya kala saboda tsabar zafin zazzafin dake fita a jikinta

"Sannu sultana.....sannu" ama ta fadi cikin kulawa ainun tana zama saman bedside drawer tana kuma sauraren wayar Dr chafa'atou dake ringing.

Dab da zata katse ta daga,cikin girmama juna suka gaisa

"Jikin patient dinki ne ba lafiya médecin(Dr)"

"Tofa,me ya sameta kuma?" Dr chafa'atou dake shirin zama saman kujerarta daga can cikin office dinta ta tambaya

"fièvre ne me zafi,dashi ta dawo daga école(school)"

"Subhanallahi,idan yayi zafi da yawa ki samu mouchoir(handkerchief) me kyau da ruwa a goge mata jikinta,gani nan na tashi gida zan wuce dama,zan qaraso na dubata"

"d'accord(okay),amma ina neman alfarma,zan saka motocin mayak'i yanzu suzo su taho dake,je ne veux pas de retard(banason jinkiri)"

"Hakan yayi ba damuwa" wayar dukka suka ajjiye.

Idanunta a lumshe,yadda jikinta ke zafi da quna haka zuciyarta,tana jin sanda ama ta iso da ruwan da qaramin towel ba tare data nema kowa ba

"Tashi a goge miki jikin sultana la fièvre est si élevée(zazzabin yayi yawa)" kai ta girgiza a hankali sannan tace

"A kiramin bibi,bibi nakeson gani"

"Za'a kirata,amma a ragewa jikin naki wannan zafin kada tazo ta gani hankalinta kuma ya tashi,ko kinaso hankalinta ya tashi kuma?" Kai ta girgiza a sanyaye,sannan ta yunqura ama na riqe da ita ta zaunar da ita sosai ta rage mata uniform din,ya zamana daga half vest din da ta soma kare martabar qirjinta da su,sai gajeran wando mahadin vest din. Sam ba wani kunya tsakaninta da ama,don ta zama tamkar uwar da babu shamaki a tsakaninsu. Tana goge mata din ta kirayi layin tanja donta kira bibi din bata sameta ba,tace ta shaida mata sultana ke rigimar son ganinta yau kuma,ta tashi da wani dan zazzabi. Tanja din ta amsa mata sannan ta kashe wayar ta maida saman drawer.

Tana gama goge matan akayi knocking qofar sannan aka turo. Bibi ce sanye da lallausan abaya cotton 'yar marocco ta mata me hade da mayafi.

Ama ce ta amsa mata tana miqewa hadi da tattare towel da roban ruwan,ta kuma jawa bibi kujera zuwa gaban gadon da sultana ke zaune.

Idanun bibi qur cikin na sultana bayan ta daidaita zamanta saman kujerar,sannan a hankali ta maida dubanta ga qirjin sultanan wanda ba baqonta bane.

Wata mummunar faduwar gaba ta samu kanta da ita

"La haula wala quwwata illa billa" ta fadi qasan zuciyarta,sannan ta janye idanunta ta juya zuwa ga ama dake qoqarin saqale towel din jikin qofar toilet

"Me ya sameta?"

"Zazzabi ama,daga tafiya makaranta"

"Zazzabi kawai?,kuma iya yau?" Ta tambayi ama cikin mamaki a sautin muryarta

"Wallahi bibi,kuma koda safen lafiya lau ta shiga ta miki sallama nima tayimin sallama,sun dawo nasa azo dubata su bilki suka samu qofanta a rufe,sai da na sauko dubata na sameta kwance" aman ta yiwa bibi bayani dalla dalla. Kai kawai bibi ta jinjina jikinta yana wani irin sanyi,dukka gwiwoyinta kamar an bubbugesu,wani irin fargaba ya cika mata zuciya,ta samu kanta tana furta addu'a can qasan zuciyarta......dai dai lokacin aka shaidawa ama isowar Dr chafa'atou wadda drivern mayak'i mansion ya daukota.

"Kiyi mata iso ta shigo" tace dame aikin nata tana komawa opposite bibi tana zama itama,jikinta yana sanyi da ganin sauyawar reaction na bibi cikin tambayoyin da tayi mata.

Har qasa Dr chafa'atou ta tsugunna ta gaida bibi. Sannan ta qarasa gaban sultana tana kallonta.

