Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da zuwa cikin harshen abzinanci. Ta amsa mata itama ta bata waje ta shigo.

Shigowar dioura ya debe mata kewa sosai,qarasa tattaunawa da kuma tsara daukan program din suka qarasa yi.

Ita daya cikin dakin sauya tufafin na musamman da aka tanadar mata a cikin office dinta,tayi wani fitinannen kyau cikin laffayar me azabar kyau da tsada,idan ka ganta a sannan zakayi tsammani shuwa ce,duk suturan data sanya yana karbarta ainun haka jikinta yake.

Fuskarta take kalla,tanason bawa kanta qwarin gwiwar shiga studio din. Ta jima tana zumudin randa zata gabatar da al'adun kanuri saboda yadda abubuwansu suke burgeta,yau ranar yazo,amma kaf ta rasa duk wani walwala da nishadi da take da buqata. Ga kasalar da take sake saukar mata,tana jin kanta da idanunta tamkar wadda ta tara bacci na shekaru aru aru a kanta.

Siririn tsaki taja sanda akayi knocking qofar dakin,sannan kuma tace

"Ina fitowa" ta sake juyawa tana gyara fuskarta,tana ambaton sunan Allah a hankali a hankali wai ko zata samu sassauci daga dukkan abinda takeji din.

"Wow......bansan wanne shiga bane yafiyi miki kyau,na last week ne ko na wannan satin?" Dioura ta fadi da kwantaccen murmushi da gurbatacciyar hausarta tana kallon sultana. Dan murmushi da yafi kama da na yaqe ta saki tana maida abubuwan hannunta data cire cikin jaka.

Har sun soma ficewa ita da dioura saita tsaya,tana buqatar wani abu da zai dawo mata da karsashinta cikin jikinta,idan ta fita a haka tabbas ba zata taba bada abinda program din yake buqata ba. A nutse ta koma ta zauna,ta fidda wayarta ta soma kiran layin ama.

Dab da zata katse ta daga da sallama a bakinta

"Good morning ama"

"Morning sultana,ban tashi da wuri ba yau din,tanja tacemin har kin wuce"

"Eh ama......"

"To ma sha Allah.....ina fatan komai lafiya?" Ta tambayeta saboda yanayi muryarta daya bata kaman akwai wani abu

"Lafiya alhamdulillah,zan shiga program.......ina buqatar addu'a" ta qarasa fada muryarta na danson yin rawa. Tausayinta sai ya saukarwa ama,ta dinga ji a ranta inda mahaifiyarta tana raye tabbas ita zata kira ta nema addu'a kaman haka,maraici ba dadi komai gatan da zaka samu,gatan uwa daban yake,mahaifiya kuma ba madadinta.

Sai muryar ama da jikinta dukka sukayi sanyi,cikin nuna kulawa tace

"Allah ya bada sa'a,yasa a gama lafiya.......zaki magana dasu batoul ne?"

"Eh ama" ta fadi qasa qasa cikin dan jin nauyi

"Gasu" ta fadi tana miqawa yaran wayar.

Da zumudinsu suka soma magana da ita don yau basuje school ba saboda jikin benazeer,koda batoul taje ita daya ba lallai ta zauna,shi yasa ama tace a barsu duka,ta dinga murmushi tana biye musu,a qalla sun kusa mintuna goma da ita tana biye dasu kafin tace su bawa ama wayar sukayi sallama.

Iska ta furzar daga bakinta tana kallon fuskar wayar,ta samu relief kaso hamsin cikin dari,amma ta rasa gane dalilin da ya sanya wannan gurbin ya gaza cikewa,ta rasa me yasa ta kasa samun satisfaction dari bisa dari?. Idanunta ta rufe tana karanto addu'o'i,tana jin zatayi managing da 50% din data samu,don haka ta miqe tana fita daga office din.

Ita kadai tasan yadda tayi forcing kanta tayi program din,a fuska ne kawai take da karsashi da kuma kuzari,amma cikin zuciyarta da gangar jikinta wani irin emptiness take ji.

