Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ajjiye nufi na,ba hamdiyya ba sultana..... shima maina tunda ya tafi....."

"Ki ajjiye batun maina,ba mune mukayi masa laifi ba,shi yayi mana laifi,sannan ya zabi tafiya ya barmu,koda kasheta yayi a yanayin da ya barta bashi da asara" ya furta maganar yana ciro wayarsa da yaji alamun kira ya shigo. Baikai ga daga wayar ba kiran ya katse,sai text din hamdiyya da ya shigo kusan awanni biyu baya,rububin taro ya sanya bai gani ba sai yanzun da ya samu ya sullubewa jama'a yayi bad da bami a mota daya ya taho gida kawo bibi ta hut sannan ya koma.

Hannunsa har rawa yake sanda ya karanta layi guda kacal na saqon,ita dai bibi batasan me yake faruwa ba,taga dai ya qarawa motar uban gudu bayan ya aje wayar da hanzari a gefensa

"Lafiya hamidou?" Bibi ta tambayeshi tana dubansa

"Hamdiyya ce ta dawo,ina kyautata zaton suna nan cikin abuja" ya bata amsa yana sake bakwa kwalta hankalinsa sosai. Idanu bibi ta fidda cikin wani mugun zumudi da ba zata

"Hamdiyya?,ita da sultanan?"

"Eh na tabbatar tare suke" ya amsa mata yana sake qara tsula gudu abinda sam ba al'adarsa ba

"Allahu qadiran Ala man yasha'u" bibin ta furta hankalinta yana daguwa,jinta takeyi kamar tayi tsuntsuwa ta isa gidan,sai kawai tayi luf jikin kujera tana kiran sunayen Allah a jejjere.


*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400
BIYU_800
UKU_900
HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875
Musaa Abdullahi safiya
Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261


*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku kudin*

09033181070


*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂*_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 27



"a hankali bibi" aba ya fada lokacin da yake tsaida motar tasa bibi na qoqarin budewa ta sauka. Ai bata saurareshi ba sai data tabbatar qafafunta sun taka qasa. Da sauri ya fita a motar yabi bayanta,yasan tana da ciwon qafafu,a yadda kuma take gaggawar kaiwa ga sultana yana gudun kada ta sarqe.

Dukka muryarta ta ware tana doka sallama kamar baquwar gidan,ta daburce gaba daya,saboda batasan ta inda zata fara ganin sultana ba.

Tana shirin shiga wanka taji kamar muryar bibinta,kamar muryar da kullum take mafarkin ji,sai kawai ta jawo babban mayafi ta yafa a kanta tana nufar qofar fita.

Qarar bude qofar ya sanya bibi maida kallonta gurin,sultanarta ce,itama sultanan bibin take kallo,kallo kallon suka hau yiwa juna kamar wasu baqin juna,sai kuma daga bisani sultana din ta nufo bibi cikin sassarfa tana kiran sunanta da rawar murya.

Jikin bibi ta fada bibi din ta maida hannayenta ta rufeta gam

"Sultana?" Itama bibin ta dinga maimaitawa tana jin wani irin abu cikin zuciyarta,abinda ya karyar da zuciyartata kenan hawaye masu sanyi suka saukar mata.

"Bibi" itama ta sake maimaitawa kowannensu hawaye yana fita a idanunsa. Da kyau bibi ta riqeta suka qarasa saman kujera,sai kawai sultana din ta kifa kanta saman kafadarta tana sakin sabon kukan.

Ya zata iya kwatantawa bibi abubuwan data fuskanta?,baki bazai iya bayyanawa ba, gwagwarmayar data ratsa har ta kawo yau din ita kadai tasan abinda taji,ba mahalukin da zai iya fuskantarta,wannan din wani abune da yake tsakanin zuciya ruhi da kuma gangar jiki ne kawai.

Kasa cewa komai da ita bibi tayi,sai sharar hawayen itama da takeyi aba yana tsaye a kansu yana basu baki,saidai fiye da rabin hankalinsa shima yana tsakanin falon da kuma qofofin da falon ke dauke dashi,yana son ganin ta inda ama zata bullo.

Dukkaninsu taga shigowarsu ta cctv camera din dake hade da system din gefan gadonta,amma bata motsa ba,sai data kammala shirya yaran tsaf bayan ta musu wanka,ta nadesu cikin overall set da wasu irin huluna masu kyau da suka boye tattausan sumarsu me azabar baqi da sulbi,fuskokinsu sun fita tarwai da wani irin haiba da annuri.