Kallo na kusan minti guda,kallon da ya sanya sultana janye nata idanun daga kan Dr chafa'atou,haushi yana cikata duk da ciwon da takeji a dukka gabobinta,don meye zata sakata gaba da kallo kaman taga wata dodo?.

"Bayan zazzabin kinajin wani abu dabanne?" Dr chafa'atou dake qoqarin bude dan akwatin aikinta ta fada. Da qyar ta motsa lallabanta ta bata amsa a gajarce

"Babu"

"Okay.....yaushe rabon da kiga period dinki na qarshe?" Tambayar da ta sake sanya razani me yawa a zuciyar bibi,ta kuma saka ama barin abinda takeyi tana duban Dr chafa'atou da batasan ma duka suna kallonta ba,don ita nata zargin yayi wani waje daban,don haka ta yankewa kanta yin abu guda daya da take da babban zato a kansa ba tare data batawa kanta lokaci ba.

"Bana tunanin zata iya riqewa,don kwata kwata al'adarta ma ina jin batayi yakai sau shida ba,niketa qoqarin tsara mata calendar dinta da sanar da ita lokaci donta dinga kiyayewa" bibi ta yiwa Dr chafa'atou bayani tana dubanta

"Okay ba matsala" ta amsawa bibi bayan ta gama fidda container dinta

"Kina Jin fitsari?" Ta tambayi sultana tana kallonta

"Kadanne"

"Yimin shi a nan koda dan kadan dinne" sai ta miqawa sultana container din.

Daga bibi har ama bin container din sukayi da.kallo,dukkansu sunsan gwaji akeyi da ita,kuma batun gwajin fitsari wani al'amari ne me zaman kanshi

"Amma ba fièvre du paludisme(zazzabin malaria) bane Médecin?(Dr)"

"Yanzun zamu gani in sha Allah hajiya" ba wanda ya iya sake cewa komai. Dr chafa'atou dince ta riqe hannun sultana har qofar toilet sannan ta dawo tana fidda kayan gwajinta. Duka duka bata wuce minti daya ba ta miqawa Dr din kwalbar ta koma saman gadon ta lafe tana rufe idanunta,don a yanzun babu abinda takeso da qauna irin ta ganta a kwance,cikin daki me qarancin hayaniya irin haka.

Duk motsin Dr chafa'atou suna biye da ita,har zuwa sanda ta kammala tsatsube tsatsubensu na likitoci,ta daga pt strip din da ya bayyana komai dara dara yana sake bata haske.

Saukeshi tayi tadan saci kallon ama da bibi,akaci sa'a dukkansu idanunsu yana kanta. Ajiyar zuciya ta sauke ta koma ta zauna,ita kanta tana jin fargabar bayyana sakamakon gwajin,amma kuma har kusan hada baki ama da bibi sukayi wajen tambayarta

"Ya dai?,an kammala?" Kai ta gyada musu,ta aro dukka jarumta da dauriya irin ta likitoci sannan tace

"JUNA BIYU GARETA!" Dif wutarsu ta dauke na dan wani wucin gadi,haka kunnuwansu suka tsaya da aiki na wucin gadin,kamar yadda kwanyarsu ta daina banbance saqon da aka aika mata dashi na wasu daqiqu. SULTANA dake a kwance kuwa taji dukka kalmomin Dr chafa'atou,amma abu daya zuciyarta da kwanyarta ta gaya mata

"Bafa dake take ba,magana take akan wata" wani sashe na zuciyarta ya gaya mata zuciyar na wani irin mugun bugu kamar ta balle daga qirjinta

"Kin duba da kyau kuwa Dr?" Ama data tattaro dukka sauran maqalallen busashen yawun dake saman halshenta ta fadi

"Na tabbata,a yadda kuma ya nuna shi sosai bana tunanin ma yana qasa da wata daya ne"

"Mun gode kawai Dr,tattara kayanki kije,banda rainin wayo ta yaya zaki kalli kaman sultana kice tana da ciki?, shekara sha ukun?,lallai na yarda da akace wani lokaci qwqwalwarku tana tabuwa" bibi ta fada da wani irin yanayi da zai gaya maka lallai ba cikin hayyacinta sosai take magana ba.*_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 page 16


"iya abinda na gaya muku hajiya bana tunanin akwai son rai a ciki ko kuma ba dai dai ba.....dukkanmu munsan me ya faru,ina ganin ba abu bane na mamaki don ance ciki ne da sultana ba......" Ta qarashe fadi cikin tausasa harshe da kuma dukka yunqurinta nason ganar da bibi abinda ke wakana.