Ita daya ta koma office ta zare dukka kayan data gabatar da program din dasu duk da cewa sun zama mallakinta. Haka kawai taji bata da buqatar barinsu a jikinta,ta maida kayanta data taho dasu ta koma saman sofa tana maida numfashi. Kanta ta juya tana kallon agogon wayarta,ta gama abinda ya shigo da ita gidan don haka tana tunanin komawa zatayi gida,don kasalar dake jikinta koda ta zauna ba zata barta tayi komai ba. Komai nata ta tattare tayi sign-in ta wuce parking lot,ta zuba duka tarkacenta cikin motar ta shiga ta tayar da ita ta fice daga gidan.


^^^^Motsa jiki yayi a safiyar na tsahon mintuna talatin da biyar,sosai yake jin kanshi fresh a safiyar,don jiya ya samu yayi bacci isashe ba laifi. Direct ya wuce toilet yayi wanka,ya dawo ya shirya kansa cikin long sleeve shirt da dogon trouser. Yayi wani fresh sosai kaman yadda zuciyarsa yake jinta da sauqin damuwa a ciki. Ta falo ya dawo yana duba abubuwan da suhail yayi kafin ya fita a gidan,bai jima ba yaron dake musu share share ya qaraso,sai ya matsa bakin window ya bashi space don ya gyara gidan.

Idanunsa saman gidan,yana kallon abun hawa aba,abinda yake tabbatar masa da aba bai fita ba kenan. Yanason shiga yaga batoul da benazeer,ya kuma gaida ama,amma bayason aba din yasan da wanzuwarsa a unguwar,har yanzu wannan lokacin baiyi ba, yafison yayi nesa dashi,ya tabbatar hakan zai sanyata yaci gaba da jin kewarsa.

Idanunsa ya mayar side din window dinta,idan ya rantse bazaiyi kaffara ba ya tabbatar ta wuce wajen aiki ne,barin hali sai mutuwa,sai kuma yanzun da ya tasamma sauyata. Murmushi ya kubce masa sanda ya tuna yanayinta a jiyan,indai har da gaske ne abinda yake gani cikin idanunta kishi ne hakan yana nufin akwai soyayyarshi koda bame yawa bace a zuciyarta?. Ajiyar zuciya ya saki,yana jin kewarta sosai cikin kowacce jijiya dake dauke da alhakin zagayawar jini a jikinta,to amma yanajin dole yadanyi step down kadan don yayi taste akan irin nata soyayyar a kanshi.

Matsawa yayi daga jikin window din sanda wayarsa ta dauki tsuwwa,ya juya a hankali yana nufar wajen wayar,a yadda ya tsara din yau gaba daya bazai fita ba saboda shirye shiryen tafiyar da zasuyi shida suhail na sati uku. Haka kawai bayason yin tafiyar,don bayason yayi nesa da ama da twins dinshi,to amma kuma hakan ya zama dole,don daddy ya nema alfarma a wajensu su wakilceshi,daddyn kuma yafi qarfin kowacce kalar alfarma a wajensu.

Tunda ya fita ya dawo ma bai duba wayar ba sai yanzun,tarin miscals ya samu,ciki harda na ayana wanda ya kusa guda goma. Yadan tsuke gira kadan,yana shirin yayi deleting na miscals din wani kiran na ayana ya sake shigowa.

Hakanan ya daga ba don ranshi yana so ba,surutunta har hawan masa kai yakeyi,baisan inda ta gaji surutu ba,tunda dai shi yasan uncle tahir ba haka yake ba.

Da dakakkiyar muryar nan tashi yayi sallama,sallamar data sanya ayana shiga taitayinta,murya ce me ratsa zuciya da qwaqwalwar wanda ake magana dashi

"Good morning yaa haidar"

"Morning,kina lafiya?"

"Lafiya Lau nake,na kira ne na gaya maka yanzu haka ina airport,yau ne taho wana,transit daya zamuyi kuma,ina saka ran nan da wajen dare anan paris in sha Allah ina Paris"

"Yayi kyau,Allah ya tsare hanya....."

"Amma ya haidar......baka manta dai da alfarman da daddy ya nema min ba ko?"