Nannadesu tayi cikin tausasan shawl sannna ta sanyasu a kafadarta hagu da dama,ta zura slippers dinta ta taka zuwa hanyar fita.

Duk da cewa takunta baya bada wani sauti amma sai fitowarta din taja hankalin bibi da aba tamkar wadanda aka jonawa mayen qarfe. Kasa miqewa bibi tayi,daga ita har aba bin ama sukayi da kallo har zuwa sanda ta qaraso ainihin cikin falon da sallama a bakinta.

Wuce aba tayi kaman ma bata ganshi ba,ta isa gaban bibi a nutse ta sauke yaran daga kafadarta tana kwantar dasu a gaban ama tana jeresu daya kusa da dayar,sannan ta miqa hannunta tana yaye shawls din da suka lullube fuskokinsu.

Dukkaninsu suka kai idanunsu kan yaran,tamkar an jona musu shock haka sukaji cikin jikinsu

"Subhanallahi wabi hamdihi, subhanallahil azeem" bakin aba ya furta yana tasowa da gaggawa daga tsaiwar da yayi daga jikin bango.

Gaban yaran ya qaraso ya zube,yasa hannu ya tallafawa bibi da hannuwanta ke rawa tana son karbar yaran,ya dauki benazeer ya dora mata ita saman cinyarta.

"Ya Allahu,ya assamadu" shine abinda take maimaitawa tana juya yaran qwalla na sauko mata

"Astagfirullah, astagfirullah....." Ta sake maimaitawa tana jin qirjinta na mata nauyi,har cikin jini da zuciyarta takejin wani irin nauyin ubangiji,har ruhinta takejin wata irin kunya tana saukar mata,yanzu wadannan halittun da taso a murqushe?, yanzu wadannan ruhin taso a niqeshi yabi rariya?.

"Allah na tuba,Allah ka yafemin,Allah kada ka barmu da soye soyen zukatanmu" ta dinga maimaitawa hawayenta yana qara yawa

Hannu ta miqa tana shafa fuskokin yaran,idanuwanta a kansu tana sake tsarkake girman zatin Allah.

"Ga jikokinku nan,kuma 'ya'yan jikoki,wadanda kukaso gushewar rayuwarsu kafin isowarsu duniya,nayi dukkan abinda nakega ya dace nayi,ga sultana nan na dawo muku da ita,yaran kuma zan riqesu,Allah ya rayaminsu" ama ta fadi hawaye yana cika idanunta taf ta sanya tafin hannunta tana sharewa

"Inaaa hamdiyya,kece kika cancanci mu bawa haquri,kece kika cancanci wannan yabon,abinda ya kamata tunaninmu yakai kai ya gaza kaiwa kece naki tunanin yakai,kika fiddamu daga halaka zuwa hanyar tsira,inda ace na aikata abinda son zuciyata ya gayamin a sannan tabbas da zuwa yanzu ina cikin fushin Allah,ku yafemin 'ya'yannan da naso kasheku tun baku shaqi iskar duniya ba" bibi ta fadi tana sake kuka.

Iya yadda bibi ta rame kadai ya isa ya gayama ama ba qaramin tashin hankali take ciki akan tafiyarsu ba. Cikin zuciyarta wani abu ya darsu me kama da tausayin bibi cikin ranta

"Zo nan hamdiyya,yaki" Bibi ta furta tana miqawa ama hannu. A nutse ta qarasa gaban bibin,ta tsugunna,har a yanzun tana jinta a matsayin suruka,kuma har yanzu babu abinda ya sauya. Ta sani dukkan wata zuciya cike take da son rai,saidai idan Allah ya baka ikon fin qarfin zuciyar taka.

"Allah yayi miki albarka,kiyi afuwa a gareni" bibi ta fadi tana dafa hannuwan ama. Qas tayi da kanta tana jin nauyin bibi din

"Ya wuce bibi,ya wuce har abada"

"Na gode hamdiyya" ta sake fadi tana sake duban fuskar yaran daya bayan daya,tare da tunanin da waye sukayi kama

"Wanne suna kika basu?" Bibi tayi tambayar sanda ama ke tashi ta zauna sosai saman kujera kamar yadda bibi ta buqata a tare da ita

"Nadeeya BENAZEER da Fatima BATOUL" a nutse aba ya daga kai ya dubeta karo na biyu yana jin kimarta na daduwa cikin ransa,yayi tsammanin zatayi zuciya ne,ta saka sunanta da kuma sunan duk wanda taga dama,sai gashi ta watsa komai a baya,ta sanya musu sunayen mutanen da suka kasance tsani na samuwarsu.