Wani irin gumi ne yake yanko musu su dukka. Yayin da sultana dake kwance taketa qoqarin fasa maganar Dr chafa'atou cikin kanta. Wanne irin ciki take nufi tana dashi?,shin mene ne ma cikin wai?. Wani muguwar razana tayi sanda tunaninta yakai inda ya kamata yakai din,ita kanta batasan yadda akayi ta isa gaban Dr chafa'atou ba bare bibi da ama dake zaune kowanne jinin dake jikinsa nason daskarewa.

Kyakkyawan riqo ta yiwa Dr chafa'atou, muryarta da wani irin galabaitaccen amo......fararen idanunta da suka sauya launi dukka sun fito waje tana duban Dr chafa'atou,hucin da jikinta ke fitarwa bai damunta ko kadan

"Ba Bibi tace ki tafi ba?,me yasa kikeson sake jefani cikin halaka?" Ta jefawa Dr chafa'atou tambayar

"Don Allah medicin kice ba haka bane.....kice kuskure kikayi......me nayi miki zaki jawomin wannan abun?,ta yaya zan iya haihuwa?,kinga cikina fa dan qarami ne amma kike cewa wai ciki ne dani?" Ta sake fada tana sakin Dr chafa'atou,sannan taja da baya da wani irin hanzari tana tattare rigar jikinta har saman qirjinta,plate tummy dinta wanda ke shafe hade da bayanta ya bayyana. Daga jajayen idanunta tayi tana maida dubanta ga Dr chafa'atou dake tsaye tana karantar yadda kwanyar sultana din ke shirim birkicewa

"Kinga cikina?,ko plate din abinci daya bazan iya cinyewa.....amma kikayi qarya kikace ciki......." Bata barta ta qarasa ba ta sanya dukka hannunta a tausashe ta jawo sultana cikin jikinta ta rungumeta tsam

"Kiyi haquri......wasa nake miki,kinyi qanqanta sultana,har yanzun ke yarinya ce" ta fada muryarta na rawa,tsananin tausayin sultana yana taba zuciyarta yana ratsa jikinta.

Daga bibi har ama gaza riqe hawayensu sukayi. Hawayen tausayin sultana,ta yaya zata iya karbar wannan qaddarar da qananun shekaru irin haka?,ta yaya zata iya fuskantar wannan qaddarar cikin rayuwarta?,ya rayuwarta zata zama?,ciki a shekarun da duka duka basufi sha uku zuwa sha hudu ba.

Sun jima a haka dakin tsit,bakajin komai sai sheshsheqar kukan sultana,wanda tun tanayi da ragowar qarfin da ya ragewa jikinta har ya zama bata iya koda motsi saboda wani mahaukacin zazzabi da yafi na baya daya sauko ya rafketa.

Cikin hanzari Dr chafa'atou ta fara bata taimakon gaggawa don kada zafin zazzabin ya kaita ga convulsion musamman da yake ba ita kadai bace,zazzabin zai iya zama illa ga abinda ke mahaifarta,duk da cewa ta lura har yanzu bibi ko kadan bata yarda da abinda ta gaya musu ba.

Kimanin awa daya kafin bacci ya dauketa,don Dr chafa'atou ta sanya ruwan allurar bacci cikin ruwan,saboda a yanayin da take ciki yanzu bacci ne kawai maslaha.

"Zan wuce,Allah ya bata lafiya,saidai koda baki yarda da abinda na fada ba yana da kyau a kula da lafiyarta,a sake gujewa sanyata damuwa" tayi musu taqaitaccen bayani dukansu da ama da bibi din.

Qwaqwwaran motsi aka rasa wanda zaiyi a cikinsu,ta tafi ta barsu da tarin tunane tunane qulle qulle da kuma kwancewa. Ita dai ama bata da abinda zata iya cewa bibi,maina ya tafi ya barta da dukkan wani nauyi da kuma kunya. Yayin da Bibi take juya maganar Dr chafa'atou wadda take jinta kamar a duniyar mafarki.

Shigowar aba dakin shi da goumar shi ya katse shurun da yake wanzuwa a dakin tsahon wani lokaci. Dukka suka daga kai suna amsa sallamar tasa yayin da nashi idanun suke kan ledar ruwan dake shiga jikin sultana.

"Dama bata da lafiya?" Yayi

Please Login or Register in order to submit comment