"Name?" Ya tamabayeta don shi bilhaqqi ya manta

"Habba ya haidar........daddy fa ya gaya maka,kaine wakili na......ya wakiltaka akan al'amurana a cikin Paris"

"Oh......,karki damu,muna tare da ama,kuma nasan She will do her best to take care of you.......ina da harkoki da yawa,ba komai ne zan iya concentrating akai ba" shuru ta danyi jikinta yana sanyaya,anya abinda take gani me sauqi ne zayazo da sauqin kuwa?.

"I know yaa haidar....but kulan mace da namiji ba daya bane......"

"She's the one who raised me......so that tana iya kula da 'ya'ya dari ma" ya datsi numfashinta. Yanajin yadda ta aje numfashi,sannan muryar qasa qasa tace

"It's okay,saina qaraso"

"Safe flight"

"Thank you" ta amsashi tana jin dadin fatansa na qarshe a gareta.

Iska ya furzar,ya soma gajiya da wadannan abubuwan,ga laila sai kuma ga ayana ta taho......ayana me sauqi ce a gareshi,laila dince yake komai da takatsantsan a kanta,ta yadda komai idan ya tashi qarewa tsakaninsu za'a yishi cikin girma da mutunci. Wayarsa ya mayar aljihu,ya koma bakin window din ya duba,ba motar aba,hakan kuma yana alamta mishi ya fita kenan,don haka ya koma ya zura lallausan fluffy dinsa yana fitowa daga gidan,yana buqatar ganin ama.


_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400
BIYU_800
UKU_900
HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875
Musaa Abdullahi safiya
Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261


*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku kudin*

09033181070


*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂*_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 105


Ya samu qofan a bude,don haka ya turata kawai ya shiga da sallama. Suna saman carfet sanye da wasu pink loungwear,an raba musu sumarsu me tsaho gida biyu,kowacce an kameta da pink din ribbon da ya dace da kayan jikinsu,sun yiwa building blocks baja baja a falon sunata qoqarin hadawa. Ama na zaune saman kujera,gabanta dan madaidaicin table ne da system akai,da alama wannan lissafe lissafen nata da ya santa dashi shekara da shekaru takeyi,akwai madaidaicin tray daga gefanta,da alama late breakfast zatayi ko kuma takeyi din.

Building blocks din dake saman cinyarsu suka watsar sunata qoqarin tararsa. Tsaiwa yayi yana kallonsu murmushi ya subuce masa,kafin su iso sai ya goce,sannan kuma ya miqa hannu ya dauki benazeer. Baya batoul tayi tana kyabe baki alamar zata saki kuka

"Daddy nifa?"

"Benazeer ce bata da lafiya,baki gani ba har wadannan kumatun sun zazzage?....." Ya fada yana jan kumatunta wadanda da gaske sundan ragu,sai kuma ya dora da cewa

"Kin manta kuma ke din babbace,qanwarki ce ita fa" hakan daya fada sai ya faranta mata ta fara tsalle,ya saku murmushi ya duqa yana miqa mata hannunsa,saita riqe ta tattakashi itama ta haye kafadarsa suka nufo ama,wadda a haka zaka dauka batasan me yake faruwa ba,saidai tana karance dasu. Duk sanda irin hakan zata faru ita kadai tasan farincikin da takeji, addu'a daya takeyi Allah ya sanyaya zuciyar sultana,tana da matuqar buqatar tarin jikoki,musamman da bata haihu da yawa ba,takanji kamar ta yiwa almu da saddi aure,saidai sunyi qanqanta sosai,amma tana ji a jikinta ko shekarun maina ba zasukai ba zata aurar dasu da ikon Allah.

Da qyar suka bari ya gaisa da ama,suja tattaro masa blocks din sukace lallai shima ya hada nasa aga waye zaiyi abu me kyau. Yanata murmushi ya fara diban nasa,yana sane ya dinga hada shirme sunata masa ihu,sai ya narke fuska shima kaman qaramin yaro ya dubi ama

"Ama kinga abinda sukema danki ko?" Tun bata kulasu har dole ta dinga sanya baki a ciki,ita ta dinga raba maki ba yadda ta iya. A daidai lokacin qararrawar qofa ta buga,tanja ta baro kitchen zata bude yace ta koma taci gaba da aikinta,ya tashi yana gyara hannun rigarsa daya tattare ya nufi qofar.