A hankali aba yakai bakinsa kunnen kowaccensu yayi mata addu'a,ya sauke batoul a nutse saman cinyar ama sanda ta fara mutsu mutsu yana miqewa idanunsa suna satar kallon ama. Ya sani akwai zantuka da yawa wadanda a yanzun ba zasu fadu ba,ba kuma zasu yiwu a tattauna ba,zai jira lokacin da ya dace.

Ta sani abinci suke da buqata a yanzun,don tunda suka taho daga Egypt bacci sukeyi abinsu basu buqaci madara ba,sai ama ta juya tana kallon tanja data rabe tana jin nauyi nauyin ama

"A sama musu ruwan zafi zan hada musu madara" dubanta bibi tayi

"Madara kaman yaya hamdiyya?,ko zasusha madara nono ai ya kamata a fara basu ko tukunna,idan basu qoshi ba saisu qara da madarar"

Ama bata dubi bibi ba tace

"Madarar sukesha,itace abincinsu" ta maidawa bibi amsa tana gyarawa benazeer kwanciya.

"Ina nonon uwarsu?" Maganar ta zowa sultana a bazata saboda ta tsammaci bibi zata bar maganar ne,sai gashi kuma ya jefo da wata tambayar.

Waiwayawa bibin tayi tana duban sultana,a hankali sultana din ta jawo gaban mayafin jikinta tana sake suturce qirjinta da bibi ke kalla

"Hamdiyya kada dai kicemin hanasu nono tayi" bibin ta fada da wani irin zafi a muryarta abun yana tabata. Kai ama ta girgiza

"A'ah,kawai dai bata taba gwadawa bane"

"To yau kuwa zata gwada yau dinnan" bibi ta furta da gaske tana zunkudawa gaba.

Dukka idanunta sultana ta fidda waje tana zarosu,nonon nata za'a zuqa kuma?,tashin hankali.

"Aje a nemo min wannan maganin duk inda yake a garin abuja,a fiddo da dukka bournvita din dake gidan nan da madara,daga yau zuwa safiya nakeso ruwan nono yazo yara su kama abinsu" sosai sultana ta sake gwalalo ido gabanta yana faduwa

"Da kin bari bibi,tunda sun riga sun saba da wannan ai..... Bakiga kuma yadda ya karbesu ba?" Ama fada tana tana fuskar bintou

"Kinga hamdiyya ki daina bata bakinki,darajar nonon uwa daban da madarar bature,kinsan Allah?, billahillazi daga yau su da madara saidai a matsayin ciko" kuka sultana ta saki tsoro yana kamata,yanzun ace nononta zasu tsotsa?, fisabilillahi har mutum biyu?,ta ina?.

"Don Allah bibi kiyi haquri"

"Yo ai bansan baki da imani ba,haba sultana,kece za'a ce kiyi haquri dai,don nono kaman sun shashi sun gama" idanu sultanan ta wuwwulga a falon,ba wani sauran me cetonta,aba ne ya rage dama,shi kuma tunda aka fara batun shayarwar ya fice.

Duk irin kukan da sultana keyi saboda tsananin tsoron shayarwar bai damu bibi ba,nan ta gwaggwafe hada wannan tsuma wancan,zuwa safiya sai ga nono yazo.

Bibi da kanta ta taka ta amso benazeer da batoul daga wajen ama,wadda tuni tayi musu wanka ta shiryasu tsaf sunata tashin qamshi sai tsotsar baki suke,da alama dama a yunwace suke. Qin bin bibi ama tayi kada tausayin sultana ya mata tasiri ta hana abinda ita kanta tasan shine dai dai,abinda ya sanya bata taba tilastata ta basu din ba alqawarin hakan ta yiwa kanta,kuma bata fatan hakan ya haifar mata da wani raunin cikin zuciya,ko taga kaman aman tana biyewa soye soyen zuciyarta ne tunda ita din bataso,biyayya kawai takeyi.*_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

Book 02 page 28


Idanunta fal ruwan hawaye take kallon bibi sanda ta fara aza mata benazeer akan cinya

"Don Allah bibi,wallahi zafi zanji na sani,bazan iya basu ba"

"Zaki koya ne,kowa ma ai da haka yake koya" bibin ta fadi tana hade rai babu alamun wasa saman fuskarta

"Yalla, fito dashi ki basu ko nazo da kaina na basu,an baki shine don kiyi ado dashi a qirjinki dama?,fito dashi" bibin ta fada cikin fada da tsawa. Hannu ta saka tanason cirosu,amma rashin sabo ma ya sanya ta kasa yadda zata fiddosu din

"Bari dai kiga" bibi tace tana motsawa kusa da ita. Kuka ta saki sanda benazeer ta cafki maman ta fara tsotso kaman dama ta saba. Idanun yarinyar qur kan fuskar sultana kaman tasan ba da son ranta take bata maman ba. Tasha kuwa sosai,bibi ta dauketa ta saka batoul itama ta kama guda daya.

Kafin su gama hawaye shabe shabe akan fuskar sultana

"Yauwa to ma sha Allah" bibi ta furta tana daga yaran. Sai yanzu zuciyarta ta samu nutsuwa,ta sanya batoul a kafada tayi gyatsa sannan ta saka benazeer. A nan saman gadon sultana din ta kwantar dasu,tanayi tana qananun mitoci,abun ya qonawa sultana rai sosai,yanzun kenan ko damuwa da damuwarta bibi ta daina?,bibi da bata barinta tayi kuka yau itake kallonta tana kuka amma bata ko dubeta ba bare ta lallasheta?.

Bibi na fita ya tura qofar dakin ya shiga da sallama. Tana tsaye bakin mirror tana daura towel,tanason shiga tayi wanka tunda ta samu bibi ta dauki yaran kafin ta dawo mata dasu. Sau daya ta juyo ta kalleshi ta dauke kai tana ci gaba da abinda takeyi din. Ya taka ya matsa gabanta yana dubanta

"Hamdiyya" ya kirayeta qasa qasa

"Na'am" ta amsa masa ba tare data juyo ba,sai kuma shuru ya biyo baya

A nutse ya qaraso,ya jingina ta a jikinsa ta baya

"Har yanzu kina fushi ne?,kin daina ta tawa gaba daya sai ta jikokinki?" Bata dai waiwayo din ba ta bashi amsa

"Fushin me zanyi?, bayan nina muku laifi?,amma aina wanke kaina ko?,tunda ga diyarku nan na dawo muku da ita ban gutsireta ba"

"Ya isa" ya fada cikin son katse zancan,don gaba daya bayason ana maimaita maganar. Hannunta ya kama ya zaunar da ita sannan ya zauna a gabanta

"Haqiqa kinyi abu me kyau,kinyi abinda kika cancanci a yaba miki da kika tseratar da Bibi daga rudani da kuma fadama nadama,na gode miki qwarai,kuma ina fata zaki yafemin bisa duka kusakurai na" ta tsammaci zaya sako zancan maina amma sai taji bai sako din ba,ya zuwa sannan zuciyarta ta qeqashe da takejin bata buqatar taimakon kowa sai nata ita d'ai,don haka itama bata tada masa zancan komai ba.

Cikin kwanakin gaba daya tare da Bibi ake rainon yaran,sam sam ta hana a basu madara sai nono. Sultanan tayi kuka tayi kuka har idanunta ya dinga motsawa me ciwon amma hakan baisa bibi ta janye ba,duk sanda za'a basu nonon bibi ke tsaiwa a kanta saita tabbatar sun sha sun qoshi. Gaba daya jin abun take banbarakwai,abubuwan da take boyansu,abubuwan da take adonsu yau sun zama abebaden shan wadansu.

Amma kuma abun mamakin da yaran sun kama sun fara sha sai taji zafin da takeji cikin zuciyarta yana sauka a hankali. Wadansu irin yara ne,masu tarin wayo da wani irin farinjini da kwarjini da Allah ya zuba musu. Idan kana kallon fuskarsu ba zakaso ka daina ba,sun iya kallon mutum kamar sun sanshi ,bibi takance

"Wannan wayon da abinku aka haifeku,so kuke ma kufi uwarku wayo".