Bata kawo komai ba sanda ta danna bell,don haka tana tsaye sosai tana jira a bude mata,duk ta qagauta ta qarasa cikin gidan,kwanciya kawai take da buqatar yi ko zata samu mode dinta da abinda takeji a jikinta ya koma daidai.

Shi da ita duka basu tsammaci ganin juna ba,idanunsu suka sarqe waje guda,kowannensu sai ya kasa janye nashi idon,kamar masu kallon quda na wani sakanni,sai yayi hanzari janye idanunsa yana juya ciki jikinsa a mace.

Duk wani feeling nashi da yake qoqarin dannewa yana controlling nasa tasa kakkaifar qwayar idanunta cikin qasa da second sittin ta rusashi,gaba daya ta saukar masa da kasala,ta tayar masa da wani irin abu cikin sassan jikinsa,amma duk da haka da yake namijinne da gaske, sai ya yaqi hakan saman fuskarsa,ya koma cikin yaran ya zauna sosai abinsa kamar dazu.

Da qyar ta daga qafanta ta sanyo kai cikin falon tana yin sallama,kallo daya ama tayi mata ta karanci ba cikin daidai dinta take ba

"Sannu da gida ama" ta furta tana qoqarin qaqalo murmushi,don ita kanta taji idanunsa har cikin tsakiyar jikinta,wani kakkaifan kallo daya tayar da kowacce tsiga ta jikinta,ya aike mata da wani irin saqo me nauyi,saqon da taji inama ace zaya shimfida mata kyakkyawan qirjinsa ta samu masauki a ciki,tana ji tana kuma tsammani a nan ne kawai zata samu sassaucin abinda takeji,a nan ne kawai zata samu nutsuwar da take da buqata.

"Yauwa sultana......lafiya kuwa?" Ta tambayeta tana tattara hankalinta a kanta sanda ta matso kusa da ama din tana kwashe mata takardunta da suka zube a qasa

"Laf.....fiya ama,na gama abinda najeyi ne" amsar data bawa ama din sai data sanyashi lumshe kyawawan idanunsa. Yanzu haka a wannan safiyar miliyoyin maza nawa ne suka kalle masa fuskarta?,anya zai qyaleta a haka kuwa?,zai iya ci gaba da yi mata wannan zurun?.

"Gajiya ce kenan?" Ta sake tambayarta,saita gyada kai kawai ba tare da tace komai ba

"Saiki shiga ciki ki kwanta ai ki huta sosai,may be idan kika samu bacci zakiji kin ware"

"To ama" ta amsata tana riqe kayanta da kyau. Sai sannan benazeer da batoul da hankalinsu yayi nisa a wasa da daddynsu sukayi mata sannu da zuwa. Tadan saci kallonsa na abinda yayi qasa da second biyu sannan ta watsa musu harara

"Sai yanzu kuka ganni?,banason sannu da zuwan" murmushi ya qwacewa ama,har sai data dora hannunta saman bakinta kadan ta maida jikinta bayan kujera tana lumshe ido

"Yaro man kaza" ama din ta fada qasan ranta. Tanajin yaran suna fadin

"Am sorry mommy.....am sorry mommy".

"Naji" ta fadi,cikin dakewar da takeson nuna tsananin kamun kanta tace

"Barka da rana" saidai tayi maganar ne tana kallon gabanta. Kamar baijita ba haka yayi mata,yasan daya daga cikin abinda bataso kenan.

"Ina wuni" ta sake maimaitawa wani abu yana tsaya mata a wuya

"Maina bakai ake gaidawa ba?" Ama tayi saurin kawo qarshen drama din

"Oh.....sorry ban ganta ba,kina lafiya?" Ya amsa yana duba letter A cikin tarkacen building blocks din. Kasa amsa masa tayi,don tayi imanin idan ta bude baki kuka zata sake masa,sai kawai ta qara wuta ta wuce dakinta.

Tana maida qofar suka hada idanu da ama,har tayi kaman ta jefa masa harara sai kuma ta dauke kai saboda wani tunani da tayi,bata harareshi ba amma ya fahimci harara taso jefa masan,sai ya qunshe dariyarsa yana dauke kai,ya maida kai ga yaransa.