Kwanansu uku kacal da dawowa saiga tawagar family din MAYAK'I sun iso. Kusan kaf kowa na gidan ba wanda aka bari acan. Duk wanda ya daga yaran sai yayi kamar bazai ajjiye ba. Sultana na daki kwance jikinta a mugun mace,ta kasa zama cikinsu,ta kuma kasa hada idanu da kowa,jinta take kamar bare a cikinsu,a dakin su aminata suka cimmata suna santin yaran

"Wallahi kaman ba kece mamarsu ba sultana,don Allah ki barmuna su kawai" kanta ta juyar wani sashen tana cewa

"Ku daukesu kawai na baku" dariya sosai yasmine ta saki

"Wallahi qarya kike,wai ke irin bakiso dinnan,wa zai samu yarannan yace baiso?,ko ke bakiso na tabbatar yaa maina yana son kayanshi" a wani irin fusace ta juyo da fuskar nata data kawar dazu tana kallon yasmine. Ambatar sunansa kawai dai dai yake da kira mata uwa uba da duk wani da take gani da kima a mazaunin mahaifi ka zageshi. Tashi tayi ta zauna sosai daga kwanciyar da tayi dazun tana duban yasmine

"Kada ki sake ki qara kiramin sunanshi a nan wajen yasmine,don ba wajen kiran sunansa bane nan din" tayi maganar kanta tsaye,idanunta na bayyana abinda ke danqare kai tsaye a zuciyarta. Sanyi jikin yasmine da aminata yayi,suka kalli juna,sai yasmine din ta koma ta zauna daga gefanta

"Kiyi haquri,mantawa nayi,amma sultana.....baki tunanin a tsahon wannan lokacin ma a ina yake?,kina da tabbacin kawo yanzu yana raye ko ya mutu?,kinsan yaa maina....."

"Yasmine ya isa da Allah....." Sultana ta fadi tana sanya yatsunta cikin kunnuwanta,da gaske take,batason jin komai da ya danganceshi,bata qaunar ambatar sunansa a gabanta.

Ama ce ta bude qofar dai dai maganar yasmine na qarshe data kirayi sunan maina. Taji komai ta kuma ga komai,sai ta saki qofar ta tako a hankali tana shigowa ciki

"Yasmine,kuje kuci abinci an kammala" miqewa sukayi dukansu,daya bayan daya suka fice a dakin,sai a sannan ama ta dawo da kallonta ga sultana.

Takawa tayi a hankali,ta sanya sannu ta zare hannuwan sultanar daga kunnenta. A nutse ta soma warware idanun nata ta saukesu a fuskar ama. Taga gaskiya muraran saman fuskar sultanar na iya girman tsanar data yiwa mainan,ta kuma tabbatar da gasken gaske take,don daga fuskarta har cikin idanunta sun canza launi zuwa ja.

Murmushi ama ta sake mata tana hadiye wani dunqulallen abu da ya tsaya mata a wuya. Habar sultanar ta dan riqe

"Karki sake damuwa,ba wanda zaya sake miki maganarsa,an rufe babinsa kinji?,tashi kiyi joining 'yanuwanki kici abinci kema,ki sake a cikinsu,mutum kike kamar kowa,idan kina ganin abinda ya farun kamar ya rage daraja ko martabarki sam sam ba haka bane,a yanzunne ma kima da darajarki ta dagu,saboda kowa na miki kallon me hankali ne a yanzun,kina da abinda kaf 'ya'yan jikoki babu me shi sai ke,tashi kije". Da irin wadannan kalaman ama ta samu ta dinga rage mata kaifin abinda takeji cikin zuciyarta,ta dan sake dasu aminata tamkar suna gida tsahon kwanaki ukun da sukayi.


*********Misalin bakwai da rabi na safiyar ranar lahadin,cikin gidan ama dake garin abuja,babban gid daya ginu ainun da wani irin tsari da kai tsaye idan ka kirashi da MANSION HOUSE bakayi kuskure ba.

Cikin faffadan dakin da ya zama masaukinsu najma aminata da yasmine,dukkansu a zaune suke kaman ba safiya ba,saboda shirin komawa nijer da sukeyi a yau din. Najma tayi wanka,aminata na zaune tana jiran yasmine ta fito ta shiga,sultana dake zaune saman sofa gab da aminata,sanye da wata rigar bacci me taushi me gajeran hannu da iyakar tsahonta gwiwa tana kallonsu kawai. Jifa jifa aminata na sanyata a hirartasu,gaba daya amsarta bata wuce daya zuwa biyu idan tayi nisa uku.