Tana ajjiye jakarta saman gado taji damshin hawaye ta eyelashes dinta,takai hannu ta tabosu,ta dawo da dubanta kan yatsun nata

"Kuka kuma?,na me?" Ta tambayi kanta cikin qarfin hali,duk kuwa dacewa sosai takeji wani abu yana damunta a zuciya

"No" ta fadi tana girgiza kai,tana gayawa kanta kada tayi kukan,tayi qoqarin hadiye komai,sai kuma taji zuciyarta tana bala'in tashi.

Gefan gadon ta samu ta zauna,ta dinga jan numfashi me zurfi tana kuma fesar da wani,dukka a qoqarinta na daidaita damuwarta. Ta kusa kashe minti ashirin a haka sannan ta danji dama dama,sai ta tashi ta cire kayan jikinta,ta nemo riga da skirt free size masu taushi ta saka.

Idan zata iya tunawa wunin yau babu abinda ta sanyawa cikinta,bata kuma jin yunwar kwata kwata,a cushe takejin cikinta,to amma kuma koma meye bai kamata takai har irin wannan lokacin ba tare da taci komai ba,don haka ta sanya baby hijab saman kayan ta fito kitchen ko zata samu wani abu taci.

Qin yarda tayi kwata kwata ta kalli sashen da suke,ta maida dubanta ga qofar kitchen din da take tunkara,saidai duk da haka hakan bai hanata jiyoshi yana gayawa ama saqo ba

"Zuwa dare idan Allah ya kaimu ayana zata iso,nace bari na gaya miki,zanje daukota around 8,don munyi magana da uncle tahir ya bani ita........" Bata bari ta gama jin sauran abinda yake fada ba ta shige kitchen din da sassarfa,ayana.....tasan ayana sosai,kusan mate ne ita da ayana din,duk a sannan ayana din ta bawa sultana shekara daya. Ama nason ayana don 'yar yayanta ne uwa daya uba daya,sannan a baya tasha jin uncle tahir yana tsokanar maina zai bashi ayana.....tun maina din yana dan makaranta.

A birkice ta dauko fresh milk,ta bude da zummar tasha ko zata wuce da abinda ya tsaya mata a maqoshi,amma data sanya baki sai taji ba zata iya ba,don haka ta dauki qaramar tukunya ta juyeta a ciki,ta jefa citta da kanunfari da cardamom da kuma mint fresh mint leaves da basa rabo dashi,ta rage wutar can qasa,ta goye hannayenta a qirji ta zubawa tukunyar idanu tunaninta kuma yana lulawa wata duniyar ta daban.

Sanda ama ta tashi tana shiga dakinta dauko wasu files ya samu ya miqe yana miqawa batoul gidan daya hada mata

"Ina zuwa,bari na samo ruwa" ya fadi yana gyara bottom na rigarshi,ya soma takawa zuwa kitchen din. Tunda ta wuce hankalinsa yayi can,yadda ya karanci sultana yayi imani koda mahaifiyarta a yanzu da zata dawo duniya ba zatayi mata karatun da yayi mata ba,ya tabbatar daga jikinta har zuciyarta bata jin dadinsu,to amma wannan hanyar daya biyo ita daya ce sassauqar hanyar da zata kawo musu qarshen komai,don dukka wata jarrabawa da zaiyi game da ita ya gama yinta,ya kuma gama fahimtar inda ta dosa gaba dayanta.

Tun kafin ya qaraso yaga madarar ta cika tukunyar tana kuma zubewa,yayi mamakin ganin tana tsaye a wajen amma bata lura da hakan ba,yadan qara sauri kadan ya isa bakin gas din ya kashe.

Gilmawarsa ta sanyata ankara da shigowarsa amma saita gaza motsawa daga wajen,tana kallonsa ya dauki rariya da cup ya tace madarar,ya dawo kusa da kitchen cabinet inda take tsaye,ya bude ya dauko zuma ya zuba ya sanya spoon ya barta a wajen. Ya qarasa bakin freezer dake daya side din ya fiddo ruwa mara sanyi cancan sannan ya juya yana barin kitchen din.

Samun kanta tayi da binsa da kallo,yana qarasa ficewa sai taji hawaye ya silalo mata,ta shafo hawayen tana kallonsu

"Again?" Ta tambayi kanta muryarta tana rawa,kawai saiga wasu hawayen sabbi suna sake fitowa.

"No.....no" ta fadi sau biyu a jere tana girgiza kanta,saita matsa gaban fanfo dake kafe a sink ta kunna,ta fara tarar ruwan tana wanke fuskarta dashi. A qalla ta kusa mintuna biyar a haka kafin ta samu nasarar tsaida hawayen,saidai abinda takeji a cikin zuciyarta bai sauya ba.

Da kadan kadan take kurbar madarar,sai taji tana zauna mata sosai,a hankali ta shanye,wanda tun kafin takai ga ajjiye kofin jikinta ya sakeyin weak,wani kasala ya sake sauko mata,saita ajjiye cup din a daddafe ta fice a kitchen din. Yaga fitarta,ya rakata da idanu har ta shige dakinta saiya fidda ajiyar zuciya a sirrance yana dauke kanshi.

Sosai ta duqunqune cikin duvet tana jin sanyi cikin qashinta kamar wadda zazzabin cikin qashi yake neman kamawa,ta lumshe idonta tana fidda numfashi,ita kanta zuwa yanzu ta tabbatar ba lafiya lau take ba,ta dinga karanto addu'o'i cikin ranta,cikin ikon Allah sannu sannu wani irin mahaukacin bacci yazo yayi awon gaba da ita.

Batasan tsahon lokacin data dauka ba,itadai ta farka ta jiyo maganganu sama sama daga falo,da alama baqi ke dasu a gidan. Ta kalli agogo,saita miqe da dan hanzarinta zata wuce toilet,mararta taji ta murda,tadan dafeta tana yamutsa fuska,a hankali kuma saita saki,ta miqe ta wuce bandaki don daura alwala ta biya bashin sallar da yake kanta.

Koda ta idar bandakin ta koma,tayi wanka da ruwa me dumi sosai sannan ta shirya cikin wata doguwar rigan kayan bacci me taushi. Ta taje gashinta da kyau ta dameshi cikin band,saita tsaya tana kallon fuskarta. Skin dinta ya sake fresh sosai,hakanan idanunta ma kaman sun qara girma da haske. Yunwa taji tana dan ji,hakan kuma ya mata dadi,don tanaso taci abincin sha'awar cinne bata jinsa. Juyawa tayi ta dauki wayarta ba tare data daura dankwali ba ta nufi falon,sam ta manta da batun zuwan ayana,hakan wannan lokacin tasan lokacine da daga su saisu a gidan.

Sai data bude qofan ta soma isa falon sannan tunaninta na daxun ya fara dawo mata. Benazeer da batoul da kuma maina suna zaune saman carfet,sun sake sosai sun kuma yiwa wajen abinda suke so,sun batashi da abinci,ayana na duqe a gabansu tana qara musu miya da lettuce. Muryarta da tasu benazeer kadai ke tashi,alamun da zai bayyana maka lallai ita din ba baya bace wajen surutu da karadi. Yayin da hannun maina na hagu ke riqe da waya yana daddanawa tamkar hankalinsa baya kansu.

Idanunta dukka ta zube akan ayana din, shirt ce a jikinta inner da top me budadden gaba,sai palazzo madadin kayan,wata irin hula ce kawai saman kanta,wannan ya sanya sumar da ta danyi gadonta ta fito ta qasan hular. Tayi kusanci da yawa da maina,ko luma bata sani ba idanunta ne suka nuna mata hakan?,koma mene sai taji ci gaba da kallonsu bashi da wani alfanu face wani abu me zafi da yake saukar mata saman zuciyarta. Tana zare idanunta daga kansu yana dago kansa suka hada idanu,tun fitowarta fitinannen qamshinta ya ziyarci.hancinsa.

Kanta ta dauke,daidai sanda ayana itama ke qoqarin dauke kanta daga kan fuskar sultana, fuskar data rudar da ita da kwantaccen zallar sassanyan kyau. Tun sultana batakai haka ba tasan ita din me kyau ce,don kaf iyalin MAYAK'I ba wanda ya kamo qafarta, mutum daya ne suke gogayya,ya haidar din,aliyyu maina,to amma a

Please Login or Register in order to submit comment