Sake kallonta aminata tayi,can qasan ranta tana mamakin sauyawar sultanar,a duniya duka idan akace mata wani lokaci zaizo da sultana zata zama miskila to tabbas zata musanta,musu kuma me tsanani,sai gashi dare daya sultanar ta tashi daga ainihin sultana ta zama wani abu daban. Sultana da a baya ko fada kakeyi da ita ta sanyaka kuka badai kai ka sakata kuka ba..... sultana da a baya idan ta fannin magana ne saidai ta cinyeka badai kai ka cinyeta ba.......saidai ka haqura kayi shuru ka barta......... saidai ka gaji kayi shuru badai ita ta gajiya ba.......yau sultana ce magana ke mata wuya,murmushi ya zama wani kayan gabas a wajenta

"Don Allah sultee......ki canza please,wannan sabon halin naki nikam baiyimin ba,kuma bayamin dadi" aminata ta fada tana bata fuska. Fararen idanunta kawai ta daga ta kalli aminata din sai ta maidasu ta lumshe. Aminatan ba zata taba ganewa ba,ba zata taba fahimtar what she goes through ba......a yanzun a cikin ruhinta itama jinta takeyi kaman ba sultana ba.

Kafin tace komai bibi ta shigo dakin,rungume take da wasu sabbin atamfofi wanda duk zuwa Nigeria sai an sayesu an tafi dasu,ayita ajiyarsu saboda tashin wata hidima ko kuma dinkin yaran gidan. Kusan al'ada ce da maina ya kafa saboda yadda ya tsani yawan ta'ammali da English wears da su sukeyi wanda ba komai bane kusan al'adarsu.

Ama ke biye da ita dauke da wasu kayan masu yawa itama data ware zata rabawa su najma,kayayyaki ne da tasan suna qanfarsu a can. Turus bibi tayi tana dan duban sultana

"Ya na ganki zaune kowa yana shiryawa?,bakisan tare zamu koma ba?,tunda shi hamidou komawarsu ba yanzun ba?" Idanu ta daga ta kalli bibi,sai kuma ta maida dubanta ga ama kafin ta janye duban nata idanun nata na cika da hawaye duk da basukai ga zubowa ba. Sam batajin zata iya komawa cikin qasar nijer taci gaba da rayuwa,a yanzun bata sha'awar hakan sam sam sam. Da wanne ido zata kalli jama'ar data sani a baya?,da wanne ido zata kalli mutane?,tace musu me?,batajin tana da rufin asirin da ya wuce mata rayuwa yanzu cikin Nigeria

"Zan zauna a nan ne,bazan biku ba" qarasawa bibi tayi ta zube kayan hannunta baki bude tana duban sultana

"Kamar yaya?,saboda me?" Hannu ta sanya ta dauke siririyar qwallar data ziraro mata

"Nafiso nan, nafison na zauna a nan kawai,ki barni a nan don Allah bibi" ta qarashe fadi muryarta tana rawa.

Baki buden bibi ta waiwaya tana duban ama,sai aman ta dagawa bibi hannu sannan ta tako kusa dasu

"Tunda hakan takeso kiyi haquri bibi ki barta a nan din,in sha Allah zanci gaba da kula da ita,zan kuma riqe amanarki,duk lokacin da taji zata iya komawa can din,zan shiryata na maida miki ita har gida in sha Allah" zama bibi tayi tana duban ama

"Yo na tafi a cuci wadannan bayin Allahn?,kina gani da idona ma ba wani nonon arziqi suke samu ba?" Da sauri ta dago kai tana duban bibi. Kaji wani sharri irin na bibi(sultana ta fadi a ranta),tun bayan abunma ba'a taba takurawa rayuwarta ba yadda bibin ke takura mata. Cikin dare zataje ta debo yaran,ta tasheta a bacci,haka zasu kwana jikinta,wani lokacin haka zata kwana tashinta wai ta basu nono,wani lokacin idan abun ya isheta saidai kawai ta sake mata kuka,ta maidata kamar wata saniya,amma yanzun cewa take ba nonon arziqi suke samu ba?.

Murmushi ama ta saki me sanyi,makauniyar qaunar da taga bibi na yiwa yaran mamaki take bata,yadda yaran suke da saurin shiga zukatan mutane ta sani wani abune kawai daga Allah

"Duk hakan ba zata faru ba in sha Allah,na miki alqawarin zan kula"

"Idan naga sabanin haka,ko nazo naga yaran nan sun zube fa ba zanwa kowa ta dadi ba" bibin ta fadi cikin salon mita

"Ba za'a yi hakan ba in sha Allah" ama ta sake tabbatarwa bibi.



Please Login or Register in order to submit comment